ina masu sai da safe ita dake barin mu yau ni na barta a gurin muka fice ta bimu da kallo.
Ranan daddy yaci ya sha daga shirin hindatu da tai mai wanda ta tabbatar da babu sauran wace mace da zai kara kallo a gidan da sunan sha, awa kuma.
Don ba karamin kudi, ta kashe ba ita da uwarta kan shirya ta kawai wai don kada wata mace tazo ta zarce ta a gidan.
Don su a ganin su babu wata mace a gaban shi data wuyace ta sai gashi nazo ina yadda basu so ko kadan a gidan.
Don su inta son ransu ne kowa ma ya fice yabarta daga ita sai shi wanda haka ko wace mace ke gurin gani a gidan mijin ta.
Sai dai abin mamaki ga ikon Allah da safe ina barci na don hutun da mukeyi naji ana shafa na a hankali.
Da kyat na bude idona don ina ganin kamar mafalki nakeyi sai da abin yai yawa ne na bude idanuwa na.
Daddy na ke shafana son ranshi nace daddy please kada mu shiga hakkin wasu please bani ce da girki ba.
Yace and so what sai akace kuma kada na taba matana don wata ko ?
Nayi kokarin hana shi amma nauyin da yai min a jiki na kasa daga shi sai da naga yana son wuce gona da iri na tattara karfina na ture shi gefe daya.
Ya dan kwanta da kafada daya yana mai da numfashi yana cewa why Rahama zaki hanani abinda Allah ya halasta min akan shi.
Nace daddy bata wanan tsigar ba na cin amanan zama tare, daddy hakan da kake son yi nima idan an min bana jin dadi.
Yana jin haka naji yai tsuki ya mike ya gyara rigan shi ya fice daga dakin ran shi a bace nace a raina yafi min.
Barcin da ban koma ba ke nan namike na shiga wanka nafito na gyara jikina a part din anty na samu Fatima don tun shigan shi ta fice sasshen mu.
Gajiye tace yau fa hajiya jikin nan sai a hankali don tun safe kwance take bata fito ba ko gado bata sauko ba.
Na nufi dakin da sauri nake cewa anty ashe kuma jikin ne yau ba dadi haka da kyat ta bude idon ta tace dani wallahi Rama bana jin dadin jikin nawa gaba daya ya dibge min ne.
Nace bari na hado maki tea ki karya ki sha magani ko tace dani banjin cin komai yanzu na dai fice ban bi ta nata ba na hado mata tea mai kauri nakawo mata.
Da kyat na kamata tasha tea din na dauko maganin ta na harhada mata tasha ta koma ta kwanta saii naga ta dan fara zufa a hankali.
Ina zaune gefe nace anty Daddy ya sani kuwa kina jin jiki haka tace ya shigo da safe dai ina kwance.
Har ta danji sauki zuwa yamma kuma sai jikin ya motsa mata haka muka kwasheta zuwa Asibiti nida Gajiye don bai dawo gida ba shi.
Mun sai da aka bata gado kusan awa biyu muna kanta ya shigo nan duk ya rude hankalin shi ya tashi sosai.
Baidade da zuwa ba wayan shi yai kara ya daga da alama tambayan shi akayi yace eh nadawo nafita gani nan asibiti wurin Saade ba lafiya .
Tace to tana jiran shi don dare ya somayi a lokacin yace da ita ban fa son rashin imani kina jirana may zanzo nai maki wanda yafi wanda nakeyi nan yanzu yai tsuki ya kashe wayan.
Barci take an samu nunfashin ta ya dawo daidai yakai dare sosai tana barci bata ma san yazo ba har ya tafi.
Ranan a gurin anty muka kwana nida Gajiye banyi barci ba ina zaune a kanta cikin damuwa da halin da take ciki.
Sai kusan uku na dare ta falka ta sauke idona a kanta tabi dakin da kallo tace Rama kwantar dani sukayi ko ?
Nace eh anty sannu yaya jikin tace da sauki Rama sannu da kokari kinji nagode.
Nace haba anty bari gode min don Allah, Allah dai ya baki lafiya ki koma cikin yaran ki lafiya tace to Amin Rama.
Barci ya kara daaukanta sai da nai sallah na dan runtsa kadan shigowan daddy kuma na falka ban kara kwantawa ba.
Ta samu sauki sosai bisa ga yadda aka kaita da daren don tana dan mikewa zuwa bandaki takuma zauna idan ta gaji da kwanciya.
Ban je gida ba haka na zauna da ita komai nike mata ina bata kulawan da ya dace sosai.
Abinci ma bacin sa nake iya wa ba sai dai na dan taba na barshi ban iya tsayawa naci don damuwan da nake ciki.
Babu wacce tazo duba anty har dare mune da ita sai yan uwanta dake shigowa dubata jefi jefi.
Sai bayan sallah magariba sai ga daddy ya dawo tare doctor din suka shigo dakin nan ya dan dubata ina yi ina mashi bayanin improvement din da ake samu.
Yace wai Alhaji na tambayeka wanan yarinyar ta gidan ka ko dai likitace itama naga tasan komai akan harkan mu haka wancan karon naga tayi.
Yace insha Allahu nan da dan lokaci ta zama kamar ka ita ma don shi take karantawa yanzu haka.
Yace very intrested amma tana da kokari wallahi don tasan aikin ta sosai wallahi.
Ina son naga mace na aikin likita don yana da kyau hakan sai dai matan mu basu son yin haka sosai.
Muna da karamcin likitoci mata a arewa amma a kudu suna dasu sosai don sun san amfanin hakan garesu.


ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENnABU
IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE DON BA A YAFE BA, , ,


IDAN KIN BIYA DON ALLAH KADA KI TURAWA WATA DON HAKA CIN AMANAN ZAMA NE DON BA A YAFE BA SABODA ONLINE NOVEL NE NA KUDI, , ,
49
Bayan likita ya fita ne daddy ya dan karasa gurin anty yake cewa da ita yaya take ji yanzu tace da sauki kanta da kafa ne kawai ke mata ciwo.
Ya zauna ya jawo ledan lemo yana wade mata a hankali yake mika mata tana sha.
Sai da tasha lemon sosai tace ya isheta ya barta hakana andan taba hira ya juyo inda nake yace to ke yaya muje ko ?
Nai saurin dago kai ina kallon shi tare da cewa daddy nan fa nake zaune tare da anty.
Anty tace Rama tashi kibi mijin ki mana baki da tausayi ne yaushe rabon shi dake da zaki zauna nan .
Alhamdullahi ai na samu sauki ga Gajiye tare dani da kuma hafsat wata yar uwarta ce tazo tana zama damu.
Ban so ba banda yadda zanyi na mike a hankali don shi har yai masu sai da safe ya fice ko.
Nima nai masu sai da safe nafice daga dakin na samay shi a mota yana jirana.
Na shiga banyi magana ba har ya tada mota muka kama hanya ba wanda yai magana cikin mu.
Ya tsaya hanya yai yan sayayya muka nufi gida muna shiga na wuce part din mu ya ce nazo na dauki leda daya nakai wa yara suci na koma na karba na shige abina.
Suna falo suna ganina suka taso suna cewa basu gannin ba tunda safe ina naje nace baku san mummy ba lafiya bane halan.
Allah ya bata lafiya suke fadi nace amin namika masu leda kazane da fresh milki nace suci su sha sai a kwanta.
Part dina na nufa na gyara jikina yadda ya dace na fito na sa suka kwanta Fatima ta rufe gida na nufi gurin daddy da shirina.
Na shiga da sallama na samu shima ya fito wanka yace dani ki rufo kofa ki shigo min da ledan nan yuwa nake ji sosai.
Nace baka ci abinci bane daddy yace wa zai bani tunda keda zaki bani bakiyi tunane na ba wakike son ya tuna dani kuma ?
Nace daddy ba hakana bane kaga anty tana son kulawa yace ba mutane ne a gurin Rahama nine ban son kulawa ko may ?
Nace naga ita bata da lafiya ne ai yace to ni baki kyauta min ba kimazo mu dawo gida kika tsaya min gardama gaban mutane.
Nace daddy kayi hakkuri idan ranka ya baci don Allah bawai nayi haka da wani manufa bane.
Yace dadina dake saurin ban hakkuri idan kinyi laifi ko mutum nason kamaki da laifi sai ki kashe mai jiki da ban hakkuri.
Bani naman nadan ci ko kadan ne na mike na dauko mai ledan na dora saman plate din da na shigo dashi daga falon.
Ni da kaina na nake yaga mai yana ci har yaci sosai yasha milki din na fahinci yaji yunwa sosai ashe.
Nakawo mai ruwa ya wanke hannuwan shi ya hau gado sai da n zubar da ruwan na kawar da kayan na wanke hannuna na shigo dakin na samu har ya kwanta ko.
Nima kwanciya nayi naji ya jawoni jikin shi yana sauke numfashi, a sannu ya fara aika min da sakkonnai wanda ban san lokacin dana fara mayar mai da martanin hakan ba ya jefa mu nida shi cikin wani duniya da ban taba shiga ba koda a mafalki ne.
Ranan mun murji junan mu don ya matar dani damuwa akan komai na duniyan nan sai kace a ranan ne muka fara sanin junan mu dashi.
Nai mamaki wanan mahaukacin son da daddy ke gwada min kamar da ya dawo bai kwanta da ko wace mace ba a gidan sai ni.
Wata hudu da kwanaki ai ba wasa ba ga maurata ba, a tare sai da muka gaji dan kan mu bawai mun gundura da juna ba yakyale ni.
Gashi daddy yakai jarumi wurin iya sarrafa mace gashi baida saurin gamsuwa sai yakai ga more bukatan sa akan ka.
Ya kuma tabbatar kema din kin gamsu dashi sosai yake sauke gajiyan shi gareki.
Dakin yai tsit na dan lokaci guda sabanin kukane ko haniniya irin na ingarman doki da yakeyi saboda irin ni,imar da yake kwasa a wajena ranan.
Naji ya furzar da iska tare da mirginowa inda nake nai lankwas a saman gado yadan yi kamar murmushi yace.
Rahama ke komai naki na davan ne ko may yasa ko yaushe nake jin ki tankar a ranan na fara sanin ki na kullun sai ya zarta na baya ?
Na yarda dacewan da akayi mata suna kuka tara amma kowace da kalar niimar ta a jikin ta wai shin may yasa nake jin ki ko yaushe daban da sauran ne ?
Na lumshe idona a raina nace baiwa ne na Allah da kuma gyaran mai gyaran harka wanan karon kam.
Ya kara rugumay ni yana sunsunar sumar kaina yana lumshe idon shi a hankali a haka barci ya kwashe mu.
Da safe ma bai barni ba saida ya debi rabon shi na samu nafito duba yaran don hankalina yana gurin su.
Na samu fatima tai masu abin karyawa na hada a gurguje na daddy da wanda zaa kai asibiti nai wanka na shirya muka tafi dubo anty da jikin ta.
Kallo daya zakaiwa daddy kasan yana cikin walwala da kuzari a tare dashi mun shiga tana zaune saman kujera muka gaida ita take tambayana kwanan yaran nace suna lafiya sai anjima zanzo dasu su duba ta.
Sai tai murmushi tace kin san fa jinior yana tsoron asibiti tunda akai mai allura bai son sunan asibiti shi.
Nace sai mu barshi gida ya zauna gadi mukan zamu zo gaida ke tace dama nasan baku son shi ai.
Hafsat tace kuma gashi angonta shine kuma basu shiri Anty tace kyaleta ai nagane takon sayayya take mashi hakan don sunan shi.
Ni dai murmushi nayi nace wanan mai wuyan sha,ani wake gane kan shi, ma ga abin karyawa nan ku karya na turawa Gajiye basket din da nazo masu dashi.
Ta zauna ta fara hadawa daddy na zaune kusa da anty yana duban wayan shi naji yana magana akan dabbobi ina ga saya zaiyi ko ma yayi din.
Don naji yace a shigo mai dasu yau din nan dasu ban dai fahinci komai ba tunda waya yakeyi.
Ashe abinda ban sani ba shine ya turawa babana kudi masu yawa wai a sayo masu shanu kuma yace idan ya sawo din ai masu kudin su su biya suna son saka su a gidan gonan su ne ai kiwon su ciki.
Ba karamin dagawa baba ya samu ba a wanan harkan sosai don riban ma kawai ya ishe shi dogaro da kan shi.
Mun dan dade asibitin mukai masu sallama muka barsu don zanje inyi abinci saboda daddy da yara dake gida.
Gajiye tace dani ai Fatima zata iya girka masu mana nace daddy kin san jiya da ban koma nayi ba haka ya kwana da yunwa baici abinci ba.
Anty tai murmushi tace ai nasan ba zaici ba dama na matan shi ma yaushe ya tsaya yaci balle na Fatima.
Nace anty bai tausayawa yaci yayi dadi fa shi dai yana da wuyan sha, ani ne kawai duk training din ki ne hakan fa anty .
Ta zaro ido tace ni Rama sherin da zaki kulla min ke nan kuma kisa matan shi suji suce gaskiya ne dama suna kuka dani ga komai.
Muna cikin magana sai gashi ya leko yana fadin malama kin shanyani a mota kin barni fa.
Nai masu sallama muka fito tare yana gaba ina binshi baya har muka kai inda ya aje mota muka shiga.
Maimakon mu tafi gida sai ya biya dani gidan gonan su mukaga shanayen da aka sayo mai iri ne masu kyau idan sun samu kiwo zasu kara bun kasa ne sosai.
Ban ya gama gani muka bargona muna hanya yace dani kin san wanda yasoyo min su Rahama nace a, a .
Yace baba na turawa kudi a kauye ta sayo min su na juyo da sauri ina mamaki nace dukka daddy yace dukka mana wasu ma zai karo min su Nasir da jinior zan sayawa da kudin maman su dake gurina.
Kallon mamaki nake mai yace kina mamakine nace ai dole daddy yace may ye na mamaki kuma ya samu da kamana yanzu.
So nake ya bunkasa ya bar aikin wahalan nan idan ya samu sai irin wanan business din tunda muna saya nan gaba kuma idan mun tara sai a canza wani sana,an.
Nace a hankali daddy na gode yace namay fa nace wanan karamcin haka ba kowa ne zai iya shi ba.
Yace ni da yaiwa karamci fa ya haifa min zukekiyar mata ina more rayuwana har tana sani kuka ?
Nai murmushi ya kamo hannuna yace wallahi Rahama duk wace ke gyara min ke haka da zan santa danaje nai mata godiya.
Nace kai daddy wa kuma zata gyarani kaima kasan abin ai natural ne tace na sani amma najiya gaskiya na daban ne don kin so zuzutani wallahi.
Yace banki ba kullun ace na samu wanan ni,imar a rayuwana dagani sai ke a rayuwan mu.
Na danyi mai har da ido nace daddy kabar wanan mafalkin don Allah kaima kasan hakan bai taba faruwa a kan mu ai.
Yace ai hasashe nayi bawai nasan zaiyi ba sai dai kuma kada ki manta da Allah.
Nace ni daddy insha Allahu bani daga cikin matayen dakan shigo gida su samu mata da mijin su su wargaza masu farin cikin su.
May zai sa nayi fatan haka tunda Allah bai mai dani baya ba a cikin su a gurin ka.
Muna shigowa gidan muka hadu da hindatu itama dawowanta ke nan ashe satan hanya tayi ta fita zuwa wani wurin sherin ta.
Sai gashi Allah ya kamata maigida ya ganta sai ji nayi yace good yau Allah ya kama min yar iskan nan watau ita bata jin magana ko ?
Muna parker itama tafito tun a mota yace dakata koma inda kika fito kada ki sake ki shiga min gida ki koma inda kika fito.
Na bude mota nafice na barsu nan suna rikici ban san yaya suka kwashe ba a can na shiga na samu fatima na aiki mukayi tare da ita.
Sai la, asar muka kwasa muka nufi asubiti don nayi abinci har na dare saboda sai dare zamu dawo ni nakai su sai dai ba motar hindatu a gidan yasa nasan suna cikin fitina ke nan.
Allah ya kyauta nace dasu muka fice abin mu anty na ganin yaran taji dadi suka manne da junan su suna murna da hira tsakanin su.
Na sulale na fita Zarah na kira ina fada mata ke zarah wallahi hajiya mai gyaran harka tayi wallahi sai na samu fita zaki rakani in kai mata tukwici.
Tai ihu tace abu yayi daidai ke nan mutumiyar nace kedai kika sani tace waya fada maki borno gabas yake yarinya kina zaune dip za, a wuce ki ga mata.
Koda na dawo dakin muna hada ido da anty tace ina kika shige nace ina waje ina waya da Zarah ne.
Nan muka shiga hira sai da naga yaran hayaniyar su na damun ta na kwashesu mu ka wuce gida don kila a gobe za, a sallamay ta akace.
Ashe bayan mu yan uwan hindu sunzo sukai ra cin mutunci a gidan a wurin
Showing 213001 words to 216000 words out of 456145 words
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22Chapter 23Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32Chapter 33Chapter 34Chapter 35Chapter 36Chapter 37Chapter 38Chapter 39Chapter 40Chapter 41Chapter 42Chapter 43Chapter 44Chapter 45Chapter 46Chapter 47Chapter 48Chapter 49Chapter 50Chapter 51Chapter 52Chapter 53Chapter 54Chapter 55Chapter 56Chapter 57Chapter 58Chapter 59Chapter 60Chapter 61Chapter 62Chapter 63Chapter 64Chapter 65Chapter 66Chapter 67Chapter 68Chapter 69Chapter 70Chapter 71Chapter 72 Chapter 73Chapter 74Chapter 75Chapter 76Chapter 77Chapter 78Chapter 79Chapter 80Chapter 81Chapter 82Chapter 83Chapter 84Chapter 85Chapter 86Chapter 87Chapter 88Chapter 89Chapter 90Chapter 91Chapter 92Chapter 93Chapter 94Chapter 95Chapter 96Chapter 97Chapter 98Chapter 99Chapter 100Chapter 101Chapter 102Chapter 103Chapter 104Chapter 105Chapter 106Chapter 107Chapter 108Chapter 109Chapter 110Chapter 111Chapter 112Chapter 113Chapter 114Chapter 115Chapter 116Chapter 117Chapter 118Chapter 119Chapter 120Chapter 121Chapter 122Chapter 123Chapter 124Chapter 125Chapter 126Chapter 127Chapter 128Chapter 129Chapter 130Chapter 131Chapter 132Chapter 133Chapter 134Chapter 135Chapter 136Chapter 137Chapter 138Chapter 139Chapter 140Chapter 141Chapter 142Chapter 143Chapter 144Chapter 145Chapter 146Chapter 147Chapter 148Chapter 149Chapter 150Chapter 151Chapter 152Chapter 153