daina fitinan suka shiga daki.
Amira tace ai dai taji kunya a gaban daddy Anty tace mata kece kika fada min shiya sai motan don tun bai aure ta ba yake maku haka ya saya mata abu kuna kallo.
Nace ji sheri fa banda motan da daddy ya saya min lokacin don zuwa makaranta yaushe ya taba sai min wani abu ni kadai.
Amira tace maman kafin ta rasu ko yaushe maganan ta shine kunyar ki take ji takance gashi an zugata ta kasa fahintar ki yanzu gasu Nasir a wajen ki tankar ke kika haife su don abinda Maman ihisan take masu anan duk yaran na fada mata da yadda kike tarewa ba ki bari tai masu sheri.
Shine fa takance ita bata san may zatai maki ta wanke laifin ta ba a gareki .
Nace Allah sarki antyna ni bata da laifin komai a wurina ni abinda tai min har na mutu bazan taba saka mata shi ba a rayuwana.
********* ********* *********
Azumi yana gabatowa kowa na shirin zuwan shi munyo odan kaya sosai ni da anty Zulfa inda ta tura kano da sauran wurare don a sayar mata muna daukowa indiya da chaina.
Ranan muna cikin daki anty Zulfa muna kallon kayan da aka shigo mata dasu sai shirya kayan su Aisha da Amira da Atika ke faman yi.
Zaune nake a saman dogon kujera sai ga Jinior ya shigo yana fadin daddy yana neman mu a falo nida maman baby yadda suke kiran anty Zulfa ke nan.
Mun fito yana kishingide a saman center carpet yaran duk sun rufe shi yana biye masu suna son kwatan abu a hannun shi.
Sai Hindatu da ke zaune daga gefen shi ta hade rai da alama yaran sun damay ta ke nan da hayaniyar su da sukeyi da uban nasu.
Mun zauna tare da gaidashi sai dan wurin Zulfa hanif ya nufo uwarshi yana fadin mama baba ya sayo muna.
Tace ai ku kenan kuyi ta faman shan zaki yana biye maku kuma bai daina saya maku kullun sai dankanoma kuke fama dashi.
Dan kanoma ko lalacewa ya mai da yara kamar wasu diyan zinare can yai zaune a cikin su yana wasu abubuwan da bai dace ba dasu.
A yanzu ko naga ko a baya haka yake da yaran shi kowa yasan halin yaya a kan yaran shi sai dai in yaran na yanzu ne ba a son ya zauna ya fahince su kuma muji.
Daddy Jinior tace kana neman mu ko na fadi hakane don kada zancen su yai nisa sosai a wurin don sun dauko sake layi.
Ya gyara zaman shi tare da dago Abdul daga jikin shi ya rugumay yaron yana dan buga bayan shi a hankali yace.
Kin shirya saurarena ke nan baki biyewa wannan haukan ba don banga dalilin dan magana kadan sai an mayar dashi dogo ya zama na fitina ba ko yaushe.
Ayi hakkuri inji Zulfa tace abin hassada ne ba a raina shi a gidan nan in bashi ba yaro kuma ace ana hassada da zama da uban shi.
Idan basu mamay ka ba wazasu mama suji sanyi a ran su bayan kai da mu da suka sani nace anty abar zancen don Allah hakana.
Mun yi shiru can yace dama ina son fada maku ne ba zai muyi azumi a gidan nan ba don na samu wani wuri a cikin nan maitama ne.
Kowan mu yai tsit yana sauraren shi yace gida ne babba da kowan ku zai samu walawa a cikin sa yadda yake so.
Part na farko mutum biyu ne zasu zauna cikin sa shima dayan hakane da sauri zulfa tace har Raliya ke nan nan zata dawo da zama ita ma ?
Yace ai kinji nace kowan ku sai kunje kunga gidan ke Zulfa zaki zauna tare da Rahama a bangare guda haka ma ita hindatu da Raliya sai su zauna a dayan bangaren.
Nace yaran fa daddy ?
Yai dan murmushi yace uwar yara inda kike ai dole dake zasu zauna dayan part din yafi girma don akwai extract dakuna har biyu sai shi dan naki akwai dakin shi a kasa shima nawa dakin sama zan zauna.
Dama dai ka gama tsarawa ne ko mu fada muna kawai kakeyi yanzu inji hindatu ta fadi haka a hasale.
Shi ya bata amsa da fadin eh na tsara komai fada maku nakeyi don umurni nake bayarwa ba wai ra, ayi ba.
Shiru mukayi gaba dayan mu sai Zulfa ce tace dashi zuwa yaushe zamu koma sai yake cewa nan da sati mai zuwa insha Allahu.
Kunga kafin azumi kun dan saba da wurin ke nan Allah yakai munace tare da fadin Allah ubangiji yasa mu koma a sa, a gabadaya kowa yace amin .
Ina kokarin mikewa ne yake cewa ga wuri yayi nisa ban san yadda zakuyi da wa yan nan kayan naku ba ?
Don ba abinda zaku dauka a nan din komai na sa an saka maku a can iri daya don ban son wani korafi ya biyo baya kuma.
Zulfa tace dashi ai wanan ba matsala bane yaya ko motar company ku ba sai kasa ya kwashe muna ba zuwa kano.
Hindatu tace shine ai yace idan kun shirya su wanan baida matsala sai kowa ta fadi inda za a sauke mata nata.
Tun daga wanan ranan aka fara shirin komawa sabon gida ba wani hira sai na komawan mu can sabon wurin kowa keyi.
Ban zauna ba ni aiki ya sha min kai sosai a lokacin sai ga helen ta dawo ta girma ita ma sosai a lokacin don tunda ba karatu takeyi ba nasan ta kusa aure ke nan
A wurin Zulfa nake samun labarin wai anyi fitina dashi da Raliya tace bazata koma ba can inda take zata zauna ita.
Tace karshe ma ashe cewa yayi dole ta nemi transfer ta dawo da aikin ta nan Abuja inda kowa yake yanzu dai ban san yadda suka kare ba.
Ai bazata so ta dawo nan ba tunda can yafi mata samu nan kuwa kinga idan ta dawo dole kasa zata koma tunda akwai na gaba da ita da yawa.
Tace a dama ai galihu ne kawai irin na mutanen mu har takewa mutane sallon wai ita saura kiris takai manager yanzu.
Yanzu akai mu gani mana in kaiwa banza ne nasan dai ba karamin kwasa zasuyi ba kan hakan matar da ta saba haka take kamar faransi ba oda ina zata iya zaman gida yadda yake so.
Ni dai ina jin ta nasan koni haka akaita zagina a baya ban ma sani ba ko yanzu ai ban debe tsanmani don kishiya sunar ta kishiya ai.
Ranan Laraba da ya zagayo ya kwashi yara ya fara kaiwa shi da Sani da motocin mu da duk wanin abinda za, a bukata sai mu da bamu tafi ba mun tsaya sai an kwashe kayan kowa a gaban idon shi.
Bayan an gama ya dauke mu shida zulfa a gaba ni da hindatu muna baya sai hadiyan rai takeyi ban san may ya bata mata rai ba a lokacin tundai safe take hakana a gidan.
Gida ne babba mai kyau ga tsari shigen ginan mu na na can kano sai dai wanan din ya nuna mai aikin wayewa da akayi na zamani.
Mun shiga da addua da godewa Allah yaran ne suke nuna muna ga inda daddy yace namu ne duk komai iri daya ne har ginan wanan dai dakunan da aka kara biyu sune banbancin mu.
Amma bayan hakan komai iri daya ne kowan mu zata tashi da dakuna biyu a bangaren ta.
Abin yaiwa kowan mu dadi sosai nace Zulfa ta fara zaben inda take so sai bayan ta zaba na farkon ta dauka ni kuma na dauki wanda ke daga ciki ni yafi min sauki ma don hayaniya da ban so sosai idan ina resache.
Wata sabuwa Hindatu ce tazo tana fadin kuji min wanan tsohuwar wofi din duk sai muka waiga gunta muna kallon ta sai take cewa wai fa Raliya ke fadin ita bazata zauna part daya dani ba sai dai wai a hada ta da Rahama su zauna wuri daya watau mu tsofin mata ya hade mu wuri guda ke nan.
Kuji min tsohuwar banza mai mayar da kanta baya don Allah wai kamar Raliya ke cewa wai mune tsofin mata jifa don Allah.
Dariya zulfa tai mata tace haba haba dai ke da mutumiyar taki kuma za a ji kan ku ai bai dace ba haka ku dai sasanta kan ku acan.
Tace bari Zulfa matar nan ta bani haushi wallahi bata san ina dakin ha ta bugo mai waya tana wanan maganan.
Ai ban bari takai karshe ba nace ke tsohuwar banza wace bata san may takeyi ba wa ye tsohuwar bake ba ke ba a gujeki ba shine ke zaki guji wani.
Dariya ta bani sosai har na kasa hadewa sai da na fasa shi nace da ita amarya ce fa maman Ihisan tace kai amma dai ke amaryan may can.
Haihuwar ta hudu fa har da bari tace min wanda ma aka sani ke nan fa na boye wayasan su.
Tunda shima uban aiki bai san hakan ba sai daga baya don ta boye mai komai da farko akan zancen diyan nata.
Nace kai hudu fa kikace tace wallahi Allah ko kuma dasu zata dawo nan gidan wai da sauri Zulfa tace wani gidan ?
Tace ai sai kiyi tunda uban aikin ya yarda mu may zamuce na san dai akwai tsiya kan a gidan nan don ban yarda agola sufi min diya na.
Dariya sosai muke mata har taji haushin mu tace ai dole kuyi mun dariya tunda baku aka taba.
To maman ihisan aiko mu ba a bari ba don gidan gaba daya ne kila tsarin zaman a tare bai mata ba ta bullo ta wanan tsigar kuma.
Kuma wallahi dole ta zauna ba tunda ba fin kowa tayi ba ta zo a zauna in kasa akaci a kwaba tare a hade shi.
Zulfa ta kallo inda nake tai min signal da idon ta wai nai shiru nace yanzu dai ai gamu gani ko tunda dai namu dama idone mai daki shiyasan in da ruwa ke mai yoyo.
Ta dan jima tana ta tonon asiri har ta gaji ta koma wurin ta Amira tace wai mummy ku baku san tana da yara bane dama ?
Nace nifa ban san komai bz a kanta kin san ba ta dade ba na tafi germany shiyasa ban ma damu da nasan komai ba akanta.
Tace wai danta ya girmay ni nisa ba kusa ba wallahi baki gan shi gudan babba dashi fa ya kusa kai daddy tsayi muka kwashe mata da dariya kawai.
Yanzu mun samu hutu da rage fitina don kowa akwai kitchen a part din ta sai daga baya nake ji ranan a wurin sani wai sayen gidan yayi ashe da kudin shi ba haya bane.
Nace a raina lalai alamarin daddy ya bunkasa sosai ke nan har ya iya sayen wanan katon gidan haka a garin Abuja don iyalin shi.
Saura kwana hudu a tashi da azumi daddy ya shigo muna zaune a falin mu Abdul na saman jikina yana rikici wai sai na goya shi bai son na kowa sai ni.
Tun daga main falo yake jin kukan yaron na tashi ya shigo bayan ya sallami bakin shi sun tafi yana fadin.
Wai may ya samay shine haka yake kuka daidai ina dukan shi don ya isheni da fitina tun safe yake hakana a gidan anyi lalashin duniya yaki yarda da kowa.
Nace fitina yake ji yau haka kawai ya tashi haka yanzu wsi shi sai na goya shi yace to may zai hana ki goya shi din yaro jeka ta goya ka kaji Allah ya taimake ka kai ba wanda ya hana ma bayan ma.
Ni wai ban gane ba fa har yanzu naji shiru in dai ba planning kike yi ba Rahama kin dai san bani kaunar wanan abin ko kadan.
Murmushi nayi nace Allah dai ne ya tausaya min don wanan dan fitinan idan ina zan iya dashi haka.
Take naga ran Zulfa ya baci har ya lalashi yaron ya dauke shi zasu fita baitai magana ba a raina nace kishiya ke nan baki da tabas ai dama sai dai a tafi a rufe kawai na ciki na ciki dama.
Ya kai kofa ya juyo yana fadin yau Raliya zasu dawo fa ina fanin don tace dani sun taso dazun.
Ita dawa zasu dawo naji kace zasu dawo inji zulfa da sai yanzu tai magana dashi tun da yai min maganan samun ciki a gaban ta.
Yace idan tazo ai zaki gani tace aiko gamu gani din Allah ya kawo su lafiya mu sha kallon yan birni.
Ya dai fice da yaron abinshi daga falon bai tanka ta ba nima don ta san na fahinci may take nufi sai na share ta na ci gaba da karatun wani takarda dake hannuna.
Haka har muka watse don ra san na gane manufanta amma kada abin yai nisa sai naji tace dani ashe yau Rahama kina da baki ke uwar yaya.
Nace gaki uwargida ina ni ina wani kwashe kwashe can kedai zata dinga barwa yaran idan zata tafi ai tunda kece uwar gida sarautar mata.
Tace a ina uwar gidan take nan kudai da kuke jin lokacin ku ai sai daku gashi yanzu har yana maki tuni kin dade baki haihu ba hakana.
Murmushi nayi ba yanzu zan bata amsa ba na kira Aisha nace ta dauki min magani daki na ba baba har Abdul din dake rikici idan an dawo dashi.
Bayan ta kawo min maganin ne na matse yaron na bashi yasha sai dan wirin Zulfa hanif yazo wai shima na bashi nace dashi allura dai zan maka sai yaron ya gudu can kuma ya sake dawowa ta nace wai sai na bashi maganin ya sha.
Uwar tace wallahi hanif zan doke ka yanzu kuwa dannema ina faman kafa kafa da ku kace a dinkira ma magani lafiyan ka kalau kuma.
Nace nima ai ba mahaukaciya bace da zan bashi magani don nasan illar yin hakan fiye da kowa.
Bance zaki hashi ba ai shi nake ma fada nace a, a bashi ba dai aiko kana dasu da yawa baka cutawa wani don baidasu yana kafakafa da abinshi.
Shiru tayi bata sake magana ba sai kallo mukeyi kowan mu yayi shiru yaron yazo ya lafe saman kafana na dauke shi na aza a saman jikina yai barci.
Haidar na ganin haka yasa rikici wai ya tashi tace yaki tashi ai ba uwarka bane kai kadai in kana son dauka zo na dauke ka nan mana.
Sai yaron yace baiyi na hawo shi nace kyale mama kaji bari in yai barci sai na sauke shi ka hau kaima.
Wani hira ta dauko min da haka muka wayance zancen kowa ya manta da abinda akayi muka basar dama shine kishin ba komai ba.
Sai wajajan shida ga Jinior ya shigo yana hakki yace mummy kin san may nace a, a jinior tace wallahi ga matar nan matar nan mai sallon nan ta zo harda wasu yara ana shiga masu da kaya wurin maman Ihisan.
Addua na fara a bakina na neman kariya da tsarin ubangiji Allah akan zaman da zamuyi da ita a gidan.
Ba wanda ya shiga don dama Allah ya taimake ni yarana basu da irin wanan shige shige na wasu dakuna ba wanda ya tafi inda suke.
Ko dakin Zulfa da muke kusa wuri daya basu shiga idan ba ya kama dole ba ka tsare yaran ka wuri daya alheri ne a wanan zamanin da muke ciki don kariyan kai.
Yaron ka in yana wanan halin zai iya shiga wani hali baka sani ba haka ma za, a iya zarga mai wani sheri ba tare dz kaika sani ba ko yaron.
Shiya ka zamo abokai da diyan ka shine kawai alheri d mafita a wurin ka don yanzu lokaci ya canza kowa nashi ya sani ba kunya a kan hakan.
********* ********* *********
Har suka kwana suka wuni ni dai ban sasu a idona ba daga ita har yaran nata data zo dasu wurin yar sa idon shiyan mune ma nake jin wai yaran ashe duk manya ne dasu.
Ni dai na jawa yara na duka kunne kan su iya kan su daga uwar har yaran ba ruwan su da kowan su nasan kuma insha Allahu zasu ji magana na.
Balle ma Amira da taki jinin ta kamar yunwar cikin ta bata ko son ai mata zancen Raliya sam taci uwar bari gunta ko.
Ban san tana falon ba na shigo a cikin shiri na, nazo na roke shi zan kai yara gun baba daga csn idan an gama masu zamu dan je nakaisu yawo.
Ganin ta baisa na fasa abinda ya kawo ne ba kai tsaye na nufi kujeran da yake zaune akai na dan zauna ina cewa sannun ku da hutawa shi kadai ya amsa min nace daddy don Allah ina son zan kai yara gun baba daga can zan dai kaisu su sayo abu yan matan.
Gaba daya ke nan zaku fita dasu ko nace eh ba iya tafiya biyu shiyasa nace su shirya mu
Showing 378001 words to 381000 words out of 456145 words
Amira tace ai dai taji kunya a gaban daddy Anty tace mata kece kika fada min shiya sai motan don tun bai aure ta ba yake maku haka ya saya mata abu kuna kallo.
Nace ji sheri fa banda motan da daddy ya saya min lokacin don zuwa makaranta yaushe ya taba sai min wani abu ni kadai.
Amira tace maman kafin ta rasu ko yaushe maganan ta shine kunyar ki take ji takance gashi an zugata ta kasa fahintar ki yanzu gasu Nasir a wajen ki tankar ke kika haife su don abinda Maman ihisan take masu anan duk yaran na fada mata da yadda kike tarewa ba ki bari tai masu sheri.
Shine fa takance ita bata san may zatai maki ta wanke laifin ta ba a gareki .
Nace Allah sarki antyna ni bata da laifin komai a wurina ni abinda tai min har na mutu bazan taba saka mata shi ba a rayuwana.
********* ********* *********
Azumi yana gabatowa kowa na shirin zuwan shi munyo odan kaya sosai ni da anty Zulfa inda ta tura kano da sauran wurare don a sayar mata muna daukowa indiya da chaina.
Ranan muna cikin daki anty Zulfa muna kallon kayan da aka shigo mata dasu sai shirya kayan su Aisha da Amira da Atika ke faman yi.
Zaune nake a saman dogon kujera sai ga Jinior ya shigo yana fadin daddy yana neman mu a falo nida maman baby yadda suke kiran anty Zulfa ke nan.
Mun fito yana kishingide a saman center carpet yaran duk sun rufe shi yana biye masu suna son kwatan abu a hannun shi.
Sai Hindatu da ke zaune daga gefen shi ta hade rai da alama yaran sun damay ta ke nan da hayaniyar su da sukeyi da uban nasu.
Mun zauna tare da gaidashi sai dan wurin Zulfa hanif ya nufo uwarshi yana fadin mama baba ya sayo muna.
Tace ai ku kenan kuyi ta faman shan zaki yana biye maku kuma bai daina saya maku kullun sai dankanoma kuke fama dashi.
Dan kanoma ko lalacewa ya mai da yara kamar wasu diyan zinare can yai zaune a cikin su yana wasu abubuwan da bai dace ba dasu.
A yanzu ko naga ko a baya haka yake da yaran shi kowa yasan halin yaya a kan yaran shi sai dai in yaran na yanzu ne ba a son ya zauna ya fahince su kuma muji.
Daddy Jinior tace kana neman mu ko na fadi hakane don kada zancen su yai nisa sosai a wurin don sun dauko sake layi.
Ya gyara zaman shi tare da dago Abdul daga jikin shi ya rugumay yaron yana dan buga bayan shi a hankali yace.
Kin shirya saurarena ke nan baki biyewa wannan haukan ba don banga dalilin dan magana kadan sai an mayar dashi dogo ya zama na fitina ba ko yaushe.
Ayi hakkuri inji Zulfa tace abin hassada ne ba a raina shi a gidan nan in bashi ba yaro kuma ace ana hassada da zama da uban shi.
Idan basu mamay ka ba wazasu mama suji sanyi a ran su bayan kai da mu da suka sani nace anty abar zancen don Allah hakana.
Mun yi shiru can yace dama ina son fada maku ne ba zai muyi azumi a gidan nan ba don na samu wani wuri a cikin nan maitama ne.
Kowan mu yai tsit yana sauraren shi yace gida ne babba da kowan ku zai samu walawa a cikin sa yadda yake so.
Part na farko mutum biyu ne zasu zauna cikin sa shima dayan hakane da sauri zulfa tace har Raliya ke nan nan zata dawo da zama ita ma ?
Yace ai kinji nace kowan ku sai kunje kunga gidan ke Zulfa zaki zauna tare da Rahama a bangare guda haka ma ita hindatu da Raliya sai su zauna a dayan bangaren.
Nace yaran fa daddy ?
Yai dan murmushi yace uwar yara inda kike ai dole dake zasu zauna dayan part din yafi girma don akwai extract dakuna har biyu sai shi dan naki akwai dakin shi a kasa shima nawa dakin sama zan zauna.
Dama dai ka gama tsarawa ne ko mu fada muna kawai kakeyi yanzu inji hindatu ta fadi haka a hasale.
Shi ya bata amsa da fadin eh na tsara komai fada maku nakeyi don umurni nake bayarwa ba wai ra, ayi ba.
Shiru mukayi gaba dayan mu sai Zulfa ce tace dashi zuwa yaushe zamu koma sai yake cewa nan da sati mai zuwa insha Allahu.
Kunga kafin azumi kun dan saba da wurin ke nan Allah yakai munace tare da fadin Allah ubangiji yasa mu koma a sa, a gabadaya kowa yace amin .
Ina kokarin mikewa ne yake cewa ga wuri yayi nisa ban san yadda zakuyi da wa yan nan kayan naku ba ?
Don ba abinda zaku dauka a nan din komai na sa an saka maku a can iri daya don ban son wani korafi ya biyo baya kuma.
Zulfa tace dashi ai wanan ba matsala bane yaya ko motar company ku ba sai kasa ya kwashe muna ba zuwa kano.
Hindatu tace shine ai yace idan kun shirya su wanan baida matsala sai kowa ta fadi inda za a sauke mata nata.
Tun daga wanan ranan aka fara shirin komawa sabon gida ba wani hira sai na komawan mu can sabon wurin kowa keyi.
Ban zauna ba ni aiki ya sha min kai sosai a lokacin sai ga helen ta dawo ta girma ita ma sosai a lokacin don tunda ba karatu takeyi ba nasan ta kusa aure ke nan
A wurin Zulfa nake samun labarin wai anyi fitina dashi da Raliya tace bazata koma ba can inda take zata zauna ita.
Tace karshe ma ashe cewa yayi dole ta nemi transfer ta dawo da aikin ta nan Abuja inda kowa yake yanzu dai ban san yadda suka kare ba.
Ai bazata so ta dawo nan ba tunda can yafi mata samu nan kuwa kinga idan ta dawo dole kasa zata koma tunda akwai na gaba da ita da yawa.
Tace a dama ai galihu ne kawai irin na mutanen mu har takewa mutane sallon wai ita saura kiris takai manager yanzu.
Yanzu akai mu gani mana in kaiwa banza ne nasan dai ba karamin kwasa zasuyi ba kan hakan matar da ta saba haka take kamar faransi ba oda ina zata iya zaman gida yadda yake so.
Ni dai ina jin ta nasan koni haka akaita zagina a baya ban ma sani ba ko yanzu ai ban debe tsanmani don kishiya sunar ta kishiya ai.
Ranan Laraba da ya zagayo ya kwashi yara ya fara kaiwa shi da Sani da motocin mu da duk wanin abinda za, a bukata sai mu da bamu tafi ba mun tsaya sai an kwashe kayan kowa a gaban idon shi.
Bayan an gama ya dauke mu shida zulfa a gaba ni da hindatu muna baya sai hadiyan rai takeyi ban san may ya bata mata rai ba a lokacin tundai safe take hakana a gidan.
Gida ne babba mai kyau ga tsari shigen ginan mu na na can kano sai dai wanan din ya nuna mai aikin wayewa da akayi na zamani.
Mun shiga da addua da godewa Allah yaran ne suke nuna muna ga inda daddy yace namu ne duk komai iri daya ne har ginan wanan dai dakunan da aka kara biyu sune banbancin mu.
Amma bayan hakan komai iri daya ne kowan mu zata tashi da dakuna biyu a bangaren ta.
Abin yaiwa kowan mu dadi sosai nace Zulfa ta fara zaben inda take so sai bayan ta zaba na farkon ta dauka ni kuma na dauki wanda ke daga ciki ni yafi min sauki ma don hayaniya da ban so sosai idan ina resache.
Wata sabuwa Hindatu ce tazo tana fadin kuji min wanan tsohuwar wofi din duk sai muka waiga gunta muna kallon ta sai take cewa wai fa Raliya ke fadin ita bazata zauna part daya dani ba sai dai wai a hada ta da Rahama su zauna wuri daya watau mu tsofin mata ya hade mu wuri guda ke nan.
Kuji min tsohuwar banza mai mayar da kanta baya don Allah wai kamar Raliya ke cewa wai mune tsofin mata jifa don Allah.
Dariya zulfa tai mata tace haba haba dai ke da mutumiyar taki kuma za a ji kan ku ai bai dace ba haka ku dai sasanta kan ku acan.
Tace bari Zulfa matar nan ta bani haushi wallahi bata san ina dakin ha ta bugo mai waya tana wanan maganan.
Ai ban bari takai karshe ba nace ke tsohuwar banza wace bata san may takeyi ba wa ye tsohuwar bake ba ke ba a gujeki ba shine ke zaki guji wani.
Dariya ta bani sosai har na kasa hadewa sai da na fasa shi nace da ita amarya ce fa maman Ihisan tace kai amma dai ke amaryan may can.
Haihuwar ta hudu fa har da bari tace min wanda ma aka sani ke nan fa na boye wayasan su.
Tunda shima uban aiki bai san hakan ba sai daga baya don ta boye mai komai da farko akan zancen diyan nata.
Nace kai hudu fa kikace tace wallahi Allah ko kuma dasu zata dawo nan gidan wai da sauri Zulfa tace wani gidan ?
Tace ai sai kiyi tunda uban aikin ya yarda mu may zamuce na san dai akwai tsiya kan a gidan nan don ban yarda agola sufi min diya na.
Dariya sosai muke mata har taji haushin mu tace ai dole kuyi mun dariya tunda baku aka taba.
To maman ihisan aiko mu ba a bari ba don gidan gaba daya ne kila tsarin zaman a tare bai mata ba ta bullo ta wanan tsigar kuma.
Kuma wallahi dole ta zauna ba tunda ba fin kowa tayi ba ta zo a zauna in kasa akaci a kwaba tare a hade shi.
Zulfa ta kallo inda nake tai min signal da idon ta wai nai shiru nace yanzu dai ai gamu gani ko tunda dai namu dama idone mai daki shiyasan in da ruwa ke mai yoyo.
Ta dan jima tana ta tonon asiri har ta gaji ta koma wurin ta Amira tace wai mummy ku baku san tana da yara bane dama ?
Nace nifa ban san komai bz a kanta kin san ba ta dade ba na tafi germany shiyasa ban ma damu da nasan komai ba akanta.
Tace wai danta ya girmay ni nisa ba kusa ba wallahi baki gan shi gudan babba dashi fa ya kusa kai daddy tsayi muka kwashe mata da dariya kawai.
Yanzu mun samu hutu da rage fitina don kowa akwai kitchen a part din ta sai daga baya nake ji ranan a wurin sani wai sayen gidan yayi ashe da kudin shi ba haya bane.
Nace a raina lalai alamarin daddy ya bunkasa sosai ke nan har ya iya sayen wanan katon gidan haka a garin Abuja don iyalin shi.
Saura kwana hudu a tashi da azumi daddy ya shigo muna zaune a falin mu Abdul na saman jikina yana rikici wai sai na goya shi bai son na kowa sai ni.
Tun daga main falo yake jin kukan yaron na tashi ya shigo bayan ya sallami bakin shi sun tafi yana fadin.
Wai may ya samay shine haka yake kuka daidai ina dukan shi don ya isheni da fitina tun safe yake hakana a gidan anyi lalashin duniya yaki yarda da kowa.
Nace fitina yake ji yau haka kawai ya tashi haka yanzu wsi shi sai na goya shi yace to may zai hana ki goya shi din yaro jeka ta goya ka kaji Allah ya taimake ka kai ba wanda ya hana ma bayan ma.
Ni wai ban gane ba fa har yanzu naji shiru in dai ba planning kike yi ba Rahama kin dai san bani kaunar wanan abin ko kadan.
Murmushi nayi nace Allah dai ne ya tausaya min don wanan dan fitinan idan ina zan iya dashi haka.
Take naga ran Zulfa ya baci har ya lalashi yaron ya dauke shi zasu fita baitai magana ba a raina nace kishiya ke nan baki da tabas ai dama sai dai a tafi a rufe kawai na ciki na ciki dama.
Ya kai kofa ya juyo yana fadin yau Raliya zasu dawo fa ina fanin don tace dani sun taso dazun.
Ita dawa zasu dawo naji kace zasu dawo inji zulfa da sai yanzu tai magana dashi tun da yai min maganan samun ciki a gaban ta.
Yace idan tazo ai zaki gani tace aiko gamu gani din Allah ya kawo su lafiya mu sha kallon yan birni.
Ya dai fice da yaron abinshi daga falon bai tanka ta ba nima don ta san na fahinci may take nufi sai na share ta na ci gaba da karatun wani takarda dake hannuna.
Haka har muka watse don ra san na gane manufanta amma kada abin yai nisa sai naji tace dani ashe yau Rahama kina da baki ke uwar yaya.
Nace gaki uwargida ina ni ina wani kwashe kwashe can kedai zata dinga barwa yaran idan zata tafi ai tunda kece uwar gida sarautar mata.
Tace a ina uwar gidan take nan kudai da kuke jin lokacin ku ai sai daku gashi yanzu har yana maki tuni kin dade baki haihu ba hakana.
Murmushi nayi ba yanzu zan bata amsa ba na kira Aisha nace ta dauki min magani daki na ba baba har Abdul din dake rikici idan an dawo dashi.
Bayan ta kawo min maganin ne na matse yaron na bashi yasha sai dan wirin Zulfa hanif yazo wai shima na bashi nace dashi allura dai zan maka sai yaron ya gudu can kuma ya sake dawowa ta nace wai sai na bashi maganin ya sha.
Uwar tace wallahi hanif zan doke ka yanzu kuwa dannema ina faman kafa kafa da ku kace a dinkira ma magani lafiyan ka kalau kuma.
Nace nima ai ba mahaukaciya bace da zan bashi magani don nasan illar yin hakan fiye da kowa.
Bance zaki hashi ba ai shi nake ma fada nace a, a bashi ba dai aiko kana dasu da yawa baka cutawa wani don baidasu yana kafakafa da abinshi.
Shiru tayi bata sake magana ba sai kallo mukeyi kowan mu yayi shiru yaron yazo ya lafe saman kafana na dauke shi na aza a saman jikina yai barci.
Haidar na ganin haka yasa rikici wai ya tashi tace yaki tashi ai ba uwarka bane kai kadai in kana son dauka zo na dauke ka nan mana.
Sai yaron yace baiyi na hawo shi nace kyale mama kaji bari in yai barci sai na sauke shi ka hau kaima.
Wani hira ta dauko min da haka muka wayance zancen kowa ya manta da abinda akayi muka basar dama shine kishin ba komai ba.
Sai wajajan shida ga Jinior ya shigo yana hakki yace mummy kin san may nace a, a jinior tace wallahi ga matar nan matar nan mai sallon nan ta zo harda wasu yara ana shiga masu da kaya wurin maman Ihisan.
Addua na fara a bakina na neman kariya da tsarin ubangiji Allah akan zaman da zamuyi da ita a gidan.
Ba wanda ya shiga don dama Allah ya taimake ni yarana basu da irin wanan shige shige na wasu dakuna ba wanda ya tafi inda suke.
Ko dakin Zulfa da muke kusa wuri daya basu shiga idan ba ya kama dole ba ka tsare yaran ka wuri daya alheri ne a wanan zamanin da muke ciki don kariyan kai.
Yaron ka in yana wanan halin zai iya shiga wani hali baka sani ba haka ma za, a iya zarga mai wani sheri ba tare dz kaika sani ba ko yaron.
Shiya ka zamo abokai da diyan ka shine kawai alheri d mafita a wurin ka don yanzu lokaci ya canza kowa nashi ya sani ba kunya a kan hakan.
********* ********* *********
Har suka kwana suka wuni ni dai ban sasu a idona ba daga ita har yaran nata data zo dasu wurin yar sa idon shiyan mune ma nake jin wai yaran ashe duk manya ne dasu.
Ni dai na jawa yara na duka kunne kan su iya kan su daga uwar har yaran ba ruwan su da kowan su nasan kuma insha Allahu zasu ji magana na.
Balle ma Amira da taki jinin ta kamar yunwar cikin ta bata ko son ai mata zancen Raliya sam taci uwar bari gunta ko.
Ban san tana falon ba na shigo a cikin shiri na, nazo na roke shi zan kai yara gun baba daga csn idan an gama masu zamu dan je nakaisu yawo.
Ganin ta baisa na fasa abinda ya kawo ne ba kai tsaye na nufi kujeran da yake zaune akai na dan zauna ina cewa sannun ku da hutawa shi kadai ya amsa min nace daddy don Allah ina son zan kai yara gun baba daga can zan dai kaisu su sayo abu yan matan.
Gaba daya ke nan zaku fita dasu ko nace eh ba iya tafiya biyu shiyasa nace su shirya mu
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22Chapter 23Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32Chapter 33Chapter 34Chapter 35Chapter 36Chapter 37Chapter 38Chapter 39Chapter 40Chapter 41Chapter 42Chapter 43Chapter 44Chapter 45Chapter 46Chapter 47Chapter 48Chapter 49Chapter 50Chapter 51Chapter 52Chapter 53Chapter 54Chapter 55Chapter 56Chapter 57Chapter 58Chapter 59Chapter 60Chapter 61Chapter 62Chapter 63Chapter 64Chapter 65Chapter 66Chapter 67Chapter 68Chapter 69Chapter 70Chapter 71Chapter 72Chapter 73Chapter 74Chapter 75Chapter 76Chapter 77Chapter 78Chapter 79Chapter 80Chapter 81Chapter 82Chapter 83Chapter 84Chapter 85Chapter 86Chapter 87Chapter 88Chapter 89Chapter 90Chapter 91Chapter 92Chapter 93Chapter 94Chapter 95Chapter 96Chapter 97Chapter 98Chapter 99Chapter 100Chapter 101Chapter 102Chapter 103Chapter 104Chapter 105Chapter 106Chapter 107Chapter 108Chapter 109Chapter 110Chapter 111Chapter 112Chapter 113Chapter 114Chapter 115Chapter 116Chapter 117Chapter 118Chapter 119Chapter 120Chapter 121Chapter 122Chapter 123Chapter 124Chapter 125Chapter 126Chapter 127 Chapter 128Chapter 129Chapter 130Chapter 131Chapter 132Chapter 133Chapter 134Chapter 135Chapter 136Chapter 137Chapter 138Chapter 139Chapter 140Chapter 141Chapter 142Chapter 143Chapter 144Chapter 145Chapter 146Chapter 147Chapter 148Chapter 149Chapter 150Chapter 151Chapter 152Chapter 153