gara kawai na barsu na koma kano komai ya fanjama fanjan.
Kinji abinda na fada aiki nace kwarai kuwa ai wanan ba matsala bane don gidan ka ne danan da can sai dai ni zan barku na koma kano na zauna tunda dama na gama abinda ya kawo ni garin ina ga zaifi maku dadi hakan ma don ku sakata ku wala ba sai na tsaya a tsakanin ku ba.
Yace aiko kina nan bazaki hanamu sakata ba kamar yadda itama bazata hanaki sakata ba din.
Don haka gara na koma inda na saba yafi min zama a cikin ku mu kadai dagani sai ku a garin mutane.
Yace wanan kuma maganan ki ne kin dai ji tsarin danayi yanzu a gidana nace naji don haka zuwa jibi zata iso don mun mai da auren mu da ita.
Nace ai naga alaman an maida aure tunda take son zuwa takurawa wacce ka sayo ba auro ta kayi ba kamar kowa dama dani tafita yanzu kuma ta dawo dani a ranta.
Yace wanan kuma tunanen ki ne hakan ni dau gidana ne kuma yadda nake so zan tsara kowa na da hakki a gare ni .
Idan zaki fahince ni ki kwantar da hankali don babu abinda zai faru tunda ita ba bakuwar ki bace.
Ni dai na fada maki abinda ake ciki in zakiyi hakkuri ku zauna lafiya dan ba wanda ya kawo wani a cikin ku nina kawo kowan ku kowa kuma da halin shi zan zauna dashi.
Na mike nace wanan sai kuma a yaudari wata ba ni ba Allah ya baku zaman lafiya dama tare na samay ku ai koda na shigo don haka kunfi kusa.
May ya kawo zancen yaudara anan dukkan ku ai mata nane babu wacce zan tsaya yaudara daga cikin ku.
Banyi tsamanin jin haka daga gareki ba a yadda na tsamoki da farko daga cikin ku na kawo ki nan don yanzu nace wata zata zo ku zauna shine zai zama matsala.
Na juyo tare da tsayawa nace tun farko ai saida na baka shawaran yin haka amma kace dani ba tsarin ka ba ke nan haka kaga dama.
Sai yanzu din ta kullo ni arai zata zo tace zata shiga min rayuwa ban sa akai ba balle a kar min .
Kuma kafin ma ta taso ni na isa gida ko sai tayi da wata amma badai Rahama ba dai kan.
Inda nasan wanan shirin kake kwana da kwanaki aida baka bata lokacin ka ba gurin shiri da kafada min tuni da angama ai.
Na juya na wuce zuwa dakina ban kara tsayawa sauraren shi ba ina shiga nafara hada kayana dake cikin wardrobe.
Tsab nagama shirins tunda dare na rufo kofana tare da hayewa gado wurin yara na da Aisha dake kwance gefen su.
Barci ya kaurace min a idona sai faman tunane nakeyi don na tabbatar da wanj manufa hindatu ta zabi biyoni Abuja wanan karon wanda manufan bai wuce kalman daukan fansa ba akaina.
Tunda dama tana cewa a dalilin shegen dana akai mata saki don haka sai ta rama abinda nai mata koda zata tafi tsirara ne.
Abubuwan da daddy ke min duk kwana kin na dama nasha jinin jikina da akwai wata akasa gashi kuwa yau naji da kunnuwa na.
Kai namiji sai a barshi kawai idan ya tashi munafuncin shi sai dabara da wayo ya bace mashi wai yau daddy ne da bakin shi yake ce min da hindatu zamu zauna gidan nan.
Matar da bata maida fitina bakin komai ba aida in zauna da ita gara nakoma can in ma dafani anty zatayi yafi da hindatu ta shigo min da balai gida.
Wai ma sai bayan da ya gama komai shine yanzu ya mayar dani sakarai yazo fada min abinda ta zaba don ta dawo mai.
Ba wani dadi naji ba koda nike ni kadai din balle ace an karo min sabon fitina akaina.
Ni wanan rayuwan auren da may yai kamane wai kullun sabon fitina da kanana kanan rashin fahinta ke zo muna.
Ni dai arabu yafi min komai sauki da wanan zaman danger da muke da kishiyoyi wi da mijin ma haka wi.
Da yake barci barawo ne sai da yai dabaran satana cikin wanan halin da nake ciki da asuba ranan shi da kan shi ya tashe ni inta dasu Aisha suyi sahur acikin waya.
Ban fito don sahur ba dama ni ban damu da yin sahur din ba kullun balle yau da raina yake a bace.
Ruwan sanyi kawai nake da bukatan sha na koma na kwanta nafito falin din in dauki ruwa a kitchen nan nagan shi zaune yana shan tea suna sahur shida Nasir don yaron akwai shi da kokarin Ibada sosai.
Ban ko kalli inda suke ba na wuce zuwa kitchen kai tsaye sai Nasir din ke cewa dani kin tashi mummy nace eh Nasir ba tare da na tsaya ba na wuce abina uban yabini da kallo kawai.
Ganin yaron ya bini da kallo yasa yai murmushi yace yau mummy ka fushi take kyale ta yaron yace but why daddy yace wa yaron nothing cikin daga kafadan shi.
Sai can yace wai bata son dawowan maman Ihisan nan gari haba daddy a gidan nan wanan matar zata dawo ta zauba da mu haba haba gidan zai zama badadi ke nan daddy .
Wani tsawa ya dakawa yaron yana fada dashi Nasir har yaushe kasan irin wanan magana ina ruwanka da harka.
Yaron ya ja bakin shi yai shiru haka ya mike ya bar uban zaune a falo ya bi bayan yaron da kallon mamaki da takaici.
Kafin karfe bakwai na shirya tsab na shirya yaran nawa kuma tare da Aisha da Atika sai helen da nake tunanen yadda zanyi da ita don dole na sallamay ta koma gida.
Muryana da Aisha ya tsinkayo daga dakin shi lokacin da nake cewa da ita kuyi sauri ku shirya bana son muyi tafiyan rana don kun san azumi ne ga helen ta dage da kukan ta wai sai ta bini a fadawa wacce ta kawo min ita tare zamu tafi.
Ban fi minti biyar ba da shiga ya shigo dakin da sallaman shi ya bi kayana dake a tsakiyan dakin cikin troler dina da kallo.
Ya juyo inda nake yana murmushi yana cewa wai ke da gaske tafiya zakiyi ne kike nufi Rahama don dan wanan magana ?
Ban juyo na kalle shi ba sai takarduna da nake cusawa a wani jakkana ganin ban juyo ba yace dani ki zauna muyi magana ban jiyo ba still sai ya karaso inda nake a tsaye din ya kamo hannuwa na duka biyo na dago idanuwa da suke cike da bacin rai na sauke a kan shi.
Ganin yanayi na yasa ya fahinci a cike nake da bacin rai tun daren jiya sai yaji baiji dadin yadda a lokaci daya na sauya ba akan may zan sawa kaina damuwa dayawa haka don kawai wata zata zo mu zauna a tare.
Amma a fili sai cewa yayi Rahama kin bani mamaki wallahi ban taba tsanmanin wanan matakin ba a gare ki don kawai wata zata zo shine abin bata rai gareki alhalin kin san dama bake kadai bane gareni.
Kiyi hakkuri ki kwantar da hankalin ki yanzu ai in kin wuce sai tace tsoron ta kike yi har kin gudu ko kina kishi da zuwan nata nan.
Na dago idanuwa na na sauke akan shi akamar zanyi magana sai na zare hannaye na daga gare shi a raina nace kai namiji dai bai da tunane shi yanzu har ya matan irin rikicin dake tsakanin mu da ita ne a baya inda bamu haduwa wuri daya ba ai fitina ba.
Balle yau ace wai har shi da kan shi zaiyi sha, awan tara mu a gida daya irin wanan wani irin gululun bakin ciki ya tokare min zuciya na naji ko ganin shi bana son yi a idona tare da dana sanin zama dashi.
Zama nayi idanuwa na suka fara fitar da hawaye n takaici zama yayi a kusa dani ya kamoni zuwa jikin shi na fisge da karfi nace kada ka soma ka tabani wallahi na gaji da yaudara irin naka.
Baka kauna ba ka sona zaman dole kake dani na sani ba yau ba don gashi yau ka nuna afili da kan ka ka dauko min tashin hankali har dakina gara na koma gida inda akasan darajana da kima ta.
Yace kamar yaya na dauko maki fitina har dakinki a kanki zata zauna idan tazo ko may kike tunane haka da zuwan ta din ina kowa da halin shi zai zauna.
Nace haba daddy kabarni don Allah na yi abinda zai fisheni kadai riga da ka zabi wacce kake da muradi a kanta ba sai ku sha zaman ku ba.
Bina yayi da kallo ganin na mike na ci gaba da shiri na ya dan dade a tsaye yana kallona sai ya juya ya fita har nagama shirina komai da yake nawa na dauka.
Waya na ke ringing na dauka a zatona ko Faiza ce da naiwa magana ta samo min mota sai naga bakuwar nomba ce na dauka da sallama a bakina.
Ina mamakin waye kuma ke kirana da safe hakane wai ban dai kai karshen tunane na ba naji muryan namiji yana karba min sallaman nawa.
Mun gaisa dashi ya kira sunana yace Rahama nasan baki gane mai magana ba ko nace eh hakanane.
Yace to yayan ki Bashir ne abokin mijin ki nace au yaya kaine ya kwana biyu ya iyalin ka yace suna lafiya sai nai shiru.
Can yace Rahama yaya akayi haka kuma daga jin hindatu zata shigo wurin ku ku zauna sai kuma ki rikicewa abokin nawa keda ake yabo kuma Rahama zaki bari har wata hindu can ta bayar dake.
Rahama duk fa wani hannkurin da kike a gidan nan kowa dake tare da ku ya sani don Allah daga yau ki dauri ki zama MARUCIN KAN DUTSE A GIDAN MIJIN KI FITAR KI SAI AN DAURE.
Nasiha sosai yai min masu ratsa jiki har yake ce min duk abinda na gani don Allah na daure na bar komai ga Allah yace dama haka take bukata a gareki ai .
Wanda yayi kaka abu don kaji haushi ka sani shine kuma har zaka bari ya fahinci ka raza da shirin shi don Allah narokeki da ki daure ki zauna dakin ki yi hakkuri yanzu idan kikai fushi kika tafi dariya za ai maki wallahi kin dai san halin ku na mata da tsegumi ba banza Hindatu ta bar mijin ku ba nina sani don ni ke ganin abinda akeyi.
Wanan kuma ba komai bane don kece zaki shawo hankalin komai da zata so aiwatar wa don kara gurbata mashi da rayuwan shi.
Shiru nayi ina sauraren shi sai hawayen da ke zubo min yace don Allah Rahama kiyi hakkuri don tafiyan ki ya tayar da hankalin mijin ku sosai wallahi shi da kan shi ya kirani yake fada min halin da kuke ciki tun jiya daya fada maki.
Shi hakkuri wuta gare shi amna a karshe dadin shi yawa gare shi idan ka daure don haka ki janye wanan maganan tafiya don Allah Rahama.
Cikin muryan kuka nace da ka barni na basu wuri yaya bashir tunda banda amfani a gare shi.
Wa ya fada maki Rahama keko keda amfani a garshi shima ya sani ai don ko sha anin Saade idan da baki hakkuri ai da ba a kai haka ba ko.
Muna gama waya da bashir sai kuma ga mama Laraba ta kirani nace itama an kai karan nawa wurinta ke nan shike nan ni nawa ya samay ni dada.
Mun gaisa ta shiga lalashina ta na bani magana fada sosai tai min tare da lurar dani illar abinda nake son yi din takuma kara fahintar dani yadda zan zauna da hindatun idan tazo tunda na riga na san halin ta nai mata godiya na share hawaye na dole in zauna kada na zamo wacce bata jin maganan manyan ta.
Aisha na kira don ta dauki yaron da ya gama shan nono take cewa dani an fasa tafiyan ne anty nace da ita eh kawai ta dauki yaton tace anty kiyi hakkuri don Allah koma may ye Allah nagani ai.
Ban fito ba shima bai shigo ba da rana nafito inda zamu hada abin buda baki tare da yaran muna kitchen din naji dawowan shi ban damu da naje gaida shi ba yadda nake matukar jin zafin shi ranan.
Shima dakin shi ya shige bai damu da yazo inda muke ba don bats kan mu yakeyi ba ma a lokacin dawowan matar shi nan yake ta faman shiryawa kawai a ganina.
Ina aiki ina tunanen yadda zan zauna dasu mutumin ma da ya ajeka ba wai ya damu da damuwar ka bane a yadda nasan hindatu zanga rayuwa kala kala a wurin ta sai dai ya zama wajibi nima dole na fito da nawa gwanin ta don nuna mata jiya ba yau bane fa.
Mun gama komai na shirya mai inda zai yi buda bakin shi na shige daki nsi wanka na shirya ina jiran lokacin sgan ruwa yayi sai tunane nake gobe iwar haka muguwar bakuwar mu ta iso gidan ko nace a fili ubangiji Allah ya haushe ni kan duk wani kulli da zatazo min dashi a gidan nan.
Sai da na idar da sallah na dan sha tea kawai a dakina don shi nake iya sha a lokacin don raina ba dadi har lokacin a haka na wuni a gidan dashi.
Nafito a cikin kwalliya na yana zaune yana waya yana hango fitowa na ya katse wayan da yakeyi din cikin nuna rashin damuwa na isa inda yake zaune na gaidashi da shan ruwa shima ya amsa min a sake.
Na juya zan wuce sai naji yace dani ina kuma zaki baki ban abinci ba juyowa nayi ina dan kallon shi kawai.
Nace zan koma daki ne naga ai komai na aje a gurin ba sai na tsaya ba yace wa kike son ya zuba min to ?
Kamar nace ya jira matar shi tazo ta zuba mai mana saidai nai shiru kada ya gane kishin nawa yakai haka da yawa.
Sai dai nace dashi naga kamar baka tashi ci bane yanzu kana waya kada na takura maku ne ai.
Yace waya kikaga inayi yanzu zo ki zuba min naci yunwa nakeji dama banci komai ba bayan ruwan da nasha dazun.
Ban musa ba na juya nakoma na fara hada mai abinda zai ci din a cikin plate.
Ya jawo zuwa gaban shi ya fara ci sai na dan so mikewa yace ina kuma zaki kin san dai ba haka kika saba yi min ba ko.
Ban musa ba na samu wuri na zauna a gefe ina amfani da wayan dake a hannu na sai cin abincin shi yake hankalin shi a kwance.
Ya gama yake cewa hada min ruwa na watsa ko zanji jikina ya dan sake min ban motsa don banda nayir tashi a lokacin sai da ya kara fafin bakiji bane sai na mike kawai ba tare da nai magana ba na wuce , uwa dakin.
Na shiga dakin ke na sai ga wayan anty ya shigo min ina hada ruwan wankan muke waya mun gaisa take tambayana ashe kuma Hindatu a wurin ku zats zauna wanan karon ?
Nai murmushi nace haka yace anty tace to akai zuciya nesa dai don kin san halinta ba bakuwar ki bace kikuma kula sosai don kin san makircin ta.
Kagin nai magana sai gashi ya shigo dakin lokavin har na gama hada msi komai da zaiyi amfani dashi a bandaki din.
Nace da anty tayi hakkuri zan kira nan da minti goma sai na kashe wayan na juyo zan fita daga dakin sai naji yai caraf ya rike ni ta bayan shi tare da juyo ni ina fuskantar shi.
Yai murmushi yace ke naga alamar ki idan na biye maki gaba zamuci gaba dayi har bakuwar taki ta samay mu a haka cikin wanan halin.
Mutum ance yayi hakkuri ba sai ya hakkura ba ya barwa Allah alamarin sa anfi son mutum ya dinga hakkuri da duk abinda yazo mai na kaddara.
Na dago idanuwa da suka rine zanyi magana yace ya isa haka please bana son jin wani magana akan zancen nan abar komai ya wuce please.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE DON BA A YAFE BA ONLINE NOVEL NE, , , , ,
78
Washegari Ina tsaye a kitchen ina duba kayan amfanin mu sai naga komai akwai sai kaayan miya da muke amfani dashi fresh ne ya dan kare.
Na dan kai lokaci a tsaye ina nazari abinda zamuyi anjima na shan ruwa ina nan a tsaye ne sai ga Aisha ta samay ni a kitchen din.
Tace tun jiya nake tunanen kayan miyan bazasu ishe mu ba yau sai dai idan na za ai miya ba sabo nace ai yazama dole Aisha tunda yaran sin fi son mai miya nagani.
Motsi mukaji na alaman an bude kofan gidaan an shigo cikin gidan sai dai bamuji sallama ba kuma.
Aisha ce ta fita ta gani don yaran suna makaranta a lokacin heleen kuma ta na baya tana wankin kayan ta.
Sai gata ta dawo tana cewa dani Anty maman Ihisan ce fa da wata
Showing 312001 words to 315000 words out of 456145 words
Kinji abinda na fada aiki nace kwarai kuwa ai wanan ba matsala bane don gidan ka ne danan da can sai dai ni zan barku na koma kano na zauna tunda dama na gama abinda ya kawo ni garin ina ga zaifi maku dadi hakan ma don ku sakata ku wala ba sai na tsaya a tsakanin ku ba.
Yace aiko kina nan bazaki hanamu sakata ba kamar yadda itama bazata hanaki sakata ba din.
Don haka gara na koma inda na saba yafi min zama a cikin ku mu kadai dagani sai ku a garin mutane.
Yace wanan kuma maganan ki ne kin dai ji tsarin danayi yanzu a gidana nace naji don haka zuwa jibi zata iso don mun mai da auren mu da ita.
Nace ai naga alaman an maida aure tunda take son zuwa takurawa wacce ka sayo ba auro ta kayi ba kamar kowa dama dani tafita yanzu kuma ta dawo dani a ranta.
Yace wanan kuma tunanen ki ne hakan ni dau gidana ne kuma yadda nake so zan tsara kowa na da hakki a gare ni .
Idan zaki fahince ni ki kwantar da hankali don babu abinda zai faru tunda ita ba bakuwar ki bace.
Ni dai na fada maki abinda ake ciki in zakiyi hakkuri ku zauna lafiya dan ba wanda ya kawo wani a cikin ku nina kawo kowan ku kowa kuma da halin shi zan zauna dashi.
Na mike nace wanan sai kuma a yaudari wata ba ni ba Allah ya baku zaman lafiya dama tare na samay ku ai koda na shigo don haka kunfi kusa.
May ya kawo zancen yaudara anan dukkan ku ai mata nane babu wacce zan tsaya yaudara daga cikin ku.
Banyi tsamanin jin haka daga gareki ba a yadda na tsamoki da farko daga cikin ku na kawo ki nan don yanzu nace wata zata zo ku zauna shine zai zama matsala.
Na juyo tare da tsayawa nace tun farko ai saida na baka shawaran yin haka amma kace dani ba tsarin ka ba ke nan haka kaga dama.
Sai yanzu din ta kullo ni arai zata zo tace zata shiga min rayuwa ban sa akai ba balle a kar min .
Kuma kafin ma ta taso ni na isa gida ko sai tayi da wata amma badai Rahama ba dai kan.
Inda nasan wanan shirin kake kwana da kwanaki aida baka bata lokacin ka ba gurin shiri da kafada min tuni da angama ai.
Na juya na wuce zuwa dakina ban kara tsayawa sauraren shi ba ina shiga nafara hada kayana dake cikin wardrobe.
Tsab nagama shirins tunda dare na rufo kofana tare da hayewa gado wurin yara na da Aisha dake kwance gefen su.
Barci ya kaurace min a idona sai faman tunane nakeyi don na tabbatar da wanj manufa hindatu ta zabi biyoni Abuja wanan karon wanda manufan bai wuce kalman daukan fansa ba akaina.
Tunda dama tana cewa a dalilin shegen dana akai mata saki don haka sai ta rama abinda nai mata koda zata tafi tsirara ne.
Abubuwan da daddy ke min duk kwana kin na dama nasha jinin jikina da akwai wata akasa gashi kuwa yau naji da kunnuwa na.
Kai namiji sai a barshi kawai idan ya tashi munafuncin shi sai dabara da wayo ya bace mashi wai yau daddy ne da bakin shi yake ce min da hindatu zamu zauna gidan nan.
Matar da bata maida fitina bakin komai ba aida in zauna da ita gara nakoma can in ma dafani anty zatayi yafi da hindatu ta shigo min da balai gida.
Wai ma sai bayan da ya gama komai shine yanzu ya mayar dani sakarai yazo fada min abinda ta zaba don ta dawo mai.
Ba wani dadi naji ba koda nike ni kadai din balle ace an karo min sabon fitina akaina.
Ni wanan rayuwan auren da may yai kamane wai kullun sabon fitina da kanana kanan rashin fahinta ke zo muna.
Ni dai arabu yafi min komai sauki da wanan zaman danger da muke da kishiyoyi wi da mijin ma haka wi.
Da yake barci barawo ne sai da yai dabaran satana cikin wanan halin da nake ciki da asuba ranan shi da kan shi ya tashe ni inta dasu Aisha suyi sahur acikin waya.
Ban fito don sahur ba dama ni ban damu da yin sahur din ba kullun balle yau da raina yake a bace.
Ruwan sanyi kawai nake da bukatan sha na koma na kwanta nafito falin din in dauki ruwa a kitchen nan nagan shi zaune yana shan tea suna sahur shida Nasir don yaron akwai shi da kokarin Ibada sosai.
Ban ko kalli inda suke ba na wuce zuwa kitchen kai tsaye sai Nasir din ke cewa dani kin tashi mummy nace eh Nasir ba tare da na tsaya ba na wuce abina uban yabini da kallo kawai.
Ganin yaron ya bini da kallo yasa yai murmushi yace yau mummy ka fushi take kyale ta yaron yace but why daddy yace wa yaron nothing cikin daga kafadan shi.
Sai can yace wai bata son dawowan maman Ihisan nan gari haba daddy a gidan nan wanan matar zata dawo ta zauba da mu haba haba gidan zai zama badadi ke nan daddy .
Wani tsawa ya dakawa yaron yana fada dashi Nasir har yaushe kasan irin wanan magana ina ruwanka da harka.
Yaron ya ja bakin shi yai shiru haka ya mike ya bar uban zaune a falo ya bi bayan yaron da kallon mamaki da takaici.
Kafin karfe bakwai na shirya tsab na shirya yaran nawa kuma tare da Aisha da Atika sai helen da nake tunanen yadda zanyi da ita don dole na sallamay ta koma gida.
Muryana da Aisha ya tsinkayo daga dakin shi lokacin da nake cewa da ita kuyi sauri ku shirya bana son muyi tafiyan rana don kun san azumi ne ga helen ta dage da kukan ta wai sai ta bini a fadawa wacce ta kawo min ita tare zamu tafi.
Ban fi minti biyar ba da shiga ya shigo dakin da sallaman shi ya bi kayana dake a tsakiyan dakin cikin troler dina da kallo.
Ya juyo inda nake yana murmushi yana cewa wai ke da gaske tafiya zakiyi ne kike nufi Rahama don dan wanan magana ?
Ban juyo na kalle shi ba sai takarduna da nake cusawa a wani jakkana ganin ban juyo ba yace dani ki zauna muyi magana ban jiyo ba still sai ya karaso inda nake a tsaye din ya kamo hannuwa na duka biyo na dago idanuwa da suke cike da bacin rai na sauke a kan shi.
Ganin yanayi na yasa ya fahinci a cike nake da bacin rai tun daren jiya sai yaji baiji dadin yadda a lokaci daya na sauya ba akan may zan sawa kaina damuwa dayawa haka don kawai wata zata zo mu zauna a tare.
Amma a fili sai cewa yayi Rahama kin bani mamaki wallahi ban taba tsanmanin wanan matakin ba a gare ki don kawai wata zata zo shine abin bata rai gareki alhalin kin san dama bake kadai bane gareni.
Kiyi hakkuri ki kwantar da hankalin ki yanzu ai in kin wuce sai tace tsoron ta kike yi har kin gudu ko kina kishi da zuwan nata nan.
Na dago idanuwa na na sauke akan shi akamar zanyi magana sai na zare hannaye na daga gare shi a raina nace kai namiji dai bai da tunane shi yanzu har ya matan irin rikicin dake tsakanin mu da ita ne a baya inda bamu haduwa wuri daya ba ai fitina ba.
Balle yau ace wai har shi da kan shi zaiyi sha, awan tara mu a gida daya irin wanan wani irin gululun bakin ciki ya tokare min zuciya na naji ko ganin shi bana son yi a idona tare da dana sanin zama dashi.
Zama nayi idanuwa na suka fara fitar da hawaye n takaici zama yayi a kusa dani ya kamoni zuwa jikin shi na fisge da karfi nace kada ka soma ka tabani wallahi na gaji da yaudara irin naka.
Baka kauna ba ka sona zaman dole kake dani na sani ba yau ba don gashi yau ka nuna afili da kan ka ka dauko min tashin hankali har dakina gara na koma gida inda akasan darajana da kima ta.
Yace kamar yaya na dauko maki fitina har dakinki a kanki zata zauna idan tazo ko may kike tunane haka da zuwan ta din ina kowa da halin shi zai zauna.
Nace haba daddy kabarni don Allah na yi abinda zai fisheni kadai riga da ka zabi wacce kake da muradi a kanta ba sai ku sha zaman ku ba.
Bina yayi da kallo ganin na mike na ci gaba da shiri na ya dan dade a tsaye yana kallona sai ya juya ya fita har nagama shirina komai da yake nawa na dauka.
Waya na ke ringing na dauka a zatona ko Faiza ce da naiwa magana ta samo min mota sai naga bakuwar nomba ce na dauka da sallama a bakina.
Ina mamakin waye kuma ke kirana da safe hakane wai ban dai kai karshen tunane na ba naji muryan namiji yana karba min sallaman nawa.
Mun gaisa dashi ya kira sunana yace Rahama nasan baki gane mai magana ba ko nace eh hakanane.
Yace to yayan ki Bashir ne abokin mijin ki nace au yaya kaine ya kwana biyu ya iyalin ka yace suna lafiya sai nai shiru.
Can yace Rahama yaya akayi haka kuma daga jin hindatu zata shigo wurin ku ku zauna sai kuma ki rikicewa abokin nawa keda ake yabo kuma Rahama zaki bari har wata hindu can ta bayar dake.
Rahama duk fa wani hannkurin da kike a gidan nan kowa dake tare da ku ya sani don Allah daga yau ki dauri ki zama MARUCIN KAN DUTSE A GIDAN MIJIN KI FITAR KI SAI AN DAURE.
Nasiha sosai yai min masu ratsa jiki har yake ce min duk abinda na gani don Allah na daure na bar komai ga Allah yace dama haka take bukata a gareki ai .
Wanda yayi kaka abu don kaji haushi ka sani shine kuma har zaka bari ya fahinci ka raza da shirin shi don Allah narokeki da ki daure ki zauna dakin ki yi hakkuri yanzu idan kikai fushi kika tafi dariya za ai maki wallahi kin dai san halin ku na mata da tsegumi ba banza Hindatu ta bar mijin ku ba nina sani don ni ke ganin abinda akeyi.
Wanan kuma ba komai bane don kece zaki shawo hankalin komai da zata so aiwatar wa don kara gurbata mashi da rayuwan shi.
Shiru nayi ina sauraren shi sai hawayen da ke zubo min yace don Allah Rahama kiyi hakkuri don tafiyan ki ya tayar da hankalin mijin ku sosai wallahi shi da kan shi ya kirani yake fada min halin da kuke ciki tun jiya daya fada maki.
Shi hakkuri wuta gare shi amna a karshe dadin shi yawa gare shi idan ka daure don haka ki janye wanan maganan tafiya don Allah Rahama.
Cikin muryan kuka nace da ka barni na basu wuri yaya bashir tunda banda amfani a gare shi.
Wa ya fada maki Rahama keko keda amfani a garshi shima ya sani ai don ko sha anin Saade idan da baki hakkuri ai da ba a kai haka ba ko.
Muna gama waya da bashir sai kuma ga mama Laraba ta kirani nace itama an kai karan nawa wurinta ke nan shike nan ni nawa ya samay ni dada.
Mun gaisa ta shiga lalashina ta na bani magana fada sosai tai min tare da lurar dani illar abinda nake son yi din takuma kara fahintar dani yadda zan zauna da hindatun idan tazo tunda na riga na san halin ta nai mata godiya na share hawaye na dole in zauna kada na zamo wacce bata jin maganan manyan ta.
Aisha na kira don ta dauki yaron da ya gama shan nono take cewa dani an fasa tafiyan ne anty nace da ita eh kawai ta dauki yaton tace anty kiyi hakkuri don Allah koma may ye Allah nagani ai.
Ban fito ba shima bai shigo ba da rana nafito inda zamu hada abin buda baki tare da yaran muna kitchen din naji dawowan shi ban damu da naje gaida shi ba yadda nake matukar jin zafin shi ranan.
Shima dakin shi ya shige bai damu da yazo inda muke ba don bats kan mu yakeyi ba ma a lokacin dawowan matar shi nan yake ta faman shiryawa kawai a ganina.
Ina aiki ina tunanen yadda zan zauna dasu mutumin ma da ya ajeka ba wai ya damu da damuwar ka bane a yadda nasan hindatu zanga rayuwa kala kala a wurin ta sai dai ya zama wajibi nima dole na fito da nawa gwanin ta don nuna mata jiya ba yau bane fa.
Mun gama komai na shirya mai inda zai yi buda bakin shi na shige daki nsi wanka na shirya ina jiran lokacin sgan ruwa yayi sai tunane nake gobe iwar haka muguwar bakuwar mu ta iso gidan ko nace a fili ubangiji Allah ya haushe ni kan duk wani kulli da zatazo min dashi a gidan nan.
Sai da na idar da sallah na dan sha tea kawai a dakina don shi nake iya sha a lokacin don raina ba dadi har lokacin a haka na wuni a gidan dashi.
Nafito a cikin kwalliya na yana zaune yana waya yana hango fitowa na ya katse wayan da yakeyi din cikin nuna rashin damuwa na isa inda yake zaune na gaidashi da shan ruwa shima ya amsa min a sake.
Na juya zan wuce sai naji yace dani ina kuma zaki baki ban abinci ba juyowa nayi ina dan kallon shi kawai.
Nace zan koma daki ne naga ai komai na aje a gurin ba sai na tsaya ba yace wa kike son ya zuba min to ?
Kamar nace ya jira matar shi tazo ta zuba mai mana saidai nai shiru kada ya gane kishin nawa yakai haka da yawa.
Sai dai nace dashi naga kamar baka tashi ci bane yanzu kana waya kada na takura maku ne ai.
Yace waya kikaga inayi yanzu zo ki zuba min naci yunwa nakeji dama banci komai ba bayan ruwan da nasha dazun.
Ban musa ba na juya nakoma na fara hada mai abinda zai ci din a cikin plate.
Ya jawo zuwa gaban shi ya fara ci sai na dan so mikewa yace ina kuma zaki kin san dai ba haka kika saba yi min ba ko.
Ban musa ba na samu wuri na zauna a gefe ina amfani da wayan dake a hannu na sai cin abincin shi yake hankalin shi a kwance.
Ya gama yake cewa hada min ruwa na watsa ko zanji jikina ya dan sake min ban motsa don banda nayir tashi a lokacin sai da ya kara fafin bakiji bane sai na mike kawai ba tare da nai magana ba na wuce , uwa dakin.
Na shiga dakin ke na sai ga wayan anty ya shigo min ina hada ruwan wankan muke waya mun gaisa take tambayana ashe kuma Hindatu a wurin ku zats zauna wanan karon ?
Nai murmushi nace haka yace anty tace to akai zuciya nesa dai don kin san halinta ba bakuwar ki bace kikuma kula sosai don kin san makircin ta.
Kagin nai magana sai gashi ya shigo dakin lokavin har na gama hada msi komai da zaiyi amfani dashi a bandaki din.
Nace da anty tayi hakkuri zan kira nan da minti goma sai na kashe wayan na juyo zan fita daga dakin sai naji yai caraf ya rike ni ta bayan shi tare da juyo ni ina fuskantar shi.
Yai murmushi yace ke naga alamar ki idan na biye maki gaba zamuci gaba dayi har bakuwar taki ta samay mu a haka cikin wanan halin.
Mutum ance yayi hakkuri ba sai ya hakkura ba ya barwa Allah alamarin sa anfi son mutum ya dinga hakkuri da duk abinda yazo mai na kaddara.
Na dago idanuwa da suka rine zanyi magana yace ya isa haka please bana son jin wani magana akan zancen nan abar komai ya wuce please.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE DON BA A YAFE BA ONLINE NOVEL NE, , , , ,
78
Washegari Ina tsaye a kitchen ina duba kayan amfanin mu sai naga komai akwai sai kaayan miya da muke amfani dashi fresh ne ya dan kare.
Na dan kai lokaci a tsaye ina nazari abinda zamuyi anjima na shan ruwa ina nan a tsaye ne sai ga Aisha ta samay ni a kitchen din.
Tace tun jiya nake tunanen kayan miyan bazasu ishe mu ba yau sai dai idan na za ai miya ba sabo nace ai yazama dole Aisha tunda yaran sin fi son mai miya nagani.
Motsi mukaji na alaman an bude kofan gidaan an shigo cikin gidan sai dai bamuji sallama ba kuma.
Aisha ce ta fita ta gani don yaran suna makaranta a lokacin heleen kuma ta na baya tana wankin kayan ta.
Sai gata ta dawo tana cewa dani Anty maman Ihisan ce fa da wata
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22Chapter 23Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32Chapter 33Chapter 34Chapter 35Chapter 36Chapter 37Chapter 38Chapter 39Chapter 40Chapter 41Chapter 42Chapter 43Chapter 44Chapter 45Chapter 46Chapter 47Chapter 48Chapter 49Chapter 50Chapter 51Chapter 52Chapter 53Chapter 54Chapter 55Chapter 56Chapter 57Chapter 58Chapter 59Chapter 60Chapter 61Chapter 62Chapter 63Chapter 64Chapter 65Chapter 66Chapter 67Chapter 68Chapter 69Chapter 70Chapter 71Chapter 72Chapter 73Chapter 74Chapter 75Chapter 76Chapter 77Chapter 78Chapter 79Chapter 80Chapter 81Chapter 82Chapter 83Chapter 84Chapter 85Chapter 86Chapter 87Chapter 88Chapter 89Chapter 90Chapter 91Chapter 92Chapter 93Chapter 94Chapter 95Chapter 96Chapter 97Chapter 98Chapter 99Chapter 100Chapter 101Chapter 102Chapter 103Chapter 104Chapter 105 Chapter 106Chapter 107Chapter 108Chapter 109Chapter 110Chapter 111Chapter 112Chapter 113Chapter 114Chapter 115Chapter 116Chapter 117Chapter 118Chapter 119Chapter 120Chapter 121Chapter 122Chapter 123Chapter 124Chapter 125Chapter 126Chapter 127Chapter 128Chapter 129Chapter 130Chapter 131Chapter 132Chapter 133Chapter 134Chapter 135Chapter 136Chapter 137Chapter 138Chapter 139Chapter 140Chapter 141Chapter 142Chapter 143Chapter 144Chapter 145Chapter 146Chapter 147Chapter 148Chapter 149Chapter 150Chapter 151Chapter 152Chapter 153