kasance yarinya mai ladabi da biyayya ga wa yanda kika sama a gidan.
Idan kinyi min haka kinyiwa kanki da nima adalcin rayuwa.
Don bazan taba jin dadi ba a rayuwa idan har wani rashin mutunci ya fito daga gare ki a zaman ki na gidan nan.
Idan kinyi haka kin min komai a rayuwana wanda hakan zai sakiji dadin zama dani bama ni kadai ba har ma kowa da zaki sama a gidan.
Nace insha Allahu zaka samay ni kamar yadda kake tsanmani a rayuwana yace to Allah yai maki albarka ya tashi kata kata ya mike tare da nufar gadon da yasha shimfida yana cewa ki dai yi hakkuri da yanayi har na dan wani lokaci amarya.
Daga haka naji yana bissimillah yabi lafiyayen gadon ya kwanta tare da mimikewa a sama yana sauke ajiyan zuciya.
Can yake cewa idan kin gama zaki kwanta sai ki rufo muna kofan dakin daga ciki kinji.
Nayi maza nace mashi tau ba, a dauki lokaci ba ina daga inda nake zaune naji ya fara nasari alaman barci ya dauke shi ke nan.
A hankali na mike na nufi kofan na rufo kamae yadda ya umurce ni da nayi idan zan kwanta.
Na koma kasa na kwanta ban dade ba sai barci dama jikina da gajiyan jigilar dana sha na jama, a atare dani.
Bani na falka ba sai asuba ana kiraye kirayen sallah naji motsin shi haka yasa na falka tare da mikewa zaune zubur yace a kasa kika kwanta Amarya ?
Ya dauki buta zuwa bandakin da akai min a kusa da dakina basai na shiga na taron gidan ba sai bayan ya fito ne na shiga nai tsarki na dauro alwala na shiga dakin.
Bayan nayi sallah ban kwanta ba tunda na saba a gida bana kwanci sai aikin gida idan na tashi na gyara gadon daya kwanta tare da sharo dakin har zuwa kofana inda aka kewaye min shi nagyara ko ina tsab.
Na fita zuwa tsakar gidan duk girman shi sai dana share shi kafin gari ya karasa waye,
Na hada kayan wanke wanken da na gani birjit ko ina na gidan na fara wankewa .
Sai lokacin matan gidan da yaran su ke fitowa daga barci duk wace ta ganni sai ta tsaya tana mamaki hakan .
Ina gaishe su daya bayan daya suna shigewa dakunan su da yaran su.
Ina gamawa na juya zuwa dakina na debi ruwa na shiga na watsa na saka wani lace mai laushi dashi cikin kayan da anty ta aiko min dashi.
Duk da ban san kudin shi ba nasan mai tsadane kwarai ga dinkin yai matukar karban jikina kamar an auna ni kafin a dinka min shi.
Can na fara jin hayaniyan matan gidan suna fitowa tsakar gida daya bayan daya haka yasa na gane cewa sun tashi ke nan na yafa gyale a kaina na fito na fara zuwa sashen mama tana kokarin fitowa daga dakin ta tana ganina tai murmushi take cewa a,a amarya baki huta ba gaki da gajiya kika fito kikai wanan aikin haka?
Hutun may zatayi bayan dama an saba da komai tun a waje muryan sabuwa ce dake bayan mu hannun ta rike da wani karamin roba kore.
Na durkusa na gaida mama da ina kwana mama tace lafiya kalau Rahama yaya dare yaya angon naki ?
Sabuwa ta kara cewa dare kan ai kinga inda alaman shi ya nuna ba a wahala ba don ansan komai.
Haba sabuwa wai may yake kawo wanan magana hakan ga wanan karamar yarinyar kuma ?
Wanan ai ba sa, an yin ki bace may ta sani akan zancen ki dakikeyi yanzu sai muryan maigidan mukaji daga bayan mu lokacin ina durkushe a gaban mama yana cewa.
Sabuwa ki kiyaye ni wallahi a gidan nan don zan iya saba maki akan yarinyar nan a gidan nan fiye da tsanmanin ki.
Idan ba hauka ba irin naki yanzu wanan yarinyar zaki titsiye a gaban ki kina fada mata wanan magana haka ?
Ina yatinyar take tashige daki ta kwana da kai ta fito kemaymay da ita har kake kiranta yarinya.
Yarinya kan na bayan uwar ta ai wace bata san shigewa daki da namiji ta kwana ba kuma ta tashi lafiya tarmazazai haka ?.
Ganin dayar matar tana cewa kai haba tunda wanan farar safiyan haka za, a tusa muna wani fitina a gida.
Na mike daga gurin mama na nufe tare da durkusawa har kasa nace ina kwana mama ?
Tace a,a amarya ni ba mamakin bace zaki iya kira na da yaya ko maman Aisha.
Nai murmushi na kara gaishe ta ta amsa fuskan ta ba yabo ba fallasa cikin sa dacewa yaya daren Amarya ya angon naki koda yake gashi nagan shi ya samu lafiya ai a gaban mu.
Inda sabuwan take na nufa itama na gaida ita a cikin ladabi sai cewa tayi ke tashi da kili bibin ki idan ban kwana ba zaki ganni ne nan ?
Yace uhumm kaji ba ke abinda baki taba yiwa yan uwan ki an maki kuma kina jin haushi yanzu .
Ni dai ina ganin sun rikice na juya zuwa dakina ban tsaya sauraren su ba.
Sai zuwa can naji ya shigo dakin shima dai gaida shi nayi tare da mai yaya jikin yace jiki da sauki sosai.
Zuwa can naji anyi sallama ya amsa wata budurwa ce daga cikin diyan shi dauke da kwanon kunu da kosai taje cewa baba ga abin karyawa inji mama akawo maku.
Yace kice ana gaida ita da aiki ko inda nake bata kalla ba tafita daga dakin har takai kofa naji ya kirata yace suwaiba kun gaisa ne da sabuwar umman taki ?
Tace baba ai ban gan ta bane tabashi amsa murmushi tayi tace ina kwana .
Nace mun tashi lafiya yaya gida bata tsaya ba tabar dakin yace taso ki dibi kunun da kosan mai isar ki kisha.
Nace sai zuwa anjima bani karyawa da safe haka ai yace to injin ku yan boko ne ?.
Da naji alaman suna aiki na fito na samu ashe kowa ce ta fito tana aikin sana, anta da takeyi a gidan .
Na kama wa mama dama kokon da takeyi za, a fita mata dashi nan da nan muka gama.
Sai mai bi mata dake dafa shinkafa da wake itama na karbi wanke shinkafan na wanke mata tas na zuba tare da gyara wutan da icce ya jaye na hura wutan sai gashi ya kama.
Ban koma daki ba sai dana kwashe mata shi a kwano na gyara yadda za, a fice dashi na koma daki na.
Na samu maigidan ya shirya zai fita yace ina kika shige ne Amarya nace ina gurin da ake aiki ne.
Yace to ni zan fita sai na dawo zan dan leka waje nagani ko akwai abinda zan iya yi a can na neman kudi.
Kin san angon naki dan bida ne ba mai zaman gida bane ni.
Na durkusa nace Allah yasa a dace Allah yaba da nasara a dawo lafiya baba.
Yace kai ni fa wanan baban ba son jin shi nake a bakinki ba da dai za, a canza min suna ko Alhajina akirani dayafi min alheri.
Nace to Alhaji Allah yaba da sa, a yasa a fita a nasara yace amin yar amarya ta yaushe rabon da naji anmin fatan alheri haka a rayuna.
Nan yasa kai yafice ni gyara dakin na dan zauna sai barci ya kwashe ni afurin mai nauyi ban sani ba.
Muryan yan gidan mu ne da suka shigo ganin kwanana ya tayar dani daga barci.
Na mike zubur ina masu sannu da zuwa idanuwan su fes a kaina suna kallona ban san may suke son fahinta ba daga gare ni.
Na gaidasu daya bayan daya tare da tambayan sauran mutanen gida.
Da yake iya yan uwan inna ne sai kadan daga dangin babana sai cewa sukayi kowa lafiya sai maman ku ne dai da ta saka muna hauka wai sai baban ku ya fada mata inda ya samo kudin da yai maki hidima haka na fita kunya.
Duk rantsuwan da yai mata ba yarda dashi ba wai idan bashi ya yi ba mijinkine yaba da kudin aka boye mata.
Nace cikin murmushi tare da zama kan makarin kujera na kai mama ho yaushe zata bar wanan halin nata ne na hassada da bakin ciki.
Ita da tace da tabar za, a kawo ni yanzu da taga sabanin haka shine kuma ta tayar da hankalinta.
Rabu da mahaukaci wacce bata son azauna lafiya iji kauna babana ta fadi hakan.
To yaya kuka kwashe da matan gidan naku yau da safe da fatan babu wani matsala dai ko daga gurin su.
Nai dan murmushi nace babu komai mama batare da na fada masu abinda ya faruba da safe akaina a gidan.
Sai dayan mama tawa tace ai ina ganin indan dai ta iya binsu zata samu sauki ga biyun mata wanan dai da take biwa ce matsala nake gani sai yaran su kuma don naga yaran a tsaye suke suma.
Nan dai sukaci ga ba da yi min nasihohi na in zauna da zuciya daya dakowa na basu girman su tunda duk sun haifeni baki dayan su.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE , ,
IDAN KIN BIYA KIKA TURAWA WANDA BAI BIYA BA KINCI AMANAN ALKAWARI DON ALLAH ZAI TAMBAYE KI HAKKINA NAYI HAKA A KAN KI DON SAI DA NA ROKE KI KADA KI FITAR MIN DA NOVEL DINA DON ONLINE NOVEL NE BA NA SHAGO BANE WANNAN DA FATAN ZAMU JI TSORON GAMUWAR MU DA UBANGIJIN MU ALLAH RANAN GOBE KIYAMA AMANA YAR UWA IDAN BAKI IYA RIKE AMANA KIYI MAGANA NA BAKI KUDIN KI DON BA ZAN YAFEWA HAKAN BA
MUJI TSORON ALLAH KADA MU BARI SHEDAN YA RUDI ZUKATAN MU PLEASE, , , ,
7
Haka rayuwan zaman sabon gurina ya kasance min agidan mijina kuma babana uwayen gidana da sukai jika dani.
Manyan diyan shi maza ko matan su sun kusa haihuwa na don haka mazan nake kiran su da yaya matan su da anty.
Haka ya jawo min saukin zama gidan don sun kula ban zo masu da fitsara ba ko kadan.
Bani kuma kyashin taya mutum aiki koda na sana, an shi tare dani za, ayi shi har a gama kuma da zuciya daya.
Wanan dalilin nee yajawo min sasauci sosai a gaare su gashi zan sha aiki idan an bani naci bana ci don ban saba da irin ciye ciye haka ba barkatai.
Wankin kayan Alhaji daya cire kafin ya tashi na kwasa na wanke sai dai ya sake wasu wanka
kuma ya zama kullun sabanin da da sau daya ko sau biyu zaiyi wanka a sati.
Ga maclean da brushe da yakeyi akai akai yanzu yake wanke baki dashi wanda na kula shi kan shi alhajin zuwa yanzu yana jin dadin sauyin rayuwan da ya samu.
Don ko wa yagan shi cikin sati dayan da nayi a gidan yasan ya samu sauyi sosai a rayuwan shi.
Don nakan ji matan shi suna mashi ba, a wai auren yarinya yasa shi ya sauya ga abinda basu san shi dashi ba a baya.
Sai ya basu amsa da nata sallon ke nan ke ai baki min ba a lokacin ki dana sauya din tun can.
Ranan da na cika sati daya ne agidan har lokacin ba wani abinda ya taba shiga tsakani da shi ban maga alaman hakan ba daga gare shi.
Ina kasa ya na saman gado kwance da ya kwanta kuma sai barci mai nauyi ya dauke shi sai safe.
Amma a gurin mutane suna ganin akwai abinda ke shiga tsakani na dashi a cikin dare don nakan ji sabuwa na cewa dashi ya daiyi a hankali kada ya takura karfin shi kan karaman yarinya yaje yajawa kan shi matsala kuma ?
Dariya yakan yi mata yace ai yafi son haka don lokacin ta ne abar ta tayi nata zamanin.
Sauran matan ba ruwan su da sha, ani na sai girmamawa amma sabuwa kan kullun sai tayi kokarin sake min magana a tsakar gida wanda zai bata min rai.
A banza don wani zancen ma ban san wai dani takeyi ba har ta kare haukan ta.
Idan ina zaune wani sain nakan ce ashe haka shine aure ba takura ba matsi ba tsangwama irin na mama a gidan mu ?
Gashi duk Alhaji zai shigo sai ya dan sayo min dan abin tabawa watarana ma har kayan shayi da biscuit da su sweet zai bayar akawo min .
Haka yasa na sake jikina sosai dasu wani sain har yar hira mukan yi dashi kafin yai barci sai dai hiran tamu nakan ga yana dariya sosai idan ina shirmay na.
Ranan ya dawo daga kasuwa ya tara mu a dakin mama Hausi uwar gidan shi kusan nice ta karshen shigowa dakin inda suke zaune.
Ina shigowa na samu guri na durkusa tare da gaida su gaba dayan su suka amsa min ina nan dai durkushe sai cewa mama tayi.
A, a Amarya samu guri mana ki zauna ai ina ganin magana Alhaji zaiyi da mu.
Nace mama har dani ?
Tace kai amarya ke ba matar shi bane yanzu har da ke mana.
Shi dai murmushi yayi kawai yana sauraren mu can bayan mama Hausi na koma na takure kamar uwata.
Can dai yai gyaran murya alaman zai fara magana ke nan a lokacin don haka naga kowan su ta natsu.
Yace to Alhamdullahi yau dai amarya ta gama satin ta daya kamar yadda sharia ya tana da.
Don haka yau ne zan koma dakin wace keda girki a cikin ku don haka ina rokon alfarma gurin ku.
Wanan yarinyar da Allah ya kaddari zaman ta a cikin mu da kuji tsoron Allah ku rike ta amana kamar yar cikin ku.
Yar cikin mu kuma Alhaji kishiya ce zan rike kamar yar cikina ta kwana da kai in kwana da kai kuma in rike ta kamar ya ta ?
Wanan maganan baiyi ba gaskiya ka dai sake wani maganan inji sabuwa dake magana a hasale a lokacin.
Murmushi yayi yace sabuwa ke nan ba laifi yadda kika dauke ta a tafi a haka sai dai saukin abin Allah yasa bake kadai nake aure ba.
Kuma bake ce uwar gidan gidan nan ba kinga ashe ba wani matsala ga hakan.
Ita Rahama har wani kishi ta sani a yanzu bayan daukan ku uwayen ta da takeyi tana maku bauta may kuma kike so a gare ta.
Eh yanzu kan hakane a/a idan ta goge ai babu shegu nan gaba kamar mu, balle yadda naga kana rawan kafa haka a kan ta wai kai ka samu yar jikan ka ka saka a daki kana abinda bai dace ba da ita.
Haba sabuwa wai may yasa baki da hakkuri ne ke inji mama Kulu matar shi ta biyu.
Yai murmushi tare da cewa ai ba rashin hakkuri bane gani takeyi abinda tazo gidan a lokacin tana maku rashin kunya shine itama yar mutane tazo dashi zatai maku.
Sai dai ki sani alama ya nuna tarbiya ba daya ba wallahi don ke ko kwana ba, ayi ba kika fara sakani ga fitina.
Amma yanzu ki duba karamar yarinya tasan daraja na tasan naku hakama na iyalina baki daya.
Au to kana nufin ta fini ke nan yanzu maji magana ai gara da ka fito fili ka fada min kowa yaji.
To bari kaji Alhaji wallahi duk ranan da yarinyar nan tai gigin shiga harka na sai dai uwarta ta haifi wata don ko ban halaka ta ba zaka dawo ka samu ankaita jiya gidan su.
Yace ke ko da kin kwana a gadirom rana wallahi da karshen zaman ki gidan nan yazo sabuwa da kinyi nadama mara adadi a rayuwan ki.
Yace naga abin naki ba wasa bane yanzu wallahi duk ranan da kikai gigin taba lafiyan yar mutane sai na lahira yafiki jin dadi a garin nan.
Lalai ma ba, ayi ba yanzu aka soma ke nan don kayi dandane haukace ka zauce kamar wanda bai taba jin dadin bujen mata ba ko ?
Yai murmushi yace kaiyya a fili tare da girgiza kan shi yace ashe kin gane wani bujen yafi wani buje ke nan.
Ranta yai matukar baci bata karasa ba taji yace dama abinda yasa na tara ku nan shiine ke hausi ke ce babba ke zan roka alfarma don Allah.
Ina son yarinyar nan ku dauke mata nauyin girki a gidan nan don kunga karfin ta bai gama kaiwa ba don Allah a dan sahirta mata wanan aikin har ta dan kara tasawa nan gaba idan Allah ya ce.
Cabdijam ba ta iya aiki amma tana iya shigewa da kai daki tai shiru har safe ko ?
Kai sabuwa inji mama kulu tace waban bai dace ba gaskiya shi fa ke da gidan shi balle ma wanan yaushe zata iya tuka tuwon gidan nan haka ?
Ai dama nasan duk da hadin kan ku don ai min bakin ciki kuka hada baki akawo ta gidan nan idan hakane bazatayi girki ba sai dai nima na dinga yi ni da yarana kawai wallahi.
Isan kinyi hakan ma daidai ne inji Alhajin amma ki sani cikin ki tayi don su nan duk suna da sarakai da zasi girka masu ba sai sunyi ba kece mai yara kanana da yawa kuma.
Tace koma maye na dai ji muddin wanan yar mussan da ka kwaso baitai girki ba nima bazan yi ba wallahi yace har da shan wallahii tace eh na sha.
Mama hausi ta bude baki zatai magana ya dakatar da
Showing 24001 words to 27000 words out of 456145 words
Idan kinyi min haka kinyiwa kanki da nima adalcin rayuwa.
Don bazan taba jin dadi ba a rayuwa idan har wani rashin mutunci ya fito daga gare ki a zaman ki na gidan nan.
Idan kinyi haka kin min komai a rayuwana wanda hakan zai sakiji dadin zama dani bama ni kadai ba har ma kowa da zaki sama a gidan.
Nace insha Allahu zaka samay ni kamar yadda kake tsanmani a rayuwana yace to Allah yai maki albarka ya tashi kata kata ya mike tare da nufar gadon da yasha shimfida yana cewa ki dai yi hakkuri da yanayi har na dan wani lokaci amarya.
Daga haka naji yana bissimillah yabi lafiyayen gadon ya kwanta tare da mimikewa a sama yana sauke ajiyan zuciya.
Can yake cewa idan kin gama zaki kwanta sai ki rufo muna kofan dakin daga ciki kinji.
Nayi maza nace mashi tau ba, a dauki lokaci ba ina daga inda nake zaune naji ya fara nasari alaman barci ya dauke shi ke nan.
A hankali na mike na nufi kofan na rufo kamae yadda ya umurce ni da nayi idan zan kwanta.
Na koma kasa na kwanta ban dade ba sai barci dama jikina da gajiyan jigilar dana sha na jama, a atare dani.
Bani na falka ba sai asuba ana kiraye kirayen sallah naji motsin shi haka yasa na falka tare da mikewa zaune zubur yace a kasa kika kwanta Amarya ?
Ya dauki buta zuwa bandakin da akai min a kusa da dakina basai na shiga na taron gidan ba sai bayan ya fito ne na shiga nai tsarki na dauro alwala na shiga dakin.
Bayan nayi sallah ban kwanta ba tunda na saba a gida bana kwanci sai aikin gida idan na tashi na gyara gadon daya kwanta tare da sharo dakin har zuwa kofana inda aka kewaye min shi nagyara ko ina tsab.
Na fita zuwa tsakar gidan duk girman shi sai dana share shi kafin gari ya karasa waye,
Na hada kayan wanke wanken da na gani birjit ko ina na gidan na fara wankewa .
Sai lokacin matan gidan da yaran su ke fitowa daga barci duk wace ta ganni sai ta tsaya tana mamaki hakan .
Ina gaishe su daya bayan daya suna shigewa dakunan su da yaran su.
Ina gamawa na juya zuwa dakina na debi ruwa na shiga na watsa na saka wani lace mai laushi dashi cikin kayan da anty ta aiko min dashi.
Duk da ban san kudin shi ba nasan mai tsadane kwarai ga dinkin yai matukar karban jikina kamar an auna ni kafin a dinka min shi.
Can na fara jin hayaniyan matan gidan suna fitowa tsakar gida daya bayan daya haka yasa na gane cewa sun tashi ke nan na yafa gyale a kaina na fito na fara zuwa sashen mama tana kokarin fitowa daga dakin ta tana ganina tai murmushi take cewa a,a amarya baki huta ba gaki da gajiya kika fito kikai wanan aikin haka?
Hutun may zatayi bayan dama an saba da komai tun a waje muryan sabuwa ce dake bayan mu hannun ta rike da wani karamin roba kore.
Na durkusa na gaida mama da ina kwana mama tace lafiya kalau Rahama yaya dare yaya angon naki ?
Sabuwa ta kara cewa dare kan ai kinga inda alaman shi ya nuna ba a wahala ba don ansan komai.
Haba sabuwa wai may yake kawo wanan magana hakan ga wanan karamar yarinyar kuma ?
Wanan ai ba sa, an yin ki bace may ta sani akan zancen ki dakikeyi yanzu sai muryan maigidan mukaji daga bayan mu lokacin ina durkushe a gaban mama yana cewa.
Sabuwa ki kiyaye ni wallahi a gidan nan don zan iya saba maki akan yarinyar nan a gidan nan fiye da tsanmanin ki.
Idan ba hauka ba irin naki yanzu wanan yarinyar zaki titsiye a gaban ki kina fada mata wanan magana haka ?
Ina yatinyar take tashige daki ta kwana da kai ta fito kemaymay da ita har kake kiranta yarinya.
Yarinya kan na bayan uwar ta ai wace bata san shigewa daki da namiji ta kwana ba kuma ta tashi lafiya tarmazazai haka ?.
Ganin dayar matar tana cewa kai haba tunda wanan farar safiyan haka za, a tusa muna wani fitina a gida.
Na mike daga gurin mama na nufe tare da durkusawa har kasa nace ina kwana mama ?
Tace a,a amarya ni ba mamakin bace zaki iya kira na da yaya ko maman Aisha.
Nai murmushi na kara gaishe ta ta amsa fuskan ta ba yabo ba fallasa cikin sa dacewa yaya daren Amarya ya angon naki koda yake gashi nagan shi ya samu lafiya ai a gaban mu.
Inda sabuwan take na nufa itama na gaida ita a cikin ladabi sai cewa tayi ke tashi da kili bibin ki idan ban kwana ba zaki ganni ne nan ?
Yace uhumm kaji ba ke abinda baki taba yiwa yan uwan ki an maki kuma kina jin haushi yanzu .
Ni dai ina ganin sun rikice na juya zuwa dakina ban tsaya sauraren su ba.
Sai zuwa can naji ya shigo dakin shima dai gaida shi nayi tare da mai yaya jikin yace jiki da sauki sosai.
Zuwa can naji anyi sallama ya amsa wata budurwa ce daga cikin diyan shi dauke da kwanon kunu da kosai taje cewa baba ga abin karyawa inji mama akawo maku.
Yace kice ana gaida ita da aiki ko inda nake bata kalla ba tafita daga dakin har takai kofa naji ya kirata yace suwaiba kun gaisa ne da sabuwar umman taki ?
Tace baba ai ban gan ta bane tabashi amsa murmushi tayi tace ina kwana .
Nace mun tashi lafiya yaya gida bata tsaya ba tabar dakin yace taso ki dibi kunun da kosan mai isar ki kisha.
Nace sai zuwa anjima bani karyawa da safe haka ai yace to injin ku yan boko ne ?.
Da naji alaman suna aiki na fito na samu ashe kowa ce ta fito tana aikin sana, anta da takeyi a gidan .
Na kama wa mama dama kokon da takeyi za, a fita mata dashi nan da nan muka gama.
Sai mai bi mata dake dafa shinkafa da wake itama na karbi wanke shinkafan na wanke mata tas na zuba tare da gyara wutan da icce ya jaye na hura wutan sai gashi ya kama.
Ban koma daki ba sai dana kwashe mata shi a kwano na gyara yadda za, a fice dashi na koma daki na.
Na samu maigidan ya shirya zai fita yace ina kika shige ne Amarya nace ina gurin da ake aiki ne.
Yace to ni zan fita sai na dawo zan dan leka waje nagani ko akwai abinda zan iya yi a can na neman kudi.
Kin san angon naki dan bida ne ba mai zaman gida bane ni.
Na durkusa nace Allah yasa a dace Allah yaba da nasara a dawo lafiya baba.
Yace kai ni fa wanan baban ba son jin shi nake a bakinki ba da dai za, a canza min suna ko Alhajina akirani dayafi min alheri.
Nace to Alhaji Allah yaba da sa, a yasa a fita a nasara yace amin yar amarya ta yaushe rabon da naji anmin fatan alheri haka a rayuna.
Nan yasa kai yafice ni gyara dakin na dan zauna sai barci ya kwashe ni afurin mai nauyi ban sani ba.
Muryan yan gidan mu ne da suka shigo ganin kwanana ya tayar dani daga barci.
Na mike zubur ina masu sannu da zuwa idanuwan su fes a kaina suna kallona ban san may suke son fahinta ba daga gare ni.
Na gaidasu daya bayan daya tare da tambayan sauran mutanen gida.
Da yake iya yan uwan inna ne sai kadan daga dangin babana sai cewa sukayi kowa lafiya sai maman ku ne dai da ta saka muna hauka wai sai baban ku ya fada mata inda ya samo kudin da yai maki hidima haka na fita kunya.
Duk rantsuwan da yai mata ba yarda dashi ba wai idan bashi ya yi ba mijinkine yaba da kudin aka boye mata.
Nace cikin murmushi tare da zama kan makarin kujera na kai mama ho yaushe zata bar wanan halin nata ne na hassada da bakin ciki.
Ita da tace da tabar za, a kawo ni yanzu da taga sabanin haka shine kuma ta tayar da hankalinta.
Rabu da mahaukaci wacce bata son azauna lafiya iji kauna babana ta fadi hakan.
To yaya kuka kwashe da matan gidan naku yau da safe da fatan babu wani matsala dai ko daga gurin su.
Nai dan murmushi nace babu komai mama batare da na fada masu abinda ya faruba da safe akaina a gidan.
Sai dayan mama tawa tace ai ina ganin indan dai ta iya binsu zata samu sauki ga biyun mata wanan dai da take biwa ce matsala nake gani sai yaran su kuma don naga yaran a tsaye suke suma.
Nan dai sukaci ga ba da yi min nasihohi na in zauna da zuciya daya dakowa na basu girman su tunda duk sun haifeni baki dayan su.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE , ,
IDAN KIN BIYA KIKA TURAWA WANDA BAI BIYA BA KINCI AMANAN ALKAWARI DON ALLAH ZAI TAMBAYE KI HAKKINA NAYI HAKA A KAN KI DON SAI DA NA ROKE KI KADA KI FITAR MIN DA NOVEL DINA DON ONLINE NOVEL NE BA NA SHAGO BANE WANNAN DA FATAN ZAMU JI TSORON GAMUWAR MU DA UBANGIJIN MU ALLAH RANAN GOBE KIYAMA AMANA YAR UWA IDAN BAKI IYA RIKE AMANA KIYI MAGANA NA BAKI KUDIN KI DON BA ZAN YAFEWA HAKAN BA
MUJI TSORON ALLAH KADA MU BARI SHEDAN YA RUDI ZUKATAN MU PLEASE, , , ,
7
Haka rayuwan zaman sabon gurina ya kasance min agidan mijina kuma babana uwayen gidana da sukai jika dani.
Manyan diyan shi maza ko matan su sun kusa haihuwa na don haka mazan nake kiran su da yaya matan su da anty.
Haka ya jawo min saukin zama gidan don sun kula ban zo masu da fitsara ba ko kadan.
Bani kuma kyashin taya mutum aiki koda na sana, an shi tare dani za, ayi shi har a gama kuma da zuciya daya.
Wanan dalilin nee yajawo min sasauci sosai a gaare su gashi zan sha aiki idan an bani naci bana ci don ban saba da irin ciye ciye haka ba barkatai.
Wankin kayan Alhaji daya cire kafin ya tashi na kwasa na wanke sai dai ya sake wasu wanka
kuma ya zama kullun sabanin da da sau daya ko sau biyu zaiyi wanka a sati.
Ga maclean da brushe da yakeyi akai akai yanzu yake wanke baki dashi wanda na kula shi kan shi alhajin zuwa yanzu yana jin dadin sauyin rayuwan da ya samu.
Don ko wa yagan shi cikin sati dayan da nayi a gidan yasan ya samu sauyi sosai a rayuwan shi.
Don nakan ji matan shi suna mashi ba, a wai auren yarinya yasa shi ya sauya ga abinda basu san shi dashi ba a baya.
Sai ya basu amsa da nata sallon ke nan ke ai baki min ba a lokacin ki dana sauya din tun can.
Ranan da na cika sati daya ne agidan har lokacin ba wani abinda ya taba shiga tsakani da shi ban maga alaman hakan ba daga gare shi.
Ina kasa ya na saman gado kwance da ya kwanta kuma sai barci mai nauyi ya dauke shi sai safe.
Amma a gurin mutane suna ganin akwai abinda ke shiga tsakani na dashi a cikin dare don nakan ji sabuwa na cewa dashi ya daiyi a hankali kada ya takura karfin shi kan karaman yarinya yaje yajawa kan shi matsala kuma ?
Dariya yakan yi mata yace ai yafi son haka don lokacin ta ne abar ta tayi nata zamanin.
Sauran matan ba ruwan su da sha, ani na sai girmamawa amma sabuwa kan kullun sai tayi kokarin sake min magana a tsakar gida wanda zai bata min rai.
A banza don wani zancen ma ban san wai dani takeyi ba har ta kare haukan ta.
Idan ina zaune wani sain nakan ce ashe haka shine aure ba takura ba matsi ba tsangwama irin na mama a gidan mu ?
Gashi duk Alhaji zai shigo sai ya dan sayo min dan abin tabawa watarana ma har kayan shayi da biscuit da su sweet zai bayar akawo min .
Haka yasa na sake jikina sosai dasu wani sain har yar hira mukan yi dashi kafin yai barci sai dai hiran tamu nakan ga yana dariya sosai idan ina shirmay na.
Ranan ya dawo daga kasuwa ya tara mu a dakin mama Hausi uwar gidan shi kusan nice ta karshen shigowa dakin inda suke zaune.
Ina shigowa na samu guri na durkusa tare da gaida su gaba dayan su suka amsa min ina nan dai durkushe sai cewa mama tayi.
A, a Amarya samu guri mana ki zauna ai ina ganin magana Alhaji zaiyi da mu.
Nace mama har dani ?
Tace kai amarya ke ba matar shi bane yanzu har da ke mana.
Shi dai murmushi yayi kawai yana sauraren mu can bayan mama Hausi na koma na takure kamar uwata.
Can dai yai gyaran murya alaman zai fara magana ke nan a lokacin don haka naga kowan su ta natsu.
Yace to Alhamdullahi yau dai amarya ta gama satin ta daya kamar yadda sharia ya tana da.
Don haka yau ne zan koma dakin wace keda girki a cikin ku don haka ina rokon alfarma gurin ku.
Wanan yarinyar da Allah ya kaddari zaman ta a cikin mu da kuji tsoron Allah ku rike ta amana kamar yar cikin ku.
Yar cikin mu kuma Alhaji kishiya ce zan rike kamar yar cikina ta kwana da kai in kwana da kai kuma in rike ta kamar ya ta ?
Wanan maganan baiyi ba gaskiya ka dai sake wani maganan inji sabuwa dake magana a hasale a lokacin.
Murmushi yayi yace sabuwa ke nan ba laifi yadda kika dauke ta a tafi a haka sai dai saukin abin Allah yasa bake kadai nake aure ba.
Kuma bake ce uwar gidan gidan nan ba kinga ashe ba wani matsala ga hakan.
Ita Rahama har wani kishi ta sani a yanzu bayan daukan ku uwayen ta da takeyi tana maku bauta may kuma kike so a gare ta.
Eh yanzu kan hakane a/a idan ta goge ai babu shegu nan gaba kamar mu, balle yadda naga kana rawan kafa haka a kan ta wai kai ka samu yar jikan ka ka saka a daki kana abinda bai dace ba da ita.
Haba sabuwa wai may yasa baki da hakkuri ne ke inji mama Kulu matar shi ta biyu.
Yai murmushi tare da cewa ai ba rashin hakkuri bane gani takeyi abinda tazo gidan a lokacin tana maku rashin kunya shine itama yar mutane tazo dashi zatai maku.
Sai dai ki sani alama ya nuna tarbiya ba daya ba wallahi don ke ko kwana ba, ayi ba kika fara sakani ga fitina.
Amma yanzu ki duba karamar yarinya tasan daraja na tasan naku hakama na iyalina baki daya.
Au to kana nufin ta fini ke nan yanzu maji magana ai gara da ka fito fili ka fada min kowa yaji.
To bari kaji Alhaji wallahi duk ranan da yarinyar nan tai gigin shiga harka na sai dai uwarta ta haifi wata don ko ban halaka ta ba zaka dawo ka samu ankaita jiya gidan su.
Yace ke ko da kin kwana a gadirom rana wallahi da karshen zaman ki gidan nan yazo sabuwa da kinyi nadama mara adadi a rayuwan ki.
Yace naga abin naki ba wasa bane yanzu wallahi duk ranan da kikai gigin taba lafiyan yar mutane sai na lahira yafiki jin dadi a garin nan.
Lalai ma ba, ayi ba yanzu aka soma ke nan don kayi dandane haukace ka zauce kamar wanda bai taba jin dadin bujen mata ba ko ?
Yai murmushi yace kaiyya a fili tare da girgiza kan shi yace ashe kin gane wani bujen yafi wani buje ke nan.
Ranta yai matukar baci bata karasa ba taji yace dama abinda yasa na tara ku nan shiine ke hausi ke ce babba ke zan roka alfarma don Allah.
Ina son yarinyar nan ku dauke mata nauyin girki a gidan nan don kunga karfin ta bai gama kaiwa ba don Allah a dan sahirta mata wanan aikin har ta dan kara tasawa nan gaba idan Allah ya ce.
Cabdijam ba ta iya aiki amma tana iya shigewa da kai daki tai shiru har safe ko ?
Kai sabuwa inji mama kulu tace waban bai dace ba gaskiya shi fa ke da gidan shi balle ma wanan yaushe zata iya tuka tuwon gidan nan haka ?
Ai dama nasan duk da hadin kan ku don ai min bakin ciki kuka hada baki akawo ta gidan nan idan hakane bazatayi girki ba sai dai nima na dinga yi ni da yarana kawai wallahi.
Isan kinyi hakan ma daidai ne inji Alhajin amma ki sani cikin ki tayi don su nan duk suna da sarakai da zasi girka masu ba sai sunyi ba kece mai yara kanana da yawa kuma.
Tace koma maye na dai ji muddin wanan yar mussan da ka kwaso baitai girki ba nima bazan yi ba wallahi yace har da shan wallahii tace eh na sha.
Mama hausi ta bude baki zatai magana ya dakatar da
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9 Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22Chapter 23Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32Chapter 33Chapter 34Chapter 35Chapter 36Chapter 37Chapter 38Chapter 39Chapter 40Chapter 41Chapter 42Chapter 43Chapter 44Chapter 45Chapter 46Chapter 47Chapter 48Chapter 49Chapter 50Chapter 51Chapter 52Chapter 53Chapter 54Chapter 55Chapter 56Chapter 57Chapter 58Chapter 59Chapter 60Chapter 61Chapter 62Chapter 63Chapter 64Chapter 65Chapter 66Chapter 67Chapter 68Chapter 69Chapter 70Chapter 71Chapter 72Chapter 73Chapter 74Chapter 75Chapter 76Chapter 77Chapter 78Chapter 79Chapter 80Chapter 81Chapter 82Chapter 83Chapter 84Chapter 85Chapter 86Chapter 87Chapter 88Chapter 89Chapter 90Chapter 91Chapter 92Chapter 93Chapter 94Chapter 95Chapter 96Chapter 97Chapter 98Chapter 99Chapter 100Chapter 101Chapter 102Chapter 103Chapter 104Chapter 105Chapter 106Chapter 107Chapter 108Chapter 109Chapter 110Chapter 111Chapter 112Chapter 113Chapter 114Chapter 115Chapter 116Chapter 117Chapter 118Chapter 119Chapter 120Chapter 121Chapter 122Chapter 123Chapter 124Chapter 125Chapter 126Chapter 127Chapter 128Chapter 129Chapter 130Chapter 131Chapter 132Chapter 133Chapter 134Chapter 135Chapter 136Chapter 137Chapter 138Chapter 139Chapter 140Chapter 141Chapter 142Chapter 143Chapter 144Chapter 145Chapter 146Chapter 147Chapter 148Chapter 149Chapter 150Chapter 151Chapter 152Chapter 153