yake so na sake cewa daddy don Allah barshi yanzu Aisha zata kara mai da abincin shi yasha.
Wallahi Rahama kiji tsoron Allah in baki son Allah ya kama ki da laifin daukan alhakin wanan yaro yaro dan wata shidda da kai ace bai sha nono ya koshi ba sai wani abinci can na bature.
Ban so ba namika hannu ina karban yaron a wurin shi nace jishi dan Allah sai dan banzan tsotso dashi aikai ka baci da ci wallahi.
Komawa mukayi daga ni har shi muna dan hira yaron na shan nono yace ina yaran nace sun fita wasan ball sukace.
Yace kai yaran basa ji wallahi nace to maza ne ba a raba su da irin haka tunda ba mata bane sai dai a saka ido ga muamulan su kawai.
Sai dai haka din amma ba kwar ba dai kan don an wuce wurin kwaliyan da ba biyan kudin sabulu ai aikin banza ne yin shi.
Gaba daya muka juya inda take tsaye tana magana cikin tafiya zuwa kofan baya shi dai na dauka bai fahinci maganan ta ba amma ni sai na fara zargin anya ba daga hindatu muke samun matsala ba kuwa ?
In ba shi ba yaya tasan abinda ke tsakanin mu ni dai na san daddy ba zai taba fada mata komai ba a tsakanin mu duk yadda suke kuwa don shi ba namijin dake zama yai maganan wata matar shi da wata ba.
Tafe take tana waka mai kama da habaici kamar an dauke ta an rada a kasa ta fadi kasa tim a tsakiyan falon.
Ba karamin buguwa tayi ba ga wanan faduwan shine yace innalillahi may ye haka ya akai haka kuma sannu tashi.
Bai mike ba yana zaune inda muke yana cewa may kika taka kuma haka ya kada ke wanan faduwan haka ai sau ki karye ko ?
Allah ai ba azzalumin bawa bane don shi ba ai mai gadara in daukan alhaki abin yine kadan mutum ya fara gani a rayuwan shi.
Ina fadin haka na mike na bar wurin ban mata sannu ba ta mike da kunya ta nufi dakin ta tana cewa ban san shege yaron da ya zubar da ruwa ba a saman ties din nan kuma ?
Bai jima ba ya tafi sallah sai bayan ya dawo ne na fito don bashi abinci mun zauna yana ta latsar wayan shi har na zuba mai abincin na aje a gaban shi ya kalli abincin yace duk ni zan cinye wanan Rama ?
Kada fa nai kiba kizo kice dani na tsufa maki nan gaba ki fara dan kwanaye kwanaye kuma kina baki son zama da tsoho.
Nai dan dariya mai kama da murmushi nace ai tunda bance ma tsoho ba da farko yanzu ma bazance ba don ni din ma yanzu ai ba yarinya bace.
Muna cikin hiran sai ga ta fito daga daki tace dear kasan na fadi a gaban ka amma ko ka shiga ka dubani kaga ya jikin nawa gashi yanzu duk jikin nawa ciwo yake min wallahi.
Yace ki sha magani mana tace ni asibiti nake son zuwa aduba min kafana don ciwo yake min yace amma ba yau ba kan don dare ya yi yanzu.
Ta wani bata rai bataso haka ba taso ne ta tasa shi a gaba sukama hanya zuwa asibi a cikin daren nan ta nuna man iyakana dashi sai bai biye mata ba yace tasha magani agani zuwa gobe.
Sai da ta wuce nace dama ina son ka huta na fada ma an turo min da sako ana neman mu ranan monday wurin interview asibitin da mukai service.
Yace a, a shine baki fada min ba Rahama wanan ai ba karamin magana bane yanzu zanyi waya da MD naji yaya ake process din abin naku.
Nan a wurin ya kira sukai dan magana yace ba matsala na shigo kawai ranan monday din za a duba ai ina da kwazo sosai sun sani.
Mutum zai iya fahinta yanayin mu a lokacin yadda muke daukin junan mu sai dai ba dama komai don engine bai aiki a kaina ko kadan dan wasan da ma yakanyi da farko idan yayi yanzu sai gari ya waye mai ba lafiya a jikin shi.
Mutum zai gane yana cikin damuwa don sai matsala ya faru zaka san idan mutum yana kaunar ka baka sanin zurfin kaunar sai idan matsala ya gitta a tsakanin ku zaka gane zurfin kaunarva gare ka kasan yadda mutum ya damu da kai.
Hakane yanzu a kullun bakin daddy bai gajiya da kwantar min da hankali yana bani hakkuri kan matsalan dake faruwa damu din.
Nakan yi murmushin yake nace haba daddy bakomai mana ai matsala ne kowa yasan ta sai yace Rahama nasan ina cuta maki sosai sai dai hakkurin ki bai bari a fahinci muna da matsala ni dake.
Don da watace da yanzu duniya ta fahinci halin da muke ciki ko ansan muna da matsala wurin wanan fannin.
Wanan kwantar min da hankalin da yake yasa ban dauku matsalan nakaishi can kasan zuciya na ba sai ma kara kaimin da nayi wurin kyautata mai fiye da koda yaushe yadda wani ba zai iya fahinta ba.
Ina shiga dakin shi kullun nake da duty na kwana a ciki indai ba mun dan samu matsala bane nai fushi dashi.
Don a dakina nake yaji bana fita bana kai kara gun kowa yadda naga sunayi ban taba kai karan shi a wani ba duk zaman mu dashi na aure.
Yau ma na shirya tsab nabi bayan shi zuwa dakin hindatu da ban san may yasa idan ina duty zata dauki lokaci zaune afalo wani lokaci sai na shige zata bar falon.
Yau ma tana ganin na shige ta mike ta fada dakinta ta jawo wani roba fari can kasan kayan ta inda ta boye ta dauko wani abu mai kama da baka ta hada shi yadda takeyi kullun.
Ina shiga dakin ya fito daga wanka yana tsaye yana fesa turare a jikin shi na shigo dakin da sallama na.
Jin sallama na yasa shi dan juyowa gare ni yana murmushi yace har yaran sun kwanta ke nan nace sunyi barci tun dazun ai.
Karban turaren nayi naci gaba da fesa mashi sai bina da kallo yake yana murmushi da kada kai kawai.
Nace daddy lafiya ko naga sai wani kallo kake min ko yau injin ta samu service ne ban sani ba daidai da nake mayar da turaren a mazaunin shi yace .
Da haka zai kasance gare mu yau din aida nafi kowa farin ciki ko yaushe burina da fatana naga wanan matsalan ya tafi a gare mu.
Yace Rahama ni har yau na kasa kai karshen fahintar ki nace namay fa daddy ?
Yace baki ganewa ke kina da wani baiwa da ba kowa ne Allah keyiwa shi ba ke kanki baki sanin kina dashi sai dai na tare dake ya sanar maki da hakan.
Nace daddy wani irin baiwa ce wanan kuwa dani ban san da shi ba haka sai kai ka san shi a gare ni ?
Ya murmusa yana nufar gado yace ba yanzu zan fada maki shi ba sai nan gaba idan komai ya daidaita tsakanin mu.
Sai ya zauna a bakin gadon yace Rahama ina tausaya maki ina cutar dake a shekarun ki baki cancanci wanan hukuncin ba haka a wanan lokacin.
Rama ba zan iya boye maki ba ina tausaya maki matuka kuma don abin nawa a kwai son kai a cikin sa na kasa sama muna mafita a matsalar mu idan wani yaji haka tsawon lokacin da muka dauka a matsalan nan sai a ga na faye zama mai son kaina da yawa.
Nace haba daddy saboda may zakace haka kuma ai komai mukkadari ne daga ubangiji mutum bai dorawa kan shi lalura ai.
Yace nasan haka Rahama amma irin hakkurin da kikayi a dan tsakankanin nan ba kowa ne zai iya daure wanan irin matsalar ba haka.
Gashi ke kinyiwa wanan matsalar kankantar dauka da ace shekarun ki ya haura hakane nasan ba matsala zaki iya jure hakan har lokacin da Allah zai kawo muna mafita.
Nace ni ban damu ba daddy Allah dai ya bamu lafiya yace kwsnan zan tafi wani guri da nake kyautata zaton kila a shawon kan matsalan a can idan na tafi.
Nace daddy ban son kasawa kan ka tunane akan wanan matsalar saukin abin ma bani kadai bace a gun ka kana iya zuwa wani wajen wata kila acan ka dan samu kadace kayi.
Ni dai burina na zama mai cin wanan jerabawan da ubangiji ya aiko muna dashi bana zamo cikin masu kasa daurewa da kaddara ba.
Murmushi yayi gami da girgiza kan shi yace hakane amma wani lokaci abubuwa da dama sukan zowa bawa da sanadi don ai a gunki ne kawai wanan matsalan yake faruwa dani.
Nace dani da sauran duk a hannun ubangijin mu muke shi kadai ne kuma yasan dalilin yi hakan a gare mu don haka ka cire wanan damuwan a zuciyan ka kawai mu koma ga Allah ya kawo muna saukin alamarin.
Haka mukai ta hiran matsalar yana kankamay dani yana wasa da gashin kaina da yasha relexzer ya kwanta baya har barci yazo ya dauke mu bamu sani ba kowa da abinda zuciyar shi ke saka mai kan maganan.
Ina jin saukan numfashin shi alamar barci ne ya dan dauke mu na lalaba na mike daga saman gadon na shiga ban daki can na darji kuka na don na fahinci shima daddy yasan akwai matsala a wani wuri kamar yadda zarah ta fada min ranan.
To wa naiwa laifi yai min wanan mumunan hukuncin haka da sai mara imani zaiyiwa dan uwan shi haka a rayuwan zaman duniyan nan na dan lokaci kalilan.
Gashi na kasa fadawa inna ta matsalar da nake ciki kada hankalinta ya tashi na rasa wanda zan fadawa bayan Zarah da itama da kyat na iya fada mata komai.
Inna ce ya kamata na fadawa kuma ina jin nauyi da kunyan fadar irin magana haka a tsakanin mu ta yaya ma zan iyace mata wai miji baya iya kwanciya dani.
Don ni da farko banyi zaton wanan matsalar babba ne haka ba sai yanzu dana fahinci abin kamar ba mai karewa bane muna tunda yana iya amfani da yan uwa na ashe nice dai muke da wanan matsala din tsakanin mu.
Haka naci kuka na da tunanena nafito na koma na kwanta ban farka ba ga dan barcin dana samu sai bakwai na safe ashe hindatu nace ta kasa ta tsare taga fitowana daga dakin don haka take min wanan dabian kullun nake da girki.
Haka na daure na ci gaba da alamura na kamar kullun sai dai daddy yazo karyawa da safe sai naga ya kura min ido ban yarda mun hada ido dashi ba sai naji yace Rahama na amsa a sanyaye ban dago na kalle shi ba.
Naci gaba da abinda nakeyi yai shiru yana nazari na nazo wucewa ya riko hannuwa na abinda yasa ni dagowa na kalleshi ke nan yace dani.
Sai naga idon ki kamar kin yi kuka a daren jiya ko?
Ban tanka mashi ba sai kokarin wucewa da nake son ya sake ni nayi kawai nake da hannuna dake rike da nashi din.
Tambaya na ya sake yi na sunkuyar da kai na kasa wani irin abu nakeji a zuciyana kuka kawai nake da bukatan yi a lokacin ko zanji sanyi.
Ya sake ni ban tsaya ba na shige dakina na rufo yakai minti talatin sai gashi dakin ya shigo yazo ya tsaya kaina ya dan jima a tsaye ba tare da yai magana ba.
Sai zuwa can yace nasan kina cutuwa Rahama nima abin ya fara fin karfina don ni kadai nasan halin da nake ciki a zuciyana.
Nace ni bashi ke damuna ba gida nake son zuwa kawai na kwana biyu ko zan huta sai naji yai murmushi yace cikin wata murya Rahama kina nufin kije gida ki fada masu matsalar da muke ciki ko may ?
Muryan shi ya ban matukat tausayi a yadda yai magana yace kina ganin idan sunji wanan matsalar da muke ciki zasu barki ki zauna dani ne haka Rahama ?
Ban sake magana ba sai kukan da nakeyi shima din bai min magana ba yana dai tsaye a wurin kawai can naji ya sa kai ya fice daga dakin a gurin Aisha nake jin wai daddy ya fita.
Mikewa nayi na shiga bandaki nai wanka tare da dauro alwala na sallah raka,a biyu nakai kuka na ga Allah.
Nan na zauna naci gaba da lazumi da jero adduoi sai tunanen abubuwa da dama dayazo min a raina na zamantakewa na a gidan daddy wanda a kullun da irin matsalar da nake fuskan ta a gidan.
Nake tunane shin haka sauran mata masu kishiya suke zaune a gidanjesu dama ake ganin kamar wani dadi mace ke ji idan anga tafito tana tunkaho a waje.
Ni kan gaskiya da muguwar rawa gwanma kin tashi da a illanta min rayuwana kan kishi gara kowa ya kama gaban shi a huta hakana.
Don in anci gaba da haka watarana inaji ina gani akan rayuwana za, a koma wama ya sani ko ana hakan nice dai ban gane hakan gare ni.
Da kyat na iya tashi na shirya na fito don duba girkin da Aisha ta riga ta dora muna ba laifi na samu taimin shi yadda nake so sai dan abinda baza, a rasa ba kawai nayi.
*** *** ***
Tun bayan fitan shi daga gidan abin duniya ya damu zuciyar shi ya rasa wa zai fadawa wanan magana sai bashir ya fado mashi a rai don ya fishi sanin irin matsalolin hakan nan.
Sun gaisa sunyi komai yace Bashir wallahi akwai matsala bashir din yace subbahanallahi matsala kuma Gentle yace wallahi babba kuwa.
Nan dai yake koro mai komai har yagama yi mai bayani Bashir din ya nisa yace lalai babban matsala ne wanan.
Yace sai dai gaskiya ko ka yarda ko kada ka yarda zan fada ma gaskiya wanan abin sihiri ne wanda mata keyi a tsakanin su.
Sai dai banyi tsanmanin yanzu wayewar kai din nan ashe an saura yin irin shi abune mai wuyan sha, ani sosai don dole sai ka nemi makarun shi.
Yace a ina zan nema Bashir kafa san ni ba wai na iya irin abubuwan nan bane a rayuwana asalima naki jinin alamari da sihiri shiyasa ma ban yarda da shi ba ni.
Yace to shike nan tunda baka yarda ba Allah ya sauwaka ko yace kamar ya ban yarda ba ai magana nake fada ma yanzu kan ai dole na yarda tunda ya faru dani.
Sunyi magana yace idan ta shigo kano akwai inda zasu tafi tare dashi aji ko may yakawo hakan sukai sallama ya kashe wayan.
Monday tunda safe na shirya don zuwa inda ake neman mu wurin interview din da za, ayi ban tafi da haidar ba gida na barshi gun Aisha na dauki mota na fita.
Koda na isa na samu wa yanda aka neme mu tare sun hallara a wurin ko na shiga don gaisawa da mutanen arzikin mu.
Ban dade da zuwa ba aka kirani na shiga ba wani tambaya sosai akai min ba don sun riga da sun san mu dama don haka bamu sha wani wuya ba sun dai karbi takardun mu kawai.
Sai bayan mun dawo ne Aisha ke fada min ai akan fitina daddy sunyi fada da maman Ihisan nan dai ta labarta min komai.
Sai da na huta nafito falon don bata ma san dawowa na ba gidan sai ganina tayi falo zaune muna kallo.
Sai naji tace an dawo ta zubar dama an saba ana mazuru ana shaho may zai sa a iya zama gida tunda an riga da ansaba hurda da wasu maza.
Take naji raina ya baci sosai sai dai Allah ya taimake ni ban tankata ba tunda na gane hassada ne abin nata ba komai ba.
Sati biyu sai ga shi anturo muzo mu karbi appointment letter din mu ya fito ban bata lokaci ba na tafi na karbo inda sabon wata zamu fara aiki dasu din .
Wanan dalilin yasa na matsawa daddy kan son zuwa gida na dubo su yaso ya hana amma da na matsa yace mu shirya idan zai shiga ya sauke mu.
Take na fara shirin tafiya tsaraba sosai na hada tunda safe muka kama hanyan kano tare da shi.
Banzo da yaran ba don suna school dagani sai Aisha da baba da haidar mukazo kawai anty tai mamakin ganin mu don bata san zan shigo ba.
Duk da halin da nake ciki amma ita a idon ta taga na mata kyau ne sosai na sake na zama wata classic lady dani.
Ban dade ba a gurin ta na fita zuwa part dina inda na samu duk yayi kura dayake dare ne inda zamu kwanta muka dan gyara tunda safe muka shiga gyaran wuri da taimakon gajiye muka gyara ya zama neat.
Nan take min hira wai yanzu ai anty ta karaya sosai tana son janta a dawo irin da can baya amma ita gaskiya tana tsoron hakana don wanda ya zarge ka a baya bayan yasan halinka amma ya rufe ido yai ma sheri ita bazata zauna da ita ba.
Tace takan dai dan
Showing 324001 words to 327000 words out of 456145 words
Wallahi Rahama kiji tsoron Allah in baki son Allah ya kama ki da laifin daukan alhakin wanan yaro yaro dan wata shidda da kai ace bai sha nono ya koshi ba sai wani abinci can na bature.
Ban so ba namika hannu ina karban yaron a wurin shi nace jishi dan Allah sai dan banzan tsotso dashi aikai ka baci da ci wallahi.
Komawa mukayi daga ni har shi muna dan hira yaron na shan nono yace ina yaran nace sun fita wasan ball sukace.
Yace kai yaran basa ji wallahi nace to maza ne ba a raba su da irin haka tunda ba mata bane sai dai a saka ido ga muamulan su kawai.
Sai dai haka din amma ba kwar ba dai kan don an wuce wurin kwaliyan da ba biyan kudin sabulu ai aikin banza ne yin shi.
Gaba daya muka juya inda take tsaye tana magana cikin tafiya zuwa kofan baya shi dai na dauka bai fahinci maganan ta ba amma ni sai na fara zargin anya ba daga hindatu muke samun matsala ba kuwa ?
In ba shi ba yaya tasan abinda ke tsakanin mu ni dai na san daddy ba zai taba fada mata komai ba a tsakanin mu duk yadda suke kuwa don shi ba namijin dake zama yai maganan wata matar shi da wata ba.
Tafe take tana waka mai kama da habaici kamar an dauke ta an rada a kasa ta fadi kasa tim a tsakiyan falon.
Ba karamin buguwa tayi ba ga wanan faduwan shine yace innalillahi may ye haka ya akai haka kuma sannu tashi.
Bai mike ba yana zaune inda muke yana cewa may kika taka kuma haka ya kada ke wanan faduwan haka ai sau ki karye ko ?
Allah ai ba azzalumin bawa bane don shi ba ai mai gadara in daukan alhaki abin yine kadan mutum ya fara gani a rayuwan shi.
Ina fadin haka na mike na bar wurin ban mata sannu ba ta mike da kunya ta nufi dakin ta tana cewa ban san shege yaron da ya zubar da ruwa ba a saman ties din nan kuma ?
Bai jima ba ya tafi sallah sai bayan ya dawo ne na fito don bashi abinci mun zauna yana ta latsar wayan shi har na zuba mai abincin na aje a gaban shi ya kalli abincin yace duk ni zan cinye wanan Rama ?
Kada fa nai kiba kizo kice dani na tsufa maki nan gaba ki fara dan kwanaye kwanaye kuma kina baki son zama da tsoho.
Nai dan dariya mai kama da murmushi nace ai tunda bance ma tsoho ba da farko yanzu ma bazance ba don ni din ma yanzu ai ba yarinya bace.
Muna cikin hiran sai ga ta fito daga daki tace dear kasan na fadi a gaban ka amma ko ka shiga ka dubani kaga ya jikin nawa gashi yanzu duk jikin nawa ciwo yake min wallahi.
Yace ki sha magani mana tace ni asibiti nake son zuwa aduba min kafana don ciwo yake min yace amma ba yau ba kan don dare ya yi yanzu.
Ta wani bata rai bataso haka ba taso ne ta tasa shi a gaba sukama hanya zuwa asibi a cikin daren nan ta nuna man iyakana dashi sai bai biye mata ba yace tasha magani agani zuwa gobe.
Sai da ta wuce nace dama ina son ka huta na fada ma an turo min da sako ana neman mu ranan monday wurin interview asibitin da mukai service.
Yace a, a shine baki fada min ba Rahama wanan ai ba karamin magana bane yanzu zanyi waya da MD naji yaya ake process din abin naku.
Nan a wurin ya kira sukai dan magana yace ba matsala na shigo kawai ranan monday din za a duba ai ina da kwazo sosai sun sani.
Mutum zai iya fahinta yanayin mu a lokacin yadda muke daukin junan mu sai dai ba dama komai don engine bai aiki a kaina ko kadan dan wasan da ma yakanyi da farko idan yayi yanzu sai gari ya waye mai ba lafiya a jikin shi.
Mutum zai gane yana cikin damuwa don sai matsala ya faru zaka san idan mutum yana kaunar ka baka sanin zurfin kaunar sai idan matsala ya gitta a tsakanin ku zaka gane zurfin kaunarva gare ka kasan yadda mutum ya damu da kai.
Hakane yanzu a kullun bakin daddy bai gajiya da kwantar min da hankali yana bani hakkuri kan matsalan dake faruwa damu din.
Nakan yi murmushin yake nace haba daddy bakomai mana ai matsala ne kowa yasan ta sai yace Rahama nasan ina cuta maki sosai sai dai hakkurin ki bai bari a fahinci muna da matsala ni dake.
Don da watace da yanzu duniya ta fahinci halin da muke ciki ko ansan muna da matsala wurin wanan fannin.
Wanan kwantar min da hankalin da yake yasa ban dauku matsalan nakaishi can kasan zuciya na ba sai ma kara kaimin da nayi wurin kyautata mai fiye da koda yaushe yadda wani ba zai iya fahinta ba.
Ina shiga dakin shi kullun nake da duty na kwana a ciki indai ba mun dan samu matsala bane nai fushi dashi.
Don a dakina nake yaji bana fita bana kai kara gun kowa yadda naga sunayi ban taba kai karan shi a wani ba duk zaman mu dashi na aure.
Yau ma na shirya tsab nabi bayan shi zuwa dakin hindatu da ban san may yasa idan ina duty zata dauki lokaci zaune afalo wani lokaci sai na shige zata bar falon.
Yau ma tana ganin na shige ta mike ta fada dakinta ta jawo wani roba fari can kasan kayan ta inda ta boye ta dauko wani abu mai kama da baka ta hada shi yadda takeyi kullun.
Ina shiga dakin ya fito daga wanka yana tsaye yana fesa turare a jikin shi na shigo dakin da sallama na.
Jin sallama na yasa shi dan juyowa gare ni yana murmushi yace har yaran sun kwanta ke nan nace sunyi barci tun dazun ai.
Karban turaren nayi naci gaba da fesa mashi sai bina da kallo yake yana murmushi da kada kai kawai.
Nace daddy lafiya ko naga sai wani kallo kake min ko yau injin ta samu service ne ban sani ba daidai da nake mayar da turaren a mazaunin shi yace .
Da haka zai kasance gare mu yau din aida nafi kowa farin ciki ko yaushe burina da fatana naga wanan matsalan ya tafi a gare mu.
Yace Rahama ni har yau na kasa kai karshen fahintar ki nace namay fa daddy ?
Yace baki ganewa ke kina da wani baiwa da ba kowa ne Allah keyiwa shi ba ke kanki baki sanin kina dashi sai dai na tare dake ya sanar maki da hakan.
Nace daddy wani irin baiwa ce wanan kuwa dani ban san da shi ba haka sai kai ka san shi a gare ni ?
Ya murmusa yana nufar gado yace ba yanzu zan fada maki shi ba sai nan gaba idan komai ya daidaita tsakanin mu.
Sai ya zauna a bakin gadon yace Rahama ina tausaya maki ina cutar dake a shekarun ki baki cancanci wanan hukuncin ba haka a wanan lokacin.
Rama ba zan iya boye maki ba ina tausaya maki matuka kuma don abin nawa a kwai son kai a cikin sa na kasa sama muna mafita a matsalar mu idan wani yaji haka tsawon lokacin da muka dauka a matsalan nan sai a ga na faye zama mai son kaina da yawa.
Nace haba daddy saboda may zakace haka kuma ai komai mukkadari ne daga ubangiji mutum bai dorawa kan shi lalura ai.
Yace nasan haka Rahama amma irin hakkurin da kikayi a dan tsakankanin nan ba kowa ne zai iya daure wanan irin matsalar ba haka.
Gashi ke kinyiwa wanan matsalar kankantar dauka da ace shekarun ki ya haura hakane nasan ba matsala zaki iya jure hakan har lokacin da Allah zai kawo muna mafita.
Nace ni ban damu ba daddy Allah dai ya bamu lafiya yace kwsnan zan tafi wani guri da nake kyautata zaton kila a shawon kan matsalan a can idan na tafi.
Nace daddy ban son kasawa kan ka tunane akan wanan matsalar saukin abin ma bani kadai bace a gun ka kana iya zuwa wani wajen wata kila acan ka dan samu kadace kayi.
Ni dai burina na zama mai cin wanan jerabawan da ubangiji ya aiko muna dashi bana zamo cikin masu kasa daurewa da kaddara ba.
Murmushi yayi gami da girgiza kan shi yace hakane amma wani lokaci abubuwa da dama sukan zowa bawa da sanadi don ai a gunki ne kawai wanan matsalan yake faruwa dani.
Nace dani da sauran duk a hannun ubangijin mu muke shi kadai ne kuma yasan dalilin yi hakan a gare mu don haka ka cire wanan damuwan a zuciyan ka kawai mu koma ga Allah ya kawo muna saukin alamarin.
Haka mukai ta hiran matsalar yana kankamay dani yana wasa da gashin kaina da yasha relexzer ya kwanta baya har barci yazo ya dauke mu bamu sani ba kowa da abinda zuciyar shi ke saka mai kan maganan.
Ina jin saukan numfashin shi alamar barci ne ya dan dauke mu na lalaba na mike daga saman gadon na shiga ban daki can na darji kuka na don na fahinci shima daddy yasan akwai matsala a wani wuri kamar yadda zarah ta fada min ranan.
To wa naiwa laifi yai min wanan mumunan hukuncin haka da sai mara imani zaiyiwa dan uwan shi haka a rayuwan zaman duniyan nan na dan lokaci kalilan.
Gashi na kasa fadawa inna ta matsalar da nake ciki kada hankalinta ya tashi na rasa wanda zan fadawa bayan Zarah da itama da kyat na iya fada mata komai.
Inna ce ya kamata na fadawa kuma ina jin nauyi da kunyan fadar irin magana haka a tsakanin mu ta yaya ma zan iyace mata wai miji baya iya kwanciya dani.
Don ni da farko banyi zaton wanan matsalar babba ne haka ba sai yanzu dana fahinci abin kamar ba mai karewa bane muna tunda yana iya amfani da yan uwa na ashe nice dai muke da wanan matsala din tsakanin mu.
Haka naci kuka na da tunanena nafito na koma na kwanta ban farka ba ga dan barcin dana samu sai bakwai na safe ashe hindatu nace ta kasa ta tsare taga fitowana daga dakin don haka take min wanan dabian kullun nake da girki.
Haka na daure na ci gaba da alamura na kamar kullun sai dai daddy yazo karyawa da safe sai naga ya kura min ido ban yarda mun hada ido dashi ba sai naji yace Rahama na amsa a sanyaye ban dago na kalle shi ba.
Naci gaba da abinda nakeyi yai shiru yana nazari na nazo wucewa ya riko hannuwa na abinda yasa ni dagowa na kalleshi ke nan yace dani.
Sai naga idon ki kamar kin yi kuka a daren jiya ko?
Ban tanka mashi ba sai kokarin wucewa da nake son ya sake ni nayi kawai nake da hannuna dake rike da nashi din.
Tambaya na ya sake yi na sunkuyar da kai na kasa wani irin abu nakeji a zuciyana kuka kawai nake da bukatan yi a lokacin ko zanji sanyi.
Ya sake ni ban tsaya ba na shige dakina na rufo yakai minti talatin sai gashi dakin ya shigo yazo ya tsaya kaina ya dan jima a tsaye ba tare da yai magana ba.
Sai zuwa can yace nasan kina cutuwa Rahama nima abin ya fara fin karfina don ni kadai nasan halin da nake ciki a zuciyana.
Nace ni bashi ke damuna ba gida nake son zuwa kawai na kwana biyu ko zan huta sai naji yai murmushi yace cikin wata murya Rahama kina nufin kije gida ki fada masu matsalar da muke ciki ko may ?
Muryan shi ya ban matukat tausayi a yadda yai magana yace kina ganin idan sunji wanan matsalar da muke ciki zasu barki ki zauna dani ne haka Rahama ?
Ban sake magana ba sai kukan da nakeyi shima din bai min magana ba yana dai tsaye a wurin kawai can naji ya sa kai ya fice daga dakin a gurin Aisha nake jin wai daddy ya fita.
Mikewa nayi na shiga bandaki nai wanka tare da dauro alwala na sallah raka,a biyu nakai kuka na ga Allah.
Nan na zauna naci gaba da lazumi da jero adduoi sai tunanen abubuwa da dama dayazo min a raina na zamantakewa na a gidan daddy wanda a kullun da irin matsalar da nake fuskan ta a gidan.
Nake tunane shin haka sauran mata masu kishiya suke zaune a gidanjesu dama ake ganin kamar wani dadi mace ke ji idan anga tafito tana tunkaho a waje.
Ni kan gaskiya da muguwar rawa gwanma kin tashi da a illanta min rayuwana kan kishi gara kowa ya kama gaban shi a huta hakana.
Don in anci gaba da haka watarana inaji ina gani akan rayuwana za, a koma wama ya sani ko ana hakan nice dai ban gane hakan gare ni.
Da kyat na iya tashi na shirya na fito don duba girkin da Aisha ta riga ta dora muna ba laifi na samu taimin shi yadda nake so sai dan abinda baza, a rasa ba kawai nayi.
*** *** ***
Tun bayan fitan shi daga gidan abin duniya ya damu zuciyar shi ya rasa wa zai fadawa wanan magana sai bashir ya fado mashi a rai don ya fishi sanin irin matsalolin hakan nan.
Sun gaisa sunyi komai yace Bashir wallahi akwai matsala bashir din yace subbahanallahi matsala kuma Gentle yace wallahi babba kuwa.
Nan dai yake koro mai komai har yagama yi mai bayani Bashir din ya nisa yace lalai babban matsala ne wanan.
Yace sai dai gaskiya ko ka yarda ko kada ka yarda zan fada ma gaskiya wanan abin sihiri ne wanda mata keyi a tsakanin su.
Sai dai banyi tsanmanin yanzu wayewar kai din nan ashe an saura yin irin shi abune mai wuyan sha, ani sosai don dole sai ka nemi makarun shi.
Yace a ina zan nema Bashir kafa san ni ba wai na iya irin abubuwan nan bane a rayuwana asalima naki jinin alamari da sihiri shiyasa ma ban yarda da shi ba ni.
Yace to shike nan tunda baka yarda ba Allah ya sauwaka ko yace kamar ya ban yarda ba ai magana nake fada ma yanzu kan ai dole na yarda tunda ya faru dani.
Sunyi magana yace idan ta shigo kano akwai inda zasu tafi tare dashi aji ko may yakawo hakan sukai sallama ya kashe wayan.
Monday tunda safe na shirya don zuwa inda ake neman mu wurin interview din da za, ayi ban tafi da haidar ba gida na barshi gun Aisha na dauki mota na fita.
Koda na isa na samu wa yanda aka neme mu tare sun hallara a wurin ko na shiga don gaisawa da mutanen arzikin mu.
Ban dade da zuwa ba aka kirani na shiga ba wani tambaya sosai akai min ba don sun riga da sun san mu dama don haka bamu sha wani wuya ba sun dai karbi takardun mu kawai.
Sai bayan mun dawo ne Aisha ke fada min ai akan fitina daddy sunyi fada da maman Ihisan nan dai ta labarta min komai.
Sai da na huta nafito falon don bata ma san dawowa na ba gidan sai ganina tayi falo zaune muna kallo.
Sai naji tace an dawo ta zubar dama an saba ana mazuru ana shaho may zai sa a iya zama gida tunda an riga da ansaba hurda da wasu maza.
Take naji raina ya baci sosai sai dai Allah ya taimake ni ban tankata ba tunda na gane hassada ne abin nata ba komai ba.
Sati biyu sai ga shi anturo muzo mu karbi appointment letter din mu ya fito ban bata lokaci ba na tafi na karbo inda sabon wata zamu fara aiki dasu din .
Wanan dalilin yasa na matsawa daddy kan son zuwa gida na dubo su yaso ya hana amma da na matsa yace mu shirya idan zai shiga ya sauke mu.
Take na fara shirin tafiya tsaraba sosai na hada tunda safe muka kama hanyan kano tare da shi.
Banzo da yaran ba don suna school dagani sai Aisha da baba da haidar mukazo kawai anty tai mamakin ganin mu don bata san zan shigo ba.
Duk da halin da nake ciki amma ita a idon ta taga na mata kyau ne sosai na sake na zama wata classic lady dani.
Ban dade ba a gurin ta na fita zuwa part dina inda na samu duk yayi kura dayake dare ne inda zamu kwanta muka dan gyara tunda safe muka shiga gyaran wuri da taimakon gajiye muka gyara ya zama neat.
Nan take min hira wai yanzu ai anty ta karaya sosai tana son janta a dawo irin da can baya amma ita gaskiya tana tsoron hakana don wanda ya zarge ka a baya bayan yasan halinka amma ya rufe ido yai ma sheri ita bazata zauna da ita ba.
Tace takan dai dan
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22Chapter 23Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32Chapter 33Chapter 34Chapter 35Chapter 36Chapter 37Chapter 38Chapter 39Chapter 40Chapter 41Chapter 42Chapter 43Chapter 44Chapter 45Chapter 46Chapter 47Chapter 48Chapter 49Chapter 50Chapter 51Chapter 52Chapter 53Chapter 54Chapter 55Chapter 56Chapter 57Chapter 58Chapter 59Chapter 60Chapter 61Chapter 62Chapter 63Chapter 64Chapter 65Chapter 66Chapter 67Chapter 68Chapter 69Chapter 70Chapter 71Chapter 72Chapter 73Chapter 74Chapter 75Chapter 76Chapter 77Chapter 78Chapter 79Chapter 80Chapter 81Chapter 82Chapter 83Chapter 84Chapter 85Chapter 86Chapter 87Chapter 88Chapter 89Chapter 90Chapter 91Chapter 92Chapter 93Chapter 94Chapter 95Chapter 96Chapter 97Chapter 98Chapter 99Chapter 100Chapter 101Chapter 102Chapter 103Chapter 104Chapter 105Chapter 106Chapter 107Chapter 108Chapter 109 Chapter 110Chapter 111Chapter 112Chapter 113Chapter 114Chapter 115Chapter 116Chapter 117Chapter 118Chapter 119Chapter 120Chapter 121Chapter 122Chapter 123Chapter 124Chapter 125Chapter 126Chapter 127Chapter 128Chapter 129Chapter 130Chapter 131Chapter 132Chapter 133Chapter 134Chapter 135Chapter 136Chapter 137Chapter 138Chapter 139Chapter 140Chapter 141Chapter 142Chapter 143Chapter 144Chapter 145Chapter 146Chapter 147Chapter 148Chapter 149Chapter 150Chapter 151Chapter 152Chapter 153