wacce ta fada baki bata fada maki daidai bane dazun yadda akayi.
Tace wakike nufin ta fada min nace wacce kika hana karban abinci ai tazo ta karba taci duk da kin hanata ci din.
Ya isa haka please yana kai loma abincin a bakin shi daga haka bai kara cewa komai ba yaci gaba da cin abincin shi na juya zan wuce yace jinan.
Sai na juyo yace ku saurare ni daga yau girki a hade za, a dinga yin shi ban yarda a kara raba tunkuya ba a gidan nan ba.
A zato ita zata fara korafin saboda may amma sai naji tace ya dai fi don bazan iya wahakan ba kaitan banza abincin ba haka.
Nace baida matsala ta fadi haka ni may zance na bada kaina duk da nasan mune zamu cuto ba zatai komai ba ita na sani.
Tun wanan rana muke komai a gidan tana daki kwance da yar ta sai in an sha ruwa sune farkon diba ni dai bance komai ba a kan hakan da yai muna din.

********* ********* *********
Nidai ranan ina barci bayan na falkane Aishs ke cewa dani wai sun fita shida hindatu din.
Ban kawo komai ba sai da suka dawone naga anata shigowa da kaya irin na raba ma dangi din nan da karshen azumi.
Aikina nake banbi ta kansu ba sai da dare ne ya kiramu nazo na zauna yake cewa kayan da za, a bawa mutane na sallah ne sai kiyu list din wa yanda kike sin abawa a part din ki.
Nace ayya angode don na riga da na saya ko har an kai masu ko ina fadan haka namike na bar wurin ban tsaya ba yabi bayana da kallo kawai.
Na koma daki ina mamakin hali irin na daddy ni may ya dauke nine wai zuwan hindatu fitan su karo na uku ke nan a gidan tare.
Na farko wai sun fita zuwa gidan wani abokin shi a bakin matar mutumin nake jin labari sai na biyu wai sunje sayaya ne a wani plaza na gida.
Sai kuma yau da sukai min wanan rainin wayon babu ko shawara haka kawai don an mayar dani yar tallakawa wai nai list din wanda za aiwa alheri a part dina don muna tallakawa ko may ?
Ban fita ba duk da ni keda girki har ya gama abinda yake ya kwanta sai washe gari ina zaune ina shafa mai ya shigo dakin.
Ban juyo ba nai mai ina kwana yace wai Rahama may yasa baki son a zauna lafiya ne ke yanzu yadda kikai min jiya kin kyauta ke nan.
Ni dai banyi magana ba sai shiri na nakeyi kawai yace badake nake magana ba ne kin kyale ni ?
Nace kaje ka karawa wacce ta sayo din takaiwa yan uwan ta can ni duk da tallakace bani daukan wullakanci kishiya idan ta mai da kai yadda take so ni ba zata mai dani ba don ba zaman ta nakeyi ba anan balle tace zata zabawa yan uwana abinda taga ya dace dasu watau gana kauye ko ?
To kubar abunku nagode Allah ya kara arziki da budi gaba na juya zuwa wardrobe na fara fitar da kayan da zan sa ajikina.
Yace yanzu nagane nufin ki Rahama watau don muje da hindatu ta tayani zaba shine bakin cikin ki ko ?
Na juyo nace bakin ciki bakin ciki akan may fa akan ka fita da matarka ko may ai ba yau ka fara fita da ita ba ko a kano ya damay ni sai yau zan damu ko may.
Ni dai nasan ban wa kishiya shishigi ba balle ni ai mina ga bara kudi ka bamu kace kowa ya saiwa yan uwan shi kayan sallah sai yanzu ne ita tasan hanyar yaudara ko may ?
Sai yai shiru ba abinda yake tunane sai yasan haka akayi da yai magana nakawo mai wanan shawaran akan kowa ya saiwa nashi da kan shi .
Yanzu ko itace ta bada wanan shawaran kan a saye a rabawa mutane kuma gaskiya wanda tace wai namu din baikai wanda yaga ta zaba ba a bangaren ta.
Yai magana tace kallan ya burgeta ne sosai kuma zai karbi yan uwan ta sosai don suna son kalan.
Yace yanzu dai kina nufin bazaki karba ba nace ba nufi bama bana karba na yafe har ga Allah aba wasu.
Yace to shike nan zaki gane kin min wullakanci ga hakan nace aina saba ba yau bane farau din hakan gareni indai wulakancin ka ne.
Wani abin ance idan bakai magana ba sai ya zama maka ciwo a zuciyan ka don maganan na da amfani saboda idan kai sa,a za a daina.
A bangare na ma maganan yai min rana don ashe wai gajiya sukayi a ranan da harda kayan sallah mu dana yara zasu sayo sai suka gaji suka dawo gida washe gari zasu koma su sayo din.
Yin maganan da nayi ne yasa shi dogon nazari duk da ran shi ya baci a yadda nai mai da farko amma daga baya dayai tunane sai yaga rashin dace wan hakan.
Don inda gaskiya ne ai kamata yayi ya dauke mu mutafi tare a sayo komai dani ba su ware ni ba yadda sukai min din.
Ya kuma tuna a bara yadda akayi saye kowa kudin ta ya bata ta sayo ita da yaran ta da nata.
Washe gari koda tai kai zancen zuwa saye sai cewa yayi da ita ya fasa zaiba wa kowa kudin shi ya saya wanda yake so da yaran shi yadda ya saba yi muna.
Ranta ya baci tace wanan ba shawaran ka bane na sani kodan jiya matar ja tai fushi taki karban kayan yasa zaka canza shawara a yadda muka tsara da farko.
Yace in ma haka din je hakan ne don ba haka na saba yi ba da farko ai tun farko sai da na so kin wanan shawaran naki amma kika kawo min kabbali da ba, adi don haka abar wanan zancen zan bawa kowa kudi yadda na saba ne.
Amma idan kai muna haka mu aka kwara ni da zulfa tunda sun fi mu yara ai yace au shine hikimar ki ashe kikai wanan shawaran bafon Allah ba ashe kikayi.
Rahama na da gaskiya ke nan ta fahinci abinda yasa kikai masu hakan ke nan ashe tace da yake ta iya yaudara ba dama ai haka yasa ta hada dayin majuju don ta haifi diyan ta samu garabasa .
Yace ke wa ta hanaki yin hakan ai kin rigata shiga gidan tace Allah ne bai kawo ba kaima ka sani ai.
Yace ashe kin san Allah may yi itama shi din ne ya bata a lokacin da kowa bai zata ba din don haka ban son dogon zance kan maganan na riga na fada maki shawara na don tun farko haka na saba yi maku ai.
Ni dai ban san sanda yaiwa yan uwana da iyayye aike ba sai ji nake suna bugo waya suna godiya amma fir naki tambayan shi abinda ya aika masu dashi.
Yaje kano gun su Anty kwanan shi goma a can gun su anty ya gama abinda ya kai shi ya dawo Abuja gurin mu da aikin shi.
Ranan ya dawo ne ya ban kudina dana yara na har dasu Aisha da Atika da helen dake wurina sai da suka samu,
Haka yasa na fahinci kowan mu haka yai mata sai da zan tashi ne ya sake miko min wasu kudin yace wanan na su Nasir ne da jinior don uwar su tace na kawo maki tunda a nan suke gun ki.
Mamaki nayi sosai yadda anty ta sauko haka ba kamar ya watan nin da suka wuce ba ashe yaran ne kan yawa fada mata komai a waya shine yasa ta kara sakewa a ranta ta dai fahinci ba wani abu a zuciya na kan ta zugin mutane ne kawai yasa ta rudani dama amma ita har yau ba zata iya cewa ga abinda nai mata ba.
Washe gari muka shiga kasuwa da yaran nai masu sayayya sosai yadda ya dace da kowan mu har haidar sai da na dan sayo mai tunda yana dasu dama aje.
Naso muje kano muyi sallah a can har daddy ya amin ce sai hidimar tafiya muke yi gaba dayan mu don baifi kwana uku ba ko hudu ai sallah.
Komai munyi na tafiya amma ranan yana dawowa sai yazo min da zancen ba tafiya mu kano sai dai zai tafi da Nasir da Jinior suyi sallah a can.
Banji dafi ba babu yadda zanyi dole muka hakkura da batun tafiyan na dai san dole akwai matsala ta wani wuri akan haka.
Cake na hada lafiyayye da su donut da sauran snacks da zasu tafi dashi nai kuma saa sunyi dadi sosai don sai kamshin vanilla flavor sukeyi na saka a fararen robobi naba yaran sukai wa anty da Alhajin daddy da Abban anty na sallah.
Washegari zasu tafi ya kira mu yake sheda muna Sani zai kawo muna naman sallah da sauran abubuwan bukata da zamu bukata na hidimar sallah din ya kuma kawo kudi masu yawa yaba kowan mu yai muna sallama suka tafi.
Da yamma sai ga nama mai yawa Sani yazo muna dashi zakace ma Saniya ce suku tum aka yan ka muna an gyara shi tun can iyakar mu dai aikin shi kawai.
Muna shirin fara aiki sai ga hindatu ta fito tana wani ya tsunar fuska tace ke Rahama a raba naman nan biyu a bani nawa nan ?
Nasan tsiya take ji don haka nace kamar ya a raba biyu adai kasa a cirewa kowa ku dauki kasan ku tunda ba mu kadai ne da hakkin shi ba.
Wasa wasa muka fara rikici kan hakan ta dauki waya ta kira maigidan cikin masifa lokacin yana falo can ma ana wani rikicin tsakanin anty da zulfa kan abin sallah din.
Sai da ya gama sauraren ta yace kisa wayan nan a handsfree muyi maga taji, ta dauka ya goyi bayan ta ne sai tace a fusace yace ki saurare shi kiji abinda zai fada nace ai gani tsaye ina jin ku.
Yace Hindatu ta ansa ya kira nawa sunan nima na karba yace a kasa abakowa dake gidan har maigadi tunda abin naku tsiya ne, yace ai gaskiya ta fada abinda aka saya don anfanin bukin salla zai kawo fitina kuma wai may ke damun kan kune haka please da wani kuke son naji ne wai haka ?
Tace haka zakace yace may kike son nace nama kuka rasa a gidan ko may da wanan zai kawo maku fitina haka don baku da tunane na gane abin naku hadin bakine don kawai kuci min mutunci ku hanani kwanciyan hankali.
Ta juya a hasale tana fadin keda keda tsiyar nama sau ki hada da namu duk ku cinye ina ruwan dan baka saba ba da ganin hakan.
Nace ni dake yanzu ai sai a banbanta wanda ya nuna zalamar shi ba ki dai kwaruwan mu kan.
Duk da ta wuce tsaye nayi aka kasa shi daidai sai kason mu ni da ita yafi na sauran yawa nace Aisha ta kai mata nata.
Can ta koroto da naman tace muje mu kara mu da ya zamawa bakon gani a gare mu tadawo min dashi nace ta saka a freeze ta aje mata.
Nan suka shiga gyaran shirgin naman da yake yaran na da hazaka zuwa goman dare har sun gama komai suka saka a wani katon roba mai marfi suka kawo dakina.
Da dare sai ga anty ta bugo min waya tana min godiya wai taga yara sun zo da abin arziki nai murmushi kamar tana gabana nace haba dai anty ai wanan ba komai bane ni ina zan iya abinda akai min.
Tace to adai ta hakkuri don kin san zaman hindu wurin ku ba alheri bane da biyu ta zabi zama can din yaran nan sun fada min irin zaman da kuke acan din kina ma da kokari Rama in nice ai da na bar mata gidan na dawo inda nafi karfi.
Nace a raina yanzu kuma haka ke son dawowa tsakanin mu bayan ta riga taba da kafa an muna dariya ta jima tana min hiran rikicin su da Zulfa tace tana ganin hadin baki sukayi akan hakan.
Nace anty ni dai nasan ban na shiga hakkin kowa shiga nawa ne dai ba zan dauka ba tace to a kara hakkuri mukai sallama ta kashe wayan ta bar ni da mamakin ta.
Washe garin sallah koda goma yayi duk mun gama komai na abincin da zamuci tunda ba wasu zamu aikawa ba sai makwabtan mu da ba musulmai ba na sawa abinci da soyayyen nama da abin sha na aika masu dashi.
Natura Aisha ta fada mata an gama abinci yana saman dining idan sun tashi ci bata ki ba ta turo yar ta ta diban mata itama ihisan din nan falo ta zauna taci nata.
Ranan da daddy zai dawo sai gashi yazo mata da wata yar aiki sai dai bai dawo da yaran ba zasu tsaya can suyi hutu a wurin uwar su ne.
Dawowan daddy babu abin da ya canza a tsakanin don har yanzu baya iya aiwatar da komai idan muna tare dashi sai dai idan da sauran matan shi yake zai iya gudanar da komai normal yadda ya saba.
Tun abin baya damun mu har ya fara yi min magana sai gashi wai laifina zai gani kan haka wai ni ban ma damu da halin da muke ciki ba ni dashi din.
Na idar da sallah asuba na zauna a wurin na fara tunane may ke kawo muna wanan matsalar ne haka tsakani na dashi don gashi har mun fara samun matsalan zama kan hakan dashi.
Na kira Zarah abokiyar shawara na nake fada mata halin da muke ciki ban ko kai karshen magana na ba ta katse ni da fadi cikin tashin hankali Rahama kina ko da hankali kuwa ?
Kina cikin wanan babban matsalan haka kika zauna tsawon lokaci mai tsawo haka abuna damun ki.
Nace Zarah ni may kike so nayi ne wai tace kin ko san abinda ke damun ku daga ke harshi bafa karamin abu bane wanan don asiri ne da akeyi tsakanin na miji da mace da hausawa ke kira da dan baka.
Ba zai taba samun natsuwa dake ba sai idan wanan asirin ya bar aiki a tsakanin ku tunda da sunan ku akayi shi amma dai anyi shuuman mata anan don yanzu ba zamu cewa ga wacce tai maki wanan abin ba tunda kina da kishiyoyi da yawa.


ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE DON BA A TAFE BA ONLINE NOVEL NE, , , ,
80
Tun bayan waya na da Zarah sai hankalina ya fara tashi don ba karamin tsoro kalamin ta ya bani ba.
Ni lafiyana shine yafi min komai a rayuwa na in dai zasu barni da lafiya ina iya bar masu mijin su a zauna lafiya.
Amma ta ina zan fara wana san yai muna wanan shamakin a tsakanin mu ni dashi don duk kishiya kishiya ce dai.
Amma wa zan zarga a wanan matsalan shin hindatu dake nan zaune tare da mune ko kuwa wa yanda ke gida ne sukai min hakan wai ?
Nan dai na zauna ina ta faman tunane wanda har na gama ban iya gane komai va daga ciki abinda dai na yake da ga karshe shine zan dukuma nafi da kaimi wurin kai kuka na ga Allah dayai min tsari akan duk mai bina da wani mugun manufa.
May na tare masu da har yai zafi haka sukai muna wanan mugun asirin da sai jahili zai iya shi.
Sannu a hankali na fara rama a tsaye gashi bayan zarah aminiyata ban iya fadawa kowa wanan zancen don da kunya aji shi a bakina haka.
Muna cikin wanan halin ne ranan sai ga massage ya shigo a email dina asibitin da nai bautan kasa suna neman mu muzo interview wurin su.
Murna farin ciki duk ya kamani a lokaci daya daddy kawai nake jira ya dawo na fada mai naji may zai ce akan zancen.
Koda ya dawo nice da girki ranan don haka na tsara kwalliya na dana bata lokaci wurin yin shi ga lafiyayyen abincin dana girka don shi a ranan.
Bai shigo ba sai yamma lis ya dawo gidan ina dakina ina bawa yarona nono naji muryan shi Atika na mikawa yaton bai koshi ba ya dan sa kuka nace fice dashi zuwa dakin ku don Allah,
Tana fitowa dashi uban yaji kukan shi yace kai Atika ya akayi ne yake kuka kawo shi nan ta mikawa uban yoron ta nacewa wai bai koshi da nono bane shine yake kuka.
Daddy yace ita nonon nata na sayarwa ne ko may zatayi dashi da bazata bashi ba ya sha ya koshi da kyau.
Daga kofa ina fitowa nace cikin wani murya najan ra, ayi nace wallahi daddy ya faye tsotso shi bai koshi da nono.
Ya dago yana kallo na na tabbatar shigan tai mashi kyau don ni kaina na sani saboda kayan ya fitar min da kurciyana a fili.
Yai murmushi yace nawa za, a sayar muna a bashi ya sha ya koshi yadda
Showing 321001 words to 324000 words out of 456145 words
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22Chapter 23Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32Chapter 33Chapter 34Chapter 35Chapter 36Chapter 37Chapter 38Chapter 39Chapter 40Chapter 41Chapter 42Chapter 43Chapter 44Chapter 45Chapter 46Chapter 47Chapter 48Chapter 49Chapter 50Chapter 51Chapter 52Chapter 53Chapter 54Chapter 55Chapter 56Chapter 57Chapter 58Chapter 59Chapter 60Chapter 61Chapter 62Chapter 63Chapter 64Chapter 65Chapter 66Chapter 67Chapter 68Chapter 69Chapter 70Chapter 71Chapter 72Chapter 73Chapter 74Chapter 75Chapter 76Chapter 77Chapter 78Chapter 79Chapter 80Chapter 81Chapter 82Chapter 83Chapter 84Chapter 85Chapter 86Chapter 87Chapter 88Chapter 89Chapter 90Chapter 91Chapter 92Chapter 93Chapter 94Chapter 95Chapter 96Chapter 97Chapter 98Chapter 99Chapter 100Chapter 101Chapter 102Chapter 103Chapter 104Chapter 105Chapter 106Chapter 107Chapter 108 Chapter 109Chapter 110Chapter 111Chapter 112Chapter 113Chapter 114Chapter 115Chapter 116Chapter 117Chapter 118Chapter 119Chapter 120Chapter 121Chapter 122Chapter 123Chapter 124Chapter 125Chapter 126Chapter 127Chapter 128Chapter 129Chapter 130Chapter 131Chapter 132Chapter 133Chapter 134Chapter 135Chapter 136Chapter 137Chapter 138Chapter 139Chapter 140Chapter 141Chapter 142Chapter 143Chapter 144Chapter 145Chapter 146Chapter 147Chapter 148Chapter 149Chapter 150Chapter 151Chapter 152Chapter 153