fa dole ne ko yaya ne su san su don jinin su ne yaran, yace dani cikin bacin rai ke dakata Rahama.
Sai nai shiru ido rufe ya hauni da fada akan naje na dawo mai da yar shi kafin raina ya baci inda yake shiga ba nan yake fita ba sai da mama Altine ta bashi hakkuri tare da fadin bari ta tafi ta dauko Amira din tin da safe.
Abubuwa duk sun taru sun min yawa a kaina ta ko ina babu dadi a gareni kan wanan magana don daddy ya rufe idanuwan shi yai min tas akan yan uwan anty Saade.
Yadda mama ta fada hakan akayi don tunda safe ta shirya nasa driver ya kaisu ita da mama Abu matar maigari da gwagon daddy da take zuwa gun mu akai akai idan muna kano.
Sai da aka kwasa dasu don gidan anty Amina suka fara zuwa tace vaza su ba da ita ba sai gobe zasu dawo da ita din.
Amma mama ta fada masu cewa idan har basu ba yarda yarinyar ba komai ma zai iya faruwa akan maganan.
Haka dai dole suka ce yarinyar tana gidan maryam daga gidan maryam aka kira masu Asmau itace ta bada Amira din suka dawo da ita gida tare da su.
Har lokacin raina ba dadi ga jama, a da suka taru don ni a gidan zakace ko yar cikina ne akewa aure a lokacin irin yadda yan uwa na sukai min kara a bukin.
Sai dai yan uwan marigayiya sun kawo min cikas a rayuwana kan zargin da suke min na wai nayi rub da ciki da dukiyan yaran yar uwan nasu.
Kamar yadda daddy ya dauki zafi nima haka na dauka dashi don ban kara bin ta kan shi ba, tun wanan lokacin.
Ban san may ya gani ba da dare ya aiko kirana ina zaune tare da su mama Suwaiba na ta ta faman hada kayan da za a kai hidan iyayyen mijin Amira na gara a cikin manyan robobi don da safe zasu tafi da kayan bauchi.
Mutum biyar aka zaba da zasu tafi Aisha Sister din daddy da fatiman shi sai Asamau sister din anty don ita kadai tace zata tafi sai Zarah yanzu ga Suwaiba tace zata tafi itama don mota biyu zasuyi amfani dashi.
Sai da na dan bata lokaci na mike na tafi inda na samay shi tare da Zulfa a zaune tare da shi.
Sallama nai masu tare da gaida daddy din sai Zulfan take tambayana yaya naji da jama, a dazun ta shiga ance mun dan fita bana ciki.
Na dan bata rai na nakai zaune ina fadin wallahi fa mun tafi wurin mai aikin cicin ne tana son kawo muna cikas ga aikin bayan munyi da ita a yau muke son mu kammala komai gobe za a tafi dasu.
Take cewa dani ai haka mutane suke wani lokaci basu da alkawari nace ai tayi muna don har ta aiko dashi ko tun dazun yanzu ma hada kayan mukeyi aka kirani.
Tace wai gashi har kin wani fada kin ramay ki na ko samun cin abinci kuwa doctor ?
Murmushi nayi nace da ita ina naga ta zama naci abinci idan banga an kamala komai ba tace ai shine ance rana baya karya sai dai uwar diya tai kunya inji manya.
Wanan uwar diyan kan a tsaye take don tun da safe ban ga kin zauna ba ga jama, a sun taru haka abin tubarkallah wallahi.
Nace gaskiya mutane sunyi kokari sosai wallahi don hakane kawai za ai wa mutum a nuna mai so da kauna yasan cewa shi din da dangi ne ta ko ina.
Mun dai dan taba hira akan bukin da ita t yana ta faman aikin shi bai tanka mu ba sai can naji yace damu.
Naga, har su suwaiban ki ai sun shigo da wuri haka abin ya ban mamaki nace ai dole ne suzo daddy wanake dashi bayan su.
Ranan wuya akace sai naka inji zulfa sai Daddy yace ga wanda yasan da hakan ko naga wasu na jikina ne amma suna ja baya ga bukin .
Sai duk mukai shiru saboda mun fahinci inda maganan shi ya dosa a lokacin da zulfa yake wanan magana din.
Yace dama na kiraki ne naji su waye zasu tafi gobe sai kuma jibi din idab za a kaita da suwa za ai tafiyan kuma ?
Na dan ya mutsa fuskana da babu saki a cikin sa nace tau dama dai ga goben sai na lissafo mai masu tafiyan kai kayan .
Nace jibi din dai ne ban san masu zuwa ba don kowa na son zuwa yaga dakin nata a can yace ba gaskiya bane kin san dai ba za, a kwasa akai masu dawainiya ba can kuma da yawa.
Nace ai yanzu sai ka fada kowa yaji yace ba manya ne zasu tafi ba idan za a je din nace ai yadda kace haka ne za ayi.
Amma maganan yana hannun Aisha da Fatima don sune masu gudanar da komai na gani yanzu don ni ba zan iya ba saboda kowa abinda ya kawo shi ke nan.
Yace to ji nan kada a wuce mutim goma dai kuma a tabbatar da an tafi da mama Laraba da mama Altine idan za a kaita din don hankalina yafi kwanciya dasu a ciki.
Nacd zan fadawa Aisha din don yanzu ta fita ta tafi aurin matar da zasu dauka don gyaran Amira din.
Yace gyara wani irin gyara kuma ni dai murmushi nayi sai Zulfa ne tace dashi kai dama ka dauka haka ake dunkula mace akaita gidan mijin ta kai tsaye ba wani dan kwaskwarima tare da ita.
Balle wanan Amaryan yar gata duk kawayen uwar ta madu ido a bude sun san komai ko su da kan su zasu iya mata komai ai.
Nace kai haba dai abin ya zama sheri kuma ai anty gyara kan Amira ta sha shi sai dai muce Allah ya bada zaman lafiya kawai.
Nace a kasalance shike nan ni zan tafi don aiki muke a can aka kirani yanzu din.
Yace tunda kika ji na kiraki aikin san magana zanyi da ke ko nace na dauka wanan maganan ne kawai ai.
Yace to bashi bane zauna kijirani ina zuwa sai yaci gaba da aikin shi kawai.
Dan lokaci kadan Zulfa ta mike tana fadin bari naje na duba yaran nan don yanzu nasan suna can sun min kaca kaca da shiya na.
Ta mike ta fice ta barni dashi zaune a wurin tana fita yake cewa dani komai dai ya kammala ke nan ko don banji kince dani komai ba again ?
Nace dashi ina ganin ba komai ai da nayi magana cikin daure fuska ya dan dago yana ksllona don jin yanayin da nai maganan.
Wai ke may kuma ke faruwane haka kike wani shan kamshi dake haka tun dazu nake lura dake a hakan.
Nace may fa kawai dai daurowa ne yace ba gaskiya bane wanan maganan ko dan maganan da akayi dazun ne kikewa wanan cikan kina batsewa haka ?
Nace dan magana fa kace daddy fisabillilahi yanzu ni may ye laifina a cikin wanan zancen haka da har ka rufe idon ka kai min haka don kawai na tura Amira wurin dangin uwar ta.
Kuma na ga dai wanan maganan ai munyi shi dakai ranan ko yace amma kuma ai daga baya da sukai min rashin mutunci na fada kada a kaita.
Nace yanzu sunzo sun bada hakkuri ai na dauka komai ya wuce ne ko idan kuma na hanata zuwa yadda suka bukata sai kuma nai wani sabin laifi ga hakan.
Yace ba dai kin tura ta ta tafi din ba ina shike nan nace kasan da hakan kuma ka rufe ido ka nunawa mutane ni ba kowa bane ga yaran da maganan.
Yai murmushi tare da ture takardun dake gaban shi yace dani yanzu dai in waban ne laifina ayi hakkuri ina shike nan ko ?
Nace ai hakkuri ya zama dole gare ni tunda haka Allah ya doro min wanan nauyin a kaina dole duk yadda yazo min na rungumay shi da hannu biyu.
Yace haka ake son musulmi dama da hakkuri amma kin daure haka aiko jama an dake tare dake bazasuji dadin ki ba don haka a washe don Allah.

Don Allah wanda na bata wa rai yayi hakkuri dani yanayi ne idan anyi la akari da yadda ake samun novel din a baya da kuma yadda yanzu yake delaiy gurin samun shi.
Ayi hakkuri dani please ba haka naso ba nima da fatan an sha ruwa lafiya yan uwa Allah ya sada mu da rahamarsa da gafaran sa albarkacin wanan watan mai albarka da muke ciki

ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE ONLINE NOVEL NE NA KUDI, , , , ,
107

Washegari tunda safe masu zuwa bauchi suka shirya tafiyan don su samu su dawo a lokaci.
Bayan tafiyan su anyi wasu event da ya shafi yan matan bukin na Amira wanda akasarin su sunzo ne daga Abuja don taya ta murnan bukin nata.
Sai yamma lis su Zarah suka dawo garin a gajiye suna ta faman yabawa irin taron da akai masu a can da kuma irin namijin kokarin da mukaiwa Amira din a dakin ta.
Don duk wani kayan kitchen da uwa zataiwa yar ta nice na sayawa Amira su da komai da ya dace na nauyin uwa a gare ni.
Haka uban nata ba a cewa komai don ya gwadawa yarsa gata sosai yadda ya dace duk wani uban da ya dace yaiwa yarsa don nuna hali.
Sun yaba sosai ga abinda idanuwan su ya gano masu a gidan na Amira da aka gyara mata shi.
Mutane nan suka shiga magana kan irin wannan gatan da aka gwadawa Amira din wanda itace ya ta farko da ya aurar ta jikin shi.
Haka yasa kowa ke son zuwa ya ganewa idanuwan shi abubuwan da ake fadi da akwai a gidan na Amira a can bauchi.
Mun tashi da aiki washegari don tun karfe hudu muka falka aka shiga yin abubuwan abinda ya dace na sha,anin bukin.
Koda gari zai waye an gudanar da komai a yadda ya dace, ayi shi don haka muka samu sararin da muka samu hutu da kimtsa kan mu sai taron jamma, a da muke muna kuma ciyar dasu da abinda ya sauwaka na bukin da muka tanada.
Daga hakan ne aka daura aure aka shiga shirin wucewa da amarya sai daga bayane nake jin ai shi daddy da kansa ne zasu kaita shi da Bashir aminin shi.
Kamar yadda yayi da za akai Aisha wannan ma haka akayi akan amira din don sai da muka gurji kukan mu a wurin kafin mama laraba da anty Asmau suka ja hannun ta suka fice da ita a falon tana kuka ina kuka har suka bacewa gani na.
Haka na wuni cikin rashin walwala a tare dani haka nai ta gudanar da harkan buki har mutane suka watse aka barni da bakin da suka zo min daga wasu garuruwan wurin bukin.
Bayan bukin kwana biyu kawai na yi a kano na kwasa sai Abuja don akwai aiki a gabana banda wani lokaci na hutu a gare ni.
Nan na bar Hindatu a kano wai bata gama abinda takeyi ba a garin ni dai na kwasa da yarana muka bar garin.
A na samo wata yar aiki sai dai ba yarinya bace ita ta dan manyanta hajiyan harka ce ta sama min ita don haka da ita muka dawo garin.
Nazo da yar wurin Suwaibana daga can da zata zauna dani sai kanina Audi daya biyo ni don zai fara karatu shima yanzu saboda sun kiyi a can sun tsaya shiririta wai neman kudi.
Saukina ma shine daga Aisha har Amira duk a Abuja muke zaune dasu ko ba kullun ba dai zan dan dinga ganin su a gidan wani lokaci.
Sannu a hankali na ke koyar da Tani mai aiki dana dauko babu wani tsangwama ko takurawa a gare ta don nima tai muna tsakani da Allah yadda muke mata din.
Ban samu matsala da ita ba don tana da hakkuri sosai matan saboda zama da yara dole sai da hakkuri tare dasu.
Tafiyan Nasir ya taso sai faman shiri muke yi na tafiyan nashi tare zamu tafi dashi mukai shi mu dawo ni da daddy sai ga wani tafiya zuwa India ya taso min daga wurin aiki inda zanyi wata uku a can don wani nazari da aka tura mu mu uku .
Wanan dalilin ne ya hana tafiyan dani a lokacin don haka na shirya ma yaron komai daya dace tare da mashi alkawarin zamuzo muyi mai hutu acan U,S din insha Allahu in na samu lokaci.
Na riga su barin kasan inda nai tafiya da kananan yarana sai Maryam dana dauko don su Aisha na karatu a lokacin.
Inna ta da mama Altine ne zasu zauna da yarana a gidan sai dai kafin ta yarda da hakan sai da akakai rana da ita daddy da kansa yaje ya dauko min ita acan kauyen mu.
Su na bari da yaran a gida su zauna min dasu don kula yadda ya dace na tafi wanan tafiyan idan nayi shi akwai alheri sosai gare ni cikin sa ba don hakan ba ba zan bar Nasir ya tafi badani ba irin yadda yaron ya nuna damuwan shi ga rashin zuwa dani a lokacin.
Gida ne aka kama muna kowan mu mai dakuna biyu da falo sai kitchen don haka na samu wani makaranta a kusa na saka yaran a nan.
Haka yasa banda matsalan komai na ci gaba da abinda ya kawo ni kasan nakan kira yara muyi waya dasu dasu inna mu gaisa dasu sai ranan muna waya ne Aisha take fada min cewa anty daddy fa yayi aure bayan ki.
Duk da maganan ya barna min rai amma sai nake cewa cikin dakewa ashe har yayi auren ko ?
Tace anty dama kin san da zancen auren ke nan ashe, nace da ita na sani mana tunda ba fasawa zaiyi ba ai.
Tace sukan maman Ihisan fada sukayi da daddy sosai sai da mamanta tazo garin baki ga matar ba wata lukekiya da ita wai yar kasuwa ce irin shi Dubai take zuwa nace kuma dai.
Tazo satin ta daya ta wuce bata dawo ba yun lokacin nan dai taita bani labarin yadda zuwan matan aka kwashe da daddy har yake cewa inda Rahama ce ba zata taba nuna tashin hankali haka ba ga duk auren da nakeyi amma ke sai ankai ruwa rana dake ko yaushe baki girma.
Yabon banza nace da ita shi dai ya sani yaje yai tayi ai watarana yana gani zai bar matan wanan wani irin rayuwane ma daddy kamar wanda keda bakin uwa akan sa.
Mun yi sallama da ita ta barni da wanan damuwar a raina ni kadai a kasan mutane daga karshe na tattara na watsar da zancen don ba zan yarda na saka wanan zancen ya ja min matsala ba.
Sai dai ina jiran shi ya fada min da kan shi kancewa yayi auren wanan karon nayi alkawarin zai jini sosai ba dadi don abin ya ishe ni hakana wallahi.
Har ina batun dawowa bai fada min ba nima ban mai magana ba akai sai gashi ranan na kira su Inna muna waya dasu nake fada masu karshen wata zamu dawo insha Allahu.
Sai bayan mun gama hiran mu nace tabawa yaran sai naji tace dani Yarinya dama ina son muyi wani magana dake kafin ki dawo nace to Inna ta.
Tace ba wani abu bane nasan a gurin ki don kin saba da hakan daga mijin ku don ya kara aure a bayan ki don haka kada ki yarda naji wani abinda bai dace ba ya fito daga gare ki kan wanan maganan kamar yadda ya uwan zaman ki sukai mashi.
Shiru nayi sai naji tace kina ko jina yarinya nace ina jinki inna ta ba ruwana da zancen auren shi ni matsala na daya shine idan ya tabbatar da lafiyan matan da yake aure ai shike nan .
Duk da dai nasan ba zai yarda yana aure haka ido a rufe ba don yana da wayen wan shi akai amma ni mace ba a kaina zata zauna ba ai shi da ya dauko shiyasan abin shi can.
Tace haka nake so ji dama a gare ki don Allah ki taushi zuciyar ki irin yadda kika saba don shima ya fadi hakan da bakin shi a gurin sulhun da akai masu da ita wanan hindatun kishiyar ki.
Nace kai maman Ihisan ma dai da wani abu take wallahi mata nawa yake daukowa agidan a yaya ake karewa dasu irin su daddy ai sai ido kawai don abin nashi kamar mai bakin uwa akai.
Inna tace min ai ba kama bane don ance uwar ce tace dashi a lokacin marigayiya na da rai da zai auri su Zulfa take cewa da ita indai kishi ne sai dai taitayi mata hudu sai ya zauna dasu a gidan tana gani ba fashi.
Nai dariya tare da fadin Allah sarki ita Allah bai nufa tagani ba amma su gashi ai suna gani da ran su shiyasa ba a son uwaye nawa diya furci ko yayane cikin bacin rai .
Inna
Showing 441001 words to 444000 words out of 456145 words
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22Chapter 23Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32Chapter 33Chapter 34Chapter 35Chapter 36Chapter 37Chapter 38Chapter 39Chapter 40Chapter 41Chapter 42Chapter 43Chapter 44Chapter 45Chapter 46Chapter 47Chapter 48Chapter 49Chapter 50Chapter 51Chapter 52Chapter 53Chapter 54Chapter 55Chapter 56Chapter 57Chapter 58Chapter 59Chapter 60Chapter 61Chapter 62Chapter 63Chapter 64Chapter 65Chapter 66Chapter 67Chapter 68Chapter 69Chapter 70Chapter 71Chapter 72Chapter 73Chapter 74Chapter 75Chapter 76Chapter 77Chapter 78Chapter 79Chapter 80Chapter 81Chapter 82Chapter 83Chapter 84Chapter 85Chapter 86Chapter 87Chapter 88Chapter 89Chapter 90Chapter 91Chapter 92Chapter 93Chapter 94Chapter 95Chapter 96Chapter 97Chapter 98Chapter 99Chapter 100Chapter 101Chapter 102Chapter 103Chapter 104Chapter 105Chapter 106Chapter 107Chapter 108Chapter 109Chapter 110Chapter 111Chapter 112Chapter 113Chapter 114Chapter 115Chapter 116Chapter 117Chapter 118Chapter 119Chapter 120Chapter 121Chapter 122Chapter 123Chapter 124Chapter 125Chapter 126Chapter 127Chapter 128Chapter 129Chapter 130Chapter 131Chapter 132Chapter 133Chapter 134Chapter 135Chapter 136Chapter 137Chapter 138Chapter 139Chapter 140Chapter 141Chapter 142Chapter 143Chapter 144Chapter 145Chapter 146Chapter 147Chapter 148 Chapter 149Chapter 150Chapter 151Chapter 152Chapter 153