sai muka duba shi garbati mutumin kirki ne zai iya rike maka ita amana.
Amma Jatau ko mutumin banza mutumin da bai san darajan kowa ba a garin nan sai kansa.
Babu wanan zancen yarinua dai bazawara ce abarta ta yi zabinta da kan ta dan doka yanuna yanzu ko budurwa ce idan bata son aure kada ai mata dole balle bazawara da tasan ciwon kan ta ko.
Fada sosai akai wa baba ya baro fada sai dai maigari ya boye mai cewa Inna ne da kan ta ta kawo karan shi yadai ce makwabtane suka zo suka fada mai wanan labarin .
Shiko a matsayin shi na maigari yana da ikon karewa yaro da babba hakin su idan za, a cuta masu.
Wanki nake yi kafin na shiga gidan mama Altine ina dan rarage kayan daudan mu ni da kanne na da Inna baba yadawo.
Kana ganin shi kasan babu lafiya tare dashi lokacin Inna ko har ta shirya tana jiran cin mutuncin da baba zai dawo mata dashi daga gidan mai gari.
Yana shigowa mama najin sallaman shi tai but tafito daga daki tana fadin malam lafiya dai ko wanan kira haka tunda sassafe haka ?
Yace lokacin da yake zama saman dutsen dake tsakar ana alwala a saman shi bari ke dai Lauratu munafunci baiyi ba wallahi.
Wai yanzu aka samu munafuki a cikin uguwan nan yakai karana kan auren yarinyar nan da Jatau gurin maigari.
Gaban mama yai mugun faduwa tace kara malam wake da wanan aikin haka yace wayasani yadai ce daga uguwar nan namu ne akai karana gurin shi.
Affan malam wa zaiyi karan ta inba ita da uwarta ba kaiwa kake tsamanin zaiyi haka waya damu da damuwan su anan balle ya kula al, amarin su.
Umm, umm lauratu daga nan ne dai aka fadawa maigari amma ai mace bata ganin mai gari kai tsaye wane ita nan.
Nan suka shiga dura ashar har mama na ikirarin ai ba maigari ne ya haifa mashi ya ba da zai mai iko akan gidan shi.
Baba yace Lauratu na rabaki da wanan zancen kada ki dauko min wani sabon rigima kuma don ni yanzu tsoron mutane nake ji su labe ta baya suna sauran ki.
Mama tace duk mai fadi yaje ya fadi amma aure ba fashi sai anyi shi tunda bashine ya haifa muna diya ba ba kuma cin shi a gidan mu.
Baba ya katse ta da cewa kina da kudin biyan taran da za ai min ke nan ko da kuma dauri kan na shiga hakkin diyata bada son ran ta ba.
Cikin mama ya duri ruwa sai da ta kewaya ban daki tafito ta samu baba a gurin yana fada har lokacin.
Nidai ina wanki na tare da hamdalla a cikin rai na don maigari da mama Altine sun ceci rayuwana ko ba komai sun kwato ni da shiga bani.
Inda nake ina buga zanin da zan shaya mama ta kalla tare da cewa tir dake Rahama kinyi hasara wallahi tunda akan yi yau akai karan mahaifin ki har gurin mai gari sukutum.
In yar arziki kike kin haihu cikun malam yau kije kice wa maigari da miyau bakikin ki za ai wanan auren.
Ban kula ta ba illa idon da suka sako min daga ita har baba din a lokaci daya.
Ganin bazan taka masu ba ne baba yace ai in taki wanan auren nikan ba dai gida na ba wallahi don ba zan zauna da ita ba haka ina ganin bakin ciki a raina.
Fat naji muryan Inna a bayan mu tana fadin a hayye nanaye wanan hukuncin yau yafi nono fari a gare mu don na dade ina jiran anan ranan dama.
Idan baka zauna da ita ba a gida don tana bazawara ai zaka zauna da gandan gadan din yan mata suna maka manne da dare a bayan katanga da samari.
Aure dai ne Allah ya kawo muna saukin shi cikin dadin rai Allah kuma yaiwa wanda yakai kara albarka.
Ikon Allah zamani yanzu Asiya bakiji kunyan wanan maganan ba a duniya ana jinki kina guda akan yar farinki don baki da kunya ga idon ki.
Kunya kunya fa kace malam ai kunya ya kaura ba yau ba ga idon Asiya don ka sani don baku so haka ba.
Gida kuma in kace yarinya bata zama maka gida sai dai dani da ita mubar maka gidan ka a tare don ni ban san zaman da zanyi ba kuma ?
Lalai Asiya kin haihu cikin fulani yau kin sheda min kun bar rugga da dadewa tun da idon ki ya kyakyashe haka kan yar farin ki.
Mu zuba dake a gidan duk inda zaku tafi ku tafi badai gidan Audi ba wallahi ba mai min gori kan abinda na fi karfi yazo yafi karfina a gida na.
Inna tace haka yafi nono fari wallahi yanzu kuwa ba sai anjima ba zamu bar maka gidan ka sai ka zauna da wa yanda kake so kajika kasha.
Magana har takai ga makwabta sun shigo gidan namu suna tambayan ba, asi nan baba ya shiga zagin mu dasu yana cewa wai duk munafukaine mu dasu afice a bar mashi gidan shi.
Hijjab dina na jawo daya bushe na saka nafice daga gidan inajin mama nace indai baki auren Jatau daga wanan fitan kin fice daga cikin mu ke nan.
Nasa kai abina na fice ko waigen ta ban tsaya yi ba sai gidan mama Altine ina shiga take cewa dani Allah mun godema da ya kawo muna saukin al, amarin nan.
Ni yanzu damuwa na shine wanan rantsuwan da mahaifanki ke yi sai kinbar maigidan shi ita kuma Inna ki ta rantse kina barin gidan itama ta bari ke nan.
Nace mama nima shine ke damuna wallahi don bazan so ace saboda ni Inna ta bar dakin auren ta ba akaina.
Zafin raine ke damun su dukan su daga ita har malam Audi din suna cikin bacin rai ne.
Muna nan muna magana sai jin hayaniya mukayi ya kaure a kofan gidan mu da sauri mama ta yafa tafita daga gidan.
Jatau ne yazo ya zauna yana cin mutunci wai kamar shi za, a tozarta a gari ai karan shi don yace yana son .
Indai har ban son shi nafito na bashi kayan shi da naci don shi bai gaji hasara ba akan shi.
But nafito daga gidan mama nace dashi dakata malam ga mutane sun taru wasu har a zanan gida matan aure ke lekowa ta kafan zanan gidan su don gulma.
Nace tsakani na dakai ko uwa ta ka taba ba mu ko kwandalan ka a hannun mu idan dai ka taba ka fada min yanzu na biya ka abinka.
Sai yadan washe baki yace ni da zaki yarda ki amince ai da babu zancen biya a tsakanin mu.
Amma ace ba a bani mata kuma a ci min dukiya na ga banza shine ba zan lamunta ba gaskiya.
Nace to kayi da wanda kaba kudin ka don ni ban san ka raba bani komai ba, muryan mama Lauratu naji daga ta cikin gida tana cewa tau mara kunya idan ke baki ci ba ai mu iyayyen ki munci don nai amfani dashi gida kowa yaci.
Nace kin dai ci ni tundana dawo kin taba girka abincin ki kika bani a gidan nan ko kiba kanne na sai naji tayi shiru nan mutane suka saka salati yan gulma suka hau bakin su.
Aka shiga zuga shi na shige cikun gida abina na barshi nan yana haukan shi shida yan kallin shi.
Nasa kafa zan karasa ciki naji muryan mahaifina cikin kakausar murya yace dakata nan Rahama badai gidana ba wallahi nai maki itaka da gida na daga yau duk inda zaki kije nayafe ki.
Inna dake daki tagama hada kayan ta naga tana fitowa da buhuhuwan data dura kayan ta a ciki.
Nan na duka nafara rusa wani sabin kuka zuciyata tana raya min nace kawai na amince da wanan sabon kaddararen auren akaina kada uwa ra ta shiga wani hali saboda ni.




ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE, ,


IDAN KIN BIYA KIKA TURAWA WANDA BAI BIYA BA MUN BARKI GA ALLAH DON CIN AMANA NE YIN HAKA, , ,

12
Sanye take a cikin kayan sanyi irin na kasan turawa rigan yakai kusan gwiwan ta hakanne ga mijin nata kamar yadda tasaka kayan tare tsananin sanyin da akeyi a garin.
Yana rike da ita a kafadan shi suke saukowa daga matakalar benen gidan nasu wayan shi ce dake aljihun shi ta ruri a lokacin yadan tura hannun shi cikin aljihun shi ya ciro ganin wacce ke kiran shi a layin yasa shi daukan wayan nata.
Sai da ya sauke wani irin ajiyan zuciya yake cewa yaya akayi ne zulfa ?
Jin sunan wacce ya ambata yasata zare jikin ta daga nashi a hankali, tafara tafiya tako biyu zuwa bakin dayan kujeran dake falon.
Ta zauna tare da tsura mai ido daga inda take a zaune daga jin yadda yake magana ta tsigan lalashi ta san fitina ne ake da shi ga wayan.
Can taga yayi dan murmushi a fuskan yana cewa ke ma ai uwarsu ce zulfa don haka kiyi yadda ya kamata dasu mana.
Kofa likita bamu samu gani ba tukun ki ke wanan zance haka idan mun gama ai zamu dawo ne ko.
Bataji may tace dashi ba sai dai murmushin da taga yayi a fuskan yake cewa wata rana kema ai zaki bar naki a gurin ta ko ?
Don haka ki yi hakkuri kifitar da komai a ranki ina diyana diyan ki ne kema koda ba, a gida kike ba.
Can taji yace kwarai da gaske zulfa aiko ita kun san dalilin zuwan namu wannan lokacin ko.
Shiru ya dan ratsa falon yana sauraren mai maganan ta waya har ta taji shi yana cewa ok shike nan sai mun yi waya anjima ke nan.
Ya kashe wayan tare da dago kai yana kallon inda take zaune, ya dan yi murmushi .
Ya zauna gap da ita yana cewa yaya tafi mana ko kin kuma zauna anan ?
Ta dago idanuwan ta fuskan shi a cikin damuwa take cewa dashi akan yaran take magana ko ?
Bai bata amsa ba don yasan ranta zai kara baci ne ga banza yace tashi mu tafi ko ?
Da kyat ta mike tsaye ga dan matashin cikin dake a jikin ta ya turo a cikin rigan dake jikin ta.
Rai bace take magana tana fadin kaga abinda nake gudu ke nan tun farko nace ka bari na kai su gurin hibba su zauna har mu dawo amma kace wai a barsu su zauna agida tunda akwai mutane.
Ya jawo hannun ta yana fadin ke ma dai kin san bazan lamunci ina da gida da iyalina a ciki kuma na dauki diya na zuwa wani gurin ba.
Tace idan baka yarda an kaisu wani wurin ba ai gashi kana shan korafi akai ni dai tsorona kada a cutawa yaran da basuci ba basu sha ba kan zancen mu.
Haba Sa,ade Zulfa ce zata cutawa yarana kuma kada ki manta fa a matsayin yar uwa take a gareni fa.
Tace a da ke nan yanzu kan ai a matsayin diyan kishiya take daukan diyan ka gare ta.
Kofa ya bude masu suka fito daga gidan wani sanyi ne ya daki fuskan ta amma ba yadda ta iya dole haka zasu fita duk da tsananin sanyin da akeyi a garin
Don fitan ya zama masu dole sai sunyi shine dole zai sata fita a hakan.
Bayan sun gama da asibiti ne suka wuce zuwa wani shago nan ta dan yo sayayan abubuwan da ya dace ta tsinta har da tufafin yaran ta dana yaran abokan zaman nata.
Ko da suka dawo gida a gajiye take don bata da kuzarin da zata dinga tafiya haka mai nisa a jikin ta.
Zama yayi kasa a daidai kafan ta ya dan fara matsa mata su a hankali tana jin dadi hakan har cikin ranta ta dan fara lumahe idanuwan ta a hankali.
Haka yasa ta samu saukin yadda take ji a ran ta a lokacin sai bata samu wani matsala komai ba ga yadda take zato.
Washe gari ta riga shi sauko wa kasa don ta karya saboda yace yana son ya dan kara barci.
Har sai bayan ta gama ne sai gashi yau sauko kasan a lokacin har yai wanka yana saye a cikin kananan kaya a jikin shi.
Sau daya ta daga kai ta kalleshi taci gaba da duban wayan ta da takeyi tana murmushi a fuskan ta.
Da alama hiran da takeyi yana mata dadi a ran ta lokacin ya iso inda take yana cewa madam yaya jikin naki ?
Ta dan dago kan ta a hankali ta dube shi tana cewa Alhamdullahi ya kokari bai amsa mata ba sai da yakai zaune yace kokarin yiwa kaine ai nidai gurina naga Alllah ya rabaki da wanan cikin na jikin ki lafiya.
Sai lokacin tabar abinda take a wayan ta ta dago kan ta ta dube shi inda ya zauna sai suka hada ido dashi tayi saurin kawar da idon ta cikin nasa .
Yace No no no kada ki soma yi min wanan kukan naki dake tayar min da hankalina please ?
Yace cikin kamo hannun ta zuwa na shi cikin girgiza mata kai yake fadin ki dinga sakawa zuciyar ki dangana Allah daya baki ciki a cikin wanan halin da kike yasan dalilin yin haka a gare ki.
Don haka ki zamo cikin bayi masu rugumar kaddaran ubangijin su ako da yaushe.
Wanan tayar da hankalin da kikeyi zai iya kara jefa ki a cikin wani sabon tashin hankali kuma har mu dake tare dake abin ya shafi zukatan mu.
Ajiyan zuciya ta sauke tace dole na daga hankalina idan na tuna da lalurar dake tare dani sai ga shi kuma wanan cikin yazo ya shiga again.
Murmushi yayi tare da jawo ta ajikin shi yana dan shafa bayan ta yake cewa lafiya lau zaki haihu insha Allah ai ciwo ba mutuwa bane.
A hankali tace dashi abin ne ke bani tsoro sosai sai yake hanani sukuni a raina.
Ya girgiza mata kai yace ai abin bada ga nan bane heartbeat ke dai Allah ya kawo muna sauki ga al,amarin.
Sai da ya tabbatar ta kwantar da hankalin ta ya mike yana cewa zai dan fita amma ba zai dade ba indan ya fita.
Nan ya fice ya barta zaune zuciyan ta cike da tunanen yan diyan ta biyu dake gida Nigeria gurin kishiyan ta.
Tun ba akai ko ina ba gashi ta fara jin Zulfa din ta bugo waya tana korafi akan rikon yaran nata gashi zasu iya share wata uku basu koma gida ba.
Shine dalilin da tun farko taso zuwa da yaran ta ko tabar su gurin yar uwarta amma sai ya nuna mata rashin yardan shi ga hakan .
Don shi mutum ne mai matukar son iyalin shi a kusa dashi akoda yaushe haka ne yasa akwai shakuwa sosai tsakanin shi da italin shi don yana fitarwa kowa da hakkin shi yadda ya dace.
Wanan zuwan da sukayi dashi ba itace ya dace tabiyo shi ba amma saboda dalilin rashin lafiyan ta yazo da ita din.
Wanda kafin su zo saida akakai ruwa rana da sauran kishiyoyin nata akan basu yarda da hakan ba don acewa su yafi nuna kulawan shi akan Sa,ade da yaran ta bisa gasu.
Don har kara suka kai shi gurin iyayyen su kan abinda yake shirin yi masu.
Ita bata da ko labari sai dai ta fahinci ya dauki zafi da sauran matan nashi a lokacin.
Ita da ake abin akan ta sai daga baya ta fahinci rigiman akan tafiyan su ne akeyin sa.
Haka ne ya dan haifar mata da rashin natsuwa a tare da ita don haka ta bukaci da ajaye tafiya sai taga likitan ta na nan gida Nigeria.
Amma amma mijin tana yaki janye zancen ba irin rokon da bata mashi ba kan ya barta amma sai yaki yarda da bukatan ta.
Karshe ma cewa yayi da ita idan ke lafiyan ki bai damay ki ba ni ya damay ni tunda bake ce keda hasara ba ai .
Hakkuru ta bashi don yadda taga ya hau tasan itama zata iya samun nata rabon fitina a ciki don haka taja bakin ta ta tsuke tai shiru har lokacin tafiya yayi suka wuce.
Don makaran ta ne kawai yasa ta bar yaran ta a hannun kishiyoyin ta ba don taso ba don tana nan ma yaya aka kwashe da su balle bata kusa.
Ko ita Zulfa ba don Allah ta rike yaran ba don sai daya zube mata kudi masu yawa ta yarda zata zauna dasu din.

****** ********* ******
Na gama aikin da nake taya mama altine na kwashi kayan na aiki tare da kaisu bakin kwata na wanke komai fes na mayar na kife mama na zaune ta zuba min ido daga inda take zaune ta motsa furan data dama ta sha.
Ina yarfar da ruwan dakw hannu na bayan na dauraye kafana take cewa sannu Rahama ai kin huta ke bakajin kiyuyan aiki ko kadan.
Da ace uwarki lauratu ta gane haka ta nemi zaman lafiya dake a gidan dan wanan zaman da zakiyi a gida aida ta more maki sosai.
Na dago kai da sauri ina kallon mama nace kai mama matar da tun ina yar kankanuwa
Showing 45001 words to 48000 words out of 456145 words
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16 Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22Chapter 23Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32Chapter 33Chapter 34Chapter 35Chapter 36Chapter 37Chapter 38Chapter 39Chapter 40Chapter 41Chapter 42Chapter 43Chapter 44Chapter 45Chapter 46Chapter 47Chapter 48Chapter 49Chapter 50Chapter 51Chapter 52Chapter 53Chapter 54Chapter 55Chapter 56Chapter 57Chapter 58Chapter 59Chapter 60Chapter 61Chapter 62Chapter 63Chapter 64Chapter 65Chapter 66Chapter 67Chapter 68Chapter 69Chapter 70Chapter 71Chapter 72Chapter 73Chapter 74Chapter 75Chapter 76Chapter 77Chapter 78Chapter 79Chapter 80Chapter 81Chapter 82Chapter 83Chapter 84Chapter 85Chapter 86Chapter 87Chapter 88Chapter 89Chapter 90Chapter 91Chapter 92Chapter 93Chapter 94Chapter 95Chapter 96Chapter 97Chapter 98Chapter 99Chapter 100Chapter 101Chapter 102Chapter 103Chapter 104Chapter 105Chapter 106Chapter 107Chapter 108Chapter 109Chapter 110Chapter 111Chapter 112Chapter 113Chapter 114Chapter 115Chapter 116Chapter 117Chapter 118Chapter 119Chapter 120Chapter 121Chapter 122Chapter 123Chapter 124Chapter 125Chapter 126Chapter 127Chapter 128Chapter 129Chapter 130Chapter 131Chapter 132Chapter 133Chapter 134Chapter 135Chapter 136Chapter 137Chapter 138Chapter 139Chapter 140Chapter 141Chapter 142Chapter 143Chapter 144Chapter 145Chapter 146Chapter 147Chapter 148Chapter 149Chapter 150Chapter 151Chapter 152Chapter 153