tace hakane sai dai ai bamu ganewa ne kawai odan ran mu ya baci a lokacin komai mutum zai iya furtawa yanzu dai kinga bako a kan shi bane ta furta amma da yake abin ya shafe shi kinga shi da yake nata a gunshi furcin ya sauka ai.
Inna Allah dai ya kuauta amma abin na daddy ai sai addua kawai don ni na rasa may yake ganewa ga wanan yawan auren da yake yi har nakan yi tunanen nace ko dai mune din baya jin dadin zama damu yasa yake hasashen wasu a waje.
Tace ummm, umm yarinya ba haka bane fa abune da ubangiji ya halasta masuyin shi shi kuma kinga yana da halin shi da zai yi wanda ma baida hali yayi wanan kokarin haka rabu da namijin baushe idan yasa rai ga yin abu bawai gazawan ku bane ko wani abu haka dai Allah ya doro mai wanan rayuwan kuma.
In bashi ba ai masu hali ma basu faye yawan aure hakan ba nagani ku dai sai kuyi ta hakkuri dashi kawai tunda haka Allah ya nufe ku da gani.
Nace nagode inna tace may ye na godiya ki dai godewa Allah da bai aza maki zafin kishi irin na hauka ba akai duk da kinayi amma ai ba irin na wasu ba har a wuce wuri akai.
Munyi sallama inna ta barni da tunanen irin matakin da naso daukawar wa daddy kan wanan aure sai naga ai duk maganan inna gaskiyane ba karyaba.
Babu abinda na rasa a rayuwana yanzu duk da ina da hanyan samu ai shi bai rage min komai ba na hakkin na daya rataya a wuyan shi don haka may zai sa na tsaya batawa kaina lokaci kan wanan shirmayn nabaya ma da yayi iba suka kai balle wai wata matafiya kuma can.
Matsala dai daya ne sai na saurara na sa ido naga ita kuma damay ta shigo gidan idan har bata shiga da sunana ba irin na Raliya da Niima may zai damay ni kuma da ita.
Bata zama bana zama banga abin damuwa ba akai kowa tashi ta fishe shi don miji mai aure aure ai ba dan goyo bane na ma godewa Allah da baiyo ni mai rawan kai ba akan miji da zan tsaya nuna ni watace a wurin shi ko wani abu.
Don wanan matsalar ne ke damun hindatu take wanan zafin kishin haka akan shi ya kamata ace tasan waye mijin mu wa muke aure muke zama dashi.
Shi fa mutum ne irin mazajen da basu da gwana a wurin su amma har yanzu basu gane hakan ba sam.
Mutimin da dan matsala kadan zai iya rufe ido a gaban kowa yai maka tas bai dauke shi komai ba ina wata wai mowa a wurin shi ko bora.
Gashi iya gwargwado yana kokarin shi wurin baiwa kowa hakkin ta a tsakanin zamantakewar mu , sai dai da yake mu matane bamu ganin wanan kokarin da yake a kan mu.
Don a kullun gani muke ai ya karkata a wani bangaren yabar sauran mata ke nan ba a iyamu duk kokarin namiji a kan mu sai mukai zuciyar mu akan abokiyar zaman mu maga may take dashi may suke da miji wanda shine wahalan mu a yau.
Mun gama abinda ya kaimu india na dawo da sakamako mai kyau akan course din da muka je inda da mun dawo zan zama consalta da zan iya shiga ko wani asibiti na kasan mu nai aiki mai amfani a cikin sa.
Ranan jumma, a da dare muka sauka lagos Nigeria ni da yarana da sauran abokan aikina wanda zamu dan tsaya lagos din muyi dan kwanaki don yin wasu cleares din wasu takardun mu a can.
Duk wanan abin maigidan bai masan mun dawo Naija ba yana can tare da amaryan shi sun tafi kaduna wai wani aiki ya kai shi can daga can zasu shiga kano da ita
Zaune yake a bakin gadon dakin hotel din da suka sauka shi da ita ya dauki waya yana hira da bashir nan dai yake wa daddy da sherin kadai san kaunata ta kusa dawowa daga course din ta gashi ina ga baka fada mata zancen auren ka ba ko ?
Ya dan shafo fuskan shi kadan yana sauke ajiyan zuciya yace hakane Bashir sai dai kuma ina ga ai ba zata rasa jin wanan nan labarin ba ko hindatu da zulfa zasu iya fada mata duk da nayi warning din su ga hakan.
Bayan gama wayan su da Bashir din a lokacin itama amaryan na gefe ta na kishingide tana waya da wata kawar ta na shakiyanci sai kwasan dariya suke yi ta wayan.
Gyara kwanciyar shi yake shirin yi yayin da yaji muryan amaryan nasa hajiya Samira tana fadin waini wanan matar taka da kowa ke magana a kanta tana ina ne wai ?
Da sauri ya dan juyo gare ta yake cewa mata wacce matar daga cikin matan nawa kike magana ne ?
Ta dan tabe baki tare da jawo room fresh tana dan fesawa a ko ina na dakin daga kwance tana fadin ita dai wacce ake cewa wai likita ko may ?
Murmushi yayi kawai yace a zuciyar shi anzo wurin indai Rahama ne ai zaki san ta ko sai dai a fili nuna mata yayi da cewa matatace mana ko wani abin ne sai tai shiru don ta fahinci irin yadda yai mata magana din.
Sunyi haka washe gari da safe ya shiga wanka na bugo nombar wayan shi baya kusa yana ban daki sai tai caraf ta daga wayan.
Muryana ne ya daki kunnuwan ta ina fadin hello daddy an tashi lafiya ya aiki ya iyali da sauran jama, an gidan ?
Ke ko wacece ta daina kiran wayan mijina da safe haka don bazan dauki wanan halin ba ga kowace mace.
Murmushi nayi nace ke kuma wacece karuwansa ne ko dadiron sa ko kuma wata yar aikin hotel ce.
Ki kama kan ki ga daukan wayan mijin wasu kina yadda kika ga dama dashi, idan kina son kafa doka gina raminki da kan ki sai ki zauna a ciki amma ba ramin da wata ko wasu suka gina ba kizo kice zaki shige ki mamaye.
Idan kina son ki san ko ni wacece tambayan shi kice dashi uwar diyan shi takwas ne ta kira layin shi don haka kibawa kan ki amsa dani dake wake da mijin yanzu ?
Ina fadin haka nai sauri na katse layin nawa ban staya sauraren abinda zata fadi ba a lokacin don kada ta jefo min mai zafin da yafin da yafi wanda na fada mata din.
Sai dai tana cikin kunduma zagi daddy din yafito daga ban dakin yana goge ruwa a kansa tambaya ta yake tare da kai idanuwan shi aka wayan shi dake hannun ta yana fadin keda waye haka ?
Take cewa wata banza ce ta bugo layin ka shine nake fada mata kada ta kara kiran layinka a wannan lokaci sai kawai ta kai min zagi ,
Ko wacece zamu hadu da ita don bata san wace ta zaga ba ke nan dan ni bana ba da bashi ko kadan,.
Bata ma san ya kawo bakin gadon ba sai ji tayi ya wafci wayan shi a hannun ta da karfi yana duba wanda ya kira layin nasa sai yaga ai nombana ne na nan gida Nigeria na kira shi dashi.
Watau ke nan da Rahama wanan take cin mutunci haka ko, sai dai gaskiya bata kyauta mai ba don ba haka yaso ba da zancen don shi so yayi sai na dawo muyi maganan.
Batare da ya damu da tana gurin ba, ya kira layin nawa kamar kada na dauka dai na dauka yake cewa kina ina ne naga nomban nigeria kika kirani dashi ?
Nace ina lagos yau six days kenan da dawowan mu gobe zan iso Abuja insha Allahu sai dai nakira ka wata yar iska naji ta dauki waya har tana min barazana wai wayan mijin tane wanan na daina kiran ka a wanan lokacin haka .
Ita din wacece daddy kardai nace kana hurda da matan banza ne kuma abinda ban san ka dashi ba a baya ?
Yace bar wanan zancen idan kin iso zamuyi magana akan sa ina yaran suke ne mu gaisa nace dashi yanzu suka fita da doctor Hauwa zuwa cikin gari.
Mukai sallama dashi ya kashe wayan tare da sauke ajiyan zuciya tana furzo iska daga bakin shi ya lumshe idanuwan shi a hankali don bai san ta ina zai fito min da zancen ba.
Muryan tane yaji tana fadin wai wata yar iskace a cikin matan naka har zatace dani wai na gina ramin kaina wanan ramin ba nawa bane naje gaba ?
A hasale yace da ita matar nawa zaki zaga da yar iska a gabana ita bata zage ki ba sai kece mai zagin ta a gabana matar da nake da zuria da ita fiye da kowa a duniya matar da, , , , ,
Haba malam ya isa haka ko ba a fada ba nasan wanan yar iskan likitar matar takace da ake fadin kana ji da ita don naga alama tunda gashi ka rufe ido a kanta kana son ci min mutunci.
Yace idan kika sake maimaita zagin da kikai mata a gabana yanzu ranki zai baci dani a wurin nan.
Ki shirya yau Abuja zamu koma don Rahama ta iso Nigeria gobe zata shigo Abuja din ita da yaran da ta tafi.
Yana fadin haka bai tsaya bin ta nata ba ya fara shirya kayan shi nan ya barta da mamakin wanan irin rawan kafan da kaduwa da yayi akan matar shi .
Wai wacece wanan da yake wa rawan kafa haka ita dai taga matan nashi ba wani abin kai gida a kan su balle ace wai wata tafita a cikin su.
Shiryawa yayi ya fita daga dakin yana fadin zai je ya dawo kafin ya dawo ta shirya yana fita taja uban tsuki wayan ta ta jawo tana fadin ni za a kawowa iskanci akan wata banza can wai Rahama ?
Kawarta ta kira take fada mata komai har take cewa ba inda zata don kano yace zasu tafi amma yanzu ya canza saboda wata wai su koma Abuja.
Kawar tace wallahi Samira kibi a hankali kin dai san ko shekara nawa muka kwasa wurin samun hankalin shi kafin ya yarde muna don haka ki rufawa kan ki asiri kibishi ku tafi.
Baki ko san yaya matar take ba balle har kikai ga daukan mataki a kan ta sai idan kin ganta ne ai zaki dauki mataki a kan ta.
Take cewa hakane kuma fa bari na shirya naje ko ganin yar iska nayi naga nata kalar wanka wata kila ma wata cus ce can ilimin ne kawai a kai.
Sai suka kwashe da dariya a lokaci daya kawar tace koke fa mutumiyar aiba haka kai tsaye ake kama makashi ba sai da kwana kwana.
Nan ta mike ta shiga shiryawa sai dai ranta abace don gani take duk ajin ta da kima ace akan wata zata rushe plain din ta da tayi na zuwa kano ziyarar dangin shi a karo na farko ?
Da yamma suka shiga Abuja kai tsaye part din maigidan ta sauka don nuna isa da gadara ga matan gidan ta nuna ita ta isa ga kowa don hamshakiyace.
Amma sai ya karya mata takon da cewa akan may zata zo nan bayan ga gurin ta can takoma can don a cikin iyalin shi ya shigo.
Duk da ranta ya baci amma dole ne tabi shawarar kawar ta ta lalaba shi taga gudun su tukun.
Haka ta mike a likacin hindatu tashigo suka hade a falon kowa yabi dan uwa da harara da hassada a fili na kishi.
Nan ta fice tabar hindatun na kallon yanayin shi ta fahinci akwai bacin rai a ciki sannu da zuwa tai mashi don har lokacin ba dadi a tsakanin su.
Washegari da safe sai shirin zuwa taron mu akeyi don na bugo waya muna iya port a lokacin da zamu taso daga lagos din.
Tsayawa fadin irin shirin da nayi bata lokaci ne dagani har yaran munyi kyau sosai don zama indiya ba wasa ba gaskiya.
Ban kawo komai ba a raina na cewa zamu hadu da wai wata amaryan shi ni dai daukina kawai shinenaga yarana dana share tsawon watan ni bama tare da su.
Mun kai wani dan lokaci kafin mu tashi don haka sai sha biyu muka sauka a Abuja inda shi da yaran ne suka zo taron mu da hindatu.
Da murna na rungumay yarana ban ko bi ta kan sgi muka kuma rugumay juna da hindatu din sai yaran da suka rugumay mahaifin su don murnan ganin shi.
Jinior yana lake a jikina na dago kai muka hada ido dashi alaman radhin gaskiya irin na maza karara a gareshi nace yallabai mun samay ku lafiya ?
Ya dan murmusa yace lafiya kalau ya karatu da zaman india nace sai hamdala na dauki yar wurin hindatu dake murnan ganin mu.
Mun dan dauki lokaci muka kwasa sai gida ina tare da yarana har muka kawo gida ina maijin dadin ganin yadda yaran ke a cikin walwalan su babu wani mairaicin rashina da suka yi.
Wani abin sai uwa dama abinda nake so ke nan na dage akan sai Inna tazo ta zauna min da yaran duk da kunyan da take nunawa na rashin son nuwa duniya itace mahaifiya na a matsayina na yar fari a gurin ta.
Muna shiga gida na hango wata mace a tafe tana bun kasa a kasa da waya a hannun ta bayan na bude motan kafana kawai na sako a kasa ba tare da na fito ba muka tsaya magana da yaran dake fadan daukar jakana na hannu.
Sai da na raba gardaman na karasa fitowa daga motar gaba daya hankalinta na a gurin mu yayin dana karasa fitowa daga cikin motar gaba daya sandarewa tayi a tsaye inda take tana rayawa a ranta ta ina zata fara dani.
Ga dai Ilimi ga kuma uwa uba kyau da tsari da ta hango muraran a wurina ga wani kwarjini da nai mata a idanuwanta a lokaci daya.
Ban ko koma ta kanta ba na ja yarana muka fara hawa steps din shiga gidan hankalina a kwance.
Sai naji shi yana fadin Samira ga docter ta dawo fa daga india ita da yaran ta yadda tai min wani irin kallo nima haka na juyo nai mata tare da fadin wacece kuma Samira ?
Kafin yai magana sai naji tace wace kike gani a gaban ki nice amaryan maigidan da fatan zaki gane ni daga yau.
Wani kallo nai mata tare da sake shuumin murmushi nake cewa amarya amarya fa ko dai uwar gidan wanan ai ba a kiran ta da amarya don ta haife mu ko ?
Ai sai dai mu bata kambun uwargidan cin gidan gaba daya shi zai fi sauki na fadi haka ne don irin yadda ta mayar min da magana itama.
Murmushi daddy tayi daga inda yake tsaye yake cewa shiga dai ki huta kafin muyi magana ko nace magana kuma may ya saura tunda ka gabatar da mu ga junar mu na juya muka shige da yaran ina jin tana fadin.
Duniya na haifa ba ku ba sai ki tsaya ga wanda ya aje ki in kina takama da kurciyane ai ya ganki a gaban shi ya dauko ni.
Ban tsaya ba don nasan su Inna na gidan muka shige ciki nan muka tari junar mu da murna ban sake bi ta kan shi ba ga yarana sun baibaye ni.
Ban samu kaina dasu ba sai da akai kiran sallah na kora su suje sallah na samu na shiga dakina sai dai zuciyana fam yake da tunanen wanan matar.
Bayan nai wanka na sauya kayan jikina sai ga Atika tashigo dakin da murnan ta don bata gida da muka iso tana school muna cikin hira da ita ne daddy ya shigo dakin ya samay mu.
Wani kallo na tsana na watsa mashi yayin da Atika ta gaidashi tafice daga dakin yake cewa dani basu dai barki kin huta ba ke nan.
Nace ba kadai barni na huta ba kai da ka kara jajibo muna wani wahala a gidan kuma.
Wahala kuma Rahama aureb nawa shine wahala nace a lalace aure ina aure a nan ka kwaso muna uwar mata wai kishiya wanan ai a gidan dabe ya dace a ganta ba a gidan ka ba.
Mace haka babu fasali a tare da ita daganin ta ma irin matan nan ne yan safara ba abin kwarai bane don tanayin ta yai kama da yan kano jidda.
Dariya yayi min cikin shuumanci yace duk ita kadai nace ni na rasa gane wanan irin rayuwan for god sake may ye ka rasa daddy a gurin mu da baka da aiki sai auren barnan suna ko yaushe.
Wanan ce zan zauna da ita a cikin gidan nan haka ga yara a haka yara zasu tashi da irin tarbiyan da muke so a garesu.
Ko yaushe suna ganin nauin mata lalatattu iri iri gaskiya ya zama dole a gare ni wanan karon na nisance ka kaje duk abinda kake nema a gun mata kaita nema amma
Showing 444001 words to 447000 words out of 456145 words
Inna Allah dai ya kuauta amma abin na daddy ai sai addua kawai don ni na rasa may yake ganewa ga wanan yawan auren da yake yi har nakan yi tunanen nace ko dai mune din baya jin dadin zama damu yasa yake hasashen wasu a waje.
Tace ummm, umm yarinya ba haka bane fa abune da ubangiji ya halasta masuyin shi shi kuma kinga yana da halin shi da zai yi wanda ma baida hali yayi wanan kokarin haka rabu da namijin baushe idan yasa rai ga yin abu bawai gazawan ku bane ko wani abu haka dai Allah ya doro mai wanan rayuwan kuma.
In bashi ba ai masu hali ma basu faye yawan aure hakan ba nagani ku dai sai kuyi ta hakkuri dashi kawai tunda haka Allah ya nufe ku da gani.
Nace nagode inna tace may ye na godiya ki dai godewa Allah da bai aza maki zafin kishi irin na hauka ba akai duk da kinayi amma ai ba irin na wasu ba har a wuce wuri akai.
Munyi sallama inna ta barni da tunanen irin matakin da naso daukawar wa daddy kan wanan aure sai naga ai duk maganan inna gaskiyane ba karyaba.
Babu abinda na rasa a rayuwana yanzu duk da ina da hanyan samu ai shi bai rage min komai ba na hakkin na daya rataya a wuyan shi don haka may zai sa na tsaya batawa kaina lokaci kan wanan shirmayn nabaya ma da yayi iba suka kai balle wai wata matafiya kuma can.
Matsala dai daya ne sai na saurara na sa ido naga ita kuma damay ta shigo gidan idan har bata shiga da sunana ba irin na Raliya da Niima may zai damay ni kuma da ita.
Bata zama bana zama banga abin damuwa ba akai kowa tashi ta fishe shi don miji mai aure aure ai ba dan goyo bane na ma godewa Allah da baiyo ni mai rawan kai ba akan miji da zan tsaya nuna ni watace a wurin shi ko wani abu.
Don wanan matsalar ne ke damun hindatu take wanan zafin kishin haka akan shi ya kamata ace tasan waye mijin mu wa muke aure muke zama dashi.
Shi fa mutum ne irin mazajen da basu da gwana a wurin su amma har yanzu basu gane hakan ba sam.
Mutimin da dan matsala kadan zai iya rufe ido a gaban kowa yai maka tas bai dauke shi komai ba ina wata wai mowa a wurin shi ko bora.
Gashi iya gwargwado yana kokarin shi wurin baiwa kowa hakkin ta a tsakanin zamantakewar mu , sai dai da yake mu matane bamu ganin wanan kokarin da yake a kan mu.
Don a kullun gani muke ai ya karkata a wani bangaren yabar sauran mata ke nan ba a iyamu duk kokarin namiji a kan mu sai mukai zuciyar mu akan abokiyar zaman mu maga may take dashi may suke da miji wanda shine wahalan mu a yau.
Mun gama abinda ya kaimu india na dawo da sakamako mai kyau akan course din da muka je inda da mun dawo zan zama consalta da zan iya shiga ko wani asibiti na kasan mu nai aiki mai amfani a cikin sa.
Ranan jumma, a da dare muka sauka lagos Nigeria ni da yarana da sauran abokan aikina wanda zamu dan tsaya lagos din muyi dan kwanaki don yin wasu cleares din wasu takardun mu a can.
Duk wanan abin maigidan bai masan mun dawo Naija ba yana can tare da amaryan shi sun tafi kaduna wai wani aiki ya kai shi can daga can zasu shiga kano da ita
Zaune yake a bakin gadon dakin hotel din da suka sauka shi da ita ya dauki waya yana hira da bashir nan dai yake wa daddy da sherin kadai san kaunata ta kusa dawowa daga course din ta gashi ina ga baka fada mata zancen auren ka ba ko ?
Ya dan shafo fuskan shi kadan yana sauke ajiyan zuciya yace hakane Bashir sai dai kuma ina ga ai ba zata rasa jin wanan nan labarin ba ko hindatu da zulfa zasu iya fada mata duk da nayi warning din su ga hakan.
Bayan gama wayan su da Bashir din a lokacin itama amaryan na gefe ta na kishingide tana waya da wata kawar ta na shakiyanci sai kwasan dariya suke yi ta wayan.
Gyara kwanciyar shi yake shirin yi yayin da yaji muryan amaryan nasa hajiya Samira tana fadin waini wanan matar taka da kowa ke magana a kanta tana ina ne wai ?
Da sauri ya dan juyo gare ta yake cewa mata wacce matar daga cikin matan nawa kike magana ne ?
Ta dan tabe baki tare da jawo room fresh tana dan fesawa a ko ina na dakin daga kwance tana fadin ita dai wacce ake cewa wai likita ko may ?
Murmushi yayi kawai yace a zuciyar shi anzo wurin indai Rahama ne ai zaki san ta ko sai dai a fili nuna mata yayi da cewa matatace mana ko wani abin ne sai tai shiru don ta fahinci irin yadda yai mata magana din.
Sunyi haka washe gari da safe ya shiga wanka na bugo nombar wayan shi baya kusa yana ban daki sai tai caraf ta daga wayan.
Muryana ne ya daki kunnuwan ta ina fadin hello daddy an tashi lafiya ya aiki ya iyali da sauran jama, an gidan ?
Ke ko wacece ta daina kiran wayan mijina da safe haka don bazan dauki wanan halin ba ga kowace mace.
Murmushi nayi nace ke kuma wacece karuwansa ne ko dadiron sa ko kuma wata yar aikin hotel ce.
Ki kama kan ki ga daukan wayan mijin wasu kina yadda kika ga dama dashi, idan kina son kafa doka gina raminki da kan ki sai ki zauna a ciki amma ba ramin da wata ko wasu suka gina ba kizo kice zaki shige ki mamaye.
Idan kina son ki san ko ni wacece tambayan shi kice dashi uwar diyan shi takwas ne ta kira layin shi don haka kibawa kan ki amsa dani dake wake da mijin yanzu ?
Ina fadin haka nai sauri na katse layin nawa ban staya sauraren abinda zata fadi ba a lokacin don kada ta jefo min mai zafin da yafin da yafi wanda na fada mata din.
Sai dai tana cikin kunduma zagi daddy din yafito daga ban dakin yana goge ruwa a kansa tambaya ta yake tare da kai idanuwan shi aka wayan shi dake hannun ta yana fadin keda waye haka ?
Take cewa wata banza ce ta bugo layin ka shine nake fada mata kada ta kara kiran layinka a wannan lokaci sai kawai ta kai min zagi ,
Ko wacece zamu hadu da ita don bata san wace ta zaga ba ke nan dan ni bana ba da bashi ko kadan,.
Bata ma san ya kawo bakin gadon ba sai ji tayi ya wafci wayan shi a hannun ta da karfi yana duba wanda ya kira layin nasa sai yaga ai nombana ne na nan gida Nigeria na kira shi dashi.
Watau ke nan da Rahama wanan take cin mutunci haka ko, sai dai gaskiya bata kyauta mai ba don ba haka yaso ba da zancen don shi so yayi sai na dawo muyi maganan.
Batare da ya damu da tana gurin ba, ya kira layin nawa kamar kada na dauka dai na dauka yake cewa kina ina ne naga nomban nigeria kika kirani dashi ?
Nace ina lagos yau six days kenan da dawowan mu gobe zan iso Abuja insha Allahu sai dai nakira ka wata yar iska naji ta dauki waya har tana min barazana wai wayan mijin tane wanan na daina kiran ka a wanan lokacin haka .
Ita din wacece daddy kardai nace kana hurda da matan banza ne kuma abinda ban san ka dashi ba a baya ?
Yace bar wanan zancen idan kin iso zamuyi magana akan sa ina yaran suke ne mu gaisa nace dashi yanzu suka fita da doctor Hauwa zuwa cikin gari.
Mukai sallama dashi ya kashe wayan tare da sauke ajiyan zuciya tana furzo iska daga bakin shi ya lumshe idanuwan shi a hankali don bai san ta ina zai fito min da zancen ba.
Muryan tane yaji tana fadin wai wata yar iskace a cikin matan naka har zatace dani wai na gina ramin kaina wanan ramin ba nawa bane naje gaba ?
A hasale yace da ita matar nawa zaki zaga da yar iska a gabana ita bata zage ki ba sai kece mai zagin ta a gabana matar da nake da zuria da ita fiye da kowa a duniya matar da, , , , ,
Haba malam ya isa haka ko ba a fada ba nasan wanan yar iskan likitar matar takace da ake fadin kana ji da ita don naga alama tunda gashi ka rufe ido a kanta kana son ci min mutunci.
Yace idan kika sake maimaita zagin da kikai mata a gabana yanzu ranki zai baci dani a wurin nan.
Ki shirya yau Abuja zamu koma don Rahama ta iso Nigeria gobe zata shigo Abuja din ita da yaran da ta tafi.
Yana fadin haka bai tsaya bin ta nata ba ya fara shirya kayan shi nan ya barta da mamakin wanan irin rawan kafan da kaduwa da yayi akan matar shi .
Wai wacece wanan da yake wa rawan kafa haka ita dai taga matan nashi ba wani abin kai gida a kan su balle ace wai wata tafita a cikin su.
Shiryawa yayi ya fita daga dakin yana fadin zai je ya dawo kafin ya dawo ta shirya yana fita taja uban tsuki wayan ta ta jawo tana fadin ni za a kawowa iskanci akan wata banza can wai Rahama ?
Kawarta ta kira take fada mata komai har take cewa ba inda zata don kano yace zasu tafi amma yanzu ya canza saboda wata wai su koma Abuja.
Kawar tace wallahi Samira kibi a hankali kin dai san ko shekara nawa muka kwasa wurin samun hankalin shi kafin ya yarde muna don haka ki rufawa kan ki asiri kibishi ku tafi.
Baki ko san yaya matar take ba balle har kikai ga daukan mataki a kan ta sai idan kin ganta ne ai zaki dauki mataki a kan ta.
Take cewa hakane kuma fa bari na shirya naje ko ganin yar iska nayi naga nata kalar wanka wata kila ma wata cus ce can ilimin ne kawai a kai.
Sai suka kwashe da dariya a lokaci daya kawar tace koke fa mutumiyar aiba haka kai tsaye ake kama makashi ba sai da kwana kwana.
Nan ta mike ta shiga shiryawa sai dai ranta abace don gani take duk ajin ta da kima ace akan wata zata rushe plain din ta da tayi na zuwa kano ziyarar dangin shi a karo na farko ?
Da yamma suka shiga Abuja kai tsaye part din maigidan ta sauka don nuna isa da gadara ga matan gidan ta nuna ita ta isa ga kowa don hamshakiyace.
Amma sai ya karya mata takon da cewa akan may zata zo nan bayan ga gurin ta can takoma can don a cikin iyalin shi ya shigo.
Duk da ranta ya baci amma dole ne tabi shawarar kawar ta ta lalaba shi taga gudun su tukun.
Haka ta mike a likacin hindatu tashigo suka hade a falon kowa yabi dan uwa da harara da hassada a fili na kishi.
Nan ta fice tabar hindatun na kallon yanayin shi ta fahinci akwai bacin rai a ciki sannu da zuwa tai mashi don har lokacin ba dadi a tsakanin su.
Washegari da safe sai shirin zuwa taron mu akeyi don na bugo waya muna iya port a lokacin da zamu taso daga lagos din.
Tsayawa fadin irin shirin da nayi bata lokaci ne dagani har yaran munyi kyau sosai don zama indiya ba wasa ba gaskiya.
Ban kawo komai ba a raina na cewa zamu hadu da wai wata amaryan shi ni dai daukina kawai shinenaga yarana dana share tsawon watan ni bama tare da su.
Mun kai wani dan lokaci kafin mu tashi don haka sai sha biyu muka sauka a Abuja inda shi da yaran ne suka zo taron mu da hindatu.
Da murna na rungumay yarana ban ko bi ta kan sgi muka kuma rugumay juna da hindatu din sai yaran da suka rugumay mahaifin su don murnan ganin shi.
Jinior yana lake a jikina na dago kai muka hada ido dashi alaman radhin gaskiya irin na maza karara a gareshi nace yallabai mun samay ku lafiya ?
Ya dan murmusa yace lafiya kalau ya karatu da zaman india nace sai hamdala na dauki yar wurin hindatu dake murnan ganin mu.
Mun dan dauki lokaci muka kwasa sai gida ina tare da yarana har muka kawo gida ina maijin dadin ganin yadda yaran ke a cikin walwalan su babu wani mairaicin rashina da suka yi.
Wani abin sai uwa dama abinda nake so ke nan na dage akan sai Inna tazo ta zauna min da yaran duk da kunyan da take nunawa na rashin son nuwa duniya itace mahaifiya na a matsayina na yar fari a gurin ta.
Muna shiga gida na hango wata mace a tafe tana bun kasa a kasa da waya a hannun ta bayan na bude motan kafana kawai na sako a kasa ba tare da na fito ba muka tsaya magana da yaran dake fadan daukar jakana na hannu.
Sai da na raba gardaman na karasa fitowa daga motar gaba daya hankalinta na a gurin mu yayin dana karasa fitowa daga cikin motar gaba daya sandarewa tayi a tsaye inda take tana rayawa a ranta ta ina zata fara dani.
Ga dai Ilimi ga kuma uwa uba kyau da tsari da ta hango muraran a wurina ga wani kwarjini da nai mata a idanuwanta a lokaci daya.
Ban ko koma ta kanta ba na ja yarana muka fara hawa steps din shiga gidan hankalina a kwance.
Sai naji shi yana fadin Samira ga docter ta dawo fa daga india ita da yaran ta yadda tai min wani irin kallo nima haka na juyo nai mata tare da fadin wacece kuma Samira ?
Kafin yai magana sai naji tace wace kike gani a gaban ki nice amaryan maigidan da fatan zaki gane ni daga yau.
Wani kallo nai mata tare da sake shuumin murmushi nake cewa amarya amarya fa ko dai uwar gidan wanan ai ba a kiran ta da amarya don ta haife mu ko ?
Ai sai dai mu bata kambun uwargidan cin gidan gaba daya shi zai fi sauki na fadi haka ne don irin yadda ta mayar min da magana itama.
Murmushi daddy tayi daga inda yake tsaye yake cewa shiga dai ki huta kafin muyi magana ko nace magana kuma may ya saura tunda ka gabatar da mu ga junar mu na juya muka shige da yaran ina jin tana fadin.
Duniya na haifa ba ku ba sai ki tsaya ga wanda ya aje ki in kina takama da kurciyane ai ya ganki a gaban shi ya dauko ni.
Ban tsaya ba don nasan su Inna na gidan muka shige ciki nan muka tari junar mu da murna ban sake bi ta kan shi ba ga yarana sun baibaye ni.
Ban samu kaina dasu ba sai da akai kiran sallah na kora su suje sallah na samu na shiga dakina sai dai zuciyana fam yake da tunanen wanan matar.
Bayan nai wanka na sauya kayan jikina sai ga Atika tashigo dakin da murnan ta don bata gida da muka iso tana school muna cikin hira da ita ne daddy ya shigo dakin ya samay mu.
Wani kallo na tsana na watsa mashi yayin da Atika ta gaidashi tafice daga dakin yake cewa dani basu dai barki kin huta ba ke nan.
Nace ba kadai barni na huta ba kai da ka kara jajibo muna wani wahala a gidan kuma.
Wahala kuma Rahama aureb nawa shine wahala nace a lalace aure ina aure a nan ka kwaso muna uwar mata wai kishiya wanan ai a gidan dabe ya dace a ganta ba a gidan ka ba.
Mace haka babu fasali a tare da ita daganin ta ma irin matan nan ne yan safara ba abin kwarai bane don tanayin ta yai kama da yan kano jidda.
Dariya yayi min cikin shuumanci yace duk ita kadai nace ni na rasa gane wanan irin rayuwan for god sake may ye ka rasa daddy a gurin mu da baka da aiki sai auren barnan suna ko yaushe.
Wanan ce zan zauna da ita a cikin gidan nan haka ga yara a haka yara zasu tashi da irin tarbiyan da muke so a garesu.
Ko yaushe suna ganin nauin mata lalatattu iri iri gaskiya ya zama dole a gare ni wanan karon na nisance ka kaje duk abinda kake nema a gun mata kaita nema amma
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22Chapter 23Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32Chapter 33Chapter 34Chapter 35Chapter 36Chapter 37Chapter 38Chapter 39Chapter 40Chapter 41Chapter 42Chapter 43Chapter 44Chapter 45Chapter 46Chapter 47Chapter 48Chapter 49Chapter 50Chapter 51Chapter 52Chapter 53Chapter 54Chapter 55Chapter 56Chapter 57Chapter 58Chapter 59Chapter 60Chapter 61Chapter 62Chapter 63Chapter 64Chapter 65Chapter 66Chapter 67Chapter 68Chapter 69Chapter 70Chapter 71Chapter 72Chapter 73Chapter 74Chapter 75Chapter 76Chapter 77Chapter 78Chapter 79Chapter 80Chapter 81Chapter 82Chapter 83Chapter 84Chapter 85Chapter 86Chapter 87Chapter 88Chapter 89Chapter 90Chapter 91Chapter 92Chapter 93Chapter 94Chapter 95Chapter 96Chapter 97Chapter 98Chapter 99Chapter 100Chapter 101Chapter 102Chapter 103Chapter 104Chapter 105Chapter 106Chapter 107Chapter 108Chapter 109Chapter 110Chapter 111Chapter 112Chapter 113Chapter 114Chapter 115Chapter 116Chapter 117Chapter 118Chapter 119Chapter 120Chapter 121Chapter 122Chapter 123Chapter 124Chapter 125Chapter 126Chapter 127Chapter 128Chapter 129Chapter 130Chapter 131Chapter 132Chapter 133Chapter 134Chapter 135Chapter 136Chapter 137Chapter 138Chapter 139Chapter 140Chapter 141Chapter 142Chapter 143Chapter 144Chapter 145Chapter 146Chapter 147Chapter 148Chapter 149 Chapter 150Chapter 151Chapter 152Chapter 153