washegari yasa akaita gida.
Ya isa gidan shi ya samu iyalin shi lafiya anty ce da girki bayan sun gaisa ne take tambayan shi su mama yace da ita ai tare suka dawo ya sauke su gida ne.
Tace a a na dauka ai tare da Rahaman zasu dawo gaba daya tunda ta gama abinda ya kaita can din ko ?
Yace cikin mamaki ta dawo ina kuma tace ban gane ta dawo ina ba, ba anan take ba dama ko a can zatai ta zama kuma ?
Yace dama kunyi da ita cewa idan ta gama zata dawo nan ne ?
Tace da kai dai mukayi haka da zata tafi yace to a can zata zauna don aiki zata fara badadewa ba da zaran danta yayi kwari.
Nan ta bishi da kallon mamaki tace au Rahaman aiki zatayi ita ke nan yace eh ba shine burinta ba ko haka zatai tsawon shekaru bakwai ya tafi a banza bata more mai ba wa alumma ?
Abin mamaki baya karewa kullun a gidan nan tace daga karshe yayi ashe nike wautana anan ina murnan zasu dawo gida.
Yace ai da nan da can duk daya ne a garesu ko may ake a can wanda ba ayi anan din waya ne kullun kuna gaisawa idan kun ga dama to sai may kuma ?
Bata iya magana ba don mamakin daya bata yawani zare a lokaci daya kamar bashi kamar wani bako ya koma mata sam yanzu ba kamar wanda ta sani ba a baya.
Mai dubaiyya da son jin bukatunta amma yanzu shi da kan shi ma ke kirkiro mata matsala.
Don tunda ya tafi da yara karatu can ta fara kawo wutan gane cewa akwai magana gaba don haka ta mike tsam ta bar falon ta barshi yana cin abinci.
Ya bita da kallo sai dai yana jiran ta tunda duk itace ta jawo mai yin haka ai ta dauko fitina ta saka a ranta bata zaman lafiya dashi kwata kwata yanzu haka ma abokan zamar ta kamar wacce asiri ke aiki a kanta har yanzu.
Shiru shiru yana jiran ta sake maganan ya bata amsa daidai da maganan ta amma sai yaji shiru bata kara yin maganan ba again.
Abinda bai sani ba ranan ta kwana tana tunane kan maganan sai daga karshe ne ta dai yanke shawaran ta hakkura tasawa kanta saida kawai akan zancen Rahama.
Don dai koma may ye dai ai itace silarshi tana ta bada kai ana mata dariya a tsakanin su ga yaranta can har biyu gunta amma bata ji wani korafi ko kadan ba daga yaran har yanzu ko sunyi waya dasu lafiya lau take jin su.
Hakkuri da nadaman abubuwa yazo mata a rai a lokaci daya ta mike ta roki Allah da ya sanyaya mata zafin Rama da take yawan ji a zuciyar ta koda yaushe.
Tasan yarinyar bazata iya cewa ga wani abinda ta taba mata ba na cutar wa amma yakai yanzu saboda halin da take gwada mata har ta fara mayar mata da amsan magana mai zafi.
Shine dalilin da taja bakinta tai shiru ta dai san halin mijin su fiye da kowa hutsune bai jin mutunci idan idon shi ya rufe.
Kowa kuma haka yakewa don may karamar yarinyar da ta raina zata fita sanin maganin zama da mijin su lafiya aiko wacce mace na kishin mijinta ta san kuma Rama na da kishin ita ma tunda mace ce amma ta iya dannewa ta boye sai itace bazata iya boye nata ba.
Aike da kira ya ishe shi a gidan su Hindatu har takai ranan an datse a gidan mahaifan shi nan Alhaji shi ya sa baki yace sai yaje ya duba matar nashi tunda yanzu ta gane kuren ta.
Baiso ba haka ya daure ya tafi da yamma shi da Bashir daya dauka don ya raka shi gidan ya ganta amma ran shi baiso haka ba.
Sun isa gidan suka aika a sanar da zuwan su hindatu naji ta fada daki tafara dauko kwallin da aka bata ta shafa tare da wani powder da turare duk tayi yadda aka umurce tayi ta yafa taiwa uwarta sallama ta fita uwar nacewa kinyi yadda akace kiyi ko kin dai san irin kudin da muka kashe a gurin nan.
Tace kada ki damu mama nayi komai yin fatan dai mu dace kawai idan ya ganni din.
A lokacin saura wata daya ta gama idda da takeyi tana fita ta samay su zaune a falo ta gaidasu a cikin wani irin ladabin shagu.
Ya dago kai da kyat yana amsa mata yana kallonta yaji wani irin shock a ilahirin jikin shi gaba daya yaga ta sauya mashi ta koma kamar wata hawai niya mai rikida ako wani lokaci.
Tai mashi kyau ta koma kamar wata yar shila a ganin shi, wani irin sonta da kaunarta yana fisgan shi.
Cikin washe baki yace da ita idon ki ke nan daga magana kadan sai ki fushi ki dawo gida.
Take ta gane cewa tarkon ta ya kama kurciyar da take hako nan ta shiga juya shi yadda take so har sukai mata sallama suka tafi Bashir dai yana kallon ikon Allah.
Sai da suka kama hanya yaji daddy ya sauke ajiyan zuciya da karfi yace yaya akayi ne mutumina ?
Yace kaina ne naji yai min wani irin sarawa wallahi muna barin wurin nan kamar kar hindatu tafito gaba daya sai na nemi natsuwana na rasa.
Yanzu kuma mun bar wurin naji kaina yana sara min ba dadi wallahi nan dai Bashir ya nisa yace dashi nifa kada nai magana nayi laifi kuma ?
Yace kamar ya kayi laifi kawai kafadi maganan ka mana kai tsaye ?
Yace abinda zan fada ne da nauyi akwai kuma kamshin gaskiya a cikin sa yace kafadi maganan ka mana kai tsaye ka tsaya kana wani kwanaye kwanaye haka dakai ?
Bashir ya nisa yace anya Hindatu bata gama da kaiba yadda naga ka zabura daka gantaka kuma sukurkuce a lokaci daya ga wani kamshi wani irin mugun turaren gargajita danaji tanayi.
Daddy yace kai amma akwai ka da wani magana yanzu nine hindatu zataiwa magani kake gani ya kamani ?
Bashir yace kai kafi karfin sherin mace ne ko may wallahi ka fada tarkon mata kace nace da kai wata rana bai yi magana ba sai murmushin da yayi yace kai akwai da wani zance wallahi hindatu fa matatace ka sani.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE DON BA A YAFE BA ONLINE NOVEL NE, , , ,
77
Idan daddy ya tafi baya wuce kwanakin da na fada a baya sai gashi wanan tafiya har ya gwauta kwana ashirin da biyu a kano.
Baya kiran mu kamar yadda ya saba kiran mu a baya idan yana can sai jefi jefi zai dan kira sama sama yaji lafiyan mu.
Sai dai abinda na dan kula dashi shine yawan kiran Ihisan da takanyi musanman ma da dare naso na dan gane wani abu amma sai kuma nai tunanen kila rashin uwar ta a gidan yanzu yasa yake yawan kula ta din.
Ranan sai gashi ya dawo sai dai ya fada ya dan yi baki kadan mun tare shi da murnan ganin shi sai dai ba wani walwala sosai a tare dashi sai na dauka duk gajiya ne hakan kawai ya kama shi.
Sai da yai wanka ya huta bai dade ba yafito ya fita daga gidan ina mai tayin abinci yace dani barshi kawai bana jin cin abinci yanzu.
Ga watan Azumi saura yan kwanaki a lokacin sai kuma ba hankalin maigidan wuri daya don da gani akwai abinda yasa a gaban shi.
Ni dai ban tsananta wa kaina sai nasan may yake ciki ba ina dai kokarin wurin ganin na sauke duk wani nauyin da ya dace ai mashi.
Wani abinda na lura dashi kuma shine duk dare sai mun kwanta za, a kira shi da waya zai dauki lokaci yana waya.
Lokacin ne na fara shan jinin jikina da gane cewa da mace yake waya sai na nemi walwala a tare dani na rasa amma duk da hakan bani nuna komai a fili na bar abin a raina kawai.
Ana azumi saura kwana ukku lokaci duk kwanan shi shidda da dawowa yace zai koma kano a gobe banyi mamaki ba ko zaton wani abu tunda nasan cewa gida ne can kuma akwai iyali.
Sai da ya shirya yafito yana waya naga shirin wucewa yakeyi nace daddy sai ya juyo yana kallo na naji yace da wanda yake wayan minti biyu ya kashe ya kara juyowa inda nakke yace dani umm,humm ?
Na dan kwantar da murya nace daddy dama naga kafin ka dawo za a tashi da azumi shine nace baka sai muna abin taron azumin ba.
Yace ban fahince ki ba may kike nufi da hakan nace wai da nace kayan shan ruwa kodon yaran nan ko ?
Yace Rahama yaushe kika fara wanan halin har ni zakice wai ban sayo maku wani abu ba ko may kike nufi da wanan maganan naki ?
Ko kin taba min magana akan na sayo maku abu a gidan nan bani ke sayowa ba in naga dacewan hakan ?
A sanyaye nace don Allah daddy kayi hakkuri nayii kuskure dama don naga wancan karon ka dan jiima baka dawo bane yasa nai magana yanzu din.
Yace o,wo yai min wani irin kallon sama da kasa kamar wanda ke hake dani dama yana jirace na tanka mai.
Nace Allah ya tsare aje lafiya adawo lafiya yace amin kamar a hasale ya juya ya wuce abin shi batare da ko juyowa ba again.
Mamaki ya kamani nakai zaune a kujeran dake kusa dani ban san abinda yasa daddy yanzu magana ba magana ba sai ya hauni da masifa sosai.
Aisha ce takawo min Haidar da ke kuka na karbe shi sai ga baba ya biyo su ya kwanta a jikina nan na sauke ajiyan zuciya na gyara ina fitar da nono nabawa yaron.
Ina shayar da yaeon ina tunane ga baba da ke tsaye rabin jikin shi kwance a jikina ya damay ni da tabe tabe a fuskana.
Nace a sanyaye don haushi nakeji a raina bari mana baba yaton bai bari ba nakai mai duka akai abinda bana yi duka sai dai inwa yaro fada.
Take yaton ya fara kuka sai kuma yabani tausayi bashi ya bata min rai ba na fashe haushin uban shi a kan shi.
Na jawo shi da hannu daya ina lalashin shi har na samu yai shiru Aisha taji kukan shi ta fito tana tambayan may ya samay shi kuma ?
Nace baijin magana ne na dan duke shi shine kikaji ya bare baki haka yana damun mutane da kukan banzan shi.
Nan dai taja yaron suka fice suka barni ina tune a zaune sai naga ni may ma yakaini yi mai magana bayan nasan yadda muke a yanzu dashi.
Sai zuwa sha biyu har lokacin banajin dadin yadda muka rabu ya tafi dani a hasale sai na yanke shawaran kiran shi na bashi hakkuri.
Kira daya biyu ga hudu ya daga yace cikin muryan shi mai nuna har yanzu baya jin dadin ranshi da fadin.
Yaya akayi kuma na dake nace ba komai sannu da hanya kawai dama zan maka sai kuma na baka hakkuri bisa ga saba makan danayi da zu a yafe min don Allah nayi kuskure na sani.
Yace is ok sai anjima ssi ya kashe wayan kit bin wayan nayi da kallon mamaki may naiwa daddy ne haka nake tambayan kaina ?
Abinda ban sani ba ashe bani kadai ke fuskantar wanan halin ba kowan mu ya rasa gane kan shi tun zuwan shi gidan su hindatu abubuwa suka jagule baki daya a kan shi.
Wanan zuwan da yayi yazo a tsayar da maganan komawan ta gidan shi har ya iso gida baida walwala ba isa gidan shi ba sai da yaje gidan su hindatu ya zube tsaraban da ya sawo masu a hanya.
Ya samu iyayyen shi da zance sai dai hajiya ta nuna bata yarda ba taso abar hindatu a hakkura hakana a hakkura kawai.
Amma yadda daddy ya dage sai hankalin su ya tashi Alhaji yai gyaran muryan yace kinga ayi hakkuri tunda shike da abin shi don haka barshi ya gyara auren shi a zauna lafiya.
Dole hajiyan ta hakkura sai dai bataso hakan ba Alhaji ya tura manya aje a gyara zancen sai ga masu zuwa sun dawo da sabuwar magana kuma.
Wai iyayyen hindatu da ita kanta sunce in har zai amincr idan ta koma ya maida ita Abuja da zama ita ma ta amince da zata dawo.
Nan hajiya ta hau fada tace sam ba zai yuyu ba anan ma gaban kowa yaya aka kare da ita balle ta bisu can inda babu idon kowa sai su yasu yasun su.
Amma daddy na zuwa yace may zai hana ya amince da nan da can ai duk gidan shine shike da iko akan komai don haka ai wanan ba matsala bane ai.
Hajiya tace yanzu da hankalinka Alhaji karami kake wanan magan kafa san halin yarinyar nan sarai bawai ta canza bane .
Yace kai hajiya ita hindatu wani haline da ita kawai ni keda gidana ai zan san yadda zanyi indon wanan ne ai ba wani matsala akan shi.
Tace a, a fa yar mutane dake can zaune kalau cikin rufin asirinta kada taje ta tayarwa yar mutane da hankali kuma ?
Hajiya ita da Rahama din ai duk ni aje su ko may zai kawo wani fitina kuma yanzu tunda kowa yasan kowa dama .
Hajiya bata dai gane komai ba don ya dage daya amince da atafi din shi ba matsalar komai ga yin hakan tace to shike nan ai may daki shiyasan inda ruwa ke mai yoyo.
An mayar da aure ko su anty dake garin basu da labari sai ji da sukayi ga bakin shi yake fada masu batace dashi kalla ba don ta fahinci irin rawan kafan da yake duk aanan lokaci ta san kuma ruwa baya tsami banza ai.
Bayan kwana biyar sai gashi ya dawo lokacin Azumi nada kwana biyu da dauka bai nuna min komai ba mun tare shi cikin mutunci.
Sai bayan an sha ruwa yana zaune da yaran suna hira na shigo falon bayan na idar da sallah nai mashi sannu da shan ruwa na juya zan wuce yace dani gobe ina son duk wani kayan daki a fitar sai za a saka sabo ne .
Na juyo da mamaki don naga kayan ai basu komai ba amma kuma sai na share don kada na daukowa kaina magana nace Allah ya kaimu kawai.
Sun gama ya sallami yaran yai shirin kwanci sai dana fahinci cewa yadan dade da shigewa na shirya naje dakin.
Na mulke jikina da ture masu kamshi don kawar da karnin nonon da nake shayarwa a lokacin.
Har na shiga na kwanta yana waya bai gama ba har barci ya dauke ni ya gama bai tayardani ba sai da muka tashi don yin sahur.
Washegari tin safe muka tashi da aikin kwashe kayan da ya umurce mu dayi bamu jima da kwashewa baaka fara shigo da wasu iri dirka dirkan kujeru masu kyau da girma.
Ma aikata suka gyara komai sai dai dakina da dayan dakin dake facin din na ihisan komai nashi iri daya ne da nawa kala ne kawai aka banbanta masu sai biyu zuwa uku suka gama lokacin ina kitchen mun fara hada abin buda baki ko.
Munyi mamakin ganin hakan amma naja bakina nai shiru ban tsaya magana ba don jin ko yaya hakan din.
Sai dare sosai ya dawo har yaran sun shige ko dakun nan su don azumi ne kowa ya gaji ba wani dogon hira.
Ko ni har na shige na kashe wutan falon ya dawo gidan jin motsin dawiwan shi yasa na fito ya na zaune yana cin abincin da ya samu an jera mai na buda baki.
Nai mai sannu da zuwa ina kokarin juyawa naji ya kira sunana na dakatar da tafiyan dana fara yi tare da juyowa gare shi.
Yace zoki samu wuri ki zauna ina son nayi magana dake ne samun wuri nayi na zauna sai dai ba gaf dashi ba.
Yace Rahama ina son yin wani magana dake ne sai dai ina fatan zaki fahince duk da nasan ba wani bakon abu bane sosai a gare ki.
Gabana ne ya soma harbawa don ban san wani magana bane wanan wanda ba bako na bane haka ?
Maganan da zanyi bawai ya sabawa sharia bane ko da wata manufa zanyi sai dai daurowan hakan .
Na tattara natsuwana ina sauraren abinda zai fada min din a yadda yake maganan shi mai kama da roko kuma da gadara yasa nasan akwai wata a kasa.
Jin nayi shiru yasa ya dago kai ya dan kalle ni yace dani kina jina kuwa nace inaji kai nake saurare ai .
Yadda nai magana yasa yasan a shirye nake ke nan da inji abinda zai fada din a lokacin.
Ba wani magana bane sai dai kiyi hakkuri a yadda na tsara zaman mu a baya yanzu an samu akasin hakan don Hindatu zata dawo nan garin ku zauna tare.
Dam dam naji gabana ya fadi shike nan ni nawa ya samay ni inko hakane
Showing 309001 words to 312000 words out of 456145 words
Ya isa gidan shi ya samu iyalin shi lafiya anty ce da girki bayan sun gaisa ne take tambayan shi su mama yace da ita ai tare suka dawo ya sauke su gida ne.
Tace a a na dauka ai tare da Rahaman zasu dawo gaba daya tunda ta gama abinda ya kaita can din ko ?
Yace cikin mamaki ta dawo ina kuma tace ban gane ta dawo ina ba, ba anan take ba dama ko a can zatai ta zama kuma ?
Yace dama kunyi da ita cewa idan ta gama zata dawo nan ne ?
Tace da kai dai mukayi haka da zata tafi yace to a can zata zauna don aiki zata fara badadewa ba da zaran danta yayi kwari.
Nan ta bishi da kallon mamaki tace au Rahaman aiki zatayi ita ke nan yace eh ba shine burinta ba ko haka zatai tsawon shekaru bakwai ya tafi a banza bata more mai ba wa alumma ?
Abin mamaki baya karewa kullun a gidan nan tace daga karshe yayi ashe nike wautana anan ina murnan zasu dawo gida.
Yace ai da nan da can duk daya ne a garesu ko may ake a can wanda ba ayi anan din waya ne kullun kuna gaisawa idan kun ga dama to sai may kuma ?
Bata iya magana ba don mamakin daya bata yawani zare a lokaci daya kamar bashi kamar wani bako ya koma mata sam yanzu ba kamar wanda ta sani ba a baya.
Mai dubaiyya da son jin bukatunta amma yanzu shi da kan shi ma ke kirkiro mata matsala.
Don tunda ya tafi da yara karatu can ta fara kawo wutan gane cewa akwai magana gaba don haka ta mike tsam ta bar falon ta barshi yana cin abinci.
Ya bita da kallo sai dai yana jiran ta tunda duk itace ta jawo mai yin haka ai ta dauko fitina ta saka a ranta bata zaman lafiya dashi kwata kwata yanzu haka ma abokan zamar ta kamar wacce asiri ke aiki a kanta har yanzu.
Shiru shiru yana jiran ta sake maganan ya bata amsa daidai da maganan ta amma sai yaji shiru bata kara yin maganan ba again.
Abinda bai sani ba ranan ta kwana tana tunane kan maganan sai daga karshe ne ta dai yanke shawaran ta hakkura tasawa kanta saida kawai akan zancen Rahama.
Don dai koma may ye dai ai itace silarshi tana ta bada kai ana mata dariya a tsakanin su ga yaranta can har biyu gunta amma bata ji wani korafi ko kadan ba daga yaran har yanzu ko sunyi waya dasu lafiya lau take jin su.
Hakkuri da nadaman abubuwa yazo mata a rai a lokaci daya ta mike ta roki Allah da ya sanyaya mata zafin Rama da take yawan ji a zuciyar ta koda yaushe.
Tasan yarinyar bazata iya cewa ga wani abinda ta taba mata ba na cutar wa amma yakai yanzu saboda halin da take gwada mata har ta fara mayar mata da amsan magana mai zafi.
Shine dalilin da taja bakinta tai shiru ta dai san halin mijin su fiye da kowa hutsune bai jin mutunci idan idon shi ya rufe.
Kowa kuma haka yakewa don may karamar yarinyar da ta raina zata fita sanin maganin zama da mijin su lafiya aiko wacce mace na kishin mijinta ta san kuma Rama na da kishin ita ma tunda mace ce amma ta iya dannewa ta boye sai itace bazata iya boye nata ba.
Aike da kira ya ishe shi a gidan su Hindatu har takai ranan an datse a gidan mahaifan shi nan Alhaji shi ya sa baki yace sai yaje ya duba matar nashi tunda yanzu ta gane kuren ta.
Baiso ba haka ya daure ya tafi da yamma shi da Bashir daya dauka don ya raka shi gidan ya ganta amma ran shi baiso haka ba.
Sun isa gidan suka aika a sanar da zuwan su hindatu naji ta fada daki tafara dauko kwallin da aka bata ta shafa tare da wani powder da turare duk tayi yadda aka umurce tayi ta yafa taiwa uwarta sallama ta fita uwar nacewa kinyi yadda akace kiyi ko kin dai san irin kudin da muka kashe a gurin nan.
Tace kada ki damu mama nayi komai yin fatan dai mu dace kawai idan ya ganni din.
A lokacin saura wata daya ta gama idda da takeyi tana fita ta samay su zaune a falo ta gaidasu a cikin wani irin ladabin shagu.
Ya dago kai da kyat yana amsa mata yana kallonta yaji wani irin shock a ilahirin jikin shi gaba daya yaga ta sauya mashi ta koma kamar wata hawai niya mai rikida ako wani lokaci.
Tai mashi kyau ta koma kamar wata yar shila a ganin shi, wani irin sonta da kaunarta yana fisgan shi.
Cikin washe baki yace da ita idon ki ke nan daga magana kadan sai ki fushi ki dawo gida.
Take ta gane cewa tarkon ta ya kama kurciyar da take hako nan ta shiga juya shi yadda take so har sukai mata sallama suka tafi Bashir dai yana kallon ikon Allah.
Sai da suka kama hanya yaji daddy ya sauke ajiyan zuciya da karfi yace yaya akayi ne mutumina ?
Yace kaina ne naji yai min wani irin sarawa wallahi muna barin wurin nan kamar kar hindatu tafito gaba daya sai na nemi natsuwana na rasa.
Yanzu kuma mun bar wurin naji kaina yana sara min ba dadi wallahi nan dai Bashir ya nisa yace dashi nifa kada nai magana nayi laifi kuma ?
Yace kamar ya kayi laifi kawai kafadi maganan ka mana kai tsaye ?
Yace abinda zan fada ne da nauyi akwai kuma kamshin gaskiya a cikin sa yace kafadi maganan ka mana kai tsaye ka tsaya kana wani kwanaye kwanaye haka dakai ?
Bashir ya nisa yace anya Hindatu bata gama da kaiba yadda naga ka zabura daka gantaka kuma sukurkuce a lokaci daya ga wani kamshi wani irin mugun turaren gargajita danaji tanayi.
Daddy yace kai amma akwai ka da wani magana yanzu nine hindatu zataiwa magani kake gani ya kamani ?
Bashir yace kai kafi karfin sherin mace ne ko may wallahi ka fada tarkon mata kace nace da kai wata rana bai yi magana ba sai murmushin da yayi yace kai akwai da wani zance wallahi hindatu fa matatace ka sani.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE DON BA A YAFE BA ONLINE NOVEL NE, , , ,
77
Idan daddy ya tafi baya wuce kwanakin da na fada a baya sai gashi wanan tafiya har ya gwauta kwana ashirin da biyu a kano.
Baya kiran mu kamar yadda ya saba kiran mu a baya idan yana can sai jefi jefi zai dan kira sama sama yaji lafiyan mu.
Sai dai abinda na dan kula dashi shine yawan kiran Ihisan da takanyi musanman ma da dare naso na dan gane wani abu amma sai kuma nai tunanen kila rashin uwar ta a gidan yanzu yasa yake yawan kula ta din.
Ranan sai gashi ya dawo sai dai ya fada ya dan yi baki kadan mun tare shi da murnan ganin shi sai dai ba wani walwala sosai a tare dashi sai na dauka duk gajiya ne hakan kawai ya kama shi.
Sai da yai wanka ya huta bai dade ba yafito ya fita daga gidan ina mai tayin abinci yace dani barshi kawai bana jin cin abinci yanzu.
Ga watan Azumi saura yan kwanaki a lokacin sai kuma ba hankalin maigidan wuri daya don da gani akwai abinda yasa a gaban shi.
Ni dai ban tsananta wa kaina sai nasan may yake ciki ba ina dai kokarin wurin ganin na sauke duk wani nauyin da ya dace ai mashi.
Wani abinda na lura dashi kuma shine duk dare sai mun kwanta za, a kira shi da waya zai dauki lokaci yana waya.
Lokacin ne na fara shan jinin jikina da gane cewa da mace yake waya sai na nemi walwala a tare dani na rasa amma duk da hakan bani nuna komai a fili na bar abin a raina kawai.
Ana azumi saura kwana ukku lokaci duk kwanan shi shidda da dawowa yace zai koma kano a gobe banyi mamaki ba ko zaton wani abu tunda nasan cewa gida ne can kuma akwai iyali.
Sai da ya shirya yafito yana waya naga shirin wucewa yakeyi nace daddy sai ya juyo yana kallo na naji yace da wanda yake wayan minti biyu ya kashe ya kara juyowa inda nakke yace dani umm,humm ?
Na dan kwantar da murya nace daddy dama naga kafin ka dawo za a tashi da azumi shine nace baka sai muna abin taron azumin ba.
Yace ban fahince ki ba may kike nufi da hakan nace wai da nace kayan shan ruwa kodon yaran nan ko ?
Yace Rahama yaushe kika fara wanan halin har ni zakice wai ban sayo maku wani abu ba ko may kike nufi da wanan maganan naki ?
Ko kin taba min magana akan na sayo maku abu a gidan nan bani ke sayowa ba in naga dacewan hakan ?
A sanyaye nace don Allah daddy kayi hakkuri nayii kuskure dama don naga wancan karon ka dan jiima baka dawo bane yasa nai magana yanzu din.
Yace o,wo yai min wani irin kallon sama da kasa kamar wanda ke hake dani dama yana jirace na tanka mai.
Nace Allah ya tsare aje lafiya adawo lafiya yace amin kamar a hasale ya juya ya wuce abin shi batare da ko juyowa ba again.
Mamaki ya kamani nakai zaune a kujeran dake kusa dani ban san abinda yasa daddy yanzu magana ba magana ba sai ya hauni da masifa sosai.
Aisha ce takawo min Haidar da ke kuka na karbe shi sai ga baba ya biyo su ya kwanta a jikina nan na sauke ajiyan zuciya na gyara ina fitar da nono nabawa yaron.
Ina shayar da yaeon ina tunane ga baba da ke tsaye rabin jikin shi kwance a jikina ya damay ni da tabe tabe a fuskana.
Nace a sanyaye don haushi nakeji a raina bari mana baba yaton bai bari ba nakai mai duka akai abinda bana yi duka sai dai inwa yaro fada.
Take yaton ya fara kuka sai kuma yabani tausayi bashi ya bata min rai ba na fashe haushin uban shi a kan shi.
Na jawo shi da hannu daya ina lalashin shi har na samu yai shiru Aisha taji kukan shi ta fito tana tambayan may ya samay shi kuma ?
Nace baijin magana ne na dan duke shi shine kikaji ya bare baki haka yana damun mutane da kukan banzan shi.
Nan dai taja yaron suka fice suka barni ina tune a zaune sai naga ni may ma yakaini yi mai magana bayan nasan yadda muke a yanzu dashi.
Sai zuwa sha biyu har lokacin banajin dadin yadda muka rabu ya tafi dani a hasale sai na yanke shawaran kiran shi na bashi hakkuri.
Kira daya biyu ga hudu ya daga yace cikin muryan shi mai nuna har yanzu baya jin dadin ranshi da fadin.
Yaya akayi kuma na dake nace ba komai sannu da hanya kawai dama zan maka sai kuma na baka hakkuri bisa ga saba makan danayi da zu a yafe min don Allah nayi kuskure na sani.
Yace is ok sai anjima ssi ya kashe wayan kit bin wayan nayi da kallon mamaki may naiwa daddy ne haka nake tambayan kaina ?
Abinda ban sani ba ashe bani kadai ke fuskantar wanan halin ba kowan mu ya rasa gane kan shi tun zuwan shi gidan su hindatu abubuwa suka jagule baki daya a kan shi.
Wanan zuwan da yayi yazo a tsayar da maganan komawan ta gidan shi har ya iso gida baida walwala ba isa gidan shi ba sai da yaje gidan su hindatu ya zube tsaraban da ya sawo masu a hanya.
Ya samu iyayyen shi da zance sai dai hajiya ta nuna bata yarda ba taso abar hindatu a hakkura hakana a hakkura kawai.
Amma yadda daddy ya dage sai hankalin su ya tashi Alhaji yai gyaran muryan yace kinga ayi hakkuri tunda shike da abin shi don haka barshi ya gyara auren shi a zauna lafiya.
Dole hajiyan ta hakkura sai dai bataso hakan ba Alhaji ya tura manya aje a gyara zancen sai ga masu zuwa sun dawo da sabuwar magana kuma.
Wai iyayyen hindatu da ita kanta sunce in har zai amincr idan ta koma ya maida ita Abuja da zama ita ma ta amince da zata dawo.
Nan hajiya ta hau fada tace sam ba zai yuyu ba anan ma gaban kowa yaya aka kare da ita balle ta bisu can inda babu idon kowa sai su yasu yasun su.
Amma daddy na zuwa yace may zai hana ya amince da nan da can ai duk gidan shine shike da iko akan komai don haka ai wanan ba matsala bane ai.
Hajiya tace yanzu da hankalinka Alhaji karami kake wanan magan kafa san halin yarinyar nan sarai bawai ta canza bane .
Yace kai hajiya ita hindatu wani haline da ita kawai ni keda gidana ai zan san yadda zanyi indon wanan ne ai ba wani matsala akan shi.
Tace a, a fa yar mutane dake can zaune kalau cikin rufin asirinta kada taje ta tayarwa yar mutane da hankali kuma ?
Hajiya ita da Rahama din ai duk ni aje su ko may zai kawo wani fitina kuma yanzu tunda kowa yasan kowa dama .
Hajiya bata dai gane komai ba don ya dage daya amince da atafi din shi ba matsalar komai ga yin hakan tace to shike nan ai may daki shiyasan inda ruwa ke mai yoyo.
An mayar da aure ko su anty dake garin basu da labari sai ji da sukayi ga bakin shi yake fada masu batace dashi kalla ba don ta fahinci irin rawan kafan da yake duk aanan lokaci ta san kuma ruwa baya tsami banza ai.
Bayan kwana biyar sai gashi ya dawo lokacin Azumi nada kwana biyu da dauka bai nuna min komai ba mun tare shi cikin mutunci.
Sai bayan an sha ruwa yana zaune da yaran suna hira na shigo falon bayan na idar da sallah nai mashi sannu da shan ruwa na juya zan wuce yace dani gobe ina son duk wani kayan daki a fitar sai za a saka sabo ne .
Na juyo da mamaki don naga kayan ai basu komai ba amma kuma sai na share don kada na daukowa kaina magana nace Allah ya kaimu kawai.
Sun gama ya sallami yaran yai shirin kwanci sai dana fahinci cewa yadan dade da shigewa na shirya naje dakin.
Na mulke jikina da ture masu kamshi don kawar da karnin nonon da nake shayarwa a lokacin.
Har na shiga na kwanta yana waya bai gama ba har barci ya dauke ni ya gama bai tayardani ba sai da muka tashi don yin sahur.
Washegari tin safe muka tashi da aikin kwashe kayan da ya umurce mu dayi bamu jima da kwashewa baaka fara shigo da wasu iri dirka dirkan kujeru masu kyau da girma.
Ma aikata suka gyara komai sai dai dakina da dayan dakin dake facin din na ihisan komai nashi iri daya ne da nawa kala ne kawai aka banbanta masu sai biyu zuwa uku suka gama lokacin ina kitchen mun fara hada abin buda baki ko.
Munyi mamakin ganin hakan amma naja bakina nai shiru ban tsaya magana ba don jin ko yaya hakan din.
Sai dare sosai ya dawo har yaran sun shige ko dakun nan su don azumi ne kowa ya gaji ba wani dogon hira.
Ko ni har na shige na kashe wutan falon ya dawo gidan jin motsin dawiwan shi yasa na fito ya na zaune yana cin abincin da ya samu an jera mai na buda baki.
Nai mai sannu da zuwa ina kokarin juyawa naji ya kira sunana na dakatar da tafiyan dana fara yi tare da juyowa gare shi.
Yace zoki samu wuri ki zauna ina son nayi magana dake ne samun wuri nayi na zauna sai dai ba gaf dashi ba.
Yace Rahama ina son yin wani magana dake ne sai dai ina fatan zaki fahince duk da nasan ba wani bakon abu bane sosai a gare ki.
Gabana ne ya soma harbawa don ban san wani magana bane wanan wanda ba bako na bane haka ?
Maganan da zanyi bawai ya sabawa sharia bane ko da wata manufa zanyi sai dai daurowan hakan .
Na tattara natsuwana ina sauraren abinda zai fada min din a yadda yake maganan shi mai kama da roko kuma da gadara yasa nasan akwai wata a kasa.
Jin nayi shiru yasa ya dago kai ya dan kalle ni yace dani kina jina kuwa nace inaji kai nake saurare ai .
Yadda nai magana yasa yasan a shirye nake ke nan da inji abinda zai fada din a lokacin.
Ba wani magana bane sai dai kiyi hakkuri a yadda na tsara zaman mu a baya yanzu an samu akasin hakan don Hindatu zata dawo nan garin ku zauna tare.
Dam dam naji gabana ya fadi shike nan ni nawa ya samay ni inko hakane
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22Chapter 23Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32Chapter 33Chapter 34Chapter 35Chapter 36Chapter 37Chapter 38Chapter 39Chapter 40Chapter 41Chapter 42Chapter 43Chapter 44Chapter 45Chapter 46Chapter 47Chapter 48Chapter 49Chapter 50Chapter 51Chapter 52Chapter 53Chapter 54Chapter 55Chapter 56Chapter 57Chapter 58Chapter 59Chapter 60Chapter 61Chapter 62Chapter 63Chapter 64Chapter 65Chapter 66Chapter 67Chapter 68Chapter 69Chapter 70Chapter 71Chapter 72Chapter 73Chapter 74Chapter 75Chapter 76Chapter 77Chapter 78Chapter 79Chapter 80Chapter 81Chapter 82Chapter 83Chapter 84Chapter 85Chapter 86Chapter 87Chapter 88Chapter 89Chapter 90Chapter 91Chapter 92Chapter 93Chapter 94Chapter 95Chapter 96Chapter 97Chapter 98Chapter 99Chapter 100Chapter 101Chapter 102Chapter 103Chapter 104 Chapter 105Chapter 106Chapter 107Chapter 108Chapter 109Chapter 110Chapter 111Chapter 112Chapter 113Chapter 114Chapter 115Chapter 116Chapter 117Chapter 118Chapter 119Chapter 120Chapter 121Chapter 122Chapter 123Chapter 124Chapter 125Chapter 126Chapter 127Chapter 128Chapter 129Chapter 130Chapter 131Chapter 132Chapter 133Chapter 134Chapter 135Chapter 136Chapter 137Chapter 138Chapter 139Chapter 140Chapter 141Chapter 142Chapter 143Chapter 144Chapter 145Chapter 146Chapter 147Chapter 148Chapter 149Chapter 150Chapter 151Chapter 152Chapter 153