Kan zasu cutawa rayuwana kasancewa ta yarinya mai kwazo ga karatu ya kamata ace ko dai secondry din ne na gama ai.
Da kyat baba ya yarda koshi sai da maigari yai mai jan ido ya yarda don yasan idan yadawo gida akwai matsala tsakanin shi da mama idan taji zan karasa karatuna a shekaran nan.
Haka kuwa akayi don ranan ba karamin tashin hankali akayi ba tsakanin baba da mama.
Take cewa ai dama har dashi cikin cin kudin da mazan dake lalata dani suke bani.
Idan bashi ba don may zaice sai na karasa karatuna may ye amfanin karatun diya mace na boko da za, a kare shi a gidan miji.
Tana kurin tana karatun boko watafi kyau da za, a nace kan sai nayi boko nakai wasu can daban
Ni dai tunda naji baba yace na shirya gobe na koma makaranta nake cikin farin ciki da zumudi don ina gani kila ina da rabo ne a duniya.
Washe gari tun da safe na bar gidan duk da na saba idan zan tafi sai na sallami kowa na gidan kafin na fita.
Yau ma dana shirya munyi sallama da inna na nufi kofan mama tun ban karaso ba tana hangoni take cewa za, a yawon tazubar din ko akuyan daure ta samu saki.
Duniya ce dai ayi ta a sannu don maza ba abin goyo bane da sun gama yayin ka su ka hango wata kai kuma ka tashi aiki ke nan.
Ni dai ban biye taba nace mama ni na tafi kafin ma naji amsan da zata bani har na fice daga gidan ko.
A kofa na hadu da babana da zai shigo gida na dan rabe gefe nai mashi ina kwana yabini da harara yana cewa har zaki tafi ke nan ?
Nace eh baba yace Rahama ki kula da rayuwan ki kada ki ja min abin kunya a garin nan.
Duk dai har yau babu wanda ya taba kawo min karan ki na assha amma dai kuma maganan maman ku abin dubawa ne.
Don diya mace ba, a saka mata ido tayi yadda take so dole sai da tsawatawa akai.
Nace nagode baba insha Allahu zan fake na tafi ina tunanen halin baba idan mama bata kusa zakaji ya dan sanyaya ma al, amarin mu .
Amma da zaran yaga idon mama damu da makiyan shi duk daya muke gare shi kamar zai yanka mu da ran mu.
Bani ba har yan kanne na biyu hakan ya shafa don dai kawai su maza ne basu zama gida su.
Ina isa makaran ta ban tsaya ba sai office din malam Mudi don nasan shine kadai zai iya min wanan kokarin.
Na samay shi yana shirin fita na duka nagaida shi cikin ladabi nake cewa kuma malam nazo ne nai ma godiya don nasan kaine da wanan kokarin.
Yace hakane Rahama don haka kema ki kula da rayuwan ki don ban san dalilin yin hakan ba ga mahaifinki.
Ko da yake mun samu labarin cewa takurawan kishiyar mahaifiyan ki ne akan ku ya shafe ki.
Ki kula ki mayar da hankalin ki wata rana sai labari idan kin dage Allah zai kawo maki mafita da yardan ubangiji.
Nai mashi godiya tare da sallama na koma class sai sheri yan uwana dalibai suke min wai ta fudu ta dawo.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE, , ,
4
IDAN KIN BIYA KIKA BA WA WANDA BAI BIYA BA MUN BARKI GA ALLAH YAR UWA, , ,
Tafe nake da robar talla na yau doya ce dafafa gishiri sai kuli, kuli da yaji aciki wana nake barbadawa mutum idan ya saya.
Daya daga cikin tufafin da Anty ta bani na saka wasu material ne masu walkiya walwal idan kana tafiya da su.
Tafe nake nayi irin digirgire din kaya a saman kai din nan hankalina a kwamce nake tafe .
Kai kai kai da sauri dayan mutumin da suke zaune a tare ya juya yana kallon gurin da nafarkon mai magana yake kallo,
Da sauri suka kawar da kan su daga kallo na don na kusa karasowa inda suke a zaune.
Dama yarinyar nan haka take da kyau ashe kamar wata matar gwauna haka da ita ?
Wai may ne ne haka salla ni duk ka cika ni da zancen yarinyar nan yace wallahi ranan da kuke zamcen ta bani kusa sai yanzu nai mata kallon tsab ai.
Garbati idan kana son abinka kawai ka shige kai tsaye nan ai babban iri ne ga wanda ya samu.
Allah na tuba ko kyawawan yaya ake haifa wa mutum a gida ai ya wadatar akan su.
Ni fa ko da kukaji nai magana a ranan ba wai har zuci nake zance na ba amma naga kuna gidada abin haka ku ?
Garbati kada kaiwa kan ka salalalan tsiya walahi in har kana so kasa kai kawai na fada maka kada ka tsaya garin kallon ruwa wani yai maka tsalle.
Kaga dama ina ga ba ai mata wani matsayi ba zuwa yanzu yan uwan tane kawai nake gani suna fitowa hira da dare amma banda ita.
Wanda ake wa fadancin ake kuma zuzuta shi a kaina sai yanzu yai magana yace.
Kai salla, banki ta naku ba fa akan maganan yarinyar nan sai dai gaskiya a yadda shekaru na yakai yanzu sai nake gani ai na wuce tsayawa koda akan yyayyenta ne da kake magana balle ita.
Sannan kaga yarinyar ga ta dai karama ce amma akwaita da kwarji a fuskanta kamar ba karamar yarinya ba.
Gashi kuma bata bada fuska kamar sauran mata ko yaushe fuskan ta a daure yake ba fara, a agare ta.
Sau tari da yawa nakan so na dan mata magana koda na wasa ne amma da na dumfare ta sai naji gabana yana faduwa tana matukar yi min kwarjini sosai a idona.
Salla yace assha Garbati kada ka zama ragon maza mana yanzu kuma manya mata ma mun sha gaban su babu gezau balle wanan yar ficiciyar karamar yarinyar zata kayar maka da gaban ka.
Don haka idan har kana ciki ka bari zan maka iso har gida na gabatar dakai tun wani bai riga ka ba.
Da zaran nema iso a gidan su insha Allahu komai zaizo daidai koda baka zo tadi ba gurin zance sai kawai ayi yadda za,a a daure aure batare da kowa ya farga ita din taka ce ba.
Kai haba salla yaushe rabon da ai irin wanan neman auren yanzu da kai ya waye wa mutane.
Sallah yace kai dai in har kana ciki ce min eh kawai kasha mamaki indai har zaka bude bakin aljihun ka komai zai tafi daidai insha Allahu.
Har na kawo daidai gurin da suke zaune suna zance na ban ko gaida dasu ba don rabin hiran su ya dan zo a kunne na naji.
In ba gulma irin ta mutanen yau ba ina ni ina su Lawisa da koda aka haifesu ba, a auri uwata ba a gidan.
Don an kawo sadakin auren su zasu yi aure aiba abin mamaki bane hakan idan anyi la, akari da irin girmuwan da sukai min.
Ban saka zancen dattijan banzan nan a raina ba don nasan ba abu bane wanda zai yiyu suke magana don jin dadin fatan bakin su ne kawai sukeyi.
Nikan inda naji zance tsofin banzan kamar yadda na sa masu suna a gurin na bar zancen.
****** ********* ******
Sai bayan kamar kwana biyu da zancen ne da dare na dawo daga tallah nayi diban ruwana da wuri na dauko littafaina ina bita don mun kusa zana jerabawan mu na fita tunda na samu an min jummping a school bana zan kare karatun secondary dina.
Ina jin lokacin da baba ya shigo gida bai jima da shigowa ba akai mai sallama yafita.
Ya dan dauki lokaci a waje kafin ya shigo ina jin mama na mitan wai abincin shi yana sanyi bai shigo yaci ba.
Ya dawo cikin gidan yanayin da ya shigo dashi kawai zaka kalla kasan yana cikin damuwa.
Sai da ya zauna yagama cin abincin shine sa, an nan ya umurci lawal yaron mama karami ya kira mai Inna.
Bata jima ba tafito ta samay su zaune da mama a saman tabar ma guda itama ta samu guri ta zauna don tasan magana ce mai muhinmanci zai yi dasu.
Bayan ta zauna ne ya dube su yace ina Asiya tace gani gaban ka ai malam ina sauraren ka.
Yace Asiya wani sha, ani ne ya taso gamay da yar ki Rahama.
Jin haka da yace yasa Inna ta kara natsuwa tana sauraren shi tunda taji yace yar ta Rahama tasan ba abin alheri bane zai fada mata a lokacin.
Don indai lafine a gidan dama bai wuce yaran dakin ta ko yaushe mussan ma ita Rahama din da take kamar ta tsone makowa ido a gidan.
Shiru baba yayi na dan lokaci kamar yana shakkun fadin abinda yake son fada masu a lokacin.
Sai zuwa can ya dan nisa yace dama wani mutum ne yazo yana son auren ita Rahama din .
Nikuma har na bashi saboda naga dacewan hakan don haka na bashi dama akan yazo yaga yarinyar.
Inna tace idan da Alheri a ciki Allah ya tabbatar da alherin sa .
Baba yaji dadin hadin kan da Inna raba shi ba tare da tsayawa jayayya ba akai ko wani kwankwanto.
Tana kokarin mikewa tabar gurin yace idan kin shiga ki turo min ita Rahama din.
Inna tace to kawai ta mike tabar gurin ran ta a bace sai dai su basu gane ba.
Bata kai ga shigewa ba taji mama na fadin ai ma an mata gata koma waye tunda har yau babu ko karen da ya taba sallama mata gidan nan.
Tana shiga daki ta samay ni nabar karatun da nakeyi ina sauraren maganan su.
Tana fada min sakon baba na saka hijjab dina nafito gurin da suke zaune tare da mama din.
Na durkusa tare da gaida baba ta amsa min a kasalance cikin wani yanayi mara dadi.
Sai da ya dan kalle ni Yake cewa Rahama nace uwarki ta kira min ke ne saboda ina son sanar dake Garbati ya gane ki yace yana son ki kuma da aure.
Ni kuma naga dacewan hakan na bashi ke ina son ki zama yarinya mai ladabi da biyayya kibi umurni na don dama nice da alhakin zaba maki mijin da ta dace dake.
Wani irin mugun faduwan gaba naji tare da wani irin jiri a lokaci daya kila badon ina a tsugunne ba dana fadi a lokacin.
A hankali na dago kai nace baba wani garbati ke nan kuma a gatin nan ?
Mama ta tare da cewa ungo nan Garbati nawa kika sani a garin nan Garbati dai mana mai arzikin garin nan dai .
Kasancewa na ya mai tarbiya ga iyayyena da sanin darajan su tare da sanin hakkin aurena ya rataya a garesu don sune ga kaidan musulunci dama ya dace su zaba min miji aure na fari a rayuwana yasa nai shiru.
Amma kuma duk da haka ace kuma Garbati Garbatin da a girmay ya girmay ma baba ba kadan ba.
Gaskiya wanan zance na baba da yanayin sa sun bani mamaki matuka ganin cewa duk yan uwana mata zabin kansu ake basu su aura tun farko.
Bayan haka aiga Lawisa da Rukkaiyya a gidan duk sun girmay min a shekaru don may su ba za, a basu shi ba sai ni da aka rainawa kurar uwata dani.
Ni da ko yaushe nake hango kaina da a mainasara nake ga rayuwana zan tsaya tsayin daka naga nayi karatu mai tsawo a gidan mu, shine zan buge ga auren wani tsoho wanda ma ya girmay ma mahaifina ga shekaru sosai don dai yana da dan abin hannun shine ba, a gane shekarun shi ko may ?
Ko kadan bazan iya yiwa babana mussu ba gama yadda naga mama ta gwagwafe ta tsura min ido tana son taji wani rashin mutunci ya fito daga guri na ko inna a lokacin.
Na sunnkuyar da kaina a kasa murya a tausashe na ce baba na gode Allah ya tabbatar da abinda yafi zama Alheri .
Yace insha Allahu hakan shine alherin ki Rahama tunda kikaga babban mutum haka yazo neman auren ki.
Don haka sai ki shirya don zai fara zuwa zance gurin ki duk da yace shi ba irin na yara zaiyi ba zai dai zo koda saudaya ne kuga juna dashi.
Ki kwantar da hankali ki kada kika kamar shi ba yaro bane kice zaki ta da hankalin ki akai na tabbatar da zakiji dadi a gidan sa don in kiyi la, akari duk kauyen nan babu maihalinsa ga kuma kula da iyalin sa da yakeyi.
Bake ba har mu nan nasan zamu amfana da auren ki dashi insha Allahu.
Take naji gabana ya yanke nace a raina watau auren kudi ne baba zai yi dani ke nan ko tunda har ya soma fadar haka.
A take naji jikina yai min wani irin sanyi a lokaci daya sai faman sake sake nake a raina wanda daga karshe ma banji abinda yake fadi ba sam.
Sai muryan shi naji yana cewa shike nan zaki iya tashi ki wuce Allah yasa mu dace.
Da kyat na iya mikewa tsaye sai kace wace kwai ya fashewa a ciki nabar gurin zuwa dakin mu .
Nan nake jin muryan mama tana cewa dama may na fada maka tunda makwadaitane daga ita har uwar ai yarda zasuyi.
Ina shiga daki inna tace a zaune ta rafka uban tagumi da hannu daya dagani tana cikin tashin hankali ita ma.
Zama nayi a kusa da mahaifiyan tawa cikin muryan kuka nace Inna kinji irin abinda yayi da rayuwana ?
Inna tace cikin jan dogon ajiyan zuciya, naji yarinya yaya zamuyi tunda shi ya haife ki ?
Kuma kin san yadda gidan nan yake da gani ba ra, ayin kasa bane saka shi yin haka akayi don kawai muyi magana ta zama muna abin gori da fade a tsakar gida.
Don haka abinda nake so dake shi kada ki sawa kanki damuwa akan zancen nan ko kadan mu bar wa Allah al, amarin shi don yana sane da komai.
Na dan dago na kalli Inba nace shi ke nan inna nabarwa Allah din komai kamar yadda kikace.
Ina fadin haka na dunkule a saman tabar man da nake kwana zuciya tab da tunane rayuwan da zan fada ciki.
A iya sani na dai gidan Garbati babban gida ne don har da sarakan shi zaune a gidan suke.
Mutum ne mai mai neman kudi yana noma yana kiwo da kuma hadawa da kasuwanci.
Gwargwado akwai kulawa za, ace ga iyalinshi a kauyen mu don baka ganin su a cikin kazanta kamar sauran matan garin.
Amma ina yarinyar yar shekara goma sha biyar za, a aura min tsohon mutum kamar Alhaji garbati.
Haka na kwana ina mutsutsuri saman tabar mana cikin tunane ga matan shi dukka uku bazasu rasa yara sama da takwas ko tara ba ni Rahama yaya zanyi zama cikin wa yan nan kakanin nawa a matsayin kishiyoyi ?
Ashe abinda mu bamu sani ba ta gurin mama suka fara biyowa da zancen itace ma ta hurewa baba kunne akan maganan don yaso yaki maganan.
Amma ra kawo mashi kabbali da ba, adi har yaji yagamsu da maganan ta ya yarda akan zai badani ga garbatin.
A yadda ya nuna ma baison a dauki lokaci ba ai auren ba don kada a hure min kunne.
****** ********* ******
Washegari dagani har inna ta babu wani mai sukuni a gidan mu sai mamace da yaran ta suke gadan su a tsakar gida.
Ina jin Rukaiyya tana wanki tana waka kamar haka yarinya ancuce ki an hada hadaki da tsoho, tsoho wari kakan ki shine kika aure ga hurhura gyamu kamar na kucaki.
Inna tace min kada ki kulata Allah yafiso idan da hannun uwar su fa alamarin nan Allah zai saka maki yarinya.
Dayake ba makaranra a ranan ban yi sana, a ba don bazan iya tallah ba a halin da nake ciki.
Da kyat na iya diban ruwa a randa na tafi na watsowa jikina ko zan danji dama.
Na zauna nai kwalliya na tare da saka tufafi a jikina inna tace na fita na gyara mata gurin girkin su kafin ta fito.
Mama dake zaune saman tabarma tana sauraren redio kaduna ana zabi kanka na yamma.
Ta izo daurin dan kwallinta a gaba kamar wata magajiya da ruwa yakarewa.
Ina fitowa tace kayya kyau da kwalliya ya kare kuma a gidin tsoho atafi akarata can a iske su sabuwa muna nan za, a bamu labari mu dai.
Wasu hawaye ne naji sun zubo min dana duka na fara shara ashe tagani sai cewa tayi ai idan mutum yace kwadayi ne yakai kashe yanzu kam.
An iya shiga lungu da mazan banza sunawa mutum juye ana muna takama wai sa, an talla kega mutum yau ga inda sa, an yakare a gidin tsoho tukuf.
Yo Allah na tuba kodai ni din nan tsuhuwa akace za, a hada da garbati ai sai inda karfina yakare to abinka da wanda ya saba da maza ko gezau babu.
Daga kofa na dago zan ba wa mama amsa naga inna a
Showing 12001 words to 15000 words out of 456145 words
Da kyat baba ya yarda koshi sai da maigari yai mai jan ido ya yarda don yasan idan yadawo gida akwai matsala tsakanin shi da mama idan taji zan karasa karatuna a shekaran nan.
Haka kuwa akayi don ranan ba karamin tashin hankali akayi ba tsakanin baba da mama.
Take cewa ai dama har dashi cikin cin kudin da mazan dake lalata dani suke bani.
Idan bashi ba don may zaice sai na karasa karatuna may ye amfanin karatun diya mace na boko da za, a kare shi a gidan miji.
Tana kurin tana karatun boko watafi kyau da za, a nace kan sai nayi boko nakai wasu can daban
Ni dai tunda naji baba yace na shirya gobe na koma makaranta nake cikin farin ciki da zumudi don ina gani kila ina da rabo ne a duniya.
Washe gari tun da safe na bar gidan duk da na saba idan zan tafi sai na sallami kowa na gidan kafin na fita.
Yau ma dana shirya munyi sallama da inna na nufi kofan mama tun ban karaso ba tana hangoni take cewa za, a yawon tazubar din ko akuyan daure ta samu saki.
Duniya ce dai ayi ta a sannu don maza ba abin goyo bane da sun gama yayin ka su ka hango wata kai kuma ka tashi aiki ke nan.
Ni dai ban biye taba nace mama ni na tafi kafin ma naji amsan da zata bani har na fice daga gidan ko.
A kofa na hadu da babana da zai shigo gida na dan rabe gefe nai mashi ina kwana yabini da harara yana cewa har zaki tafi ke nan ?
Nace eh baba yace Rahama ki kula da rayuwan ki kada ki ja min abin kunya a garin nan.
Duk dai har yau babu wanda ya taba kawo min karan ki na assha amma dai kuma maganan maman ku abin dubawa ne.
Don diya mace ba, a saka mata ido tayi yadda take so dole sai da tsawatawa akai.
Nace nagode baba insha Allahu zan fake na tafi ina tunanen halin baba idan mama bata kusa zakaji ya dan sanyaya ma al, amarin mu .
Amma da zaran yaga idon mama damu da makiyan shi duk daya muke gare shi kamar zai yanka mu da ran mu.
Bani ba har yan kanne na biyu hakan ya shafa don dai kawai su maza ne basu zama gida su.
Ina isa makaran ta ban tsaya ba sai office din malam Mudi don nasan shine kadai zai iya min wanan kokarin.
Na samay shi yana shirin fita na duka nagaida shi cikin ladabi nake cewa kuma malam nazo ne nai ma godiya don nasan kaine da wanan kokarin.
Yace hakane Rahama don haka kema ki kula da rayuwan ki don ban san dalilin yin hakan ba ga mahaifinki.
Ko da yake mun samu labarin cewa takurawan kishiyar mahaifiyan ki ne akan ku ya shafe ki.
Ki kula ki mayar da hankalin ki wata rana sai labari idan kin dage Allah zai kawo maki mafita da yardan ubangiji.
Nai mashi godiya tare da sallama na koma class sai sheri yan uwana dalibai suke min wai ta fudu ta dawo.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE, , ,
4
IDAN KIN BIYA KIKA BA WA WANDA BAI BIYA BA MUN BARKI GA ALLAH YAR UWA, , ,
Tafe nake da robar talla na yau doya ce dafafa gishiri sai kuli, kuli da yaji aciki wana nake barbadawa mutum idan ya saya.
Daya daga cikin tufafin da Anty ta bani na saka wasu material ne masu walkiya walwal idan kana tafiya da su.
Tafe nake nayi irin digirgire din kaya a saman kai din nan hankalina a kwamce nake tafe .
Kai kai kai da sauri dayan mutumin da suke zaune a tare ya juya yana kallon gurin da nafarkon mai magana yake kallo,
Da sauri suka kawar da kan su daga kallo na don na kusa karasowa inda suke a zaune.
Dama yarinyar nan haka take da kyau ashe kamar wata matar gwauna haka da ita ?
Wai may ne ne haka salla ni duk ka cika ni da zancen yarinyar nan yace wallahi ranan da kuke zamcen ta bani kusa sai yanzu nai mata kallon tsab ai.
Garbati idan kana son abinka kawai ka shige kai tsaye nan ai babban iri ne ga wanda ya samu.
Allah na tuba ko kyawawan yaya ake haifa wa mutum a gida ai ya wadatar akan su.
Ni fa ko da kukaji nai magana a ranan ba wai har zuci nake zance na ba amma naga kuna gidada abin haka ku ?
Garbati kada kaiwa kan ka salalalan tsiya walahi in har kana so kasa kai kawai na fada maka kada ka tsaya garin kallon ruwa wani yai maka tsalle.
Kaga dama ina ga ba ai mata wani matsayi ba zuwa yanzu yan uwan tane kawai nake gani suna fitowa hira da dare amma banda ita.
Wanda ake wa fadancin ake kuma zuzuta shi a kaina sai yanzu yai magana yace.
Kai salla, banki ta naku ba fa akan maganan yarinyar nan sai dai gaskiya a yadda shekaru na yakai yanzu sai nake gani ai na wuce tsayawa koda akan yyayyenta ne da kake magana balle ita.
Sannan kaga yarinyar ga ta dai karama ce amma akwaita da kwarji a fuskanta kamar ba karamar yarinya ba.
Gashi kuma bata bada fuska kamar sauran mata ko yaushe fuskan ta a daure yake ba fara, a agare ta.
Sau tari da yawa nakan so na dan mata magana koda na wasa ne amma da na dumfare ta sai naji gabana yana faduwa tana matukar yi min kwarjini sosai a idona.
Salla yace assha Garbati kada ka zama ragon maza mana yanzu kuma manya mata ma mun sha gaban su babu gezau balle wanan yar ficiciyar karamar yarinyar zata kayar maka da gaban ka.
Don haka idan har kana ciki ka bari zan maka iso har gida na gabatar dakai tun wani bai riga ka ba.
Da zaran nema iso a gidan su insha Allahu komai zaizo daidai koda baka zo tadi ba gurin zance sai kawai ayi yadda za,a a daure aure batare da kowa ya farga ita din taka ce ba.
Kai haba salla yaushe rabon da ai irin wanan neman auren yanzu da kai ya waye wa mutane.
Sallah yace kai dai in har kana ciki ce min eh kawai kasha mamaki indai har zaka bude bakin aljihun ka komai zai tafi daidai insha Allahu.
Har na kawo daidai gurin da suke zaune suna zance na ban ko gaida dasu ba don rabin hiran su ya dan zo a kunne na naji.
In ba gulma irin ta mutanen yau ba ina ni ina su Lawisa da koda aka haifesu ba, a auri uwata ba a gidan.
Don an kawo sadakin auren su zasu yi aure aiba abin mamaki bane hakan idan anyi la, akari da irin girmuwan da sukai min.
Ban saka zancen dattijan banzan nan a raina ba don nasan ba abu bane wanda zai yiyu suke magana don jin dadin fatan bakin su ne kawai sukeyi.
Nikan inda naji zance tsofin banzan kamar yadda na sa masu suna a gurin na bar zancen.
****** ********* ******
Sai bayan kamar kwana biyu da zancen ne da dare na dawo daga tallah nayi diban ruwana da wuri na dauko littafaina ina bita don mun kusa zana jerabawan mu na fita tunda na samu an min jummping a school bana zan kare karatun secondary dina.
Ina jin lokacin da baba ya shigo gida bai jima da shigowa ba akai mai sallama yafita.
Ya dan dauki lokaci a waje kafin ya shigo ina jin mama na mitan wai abincin shi yana sanyi bai shigo yaci ba.
Ya dawo cikin gidan yanayin da ya shigo dashi kawai zaka kalla kasan yana cikin damuwa.
Sai da ya zauna yagama cin abincin shine sa, an nan ya umurci lawal yaron mama karami ya kira mai Inna.
Bata jima ba tafito ta samay su zaune da mama a saman tabar ma guda itama ta samu guri ta zauna don tasan magana ce mai muhinmanci zai yi dasu.
Bayan ta zauna ne ya dube su yace ina Asiya tace gani gaban ka ai malam ina sauraren ka.
Yace Asiya wani sha, ani ne ya taso gamay da yar ki Rahama.
Jin haka da yace yasa Inna ta kara natsuwa tana sauraren shi tunda taji yace yar ta Rahama tasan ba abin alheri bane zai fada mata a lokacin.
Don indai lafine a gidan dama bai wuce yaran dakin ta ko yaushe mussan ma ita Rahama din da take kamar ta tsone makowa ido a gidan.
Shiru baba yayi na dan lokaci kamar yana shakkun fadin abinda yake son fada masu a lokacin.
Sai zuwa can ya dan nisa yace dama wani mutum ne yazo yana son auren ita Rahama din .
Nikuma har na bashi saboda naga dacewan hakan don haka na bashi dama akan yazo yaga yarinyar.
Inna tace idan da Alheri a ciki Allah ya tabbatar da alherin sa .
Baba yaji dadin hadin kan da Inna raba shi ba tare da tsayawa jayayya ba akai ko wani kwankwanto.
Tana kokarin mikewa tabar gurin yace idan kin shiga ki turo min ita Rahama din.
Inna tace to kawai ta mike tabar gurin ran ta a bace sai dai su basu gane ba.
Bata kai ga shigewa ba taji mama na fadin ai ma an mata gata koma waye tunda har yau babu ko karen da ya taba sallama mata gidan nan.
Tana shiga daki ta samay ni nabar karatun da nakeyi ina sauraren maganan su.
Tana fada min sakon baba na saka hijjab dina nafito gurin da suke zaune tare da mama din.
Na durkusa tare da gaida baba ta amsa min a kasalance cikin wani yanayi mara dadi.
Sai da ya dan kalle ni Yake cewa Rahama nace uwarki ta kira min ke ne saboda ina son sanar dake Garbati ya gane ki yace yana son ki kuma da aure.
Ni kuma naga dacewan hakan na bashi ke ina son ki zama yarinya mai ladabi da biyayya kibi umurni na don dama nice da alhakin zaba maki mijin da ta dace dake.
Wani irin mugun faduwan gaba naji tare da wani irin jiri a lokaci daya kila badon ina a tsugunne ba dana fadi a lokacin.
A hankali na dago kai nace baba wani garbati ke nan kuma a gatin nan ?
Mama ta tare da cewa ungo nan Garbati nawa kika sani a garin nan Garbati dai mana mai arzikin garin nan dai .
Kasancewa na ya mai tarbiya ga iyayyena da sanin darajan su tare da sanin hakkin aurena ya rataya a garesu don sune ga kaidan musulunci dama ya dace su zaba min miji aure na fari a rayuwana yasa nai shiru.
Amma kuma duk da haka ace kuma Garbati Garbatin da a girmay ya girmay ma baba ba kadan ba.
Gaskiya wanan zance na baba da yanayin sa sun bani mamaki matuka ganin cewa duk yan uwana mata zabin kansu ake basu su aura tun farko.
Bayan haka aiga Lawisa da Rukkaiyya a gidan duk sun girmay min a shekaru don may su ba za, a basu shi ba sai ni da aka rainawa kurar uwata dani.
Ni da ko yaushe nake hango kaina da a mainasara nake ga rayuwana zan tsaya tsayin daka naga nayi karatu mai tsawo a gidan mu, shine zan buge ga auren wani tsoho wanda ma ya girmay ma mahaifina ga shekaru sosai don dai yana da dan abin hannun shine ba, a gane shekarun shi ko may ?
Ko kadan bazan iya yiwa babana mussu ba gama yadda naga mama ta gwagwafe ta tsura min ido tana son taji wani rashin mutunci ya fito daga guri na ko inna a lokacin.
Na sunnkuyar da kaina a kasa murya a tausashe na ce baba na gode Allah ya tabbatar da abinda yafi zama Alheri .
Yace insha Allahu hakan shine alherin ki Rahama tunda kikaga babban mutum haka yazo neman auren ki.
Don haka sai ki shirya don zai fara zuwa zance gurin ki duk da yace shi ba irin na yara zaiyi ba zai dai zo koda saudaya ne kuga juna dashi.
Ki kwantar da hankali ki kada kika kamar shi ba yaro bane kice zaki ta da hankalin ki akai na tabbatar da zakiji dadi a gidan sa don in kiyi la, akari duk kauyen nan babu maihalinsa ga kuma kula da iyalin sa da yakeyi.
Bake ba har mu nan nasan zamu amfana da auren ki dashi insha Allahu.
Take naji gabana ya yanke nace a raina watau auren kudi ne baba zai yi dani ke nan ko tunda har ya soma fadar haka.
A take naji jikina yai min wani irin sanyi a lokaci daya sai faman sake sake nake a raina wanda daga karshe ma banji abinda yake fadi ba sam.
Sai muryan shi naji yana cewa shike nan zaki iya tashi ki wuce Allah yasa mu dace.
Da kyat na iya mikewa tsaye sai kace wace kwai ya fashewa a ciki nabar gurin zuwa dakin mu .
Nan nake jin muryan mama tana cewa dama may na fada maka tunda makwadaitane daga ita har uwar ai yarda zasuyi.
Ina shiga daki inna tace a zaune ta rafka uban tagumi da hannu daya dagani tana cikin tashin hankali ita ma.
Zama nayi a kusa da mahaifiyan tawa cikin muryan kuka nace Inna kinji irin abinda yayi da rayuwana ?
Inna tace cikin jan dogon ajiyan zuciya, naji yarinya yaya zamuyi tunda shi ya haife ki ?
Kuma kin san yadda gidan nan yake da gani ba ra, ayin kasa bane saka shi yin haka akayi don kawai muyi magana ta zama muna abin gori da fade a tsakar gida.
Don haka abinda nake so dake shi kada ki sawa kanki damuwa akan zancen nan ko kadan mu bar wa Allah al, amarin shi don yana sane da komai.
Na dan dago na kalli Inba nace shi ke nan inna nabarwa Allah din komai kamar yadda kikace.
Ina fadin haka na dunkule a saman tabar man da nake kwana zuciya tab da tunane rayuwan da zan fada ciki.
A iya sani na dai gidan Garbati babban gida ne don har da sarakan shi zaune a gidan suke.
Mutum ne mai mai neman kudi yana noma yana kiwo da kuma hadawa da kasuwanci.
Gwargwado akwai kulawa za, ace ga iyalinshi a kauyen mu don baka ganin su a cikin kazanta kamar sauran matan garin.
Amma ina yarinyar yar shekara goma sha biyar za, a aura min tsohon mutum kamar Alhaji garbati.
Haka na kwana ina mutsutsuri saman tabar mana cikin tunane ga matan shi dukka uku bazasu rasa yara sama da takwas ko tara ba ni Rahama yaya zanyi zama cikin wa yan nan kakanin nawa a matsayin kishiyoyi ?
Ashe abinda mu bamu sani ba ta gurin mama suka fara biyowa da zancen itace ma ta hurewa baba kunne akan maganan don yaso yaki maganan.
Amma ra kawo mashi kabbali da ba, adi har yaji yagamsu da maganan ta ya yarda akan zai badani ga garbatin.
A yadda ya nuna ma baison a dauki lokaci ba ai auren ba don kada a hure min kunne.
****** ********* ******
Washegari dagani har inna ta babu wani mai sukuni a gidan mu sai mamace da yaran ta suke gadan su a tsakar gida.
Ina jin Rukaiyya tana wanki tana waka kamar haka yarinya ancuce ki an hada hadaki da tsoho, tsoho wari kakan ki shine kika aure ga hurhura gyamu kamar na kucaki.
Inna tace min kada ki kulata Allah yafiso idan da hannun uwar su fa alamarin nan Allah zai saka maki yarinya.
Dayake ba makaranra a ranan ban yi sana, a ba don bazan iya tallah ba a halin da nake ciki.
Da kyat na iya diban ruwa a randa na tafi na watsowa jikina ko zan danji dama.
Na zauna nai kwalliya na tare da saka tufafi a jikina inna tace na fita na gyara mata gurin girkin su kafin ta fito.
Mama dake zaune saman tabarma tana sauraren redio kaduna ana zabi kanka na yamma.
Ta izo daurin dan kwallinta a gaba kamar wata magajiya da ruwa yakarewa.
Ina fitowa tace kayya kyau da kwalliya ya kare kuma a gidin tsoho atafi akarata can a iske su sabuwa muna nan za, a bamu labari mu dai.
Wasu hawaye ne naji sun zubo min dana duka na fara shara ashe tagani sai cewa tayi ai idan mutum yace kwadayi ne yakai kashe yanzu kam.
An iya shiga lungu da mazan banza sunawa mutum juye ana muna takama wai sa, an talla kega mutum yau ga inda sa, an yakare a gidin tsoho tukuf.
Yo Allah na tuba kodai ni din nan tsuhuwa akace za, a hada da garbati ai sai inda karfina yakare to abinka da wanda ya saba da maza ko gezau babu.
Daga kofa na dago zan ba wa mama amsa naga inna a
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5 Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22Chapter 23Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32Chapter 33Chapter 34Chapter 35Chapter 36Chapter 37Chapter 38Chapter 39Chapter 40Chapter 41Chapter 42Chapter 43Chapter 44Chapter 45Chapter 46Chapter 47Chapter 48Chapter 49Chapter 50Chapter 51Chapter 52Chapter 53Chapter 54Chapter 55Chapter 56Chapter 57Chapter 58Chapter 59Chapter 60Chapter 61Chapter 62Chapter 63Chapter 64Chapter 65Chapter 66Chapter 67Chapter 68Chapter 69Chapter 70Chapter 71Chapter 72Chapter 73Chapter 74Chapter 75Chapter 76Chapter 77Chapter 78Chapter 79Chapter 80Chapter 81Chapter 82Chapter 83Chapter 84Chapter 85Chapter 86Chapter 87Chapter 88Chapter 89Chapter 90Chapter 91Chapter 92Chapter 93Chapter 94Chapter 95Chapter 96Chapter 97Chapter 98Chapter 99Chapter 100Chapter 101Chapter 102Chapter 103Chapter 104Chapter 105Chapter 106Chapter 107Chapter 108Chapter 109Chapter 110Chapter 111Chapter 112Chapter 113Chapter 114Chapter 115Chapter 116Chapter 117Chapter 118Chapter 119Chapter 120Chapter 121Chapter 122Chapter 123Chapter 124Chapter 125Chapter 126Chapter 127Chapter 128Chapter 129Chapter 130Chapter 131Chapter 132Chapter 133Chapter 134Chapter 135Chapter 136Chapter 137Chapter 138Chapter 139Chapter 140Chapter 141Chapter 142Chapter 143Chapter 144Chapter 145Chapter 146Chapter 147Chapter 148Chapter 149Chapter 150Chapter 151Chapter 152Chapter 153