taimaka mata wani lokaci can ba, a rasa ba sai da nai kwana biyu a kano na shirya muka wuce gida.
Mun isa da wuri don haka kafin wani lokaci akasan da zuwan mu nan yan uwa da abokan arziki suka dinga shigowa taron mu sai dai naje washe gari Allah yaiwa Jatau mijin Suwaiba na rasuwa muka tashi da wanan tashin hankalin kuma a gare mu.
Koda naje gidan abin ba dadi ruwa ma babu shi a gidan ko kadan nasa akira masu ruwa suka cika duk wani kayan dake gidan take na bada kudi aka sayo masu abinci sai dai suwaiba ke cewa dani ai rabawa akeyi kowa yai nasa nace ba matsala tabar masu sai a kawo mata nata.
Ban samu zama ba don kwana uku a gidanta muke wuni sai dare nake dawowa gida don haka ban samu kebewa da Innata ba.
Sai ranan da aika sadakan uku bandawo ba saida na wadata Suwaiba da duk wani abin bukata suma kishiyoyin nata nai masu nasu irin alherin gwargwadon hali na dawo gida ban kai dare baranan gidan .
Da dare muna zaune muna hira da Aisha uwarta ta kirata bayan fitan ta ne Inba ta ke cewa dani wai niko yarinya lafiya kuke kuwa don naji ance wanan hatsabibiyar kishiyar taki takoma can inda kike da zama yanzu ?
Nace a sanyaye lafiya muke inna sai dai dan abinda ba a rasa ba can kuma ba kullun bane tace to Allah ya kyauta a daita hakkuri da jama, a don Allah.
Nace insha Allahu Inna sai na boye mata don ban san yadda zan iya fada mata komai dake faruwa ba a tsakanina da daddy din.
Sai wurin Attu ne da naje cikin hikima irin nasu na manya take tambaya na na sake jiki sosai ina fada mata matsalar dake damuwar mu tsakani na da daddy din.
Take naji yar tsohuwar ta saka min salalami tana tafa hannayen ta tace yar nan tun yaushe hakan ke faruwa na fada mata tace to kin fadawa uwar ki da kikazo nace haba attu ko nasha giyar wake yaya zan iya fadawa inna wanan maganan kuma.
Ko ke dai daurowa tayi da har na koma bazaki ji shi ba a bakina ba tace ki koma ina cikin wanan irin laluran haka na ai banga ta zama ba .
Dole ne na bazama wurin masana a walwale maki wanan sihirin don idan ba walwale shi ba ku ba zaman lafiya ko zaman aure a tsakanin ku tunda akwai cutawa ga hakan.
Wunin da banyi ba ke nan don Attu ta fita tabar mu don haka na wuce uguwar mu na gaida mama Altine da matan babana.
Gidan mama Altine na fara shiga duk da mun hadu a gidan Suwaiba da ita amma tana ganina ta shiga ina taka saka dani ta shimfida tabar muka zauna ni da yaran ta kawo ruwan randan kasan ta mai tsabta muka sha.
Tace Rahama har na fara zargin ko don irin halin da uwar dakin naki ta tsiro dashi yasa kike ja baya dani kuma yanzu.
Nace ni kan yaya zanyi na gujeki mama aisai butulu ke mantawa da uwar shi irin halarcin da kikai min duniya ko uwata data haifeni ai ya tsaya nan.
Tace to na gode Rahama nan muka shiga hira tace zata dafawa yaran abinci suci nace barsu mama kada ki wahalar da kanki mama kinga abincin su nan biscuit tace yaran birni ke nan.
Mun sha hira da mama amma ko ta dauki halin da anty take min sai na kawar da zancen nace da ita ai yanzu an daina dama rudin shedan ne kawai.
Sai bayan la,asar na bar gidan na shiga gidan mu tsatsaye na gaidasu mama tsufa ya taso mata kanta yai wani farin gashi gashi a dankare mata ba gyara hakoranta na gaba sun zube.
Tabani tausayi sosai nace da ita idan na koma zan sa ai mata hakoran roba tunda dai batai tsufan da zata rasa hakora ba haka na san dai daya ya fadi wurin fadan su da amaryan ta a baya amma sauran biyun fa ?
Nakawo alheri nai masu nace zan dawo don in gana da babana naga jikin nashi yadda yake yanzu.
Sai gap da magariba nakoma gida inda na samu har Attu tazo nema har sau biyu ban dawo ba sai ta bar sako da magariba zata dawo mu fita.
Na samu yaran sunyi barci koda tazo ban zauna ba muka fice tare zuwa inda zamu nida ita sai kanina Audi da ya raka mu zuwa unguwar da zamu.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABUIDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE DON BA A TAFE BA ONLINE NOVEL NE, , , ,
80
Tun bayan waya na da Zarah sai hankalina ya fara tashi don ba karamin tsoro kalamin ta ya bani ba.
Ni lafiyana shine yafi min komai a rayuwa na in dai zasu barni da lafiya ina iya bar masu mijin su a zauna lafiya.
Amma ta ina zan fara wana san yai muna wanan shamakin a tsakanin mu ni dashi don duk kishiya kishiya ce dai.
Amma wa zan zarga a wanan matsalan shin hindatu dake nan zaune tare da mune ko kuwa wa yanda ke gida ne sukai min hakan wai ?
Nan dai na zauna ina ta faman tunane wanda har na gama ban iya gane komai va daga ciki abinda dai na yake da ga karshe shine zan dukuma nafi da kaimi wurin kai kuka na ga Allah dayai min tsari akan duk mai bina da wani mugun manufa.
May na tare masu da har yai zafi haka sukai muna wanan mugun asirin da sai jahili zai iya shi.
Sannu a hankali na fara rama a tsaye gashi bayan zarah aminiyata ban iya fadawa kowa wanan zancen don da kunya aji shi a bakina haka.
Muna cikin wanan halin ne ranan sai ga massage ya shigo a email dina asibitin da nai bautan kasa suna neman mu muzo interview wurin su.
Murna farin ciki duk ya kamani a lokaci daya daddy kawai nake jira ya dawo na fada mai naji may zai ce akan zancen.
Koda ya dawo nice da girki ranan don haka na tsara kwalliya na dana bata lokaci wurin yin shi ga lafiyayyen abincin dana girka don shi a ranan.
Bai shigo ba sai yamma lis ya dawo gidan ina dakina ina bawa yarona nono naji muryan shi Atika na mikawa yaton bai koshi ba ya dan sa kuka nace fice dashi zuwa dakin ku don Allah,
Tana fitowa dashi uban yaji kukan shi yace kai Atika ya akayi ne yake kuka kawo shi nan ta mikawa uban yoron ta nacewa wai bai koshi da nono bane shine yake kuka.
Daddy yace ita nonon nata na sayarwa ne ko may zatayi dashi da bazata bashi ba ya sha ya koshi da kyau.
Daga kofa ina fitowa nace cikin wani murya najan ra, ayi nace wallahi daddy ya faye tsotso shi bai koshi da nono.
Ya dago yana kallo na na tabbatar shigan tai mashi kyau don ni kaina na sani saboda kayan ya fitar min da kurciyana a fili.
Yai murmushi yace nawa za, a sayar muna a bashi ya sha ya koshi yadda yake so na sake cewa daddy don Allah barshi yanzu Aisha zata kara mai da abincin shi yasha.
Wallahi Rahama kiji tsoron Allah in baki son Allah ya kama ki da laifin daukan alhakin wanan yaro yaro dan wata shidda da kai ace bai sha nono ya koshi ba sai wani abinci can na bature.
Ban so ba namika hannu ina karban yaron a wurin shi nace jishi dan Allah sai dan banzan tsotso dashi aikai ka baci da ci wallahi.
Komawa mukayi daga ni har shi muna dan hira yaron na shan nono yace ina yaran nace sun fita wasan ball sukace.
Yace kai yaran basa ji wallahi nace to maza ne ba a raba su da irin haka tunda ba mata bane sai dai a saka ido ga muamulan su kawai.
Sai dai haka din amma ba kwar ba dai kan don an wuce wurin kwaliyan da ba biyan kudin sabulu ai aikin banza ne yin shi.
Gaba daya muka juya inda take tsaye tana magana cikin tafiya zuwa kofan baya shi dai na dauka bai fahinci maganan ta ba amma ni sai na fara zargin anya ba daga hindatu muke samun matsala ba kuwa ?
In ba shi ba yaya tasan abinda ke tsakanin mu ni dai na san daddy ba zai taba fada mata komai ba a tsakanin mu duk yadda suke kuwa don shi ba namijin dake zama yai maganan wata matar shi da wata ba.
Tafe take tana waka mai kama da habaici kamar an dauke ta an rada a kasa ta fadi kasa tim a tsakiyan falon.
Ba karamin buguwa tayi ba ga wanan faduwan shine yace innalillahi may ye haka ya akai haka kuma sannu tashi.
Bai mike ba yana zaune inda muke yana cewa may kika taka kuma haka ya kada ke wanan faduwan haka ai sau ki karye ko ?
Allah ai ba azzalumin bawa bane don shi ba ai mai gadara in daukan alhaki abin yine kadan mutum ya fara gani a rayuwan shi.
Ina fadin haka na mike na bar wurin ban mata sannu ba ta mike da kunya ta nufi dakin ta tana cewa ban san shege yaron da ya zubar da ruwa ba a saman ties din nan kuma ?
Bai jima ba ya tafi sallah sai bayan ya dawo ne na fito don bashi abinci mun zauna yana ta latsar wayan shi har na zuba mai abincin na aje a gaban shi ya kalli abincin yace duk ni zan cinye wanan Rama ?
Kada fa nai kiba kizo kice dani na tsufa maki nan gaba ki fara dan kwanaye kwanaye kuma kina baki son zama da tsoho.
Nai dan dariya mai kama da murmushi nace ai tunda bance ma tsoho ba da farko yanzu ma bazance ba don ni din ma yanzu ai ba yarinya bace.
Muna cikin hiran sai ga ta fito daga daki tace dear kasan na fadi a gaban ka amma ko ka shiga ka dubani kaga ya jikin nawa gashi yanzu duk jikin nawa ciwo yake min wallahi.
Yace ki sha magani mana tace ni asibiti nake son zuwa aduba min kafana don ciwo yake min yace amma ba yau ba kan don dare ya yi yanzu.
Ta wani bata rai bataso haka ba taso ne ta tasa shi a gaba sukama hanya zuwa asibi a cikin daren nan ta nuna man iyakana dashi sai bai biye mata ba yace tasha magani agani zuwa gobe.
Sai da ta wuce nace dama ina son ka huta na fada ma an turo min da sako ana neman mu ranan monday wurin interview asibitin da mukai service.
Yace a, a shine baki fada min ba Rahama wanan ai ba karamin magana bane yanzu zanyi waya da MD naji yaya ake process din abin naku.
Nan a wurin ya kira sukai dan magana yace ba matsala na shigo kawai ranan monday din za a duba ai ina da kwazo sosai sun sani.
Mutum zai iya fahinta yanayin mu a lokacin yadda muke daukin junan mu sai dai ba dama komai don engine bai aiki a kaina ko kadan dan wasan da ma yakanyi da farko idan yayi yanzu sai gari ya waye mai ba lafiya a jikin shi.
Mutum zai gane yana cikin damuwa don sai matsala ya faru zaka san idan mutum yana kaunar ka baka sanin zurfin kaunar sai idan matsala ya gitta a tsakanin ku zaka gane zurfin kaunarva gare ka kasan yadda mutum ya damu da kai.
Hakane yanzu a kullun bakin daddy bai gajiya da kwantar min da hankali yana bani hakkuri kan matsalan dake faruwa damu din.
Nakan yi murmushin yake nace haba daddy bakomai mana ai matsala ne kowa yasan ta sai yace Rahama nasan ina cuta maki sosai sai dai hakkurin ki bai bari a fahinci muna da matsala ni dake.
Don da watace da yanzu duniya ta fahinci halin da muke ciki ko ansan muna da matsala wurin wanan fannin.
Wanan kwantar min da hankalin da yake yasa ban dauku matsalan nakaishi can kasan zuciya na ba sai ma kara kaimin da nayi wurin kyautata mai fiye da koda yaushe yadda wani ba zai iya fahinta ba.
Ina shiga dakin shi kullun nake da duty na kwana a ciki indai ba mun dan samu matsala bane nai fushi dashi.
Don a dakina nake yaji bana fita bana kai kara gun kowa yadda naga sunayi ban taba kai karan shi a wani ba duk zaman mu dashi na aure.
Yau ma na shirya tsab nabi bayan shi zuwa dakin hindatu da ban san may yasa idan ina duty zata dauki lokaci zaune afalo wani lokaci sai na shige zata bar falon.
Yau ma tana ganin na shige ta mike ta fada dakinta ta jawo wani roba fari can kasan kayan ta inda ta boye ta dauko wani abu mai kama da baka ta hada shi yadda takeyi kullun.
Ina shiga dakin ya fito daga wanka yana tsaye yana fesa turare a jikin shi na shigo dakin da sallama na.
Jin sallama na yasa shi dan juyowa gare ni yana murmushi yace har yaran sun kwanta ke nan nace sunyi barci tun dazun ai.
Karban turaren nayi naci gaba da fesa mashi sai bina da kallo yake yana murmushi da kada kai kawai.
Nace daddy lafiya ko naga sai wani kallo kake min ko yau injin ta samu service ne ban sani ba daidai da nake mayar da turaren a mazaunin shi yace .
Da haka zai kasance gare mu yau din aida nafi kowa farin ciki ko yaushe burina da fatana naga wanan matsalan ya tafi a gare mu.
Yace Rahama ni har yau na kasa kai karshen fahintar ki nace namay fa daddy ?
Yace baki ganewa ke kina da wani baiwa da ba kowa ne Allah keyiwa shi ba ke kanki baki sanin kina dashi sai dai na tare dake ya sanar maki da hakan.
Nace daddy wani irin baiwa ce wanan kuwa dani ban san da shi ba haka sai kai ka san shi a gare ni ?
Ya murmusa yana nufar gado yace ba yanzu zan fada maki shi ba sai nan gaba idan komai ya daidaita tsakanin mu.
Sai ya zauna a bakin gadon yace Rahama ina tausaya maki ina cutar dake a shekarun ki baki cancanci wanan hukuncin ba haka a wanan lokacin.
Rama ba zan iya boye maki ba ina tausaya maki matuka kuma don abin nawa a kwai son kai a cikin sa na kasa sama muna mafita a matsalar mu idan wani yaji haka tsawon lokacin da muka dauka a matsalan nan sai a ga na faye zama mai son kaina da yawa.
Nace haba daddy saboda may zakace haka kuma ai komai mukkadari ne daga ubangiji mutum bai dorawa kan shi lalura ai.
Yace nasan haka Rahama amma irin hakkurin da kikayi a dan tsakankanin nan ba kowa ne zai iya daure wanan irin matsalar ba haka.
Gashi ke kinyiwa wanan matsalar kankantar dauka da ace shekarun ki ya haura hakane nasan ba matsala zaki iya jure hakan har lokacin da Allah zai kawo muna mafita.
Nace ni ban damu ba daddy Allah dai ya bamu lafiya yace kwsnan zan tafi wani guri da nake kyautata zaton kila a shawon kan matsalan a can idan na tafi.
Nace daddy ban son kasawa kan ka tunane akan wanan matsalar saukin abin ma bani kadai bace a gun ka kana iya zuwa wani wajen wata kila acan ka dan samu kadace kayi.
Ni dai burina na zama mai cin wanan jerabawan da ubangiji ya aiko muna dashi bana zamo cikin masu kasa daurewa da kaddara ba.
Murmushi yayi gami da girgiza kan shi yace hakane amma wani lokaci abubuwa da dama sukan zowa bawa da sanadi don ai a gunki ne kawai wanan matsalan yake faruwa dani.
Nace dani da sauran duk a hannun ubangijin mu muke shi kadai ne kuma yasan dalilin yi hakan a gare mu don haka ka cire wanan damuwan a zuciyan ka kawai mu koma ga Allah ya kawo muna saukin alamarin.
Haka mukai ta hiran matsalar yana kankamay dani yana wasa da gashin kaina da yasha relexzer ya kwanta baya har barci yazo ya dauke mu bamu sani ba kowa da abinda zuciyar shi ke saka mai kan maganan.
Ina jin saukan numfashin shi alamar barci ne ya dan dauke mu na lalaba na mike daga saman gadon na shiga ban daki can na darji kuka na don na fahinci shima daddy yasan akwai matsala a wani wuri kamar yadda zarah ta fada min ranan.
To wa naiwa laifi yai min wanan mumunan hukuncin haka da sai mara imani zaiyiwa dan uwan shi haka a rayuwan zaman duniyan nan na dan lokaci kalilan.
Gashi na kasa fadawa inna ta matsalar da nake ciki kada hankalinta ya tashi na rasa wanda zan fadawa bayan Zarah da itama da kyat na iya fada mata komai.
Inna ce ya kamata na fadawa kuma ina jin nauyi da kunyan fadar irin magana haka a tsakanin mu ta yaya ma zan iyace mata wai miji baya iya kwanciya dani.
Don ni da farko banyi zaton wanan
Showing 327001 words to 330000 words out of 456145 words
Mun isa da wuri don haka kafin wani lokaci akasan da zuwan mu nan yan uwa da abokan arziki suka dinga shigowa taron mu sai dai naje washe gari Allah yaiwa Jatau mijin Suwaiba na rasuwa muka tashi da wanan tashin hankalin kuma a gare mu.
Koda naje gidan abin ba dadi ruwa ma babu shi a gidan ko kadan nasa akira masu ruwa suka cika duk wani kayan dake gidan take na bada kudi aka sayo masu abinci sai dai suwaiba ke cewa dani ai rabawa akeyi kowa yai nasa nace ba matsala tabar masu sai a kawo mata nata.
Ban samu zama ba don kwana uku a gidanta muke wuni sai dare nake dawowa gida don haka ban samu kebewa da Innata ba.
Sai ranan da aika sadakan uku bandawo ba saida na wadata Suwaiba da duk wani abin bukata suma kishiyoyin nata nai masu nasu irin alherin gwargwadon hali na dawo gida ban kai dare baranan gidan .
Da dare muna zaune muna hira da Aisha uwarta ta kirata bayan fitan ta ne Inba ta ke cewa dani wai niko yarinya lafiya kuke kuwa don naji ance wanan hatsabibiyar kishiyar taki takoma can inda kike da zama yanzu ?
Nace a sanyaye lafiya muke inna sai dai dan abinda ba a rasa ba can kuma ba kullun bane tace to Allah ya kyauta a daita hakkuri da jama, a don Allah.
Nace insha Allahu Inna sai na boye mata don ban san yadda zan iya fada mata komai dake faruwa ba a tsakanina da daddy din.
Sai wurin Attu ne da naje cikin hikima irin nasu na manya take tambaya na na sake jiki sosai ina fada mata matsalar dake damuwar mu tsakani na da daddy din.
Take naji yar tsohuwar ta saka min salalami tana tafa hannayen ta tace yar nan tun yaushe hakan ke faruwa na fada mata tace to kin fadawa uwar ki da kikazo nace haba attu ko nasha giyar wake yaya zan iya fadawa inna wanan maganan kuma.
Ko ke dai daurowa tayi da har na koma bazaki ji shi ba a bakina ba tace ki koma ina cikin wanan irin laluran haka na ai banga ta zama ba .
Dole ne na bazama wurin masana a walwale maki wanan sihirin don idan ba walwale shi ba ku ba zaman lafiya ko zaman aure a tsakanin ku tunda akwai cutawa ga hakan.
Wunin da banyi ba ke nan don Attu ta fita tabar mu don haka na wuce uguwar mu na gaida mama Altine da matan babana.
Gidan mama Altine na fara shiga duk da mun hadu a gidan Suwaiba da ita amma tana ganina ta shiga ina taka saka dani ta shimfida tabar muka zauna ni da yaran ta kawo ruwan randan kasan ta mai tsabta muka sha.
Tace Rahama har na fara zargin ko don irin halin da uwar dakin naki ta tsiro dashi yasa kike ja baya dani kuma yanzu.
Nace ni kan yaya zanyi na gujeki mama aisai butulu ke mantawa da uwar shi irin halarcin da kikai min duniya ko uwata data haifeni ai ya tsaya nan.
Tace to na gode Rahama nan muka shiga hira tace zata dafawa yaran abinci suci nace barsu mama kada ki wahalar da kanki mama kinga abincin su nan biscuit tace yaran birni ke nan.
Mun sha hira da mama amma ko ta dauki halin da anty take min sai na kawar da zancen nace da ita ai yanzu an daina dama rudin shedan ne kawai.
Sai bayan la,asar na bar gidan na shiga gidan mu tsatsaye na gaidasu mama tsufa ya taso mata kanta yai wani farin gashi gashi a dankare mata ba gyara hakoranta na gaba sun zube.
Tabani tausayi sosai nace da ita idan na koma zan sa ai mata hakoran roba tunda dai batai tsufan da zata rasa hakora ba haka na san dai daya ya fadi wurin fadan su da amaryan ta a baya amma sauran biyun fa ?
Nakawo alheri nai masu nace zan dawo don in gana da babana naga jikin nashi yadda yake yanzu.
Sai gap da magariba nakoma gida inda na samu har Attu tazo nema har sau biyu ban dawo ba sai ta bar sako da magariba zata dawo mu fita.
Na samu yaran sunyi barci koda tazo ban zauna ba muka fice tare zuwa inda zamu nida ita sai kanina Audi da ya raka mu zuwa unguwar da zamu.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABUIDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE DON BA A TAFE BA ONLINE NOVEL NE, , , ,
80
Tun bayan waya na da Zarah sai hankalina ya fara tashi don ba karamin tsoro kalamin ta ya bani ba.
Ni lafiyana shine yafi min komai a rayuwa na in dai zasu barni da lafiya ina iya bar masu mijin su a zauna lafiya.
Amma ta ina zan fara wana san yai muna wanan shamakin a tsakanin mu ni dashi don duk kishiya kishiya ce dai.
Amma wa zan zarga a wanan matsalan shin hindatu dake nan zaune tare da mune ko kuwa wa yanda ke gida ne sukai min hakan wai ?
Nan dai na zauna ina ta faman tunane wanda har na gama ban iya gane komai va daga ciki abinda dai na yake da ga karshe shine zan dukuma nafi da kaimi wurin kai kuka na ga Allah dayai min tsari akan duk mai bina da wani mugun manufa.
May na tare masu da har yai zafi haka sukai muna wanan mugun asirin da sai jahili zai iya shi.
Sannu a hankali na fara rama a tsaye gashi bayan zarah aminiyata ban iya fadawa kowa wanan zancen don da kunya aji shi a bakina haka.
Muna cikin wanan halin ne ranan sai ga massage ya shigo a email dina asibitin da nai bautan kasa suna neman mu muzo interview wurin su.
Murna farin ciki duk ya kamani a lokaci daya daddy kawai nake jira ya dawo na fada mai naji may zai ce akan zancen.
Koda ya dawo nice da girki ranan don haka na tsara kwalliya na dana bata lokaci wurin yin shi ga lafiyayyen abincin dana girka don shi a ranan.
Bai shigo ba sai yamma lis ya dawo gidan ina dakina ina bawa yarona nono naji muryan shi Atika na mikawa yaton bai koshi ba ya dan sa kuka nace fice dashi zuwa dakin ku don Allah,
Tana fitowa dashi uban yaji kukan shi yace kai Atika ya akayi ne yake kuka kawo shi nan ta mikawa uban yoron ta nacewa wai bai koshi da nono bane shine yake kuka.
Daddy yace ita nonon nata na sayarwa ne ko may zatayi dashi da bazata bashi ba ya sha ya koshi da kyau.
Daga kofa ina fitowa nace cikin wani murya najan ra, ayi nace wallahi daddy ya faye tsotso shi bai koshi da nono.
Ya dago yana kallo na na tabbatar shigan tai mashi kyau don ni kaina na sani saboda kayan ya fitar min da kurciyana a fili.
Yai murmushi yace nawa za, a sayar muna a bashi ya sha ya koshi yadda yake so na sake cewa daddy don Allah barshi yanzu Aisha zata kara mai da abincin shi yasha.
Wallahi Rahama kiji tsoron Allah in baki son Allah ya kama ki da laifin daukan alhakin wanan yaro yaro dan wata shidda da kai ace bai sha nono ya koshi ba sai wani abinci can na bature.
Ban so ba namika hannu ina karban yaron a wurin shi nace jishi dan Allah sai dan banzan tsotso dashi aikai ka baci da ci wallahi.
Komawa mukayi daga ni har shi muna dan hira yaron na shan nono yace ina yaran nace sun fita wasan ball sukace.
Yace kai yaran basa ji wallahi nace to maza ne ba a raba su da irin haka tunda ba mata bane sai dai a saka ido ga muamulan su kawai.
Sai dai haka din amma ba kwar ba dai kan don an wuce wurin kwaliyan da ba biyan kudin sabulu ai aikin banza ne yin shi.
Gaba daya muka juya inda take tsaye tana magana cikin tafiya zuwa kofan baya shi dai na dauka bai fahinci maganan ta ba amma ni sai na fara zargin anya ba daga hindatu muke samun matsala ba kuwa ?
In ba shi ba yaya tasan abinda ke tsakanin mu ni dai na san daddy ba zai taba fada mata komai ba a tsakanin mu duk yadda suke kuwa don shi ba namijin dake zama yai maganan wata matar shi da wata ba.
Tafe take tana waka mai kama da habaici kamar an dauke ta an rada a kasa ta fadi kasa tim a tsakiyan falon.
Ba karamin buguwa tayi ba ga wanan faduwan shine yace innalillahi may ye haka ya akai haka kuma sannu tashi.
Bai mike ba yana zaune inda muke yana cewa may kika taka kuma haka ya kada ke wanan faduwan haka ai sau ki karye ko ?
Allah ai ba azzalumin bawa bane don shi ba ai mai gadara in daukan alhaki abin yine kadan mutum ya fara gani a rayuwan shi.
Ina fadin haka na mike na bar wurin ban mata sannu ba ta mike da kunya ta nufi dakin ta tana cewa ban san shege yaron da ya zubar da ruwa ba a saman ties din nan kuma ?
Bai jima ba ya tafi sallah sai bayan ya dawo ne na fito don bashi abinci mun zauna yana ta latsar wayan shi har na zuba mai abincin na aje a gaban shi ya kalli abincin yace duk ni zan cinye wanan Rama ?
Kada fa nai kiba kizo kice dani na tsufa maki nan gaba ki fara dan kwanaye kwanaye kuma kina baki son zama da tsoho.
Nai dan dariya mai kama da murmushi nace ai tunda bance ma tsoho ba da farko yanzu ma bazance ba don ni din ma yanzu ai ba yarinya bace.
Muna cikin hiran sai ga ta fito daga daki tace dear kasan na fadi a gaban ka amma ko ka shiga ka dubani kaga ya jikin nawa gashi yanzu duk jikin nawa ciwo yake min wallahi.
Yace ki sha magani mana tace ni asibiti nake son zuwa aduba min kafana don ciwo yake min yace amma ba yau ba kan don dare ya yi yanzu.
Ta wani bata rai bataso haka ba taso ne ta tasa shi a gaba sukama hanya zuwa asibi a cikin daren nan ta nuna man iyakana dashi sai bai biye mata ba yace tasha magani agani zuwa gobe.
Sai da ta wuce nace dama ina son ka huta na fada ma an turo min da sako ana neman mu ranan monday wurin interview asibitin da mukai service.
Yace a, a shine baki fada min ba Rahama wanan ai ba karamin magana bane yanzu zanyi waya da MD naji yaya ake process din abin naku.
Nan a wurin ya kira sukai dan magana yace ba matsala na shigo kawai ranan monday din za a duba ai ina da kwazo sosai sun sani.
Mutum zai iya fahinta yanayin mu a lokacin yadda muke daukin junan mu sai dai ba dama komai don engine bai aiki a kaina ko kadan dan wasan da ma yakanyi da farko idan yayi yanzu sai gari ya waye mai ba lafiya a jikin shi.
Mutum zai gane yana cikin damuwa don sai matsala ya faru zaka san idan mutum yana kaunar ka baka sanin zurfin kaunar sai idan matsala ya gitta a tsakanin ku zaka gane zurfin kaunarva gare ka kasan yadda mutum ya damu da kai.
Hakane yanzu a kullun bakin daddy bai gajiya da kwantar min da hankali yana bani hakkuri kan matsalan dake faruwa damu din.
Nakan yi murmushin yake nace haba daddy bakomai mana ai matsala ne kowa yasan ta sai yace Rahama nasan ina cuta maki sosai sai dai hakkurin ki bai bari a fahinci muna da matsala ni dake.
Don da watace da yanzu duniya ta fahinci halin da muke ciki ko ansan muna da matsala wurin wanan fannin.
Wanan kwantar min da hankalin da yake yasa ban dauku matsalan nakaishi can kasan zuciya na ba sai ma kara kaimin da nayi wurin kyautata mai fiye da koda yaushe yadda wani ba zai iya fahinta ba.
Ina shiga dakin shi kullun nake da duty na kwana a ciki indai ba mun dan samu matsala bane nai fushi dashi.
Don a dakina nake yaji bana fita bana kai kara gun kowa yadda naga sunayi ban taba kai karan shi a wani ba duk zaman mu dashi na aure.
Yau ma na shirya tsab nabi bayan shi zuwa dakin hindatu da ban san may yasa idan ina duty zata dauki lokaci zaune afalo wani lokaci sai na shige zata bar falon.
Yau ma tana ganin na shige ta mike ta fada dakinta ta jawo wani roba fari can kasan kayan ta inda ta boye ta dauko wani abu mai kama da baka ta hada shi yadda takeyi kullun.
Ina shiga dakin ya fito daga wanka yana tsaye yana fesa turare a jikin shi na shigo dakin da sallama na.
Jin sallama na yasa shi dan juyowa gare ni yana murmushi yace har yaran sun kwanta ke nan nace sunyi barci tun dazun ai.
Karban turaren nayi naci gaba da fesa mashi sai bina da kallo yake yana murmushi da kada kai kawai.
Nace daddy lafiya ko naga sai wani kallo kake min ko yau injin ta samu service ne ban sani ba daidai da nake mayar da turaren a mazaunin shi yace .
Da haka zai kasance gare mu yau din aida nafi kowa farin ciki ko yaushe burina da fatana naga wanan matsalan ya tafi a gare mu.
Yace Rahama ni har yau na kasa kai karshen fahintar ki nace namay fa daddy ?
Yace baki ganewa ke kina da wani baiwa da ba kowa ne Allah keyiwa shi ba ke kanki baki sanin kina dashi sai dai na tare dake ya sanar maki da hakan.
Nace daddy wani irin baiwa ce wanan kuwa dani ban san da shi ba haka sai kai ka san shi a gare ni ?
Ya murmusa yana nufar gado yace ba yanzu zan fada maki shi ba sai nan gaba idan komai ya daidaita tsakanin mu.
Sai ya zauna a bakin gadon yace Rahama ina tausaya maki ina cutar dake a shekarun ki baki cancanci wanan hukuncin ba haka a wanan lokacin.
Rama ba zan iya boye maki ba ina tausaya maki matuka kuma don abin nawa a kwai son kai a cikin sa na kasa sama muna mafita a matsalar mu idan wani yaji haka tsawon lokacin da muka dauka a matsalan nan sai a ga na faye zama mai son kaina da yawa.
Nace haba daddy saboda may zakace haka kuma ai komai mukkadari ne daga ubangiji mutum bai dorawa kan shi lalura ai.
Yace nasan haka Rahama amma irin hakkurin da kikayi a dan tsakankanin nan ba kowa ne zai iya daure wanan irin matsalar ba haka.
Gashi ke kinyiwa wanan matsalar kankantar dauka da ace shekarun ki ya haura hakane nasan ba matsala zaki iya jure hakan har lokacin da Allah zai kawo muna mafita.
Nace ni ban damu ba daddy Allah dai ya bamu lafiya yace kwsnan zan tafi wani guri da nake kyautata zaton kila a shawon kan matsalan a can idan na tafi.
Nace daddy ban son kasawa kan ka tunane akan wanan matsalar saukin abin ma bani kadai bace a gun ka kana iya zuwa wani wajen wata kila acan ka dan samu kadace kayi.
Ni dai burina na zama mai cin wanan jerabawan da ubangiji ya aiko muna dashi bana zamo cikin masu kasa daurewa da kaddara ba.
Murmushi yayi gami da girgiza kan shi yace hakane amma wani lokaci abubuwa da dama sukan zowa bawa da sanadi don ai a gunki ne kawai wanan matsalan yake faruwa dani.
Nace dani da sauran duk a hannun ubangijin mu muke shi kadai ne kuma yasan dalilin yi hakan a gare mu don haka ka cire wanan damuwan a zuciyan ka kawai mu koma ga Allah ya kawo muna saukin alamarin.
Haka mukai ta hiran matsalar yana kankamay dani yana wasa da gashin kaina da yasha relexzer ya kwanta baya har barci yazo ya dauke mu bamu sani ba kowa da abinda zuciyar shi ke saka mai kan maganan.
Ina jin saukan numfashin shi alamar barci ne ya dan dauke mu na lalaba na mike daga saman gadon na shiga ban daki can na darji kuka na don na fahinci shima daddy yasan akwai matsala a wani wuri kamar yadda zarah ta fada min ranan.
To wa naiwa laifi yai min wanan mumunan hukuncin haka da sai mara imani zaiyiwa dan uwan shi haka a rayuwan zaman duniyan nan na dan lokaci kalilan.
Gashi na kasa fadawa inna ta matsalar da nake ciki kada hankalinta ya tashi na rasa wanda zan fadawa bayan Zarah da itama da kyat na iya fada mata komai.
Inna ce ya kamata na fadawa kuma ina jin nauyi da kunyan fadar irin magana haka a tsakanin mu ta yaya ma zan iyace mata wai miji baya iya kwanciya dani.
Don ni da farko banyi zaton wanan
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22Chapter 23Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32Chapter 33Chapter 34Chapter 35Chapter 36Chapter 37Chapter 38Chapter 39Chapter 40Chapter 41Chapter 42Chapter 43Chapter 44Chapter 45Chapter 46Chapter 47Chapter 48Chapter 49Chapter 50Chapter 51Chapter 52Chapter 53Chapter 54Chapter 55Chapter 56Chapter 57Chapter 58Chapter 59Chapter 60Chapter 61Chapter 62Chapter 63Chapter 64Chapter 65Chapter 66Chapter 67Chapter 68Chapter 69Chapter 70Chapter 71Chapter 72Chapter 73Chapter 74Chapter 75Chapter 76Chapter 77Chapter 78Chapter 79Chapter 80Chapter 81Chapter 82Chapter 83Chapter 84Chapter 85Chapter 86Chapter 87Chapter 88Chapter 89Chapter 90Chapter 91Chapter 92Chapter 93Chapter 94Chapter 95Chapter 96Chapter 97Chapter 98Chapter 99Chapter 100Chapter 101Chapter 102Chapter 103Chapter 104Chapter 105Chapter 106Chapter 107Chapter 108Chapter 109Chapter 110 Chapter 111Chapter 112Chapter 113Chapter 114Chapter 115Chapter 116Chapter 117Chapter 118Chapter 119Chapter 120Chapter 121Chapter 122Chapter 123Chapter 124Chapter 125Chapter 126Chapter 127Chapter 128Chapter 129Chapter 130Chapter 131Chapter 132Chapter 133Chapter 134Chapter 135Chapter 136Chapter 137Chapter 138Chapter 139Chapter 140Chapter 141Chapter 142Chapter 143Chapter 144Chapter 145Chapter 146Chapter 147Chapter 148Chapter 149Chapter 150Chapter 151Chapter 152Chapter 153