wanan din ya baci yaron cikin san murya da nuna fushi a fuskan shi yace kai mummy please go now.
Tace cikin dariya dama abinda yake so ke nan shegen tsabta gare shi kaman ba karamin yaro ba.
Sauran yaran ne suka shigo dakin suna cewa anty is time for prayer mun zo muyi sallah ne tare da ke nace tau ayi alwala.
Tace masha Allahu ashe har jam,in sallah ake a dakin lalai an samu ci gaba.
Suka ce anty ta fada muna cewa idan bamu sallah za, a kona mu ne wai da wuta.
Tace gaskiya ta fada maku oya aje zuwa alwala kafin anty tazo nan suka shige bandaki kafin su fito na fitar masu da hijjab din su.
Anty ke cewa idan mun koma wancan gidan zakuji dadin shi don yafi wanan girma sai dai aikin zai karune don haka nace a samo min wata yar dattijuwa mai dan dama don akwai dakuna da yawa sosai a kowani part gidan babbane kwarai.
Nace cikin mamaki anty yakuma fi wanan girma da kuk ciki tace babban gidane sosai Rama sai in kin gani zaki sheda .
Ba karamin kudi ya kashe ba gurin gina gidan don har ginan yaso ya taba mai aikin shi da kasuwan cin shi don mutane nata magana akai.
Nace ashe harda babban gari akwai tsegumi kamar mu kauye tace inane babu gulma yanzu haka duniya ya koma fa.
Ranan itama a dakin mu tai sallah tana kallo yadda muke sallah da yaran sai sun kalla sun ga abinda nayi zasu kwaikwaya suma suyi hakan.
Muna gamawa taji mun fara karatu duk sun haye min jiki na amma haka muke karatun tai mamaki jin har mun kai kulhuwallahu da yaran don tare muke hadda dasu da baki.
Abin yai matukar bata sha, a take cewa lalai munyi kure dole a samo malamin mai koyar da addini koda da dare ne sai yazo a dan taba.

****** ********* ******
Fitina yakai fita don Jatau ya saka mama da baba a gaba daya samu labarin bani garin.
Haka magana har takai gidan maigari dole sai da aka kira mama taje da kanta.
Nan dai ya koro bayani mama tai tsuru tsuru sai kamay kamay takeyi tarasa na cewa gashi babu kudi don har kudin sadakin ta kashe wai tayi sayayya dasu na aure.
An basu sati biyu kacal su kawo mai kudin shi ko su dauki hukunci kan ta nan suka bar gurin kan wanan magana.
Suna dawowa gida ta saka baba a gaba kan sai dai ya tafi birni yazo dani a daura aure akai ma jatau don bata san inda zata samo mai kudin shi ba cikin sati biyu.
Yana gama sauraren ta yace amma kina da wani magana ni ina zanje cikin kano na dauko Rahama ?
Altine ce tasan inda ta kaita kuma suna can tare ban san wanda zan tambaya inda suke ba yanzu don ba wanda yasan gidan yan uwan nata.
Hankalin mama ya kara tashi sosai har gurin Inna ta taje cikin kwantar da murya take cewa a tsaya a fahinci juna kada abin yakai ga bacin rai.
Inna tace rai shi ya dade baici ba ita ko kano bata taba zuwa ba balle ta ce tasan inda muke.
Su dai da suka ci kudin shi sai su tafi can su karata dashi ita babu ruwan ta cikin wanan magana kuma daga yau su fitar da rai ga tinanen zasu hada ni aure da wani jatau a yanzu.
Mama ta bar gidan cikin bacin rai take cewa yadda ba, a so sai ankai ga yin hakan Inna tace to bissimillah kuma tai mata kashedi akan zuwa gurin ta don babu hadin kifi da kaska yanzu.
Haka ta dawo gids cikin tashin hankali ga kwanaki sai matsowa sukeyi tace idan baba ba zai je nemo mu ba ita zata shirya taje kano da kanta ai mai tambaya baya bata sai ta gano inda muke a kano ta dawo dani an mata aure.
Yace bissimillah gaki ga hanya nidai banci komai na Jatau ba balle ya damay ni.
Haka tashirya ita da Larai kawar ta suka tafi kano tun shigan su garin hankalin su ya fara tashi duk wanda suka gani a bakin tasha sai su tsayar dashi suce don Allah ko yasan wata Rahama tare da Altine mai kulli kulli.
Wasu suyi masu daukan mahaukata wasu kuma su tsaya masu tambayan a wani unguwa sukace daku suke ?
Basu sani ba sai a barsu a tafi sun koma kamar mahaukata suka dawo gida cikin dare hankali a tashe.
Ko sannu baba bai mata ba shiya tayar mata da hankali ke nan ta haufada tana cewa munafuki dama ashe tare dashi aka hada baki don aga bayan ta ai tasan zaman ta dashi.
Hankalinsu har baba ba, a kwance yake ba gashi gidan ya fara yi wa baba tsamin har ya fara kewan Innata a lokacin sai dai yana gundu yanuna yaji masifan mama.
Har bakon da mama Altine ta aje gidan ta da iyalinshi sai da mama ta tayar mai da hankali tace yasan inda mama Altine take inba haka ba may zai sa ta aje shi gida bata sanshi ba.
Nan sukayi tas da mutumin ya nuna mata yafita kwaya dole ta fita batun shi ta kyale shi don yace idan ta sake shigowa ta tayar mai da iyalin shi hankali kan abinda bai shafe shi ba sai yai mata tsinanen dukan da sai an kaita asibiti ta kwanta.
Gidan Lairai taje neman shawara nan dai suka kasa kai mafita ga maganan sai larai ne ke cewa nifa ina ganin mafita daya ne a gareki yanzu shine ki daure ki bashi daya daga cikin yaran nan a zauna lafiya.
Cikin mamaki mama tace wa kawar nata Larai yaushe kika fara hassada na a garin nan ban sani ba Jatau ne zan dauki yar cikina naba aure ko may ?
Larai tace to may ye a hakan ba mafita muke nema ba ko kina da jakka dari da tamanin da zaki ba jatau ne kudin shi.
Nu naga haka shine mafita kawai cikin wanan magana ki samu a zauna lafiya don kin san dai Jatau bai daukan kaddara shi.
Aiko mama tai cikin Larai da masifa suka dinga tonon asiri a tsakanin su kaca kaca sukayi tabar gidan Larai a hasale kowa ya kama gaban shi daga ranan.
Duk wanda yaga mama a lokacin yasan tana cikin tashin hankali sosai don ko ba, a fada ba duk ta ramay ta fita hayacin ta fa fitinan yaran ta da yai mata yawa.
Don babu ragowa ko kadan tsakanin ta dasu sai cin mutunci kamar ba uwarsu ba.
Ana cikin haka akace an kama Rukkaiya da mai nama a shagon shi suna lalata wanda dama ba ranan ne farkon yin haka ba a gare su.
Nan wani sabon magana ya bi gari kwaaa ga kauye da iya daukan magana ko karami ne balle irin wanan.
Da labari yaje wa Inna tace ita kan dai ta godewa Allah da yaraba ta salin alin da wanan fitinanen gida a wanan lokacin.
Ranan komawan su gurin maigari yazo dole ba don taso ba ta hada dubu goma da kyat koshi sai da ta sayar da yan kaddarorin ta ta samay su.
Bayan ta gabatar da kudin da tazo dasu ne aiko Jatau ya buga kasa yace bai san da haka ba shi kudi shi minamina yake so don ba zai dauki hasara ba baiga mata baiga kudin shi.
An kai ruwa rana so sai a gurin dole aka bata zabi idan babu kudi a turasu kotun birni ko kuma ta samu mafita ta bashi kudin shi.
Maiunguwa ne ya kebe da ita gefe ya bata shawara ta bashi yarta daya a wuce gurin don idan ta bari aka tafi kotu daure ta za, ayi can babu kuma may sanin inda aka kaita.
Kuka ta saka ma maiunguwa tana cewa ya cece ta yai mata rai ita bazata iya ba Jatau yar ciki ta ba yadda yake din nan gashi kazami fa tsufa ga rowa da cin mutunci.
Maiunguwa yace ni wanan shawaran shine nake gani kawai mafita a gurinki a wuce gurin don gujewa shigan ki gidan yari.
Bata da zabi dole da wanan shawaran suka koma tabarman mai gari nan mai uguwa ya gabatar da shawaran da sukayi da ita.
Baba dake zaune yace idan haka zai kashe maganan shima ya aminta da hakan .
Aka tambayi Jatau idan ya yarda da hakan yace sai dai yayi maneji don dai shi ba cikin su yaso ba.
Mama naji ta dago kai ta kalli Jatau mutum haka a kazance har yake kiran wai maneji zaiyi da yarta.
Muryan mai gari taji yana tambayan su daga cikin diyan wacece zata bayar.
Nan wani sabon tashin hankali yazo mata to ita wa zata bashi don duk yaran nata ba mutunci ne dasu ba ai.
Babu wace zata fahince ta ta fitar da ita wanan kangin da take ciki cikin ruwan sanyi.
Sai bude baki tayi tace kai kai Rahama Allah ya isa tsakani dake da uwar ki da kika jefa ni wanan halin haka.
Maigari ya matsa mata tace a bashi Rukaiyya nan jatau yace wa shi Allah ya sauwaka mai yarinyar da ta zama ba gari dadi zai aura yagane may gurin ta.
Ran mama ya kara baci tai cikin shi da masifa karshe dai da aka kai ruwa akai rana yace sai dai Lawisa dan dama dama zai laba da ita hakana.
Haka a kawatse kan za a daura aure nan da sati daya ta tare dakin ta mama ta dawo gida cikin bacin rai ta isa gida har da suma sai da tayi hankalinta ya tashi baci ba sha ta shiga wani hali na tashin hankali.



ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE, , ,


IDAN KIN BIYA KADA KI TURAWA WANDA BAI BIYA BA KI TUNA DA AMANA NE HAKAN A TSAKANIN MU , , , ,

14
Ina duke a gurin naji an dafa ni mama altine ce a bayana take fadin taso daina kuka haka zo mu shiga gida wanan tonon asirin haka da may yai kamane wai ?
Ban kiba namike na bita sai ga yara na shigo da kayan inna ta gidan buhu har uku duk na komatsen ta ta hada ciki.
Ba a jima ba tashigo gidan ran ta abace sai dai kana ganin idon ta kasan ranan ba sauki sai na Allah.
Nan mama ta shiga bata hakkuri akan ta zauna amma tace indai ba zai barni gidan shi itama may zata zauna yi a gidan.
Dama don ni da kanne take zama badon wani abuba don haka bazata koma ba sai idan nima ya mayar dani gidan.
Nan dai abu ya yamutse daddatawan unguwa duk sun taru suna ba baba na baki amma ya kyakyshe kasa yace bai san zancen ba tunda mama da tai jagoran ci muke son tozartawa.
Magana zabban kunya yadda baba ke magana kai daji kasan an fi katfin shi.
Shi dai jatau anbashi hakkuri akan cewa ya bari a sulhunta maganan nan da sati daya za, a nemay shi insha Allahu.
Sai dare Inna ta nufi gidan su can taiwa mutanen gidan su bayani suka ce ta zauna suma halin gidan ya ishe su haka na.
Magana har gurin maigari ya koma kan fitinan gidan mu aka kira babana aka bikon Innata amma yace shi ba zai tafi ba kuma zancen Rahama ya yafe ta cikin zurian shi.
Ba, a watse gurin ba sai ga Jatau yazo kan zancen kudin shi yace yai lissafi har sadakin shi dubu sittin yaba mama din.
Akace wa babana to kai kaji abinda ya fadi sai da baba ya share zufan dake karyo mashi yake cewa baida wanan labarin .
Amma abari yaje gida ya tambayi mai dakin shi yadda akayi haka don shi dai bai san komai ba akai.
Sadaki kawai ta nuna mai kuma suna hannun ta tace zataiwa yarinya sayaya da su ne ya bar mata a gurin ta .
Nan yabar fada maimakon suji haushin shi sai tausaya mashi sukayi don sun san baida tacewa a gidan shi don mama tafi karfin shi.
In bashi sadaki da maza ke karba ina mace ina karba sadaki hannun mijin yarta.
Washe gari da aka sake tuntuban shi kan zancen Inna sai cewa yayi suje ya sauwaka mata .
Wanan labarin yai matukar tayar muna da hankali sosai dayazo muna kowa na ma baba kaico da rabuwa da Inna dayi.
Don yayi hasaran macen rufin asirin shi a duniya gashi tana haifa mai diya kyawawa masu tarbiya yace ta tafi da kanne na maza biyu duk ya yafe mata don mama tace bata rika su.
Sabon tashin hankali na shirya ni da mama sai gidan su Inna ta a yadda nai tsanmanin na samay ta cikin damuwa sai naga sabanin haka don dan kwana biyun da tayi har ta dan murmure sosai abinta.
Nan hankalina ya dan kwanta muka ba juna magana take ce min indai naga zaman bai min gurin mama na dawo nan na zauna tare da ita a gidan su.
Nace inna banda matsala gurin mama ko kadan tabkar a furin ki nake zaune a gidan ta don haka zan zauna gurin ta kusa da babana watakila idan yana gani na ya sauko ga fushin shi a samu ku shirya dashi.
Tace Allah sarki yarinya idan har kina hasashen komawa na wanan gidan to kina kaunan mutuwa na ke nan.
May zai mayar dani gidan Audi kuma indai ba wani ikon Allah ba kuma ai na bar gidan shi har abada insha Allahu.
Banji dadin hukuncin Inna ba nashiga damuwa take cewa dani na kwantar da hankalina gurin mama in Allah yakawo min manemin da hankalina ya kwanta dashi a daura min aure na nima na huta.
Cabdijam ni zawarci uwata zawarci dawani ido mutanen gari zasu kalle ni dashi ace auren uwata ya mutu akaina ko may.
Cikin tashin hankalin da na wuni ke nan a gidan su innata ina lalashinta ko zata sauko in baba ya huce ya aiko bikon ta ta koma dakin ta amma fir inna tace badai ita ba kan.
Haka na dawo gida da dare gidan mama ban gane komai ba a gurin Inna sai hakkuri da kwantar min da hankali da tayi.
Ina shigowa gida na samu mama tana waya ga alwal mai wayan sadawa tsaye kofan gida uana jiran tagama abashi kudin shi ya tafi.
Ko ban tambaya ba nasan da yarta take waya a lokacin don yadda naji suna magana na fahinci hakan.
Don naji tana cewa yanzu haka ma rikicin auren ta ake a gari don uban ta ya kara jajibo mata wani tsohon wai ta aura har kai tashin hankalin daya sauwaka wa uwarta tabar gidan nasu.
Banji may tace ba sai cewa tayi abani waya naji mama tana ce min karbi wayan anty ki ce daga birni ke magana dake.
Nakarba muka gaisa da inta take ce min ashe abinda ya faru ke nan Ramana ?
Sai na sa kuka take cewa nayi shiru na saurareta zata dawo wani sati in Allah ya yarda da tadawo zata turo a dauki mama sai mu taho tare da mama na huta da kauyen nan idan ba a ganni ba aibabu mai saka ido a kaina kuma.
Nan dai tai ta bani magana har na gamsu da maganan ta mukai sallama muka awal wayan shi da kudin shi yatafi yana godiya.
Mama tace min kin dawo a lalace na amsa mata tare da neman guri na zauna ina cewa ehmama.
Tace ga abincin ki can dauko kici nace da ita mama na koshi kunu kawai nake son na dan sha na kwanta.
Ina cire kayan jikina ne naji mama nace kinji abinda yar uwar ki ta fada ko akan ki.
Nace naji mama amma ai al, amarin babane da wuya don nasan mama bazata bari ba idan taji tace nima hasashen da na keyi ke nan Allah dai ya haushe mu kan ta.
Mun bar zancen don ko inna ta ban fadawa maganan ba kada hankalin ta ya tashi sai in abin ya tabbata zataji.


****** ********* ******
Bai fadawa kowa dawowan su kasar ba bayan sun gama ganin likita haka ita ma yace bai son ta bugawa kowa waya zasu dawo.
Taja bakin ta tai shiru bata fada ga ranan da zasu dawo ba gidan har suka shigo b Nageria ba wanda yasan da zuwan su.
Karfe goma sha biyun rana suka sauka gida kano ya daukan masu shatan taxi din airport sai gida.
Alama ya nuna matan gidan basu gida a lokacin duk da weekend ne ranan hutu don motocin su baya gida.
A can kan hawa step din gidan ne ya hango Nasir a zaune yayi tagumi sai Amira dake tsaye bayan dan uwan nata tana wasa tsaletsalle akan steps.
Tun hango yaran ya sauke ajiyan zuciya yaran basu damu da tsayawan mota ba a haraban gidan nasu sai harkan gaban su sukeyi kawai.
Muryan mahaifiyar su ne sukaji tace Sweethearts da sauri yaran suka yo kan su cikin murna da jin dadi nan ta durkusa tare da rungumay su zuwa jikin ta sai kuma ta sake kuka.
Ya gama sallaman mai taxes yazo inda suke shima suka rungumay shi cikin murna yake tambayan su ina anty ta tafi yaran sukace tun
Showing 54001 words to 57000 words out of 456145 words
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19 Chapter 20Chapter 21Chapter 22Chapter 23Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32Chapter 33Chapter 34Chapter 35Chapter 36Chapter 37Chapter 38Chapter 39Chapter 40Chapter 41Chapter 42Chapter 43Chapter 44Chapter 45Chapter 46Chapter 47Chapter 48Chapter 49Chapter 50Chapter 51Chapter 52Chapter 53Chapter 54Chapter 55Chapter 56Chapter 57Chapter 58Chapter 59Chapter 60Chapter 61Chapter 62Chapter 63Chapter 64Chapter 65Chapter 66Chapter 67Chapter 68Chapter 69Chapter 70Chapter 71Chapter 72Chapter 73Chapter 74Chapter 75Chapter 76Chapter 77Chapter 78Chapter 79Chapter 80Chapter 81Chapter 82Chapter 83Chapter 84Chapter 85Chapter 86Chapter 87Chapter 88Chapter 89Chapter 90Chapter 91Chapter 92Chapter 93Chapter 94Chapter 95Chapter 96Chapter 97Chapter 98Chapter 99Chapter 100Chapter 101Chapter 102Chapter 103Chapter 104Chapter 105Chapter 106Chapter 107Chapter 108Chapter 109Chapter 110Chapter 111Chapter 112Chapter 113Chapter 114Chapter 115Chapter 116Chapter 117Chapter 118Chapter 119Chapter 120Chapter 121Chapter 122Chapter 123Chapter 124Chapter 125Chapter 126Chapter 127Chapter 128Chapter 129Chapter 130Chapter 131Chapter 132Chapter 133Chapter 134Chapter 135Chapter 136Chapter 137Chapter 138Chapter 139Chapter 140Chapter 141Chapter 142Chapter 143Chapter 144Chapter 145Chapter 146Chapter 147Chapter 148Chapter 149Chapter 150Chapter 151Chapter 152Chapter 153