ta shiga dukan kofan mu da karfi amma ko motsi Inna batayi ba ga wani katon dutse da tasa ta kare kofan dashi.
Ranan inna tasha zagi gurin mama shima baba yazo ya buga amma taki budewa ban san ya suka karasa ba da yarasu yan so a gidan mudai basu kwana ba a dakin mu.
Haka na kwana da wanan damuwan a rana washe gari tun da farar safiya na fito daga dakin da nake mu dana kwana.
Ina alwala naji mama na tayar dasu Lawisa wai su fito kada beraye su kashe su a dakin wai sun kwana suna ihun bera.
Dariya ya kumay ni daga inda nake nace farau da dadi ramuwa da ciwo ke nan tai min taji dadi yanzu an mata wai taji zafi.
Baba da ya dawo daga sallah dakin mu ya fado yanawa Inna fada wai bata kyauta ba da ta rufe dakin ta inda yake shiga ba nan yake fita ba.
Har ya gaji ya juya ya fita daga dakin don kan sa ba wanda ya kula shi.
Na fito ina shara naga fitowan Inna daga dakin saye cikin zumbudeden hijjab din ta na sallah idanuwan ta yana fitar da hawaye.
Kai tsaye na fahinci manufarta da sauri na yada tsintsiyar dake hannuna na nufe ta tare da shan gaban ta na riko mata hijjab din ta.
Allah ya taimake ni duk suna daki a lokacin nace inna ina zaki ?
Inna ta juyo idon ta yana zubar da hawaye cikin raunaniyar murya take ce min.
Yarinya bari na tafi gidan mu na gaji da wanan tauye incin da ake min a gidan nan haka.
Take nawa idanuwan suka kawo ruwa a lokaci daya ganin yadda Inna ke zubar da hawaye ga nata idon.
Nace Inna may zai sa ki tafi a lokacin da nafi bukatan ki a kusa dani ?
Hannun ta na kama sai naga bata mussa min ba na jata muka koma dakin mu ni da ita.
Sai bayan mun shiga naji motsi a tsakar gida ashe mama ce tafito don ta hura wutan kunu.
Nace haba Inna may zai sa ki bari shedan ya rude ki a daidai lokacin da mukafi bukatan zaman ki a gidan nan a tare da mu.
Don Allah inna kiyi hakkuri hakan mama ta dade tana son gani daga gareki.
Inna sai kuma da komai ya kusa kai karshe zakice zaki fice kibar mata gida taji dadin gallazawa rayuwan mu yadda take so.
Kiyi hakkuri Inna wata rana sai labari insha Allahu.
Kallona Inna take yadda karama dani nake jero mata wanan maganan haka.
Zama naga tayi bakin gadon ta sai da ta share hawayen dake fuskan ta hakan ya nuna min tayi taushi ga magana na.
Tace haba yarinya da za, a daina da zuwa yanzu yaci su daina sai abu yai dan sauki sai kuma abu ya sake dawowa sabo.
Ni wallahi nagaji nagaji wallahi duk haihuwan da nayi a gidan nan nayi shi ne bisa rantsatsen rabo kawai amma ba da son raina ba.
Nace cikin sanyin murya inna ki dai yi hakkuri ko dan darajan mu don Allah.
Cikin fushi tace dani yarinya ina son na kwaci inci mune a gidan nan daga ni har ku an mayar damu kamar wasu bayi can a gidan nan bamu da incin kan mu ko kadan.
Nace ki dai dan kara hakkuri inna don Allah komai da sanin ubangji akeyin sa baki san tana din da Allah yai ma hakkurin mu ba.
Shiru tayi tana nazari niko ina tsaye na kura mata ido cikin tausayi nasan Inna tana matukar hakkuri agidan mu sosai.
Na share hawaye nace inna ki saki ranki kamar komai bai damay ki ba zakiga mama abin ya kuma koma mata ciki.
Ai ance mace ko a dakin ta tana yaji ko ?
Gashi naga kin fara daukan wa kanki fansa a gare su ai basu taba tsan manin zaki iya masu haka ba da kikeyi yanzu.
Nan dai nai ta bata hakkuri har na samu ta sauko naga ta dan sake jikin ta muryan mama ce ke cewa ina mai sharan nan take ne kin bar shara iska zai kwashe.
Sai ji nayi Inna na fadi aiki take min a daki a sa wasu su share ba ita kadai bace ai a gidan.
Nace a raina taufa ance mai hakkuri dama bai iya fushi ba mama zata kai inna ga bango ke nan.
Muna nan zaune wani dabara ya fado min a raina na saurin daukan hijjab dina nace wa Inna ta ina zuwa na fice daga gidan.
Kofan gida na koma na tsaya ban dade ba naga baba ya fito gaidashi nayi yana kallona yace Rahama may kike a wanan gurin da sanyin safiyan nan haka ?
Nace baba kai nake dako kafito akwai maganan da nake son muyi dakai ne.
Kallon mamaki ne yai min nakai durkushe a gaban shi nace don Allah baba alfarma nake nemawa inna ta akan zaman su da mama a gidan nan.
Duk zaman da suke na kishi a tsakanin su baba ba wai lalai bane sai ka saka bakin ka a ciki tunda kai ba mazauni gida bane baka san waina da ake toyawa ba a bayan fitan ka.
Kallona yake cikin mamaki yace Rahama har ankai lokacin da za ki tari gabana akan maganan uwayen ki.
Nai saurin cewa baba ba hakana bane yaune naga inna har ta shirya wai zata bar gidan bata iyawa ta gaji da abinda ake mata shine nace bari nai magana.
Yanzun haka wallahi inna batasan zan yi wanan maganan da kai ba ma hakkuri dai nake baka baba ko dan darajan mu a tsakanin ku ka rangwanta ma rayuwan ta hakana.
Shiru yayi kamar mai nazarina can yace naji amma ita Asiya ne yau har tai niyar yaji ?
Nace kwarai kuwa baba Allah ya gyara ni kadaine a waje na tare ta data fice daga gidan.
Yace to jeki naji Allah yai maki albarka idan nadawo zanga ita innar taki zamuyi magana da ita na fahinta nace baba nagode Allah ya kara rufa asiri.
Ya wuce na juya na shiga gida zuciyana fes na san ko ba komai killa Allah ya kusa kawo muna saukin al, amarin mu ne a gidan.
****** ********* ******
Tun daga wanan lokacin da mukai magana da babana ta fahinta naga al, amura sunyi wa inna sauki sosai ba inna kawai ba har ma diyan ta da akewa kahonzuka a gidan mun dan samu saida sosai.
Ya zuwa yanzu ba karamin alheri Garbati yake kawowa ba gidan mu wani naci wani kuma dangin tufafi ne duk ba, a tabawa sai gurin mama altine ake boyewa.
Cikin hakane na roke shi yai hakkuri har na zana jerabawa na na karshe kafin ayi bukina dashi.
Da kyat na samu ya amince min wanda zuwa lokacin har labarin zancen aure na dashi yabi gari wanda mama ce da diyan ta suke yada zancen a gari.
Don mama har iyalin shi sai da ta fada masu irin alherin da yake kawo muna gidan mu .
Wai yanzu duk neman shi a kaina yake karewa komai kawo muna yake dani da uwata idan anga yadda muka koma wasu bulbul damu don mun samu ya rike muna kan maciji muna wasa da bindin shi.
Haka yasa matan shi suka tayar da hankalin su su basu yarda ba ya dauko masu yar jikan su a matsayin kishiyar su mafarin nazo ina masu rashin kunya a cikin gida.
Yace shi ra, ayin shi ke nan mai zama ta zauna wacce bata iyawa hanya a bude yake mata.
GNin da gaske yakeyi yasa suka kama kan su bayan ya saka masu waigi ga zancen da cewa.
Kada yaji wani ko wata yaiwa yarinyar nan ko iyayyen ta wani sheri zai dauki mumunan mataki akan ko waye a gidan.
Dole suka saka mai ido ba yadda zasuyi namiji idan yaso abu kunya fice mai yake a idon shi.
Mama altine ta tafi birni ganin anty da tadawo daga waje ganin likita akan matsalan ciwon ta.
Sai washe gari bayan ta huta anty ke tambayan ta wai mama ina Rama na take tana nan tana karatun ko ?
Mama tace wani karatu Sa, ade Raman ki kan aure zatayi bada dadewan nan ba.
Haba mama wani aure yarinya kamar Rama kuma ?
To ai sai kiyi Rahama kan har an kawo sadakin ta itace ma ta hudu a gidan mijin ta.
Anty dake kwance tace what ?
Mama wai da gake kike ko wasa tace ina wasa dake ne balle na fada maki wasa.
Uban ta yaba da ita ga wani tsohon maikudi na garin mu aure yanzu haka karatun data kwallafawa raine ya hana ayi bukin kin san ta samu sa, a don kokarin ta an kaita gaba yanzu bana zata fita daga makarantan ma.
Ran anty yai matukar baci dajin wanan labarin da tayi na zancen aure na nan dai mama ta koro mata komai akan zancen.
Na bata matukar tausayi tace mama in ba abin kauye ba ko mu da mukai aure da girman mu yaya muka kwashe da kaidin kishiya balle yarinya karama akaita cikin guzamay mata haka ?
Mama tace mu a kauye ai hakan ba komai bane gare mu amma duk da haka Rahama tayi kankanta kwarai agidan nan.
Da mama zata dawo sakon zannuwan gado da sauran kayan aiki dasu kudi anty ta bayar akawo na shagalin buki na wanda baifi wata biyu ba ayi yanzu.
Harda yan din kuna kala biyar da sauran abubuwa duk ta hado min tace aba Inna hakkuri saboda jikin ta bata samun zuwa bukin .
Amma idan ta samu lafiya zata zo taga dakina daga baya insha Allahu.
Mama tace kice wanan tafiyan na Rahama ne nayi ai taso ta biyoni sosai amma nasan mahaifinta ba zai yarda ba shiyasa na bata hakkuri.
Da mama ta dawo daga birni sai washe gari muka shiga taron ta don da dare ta iso garin.
Ai nan ta baje muna sakon anty na muna kallo wani abin ma ni ban san yadda za, ai amfani dashi ba agidan.
Ban san lokacin da na dunkule na fara kuka ba da kyat mama ta lalashe ni na wanke fuska na.
Sai da naje gida nake labartawa Inna ta abinda ya faru ta rike baki cikin mamaki tana cewa kai wanan boyar Allah ni ban san abinda zan saka mata dashi ba a duniyan nan ?
Mama ko sai gori take sake muna da habaici wai rana bata karya sai dai uwar diya tai kunya.
Daga uwar har uban sai kudi ake ci amma ko roba ba asai wa yarinya ba na aure .
Su dai gasu gani wai an bizzine tsohuwa da ranta suga yadda za afita kunya duk tallan da nayi Inna ta kasa saye min wani abin kwarai.
Dama tayi haka ne don ta kure inna don tasan ba, a aje min komai na aure ba a yanzu tunda mun sakakance cewa ni
boko zanyi ba aure ba yanzu.
To yanzu ga aure ya taso suga ta tsiya tasan dai gidan su Inna ba wata tsiya zasu barkata min ba don suma nema sukeyi.
Magana duk yabi gari inna bata aje min komai ba ga aure ya taso ba abin kaiwa gidan miji.
Lokaci ko kamar jira yake sai kara matsowa yake niko sai karatun jerabawa na dake gabana nakeyi kawai.
Ba abinda yai min tsinanen zafi akan maganan mama da diyan ta a gidan mu.
Garbati yasa aka gina min daki mai girma da fadi yadda zai isheni aka kewaye shiyan daban cikin na iyalin shi can gefe daya an shafa farar kasa yaji sai kyali yakeyi.
Haka ya kara bankantawa iyalin shi rai sosai har suka so tayar da hankalin su.
Amma da ya basu dan wani abu suma suyi gyara sai baki ya mutu murus kowa ta shiga sha, anin gaban ta da diyan ta amma kishin yana nan daram a ran su.
Duk inda yabi sai ba, a ake mai na ya fado gari ya zarta maza zai bare yarinyar dalleliya a ledan ta sai ya washe baki cikin jin dadi yana dariya.
Mama ko sai auki fadawa mutane karya da gaskiya takeyi akan zancen bukin tana zunden inna ta.
Inna ta duk tabi ta ramay sai dan wuya daga ita sai uwar dakin ta mama altine suke shirin bukin sai yan uwan su tsiraru da sukaji suka gani.
Ko su ba wai sun san shirin da Inna da mama altine sukayi min bane haka ake tafiyan a dunkule.
Gaba daya daga inna har baba babu wani mai kwanciyan hankali dama ma inna dake nuna halin ko in kula da bukin.
Idan ka cire mama da yaran ta wanda su ko a kwalar rigan su bai shafe su ba.
Ta dai zuga shi ya zugu yanzu kuma ta saka mai ido yaji kunya dan kudin sadakina da aka kawo dashi ne yake kokarin sayen komai.
Na dan gadon katakon da za, a sai min ma ya gagara daga karshe ganin haka tasa inna dabaran cewa yaba mama altine kudin ta shiga birni ko na hannu ne ta sayo min.
Tayi hakane don idan kudin ya shiga hannun su sai su san dabara mama altine ne ce ta koya mata wannan dabaran.
Baiki shawaran Inna ba tamika masu dan abinda ya saura takaiwa mama altine ta shirya sai birni da kudin daga karshe anty ce ta cika aka sayi min saitin gado da dan wardrove da katifa har da karin tarkace.
Wanan matar ba abinda zamuce mata sai dai Allah ya bata lafiya ya shirya mata zurian ta da albarkan sa kawai.
Ganin babu komai a dakin inna ta yasa mama ta samu baba da zancen da yamma bayan ya dawo gida take cewa.
Yanzu malam kana ganin haka zaku kai yarinyar na aure babban gida irin haka babu komai da uwarta ta tana da mata na fita kunya kaima sai nake ganin a furin ka hakan ne ?
Baba da yanzu ya fahinci mama so take taga wallen shi kuma tasan sirin abin sai ya boye mata ba su mama kudin sadakin da yayi yace anyi auren ne ko kikaga uwarta ta kaita hakana ?
Haka yasa taji haushi taja bakin ta ta tsuke ta bar zancen sai ido tana cewa ni dama taimakon ku naso nayi ko mu tafi gida tumba dillaliya adan samu abinda aka tsintar mata gurin ta in yaso bayan bukin abinda aka samu sai abata kudin ta.
Baba yace ko tabarma Allah ya hore mata daga gare ni sai na kaita dashi .
Yafice abin shi gidan ya barta nan tana mashi dariyar mumuke ta baya tana an daiji kunya wallahi anyi shigewa ai ciki amma ba, a iya fitar da yarinya kunya.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE NA FADA IDAN BAKI BIYA BA KIKA KARANTA MIN NOVEL NA BARKI GA ALLAH.
IDAN KIN BIYA KIKA TURA MIN NOVEL WANI GROUP KO KIKA BA WA WANDA BAI BIYA BA KE MA NA BARKI GA ALLAH DON KINCI AMANATA ALLAH ZAI SAKA MIN A KAN INSHA ALLAHU WACE TASAN BAZATA IYA RIKE AMANA BA DON ALLAH TAI MAGANA NA BATA KUDIN TA TAFITA MIN GROUP DON AMANA NAUYI GARE SHI ABINDA KA RAINA SAI YA HANAKA KETARE SIRADI GOBE KIYAMA ALLAH YA BAMU IKON RIKON AMANA A TSAKANIN MU.
DON NAGA NOVEL DINA A WANI GROUP KUMA NASAN WACE TA FITAR DON BATAI MAGANA BA NA BARTA GA ALLAH DON ALLAH SHEDA NE GA ALKAWARIN MU DA KU, ,
6
Ranan da na zana jerabawan karshe na na secondarya rana ce da ya kamata nai mafarin ciki a raina don kowa ka gani a cikin mu yana cikin farin ciki da jin dadi a ran shi.
Sai dai ni a gareni sabanin hakane don ya kasance min kamar rana na bakin ciki a gare ni.
Lokaci daya yanayi na ya sauya min naji duniya tai min kunci a raina komai ganin sa nake yai min baki a raina a dalilin tunawan da nayi wanan jin dadin rayuwan ya kusa yanke min.
Don wanan auren jarabtan da na tsinci rayuwana dashi na auren tsoho da mahaifina zai min a lokaci daya haka, batare da yai la, akari da irin rayuwan da zanje gidan miji na tarar.
Wanda yau baifi saura kwana goma ba naje gidan Alhaji garbati a matsayin matar auren shi nima a gidan.
Juyawa nayi zuwa staff room don nai sallama da malam mutumin da yai tsaye a kaina har nakai wanan matsayin na yau a gare ni.
Malam yana ganina yace a, a Rahama an kanmala ko ?
Maimakon na nuna farin ciki na sai na kai durkushe a gaban shi na fara kuka yace subbahanallahi Rahama lafiya dai ko ?
Cikin kuka nafara cewa malam nazo ne nai maku godiya akan tsaya min da kukayi har na kai ga wanan ranan ga karatuna.
Sai dai kuma gashi guri na ba zai kai na zama likitan da nake son zama ba na taimakawa yan garin mu kamar yadda nake da gurin haka a rayuwana.
Mahaifina ya yanke min wanan gurin nawa ta bayar dani aure ga wanda yaso yau saura kwana goma ayi bikina akaini.
Subbahanallahi inji malam yace yaushe haka ya faru kuma Rahama waye kuma miji ?
Sai na dan kakaro murmushi a fuskana nakw cewa malam an kwana biyu da hakan ba kuma kowa bane mijin sai Alhaji Garbati dan bida na garin nan.
Shi da sauran malamai da suke saurare na cikin tausayi
Showing 18001 words to 21000 words out of 456145 words
Ranan inna tasha zagi gurin mama shima baba yazo ya buga amma taki budewa ban san ya suka karasa ba da yarasu yan so a gidan mudai basu kwana ba a dakin mu.
Haka na kwana da wanan damuwan a rana washe gari tun da farar safiya na fito daga dakin da nake mu dana kwana.
Ina alwala naji mama na tayar dasu Lawisa wai su fito kada beraye su kashe su a dakin wai sun kwana suna ihun bera.
Dariya ya kumay ni daga inda nake nace farau da dadi ramuwa da ciwo ke nan tai min taji dadi yanzu an mata wai taji zafi.
Baba da ya dawo daga sallah dakin mu ya fado yanawa Inna fada wai bata kyauta ba da ta rufe dakin ta inda yake shiga ba nan yake fita ba.
Har ya gaji ya juya ya fita daga dakin don kan sa ba wanda ya kula shi.
Na fito ina shara naga fitowan Inna daga dakin saye cikin zumbudeden hijjab din ta na sallah idanuwan ta yana fitar da hawaye.
Kai tsaye na fahinci manufarta da sauri na yada tsintsiyar dake hannuna na nufe ta tare da shan gaban ta na riko mata hijjab din ta.
Allah ya taimake ni duk suna daki a lokacin nace inna ina zaki ?
Inna ta juyo idon ta yana zubar da hawaye cikin raunaniyar murya take ce min.
Yarinya bari na tafi gidan mu na gaji da wanan tauye incin da ake min a gidan nan haka.
Take nawa idanuwan suka kawo ruwa a lokaci daya ganin yadda Inna ke zubar da hawaye ga nata idon.
Nace Inna may zai sa ki tafi a lokacin da nafi bukatan ki a kusa dani ?
Hannun ta na kama sai naga bata mussa min ba na jata muka koma dakin mu ni da ita.
Sai bayan mun shiga naji motsi a tsakar gida ashe mama ce tafito don ta hura wutan kunu.
Nace haba Inna may zai sa ki bari shedan ya rude ki a daidai lokacin da mukafi bukatan zaman ki a gidan nan a tare da mu.
Don Allah inna kiyi hakkuri hakan mama ta dade tana son gani daga gareki.
Inna sai kuma da komai ya kusa kai karshe zakice zaki fice kibar mata gida taji dadin gallazawa rayuwan mu yadda take so.
Kiyi hakkuri Inna wata rana sai labari insha Allahu.
Kallona Inna take yadda karama dani nake jero mata wanan maganan haka.
Zama naga tayi bakin gadon ta sai da ta share hawayen dake fuskan ta hakan ya nuna min tayi taushi ga magana na.
Tace haba yarinya da za, a daina da zuwa yanzu yaci su daina sai abu yai dan sauki sai kuma abu ya sake dawowa sabo.
Ni wallahi nagaji nagaji wallahi duk haihuwan da nayi a gidan nan nayi shi ne bisa rantsatsen rabo kawai amma ba da son raina ba.
Nace cikin sanyin murya inna ki dai yi hakkuri ko dan darajan mu don Allah.
Cikin fushi tace dani yarinya ina son na kwaci inci mune a gidan nan daga ni har ku an mayar damu kamar wasu bayi can a gidan nan bamu da incin kan mu ko kadan.
Nace ki dai dan kara hakkuri inna don Allah komai da sanin ubangji akeyin sa baki san tana din da Allah yai ma hakkurin mu ba.
Shiru tayi tana nazari niko ina tsaye na kura mata ido cikin tausayi nasan Inna tana matukar hakkuri agidan mu sosai.
Na share hawaye nace inna ki saki ranki kamar komai bai damay ki ba zakiga mama abin ya kuma koma mata ciki.
Ai ance mace ko a dakin ta tana yaji ko ?
Gashi naga kin fara daukan wa kanki fansa a gare su ai basu taba tsan manin zaki iya masu haka ba da kikeyi yanzu.
Nan dai nai ta bata hakkuri har na samu ta sauko naga ta dan sake jikin ta muryan mama ce ke cewa ina mai sharan nan take ne kin bar shara iska zai kwashe.
Sai ji nayi Inna na fadi aiki take min a daki a sa wasu su share ba ita kadai bace ai a gidan.
Nace a raina taufa ance mai hakkuri dama bai iya fushi ba mama zata kai inna ga bango ke nan.
Muna nan zaune wani dabara ya fado min a raina na saurin daukan hijjab dina nace wa Inna ta ina zuwa na fice daga gidan.
Kofan gida na koma na tsaya ban dade ba naga baba ya fito gaidashi nayi yana kallona yace Rahama may kike a wanan gurin da sanyin safiyan nan haka ?
Nace baba kai nake dako kafito akwai maganan da nake son muyi dakai ne.
Kallon mamaki ne yai min nakai durkushe a gaban shi nace don Allah baba alfarma nake nemawa inna ta akan zaman su da mama a gidan nan.
Duk zaman da suke na kishi a tsakanin su baba ba wai lalai bane sai ka saka bakin ka a ciki tunda kai ba mazauni gida bane baka san waina da ake toyawa ba a bayan fitan ka.
Kallona yake cikin mamaki yace Rahama har ankai lokacin da za ki tari gabana akan maganan uwayen ki.
Nai saurin cewa baba ba hakana bane yaune naga inna har ta shirya wai zata bar gidan bata iyawa ta gaji da abinda ake mata shine nace bari nai magana.
Yanzun haka wallahi inna batasan zan yi wanan maganan da kai ba ma hakkuri dai nake baka baba ko dan darajan mu a tsakanin ku ka rangwanta ma rayuwan ta hakana.
Shiru yayi kamar mai nazarina can yace naji amma ita Asiya ne yau har tai niyar yaji ?
Nace kwarai kuwa baba Allah ya gyara ni kadaine a waje na tare ta data fice daga gidan.
Yace to jeki naji Allah yai maki albarka idan nadawo zanga ita innar taki zamuyi magana da ita na fahinta nace baba nagode Allah ya kara rufa asiri.
Ya wuce na juya na shiga gida zuciyana fes na san ko ba komai killa Allah ya kusa kawo muna saukin al, amarin mu ne a gidan.
****** ********* ******
Tun daga wanan lokacin da mukai magana da babana ta fahinta naga al, amura sunyi wa inna sauki sosai ba inna kawai ba har ma diyan ta da akewa kahonzuka a gidan mun dan samu saida sosai.
Ya zuwa yanzu ba karamin alheri Garbati yake kawowa ba gidan mu wani naci wani kuma dangin tufafi ne duk ba, a tabawa sai gurin mama altine ake boyewa.
Cikin hakane na roke shi yai hakkuri har na zana jerabawa na na karshe kafin ayi bukina dashi.
Da kyat na samu ya amince min wanda zuwa lokacin har labarin zancen aure na dashi yabi gari wanda mama ce da diyan ta suke yada zancen a gari.
Don mama har iyalin shi sai da ta fada masu irin alherin da yake kawo muna gidan mu .
Wai yanzu duk neman shi a kaina yake karewa komai kawo muna yake dani da uwata idan anga yadda muka koma wasu bulbul damu don mun samu ya rike muna kan maciji muna wasa da bindin shi.
Haka yasa matan shi suka tayar da hankalin su su basu yarda ba ya dauko masu yar jikan su a matsayin kishiyar su mafarin nazo ina masu rashin kunya a cikin gida.
Yace shi ra, ayin shi ke nan mai zama ta zauna wacce bata iyawa hanya a bude yake mata.
GNin da gaske yakeyi yasa suka kama kan su bayan ya saka masu waigi ga zancen da cewa.
Kada yaji wani ko wata yaiwa yarinyar nan ko iyayyen ta wani sheri zai dauki mumunan mataki akan ko waye a gidan.
Dole suka saka mai ido ba yadda zasuyi namiji idan yaso abu kunya fice mai yake a idon shi.
Mama altine ta tafi birni ganin anty da tadawo daga waje ganin likita akan matsalan ciwon ta.
Sai washe gari bayan ta huta anty ke tambayan ta wai mama ina Rama na take tana nan tana karatun ko ?
Mama tace wani karatu Sa, ade Raman ki kan aure zatayi bada dadewan nan ba.
Haba mama wani aure yarinya kamar Rama kuma ?
To ai sai kiyi Rahama kan har an kawo sadakin ta itace ma ta hudu a gidan mijin ta.
Anty dake kwance tace what ?
Mama wai da gake kike ko wasa tace ina wasa dake ne balle na fada maki wasa.
Uban ta yaba da ita ga wani tsohon maikudi na garin mu aure yanzu haka karatun data kwallafawa raine ya hana ayi bukin kin san ta samu sa, a don kokarin ta an kaita gaba yanzu bana zata fita daga makarantan ma.
Ran anty yai matukar baci dajin wanan labarin da tayi na zancen aure na nan dai mama ta koro mata komai akan zancen.
Na bata matukar tausayi tace mama in ba abin kauye ba ko mu da mukai aure da girman mu yaya muka kwashe da kaidin kishiya balle yarinya karama akaita cikin guzamay mata haka ?
Mama tace mu a kauye ai hakan ba komai bane gare mu amma duk da haka Rahama tayi kankanta kwarai agidan nan.
Da mama zata dawo sakon zannuwan gado da sauran kayan aiki dasu kudi anty ta bayar akawo na shagalin buki na wanda baifi wata biyu ba ayi yanzu.
Harda yan din kuna kala biyar da sauran abubuwa duk ta hado min tace aba Inna hakkuri saboda jikin ta bata samun zuwa bukin .
Amma idan ta samu lafiya zata zo taga dakina daga baya insha Allahu.
Mama tace kice wanan tafiyan na Rahama ne nayi ai taso ta biyoni sosai amma nasan mahaifinta ba zai yarda ba shiyasa na bata hakkuri.
Da mama ta dawo daga birni sai washe gari muka shiga taron ta don da dare ta iso garin.
Ai nan ta baje muna sakon anty na muna kallo wani abin ma ni ban san yadda za, ai amfani dashi ba agidan.
Ban san lokacin da na dunkule na fara kuka ba da kyat mama ta lalashe ni na wanke fuska na.
Sai da naje gida nake labartawa Inna ta abinda ya faru ta rike baki cikin mamaki tana cewa kai wanan boyar Allah ni ban san abinda zan saka mata dashi ba a duniyan nan ?
Mama ko sai gori take sake muna da habaici wai rana bata karya sai dai uwar diya tai kunya.
Daga uwar har uban sai kudi ake ci amma ko roba ba asai wa yarinya ba na aure .
Su dai gasu gani wai an bizzine tsohuwa da ranta suga yadda za afita kunya duk tallan da nayi Inna ta kasa saye min wani abin kwarai.
Dama tayi haka ne don ta kure inna don tasan ba, a aje min komai na aure ba a yanzu tunda mun sakakance cewa ni
boko zanyi ba aure ba yanzu.
To yanzu ga aure ya taso suga ta tsiya tasan dai gidan su Inna ba wata tsiya zasu barkata min ba don suma nema sukeyi.
Magana duk yabi gari inna bata aje min komai ba ga aure ya taso ba abin kaiwa gidan miji.
Lokaci ko kamar jira yake sai kara matsowa yake niko sai karatun jerabawa na dake gabana nakeyi kawai.
Ba abinda yai min tsinanen zafi akan maganan mama da diyan ta a gidan mu.
Garbati yasa aka gina min daki mai girma da fadi yadda zai isheni aka kewaye shiyan daban cikin na iyalin shi can gefe daya an shafa farar kasa yaji sai kyali yakeyi.
Haka ya kara bankantawa iyalin shi rai sosai har suka so tayar da hankalin su.
Amma da ya basu dan wani abu suma suyi gyara sai baki ya mutu murus kowa ta shiga sha, anin gaban ta da diyan ta amma kishin yana nan daram a ran su.
Duk inda yabi sai ba, a ake mai na ya fado gari ya zarta maza zai bare yarinyar dalleliya a ledan ta sai ya washe baki cikin jin dadi yana dariya.
Mama ko sai auki fadawa mutane karya da gaskiya takeyi akan zancen bukin tana zunden inna ta.
Inna ta duk tabi ta ramay sai dan wuya daga ita sai uwar dakin ta mama altine suke shirin bukin sai yan uwan su tsiraru da sukaji suka gani.
Ko su ba wai sun san shirin da Inna da mama altine sukayi min bane haka ake tafiyan a dunkule.
Gaba daya daga inna har baba babu wani mai kwanciyan hankali dama ma inna dake nuna halin ko in kula da bukin.
Idan ka cire mama da yaran ta wanda su ko a kwalar rigan su bai shafe su ba.
Ta dai zuga shi ya zugu yanzu kuma ta saka mai ido yaji kunya dan kudin sadakina da aka kawo dashi ne yake kokarin sayen komai.
Na dan gadon katakon da za, a sai min ma ya gagara daga karshe ganin haka tasa inna dabaran cewa yaba mama altine kudin ta shiga birni ko na hannu ne ta sayo min.
Tayi hakane don idan kudin ya shiga hannun su sai su san dabara mama altine ne ce ta koya mata wannan dabaran.
Baiki shawaran Inna ba tamika masu dan abinda ya saura takaiwa mama altine ta shirya sai birni da kudin daga karshe anty ce ta cika aka sayi min saitin gado da dan wardrove da katifa har da karin tarkace.
Wanan matar ba abinda zamuce mata sai dai Allah ya bata lafiya ya shirya mata zurian ta da albarkan sa kawai.
Ganin babu komai a dakin inna ta yasa mama ta samu baba da zancen da yamma bayan ya dawo gida take cewa.
Yanzu malam kana ganin haka zaku kai yarinyar na aure babban gida irin haka babu komai da uwarta ta tana da mata na fita kunya kaima sai nake ganin a furin ka hakan ne ?
Baba da yanzu ya fahinci mama so take taga wallen shi kuma tasan sirin abin sai ya boye mata ba su mama kudin sadakin da yayi yace anyi auren ne ko kikaga uwarta ta kaita hakana ?
Haka yasa taji haushi taja bakin ta ta tsuke ta bar zancen sai ido tana cewa ni dama taimakon ku naso nayi ko mu tafi gida tumba dillaliya adan samu abinda aka tsintar mata gurin ta in yaso bayan bukin abinda aka samu sai abata kudin ta.
Baba yace ko tabarma Allah ya hore mata daga gare ni sai na kaita dashi .
Yafice abin shi gidan ya barta nan tana mashi dariyar mumuke ta baya tana an daiji kunya wallahi anyi shigewa ai ciki amma ba, a iya fitar da yarinya kunya.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE NA FADA IDAN BAKI BIYA BA KIKA KARANTA MIN NOVEL NA BARKI GA ALLAH.
IDAN KIN BIYA KIKA TURA MIN NOVEL WANI GROUP KO KIKA BA WA WANDA BAI BIYA BA KE MA NA BARKI GA ALLAH DON KINCI AMANATA ALLAH ZAI SAKA MIN A KAN INSHA ALLAHU WACE TASAN BAZATA IYA RIKE AMANA BA DON ALLAH TAI MAGANA NA BATA KUDIN TA TAFITA MIN GROUP DON AMANA NAUYI GARE SHI ABINDA KA RAINA SAI YA HANAKA KETARE SIRADI GOBE KIYAMA ALLAH YA BAMU IKON RIKON AMANA A TSAKANIN MU.
DON NAGA NOVEL DINA A WANI GROUP KUMA NASAN WACE TA FITAR DON BATAI MAGANA BA NA BARTA GA ALLAH DON ALLAH SHEDA NE GA ALKAWARIN MU DA KU, ,
6
Ranan da na zana jerabawan karshe na na secondarya rana ce da ya kamata nai mafarin ciki a raina don kowa ka gani a cikin mu yana cikin farin ciki da jin dadi a ran shi.
Sai dai ni a gareni sabanin hakane don ya kasance min kamar rana na bakin ciki a gare ni.
Lokaci daya yanayi na ya sauya min naji duniya tai min kunci a raina komai ganin sa nake yai min baki a raina a dalilin tunawan da nayi wanan jin dadin rayuwan ya kusa yanke min.
Don wanan auren jarabtan da na tsinci rayuwana dashi na auren tsoho da mahaifina zai min a lokaci daya haka, batare da yai la, akari da irin rayuwan da zanje gidan miji na tarar.
Wanda yau baifi saura kwana goma ba naje gidan Alhaji garbati a matsayin matar auren shi nima a gidan.
Juyawa nayi zuwa staff room don nai sallama da malam mutumin da yai tsaye a kaina har nakai wanan matsayin na yau a gare ni.
Malam yana ganina yace a, a Rahama an kanmala ko ?
Maimakon na nuna farin ciki na sai na kai durkushe a gaban shi na fara kuka yace subbahanallahi Rahama lafiya dai ko ?
Cikin kuka nafara cewa malam nazo ne nai maku godiya akan tsaya min da kukayi har na kai ga wanan ranan ga karatuna.
Sai dai kuma gashi guri na ba zai kai na zama likitan da nake son zama ba na taimakawa yan garin mu kamar yadda nake da gurin haka a rayuwana.
Mahaifina ya yanke min wanan gurin nawa ta bayar dani aure ga wanda yaso yau saura kwana goma ayi bikina akaini.
Subbahanallahi inji malam yace yaushe haka ya faru kuma Rahama waye kuma miji ?
Sai na dan kakaro murmushi a fuskana nakw cewa malam an kwana biyu da hakan ba kuma kowa bane mijin sai Alhaji Garbati dan bida na garin nan.
Shi da sauran malamai da suke saurare na cikin tausayi
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7 Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22Chapter 23Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32Chapter 33Chapter 34Chapter 35Chapter 36Chapter 37Chapter 38Chapter 39Chapter 40Chapter 41Chapter 42Chapter 43Chapter 44Chapter 45Chapter 46Chapter 47Chapter 48Chapter 49Chapter 50Chapter 51Chapter 52Chapter 53Chapter 54Chapter 55Chapter 56Chapter 57Chapter 58Chapter 59Chapter 60Chapter 61Chapter 62Chapter 63Chapter 64Chapter 65Chapter 66Chapter 67Chapter 68Chapter 69Chapter 70Chapter 71Chapter 72Chapter 73Chapter 74Chapter 75Chapter 76Chapter 77Chapter 78Chapter 79Chapter 80Chapter 81Chapter 82Chapter 83Chapter 84Chapter 85Chapter 86Chapter 87Chapter 88Chapter 89Chapter 90Chapter 91Chapter 92Chapter 93Chapter 94Chapter 95Chapter 96Chapter 97Chapter 98Chapter 99Chapter 100Chapter 101Chapter 102Chapter 103Chapter 104Chapter 105Chapter 106Chapter 107Chapter 108Chapter 109Chapter 110Chapter 111Chapter 112Chapter 113Chapter 114Chapter 115Chapter 116Chapter 117Chapter 118Chapter 119Chapter 120Chapter 121Chapter 122Chapter 123Chapter 124Chapter 125Chapter 126Chapter 127Chapter 128Chapter 129Chapter 130Chapter 131Chapter 132Chapter 133Chapter 134Chapter 135Chapter 136Chapter 137Chapter 138Chapter 139Chapter 140Chapter 141Chapter 142Chapter 143Chapter 144Chapter 145Chapter 146Chapter 147Chapter 148Chapter 149Chapter 150Chapter 151Chapter 152Chapter 153