wanan tanbadar badani Rahama ba gaskiya.
Ysi yar dariya yace dake kuwa zaku zauna a gidan nan ba wani gida ba auren da nake may nake rage ku dashi dakuke wanan kishin haka wai ?
Nace kishi kishin wa zanyi wanan ai uwatace ba kishiya ba ni bata a gabana gani nayi kawai a tsaye take tana daukan kanta hamshakiya .
Ya kai zaune tare da kai hannun shi a saman cinyana nai saurin kabe hannun nashi ina fadin kada ka soma don nagaji da wanan halin naka daddy a yau nayi nadamar auren ka da samun zuria da kai a duniyan nan.
Da sauri ya katse ni yana fadin Rahama ni keke fadawa kinyi nadaman aure na da kikayi nace na fada don abin ya isheni haka.
Bai yi magana ba sai naga ya mike ya fice daga dakin ran shi a bace nima na raka shi da haraea tare da tsuki na haye gadona don daukan shi ma nake bai san ciwon kan shi ba kuma.
Mutum ya koma na mamajo haka baida aiki sai aure may ya rasa a gun matan shi da yake muna wanan hakin auren kuma ko yaushe kamar ba aure na kai sake ba idan yayi.
Kai da zakaga matan sai kaji nauyi da kunya don basu dace da ajin shi ba abu dai gashi bai faduwa ga mutum.
Abinda mu ba musani ba shine ashe idan namiji ba mazinaci bane haka wani lokaci yakan kasance dashi ga matan yanzu basu tunkaran namiji sai sun shirya mashi da saddabaru da dan sihiri shi ke saka idan namiji ya yi wani abin kaji wani iri a ran ka.



ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU

Kuyi hakkuri masu fadin wai novel din ya dau lokaci anayin sa ba laifina bane yadda labarin yazo ne idan kuma na katse shi yadda na katse tarko nasan bazaku ji dadina ba zan ta samun korafi ne kuyi hakkuri saura kadan mu karasa da yardan ubangiji
Na gode da fatan zaku fahince ni yan uwa kuma kuyi hakkuri dani please rashin waya ya kaimu har wanan lokacin haka.
IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE, DON BA A YAFE BA ONLINE NOVEL NE, , , , ,

108
Daga wanan fitan bai kara kulani ba nima haka inda na shiga harkokina da yara da abokan arziki masu zuwa yi min sannu da zuwa .
Ba wai share junan da mukayi baya damuna bane a a na dai yi niyar daukarwa kaina matakin da ya dace ne don abin nashi ya fara bada tsoro a zuciya na.
Tafiyan wata uku kacal sai aure a bayana daga mutuwan anty yai auren Raliya, Raliya tana fita ba a dade ba ya dauko Niima itama ta debi rabonta tai gaba.
Nisawa nayi a fili nace mijin bahausa ke nan ke mace baki da tabbas zama da mata daya ko biyu zuwa uku sai ranan da rayuwa ya kare wa bawa.
Mun koma bakin aikin mu bayan sati daya ga Inna sai shirin komawa take kano don zaman nan ya kai mata ko ina don bata saba ba zaman dole takeyi.
Ranan da na fara fita na dawo a gajiye don yan aiyukan da nayi a office wanka nayi na shirya nafito zuwa dakin da su inna da mama suke na gaidasu.
Suna zaune hiran su suke na shigo da sallama na dakin tare da masu barka da gida suka amsa min cikin kulawa da kauna.
Na samu wuri na zauna tare da kallon kwanon abincin da aka aje a gefen su basu ci ba har lokacin nake cewa dasu sai naga kamar baku taba abincin ba mana ?
Mamace tace dani Rahama in ba so kike mu fashe ba da wanan irin dadin da kuke bamu haka Allah dai ya baku hakkuri zama da mijin ku.
Inna tace ai mai kuli wanan mutumin ba abin da za, ace dashi sai fatan alheri ku dai ta hakkuri kowa da halinsa ake zama dashi duniya balle ni banga wani abin gazawa a gare shi ba akan ku.
Baida maraina akan iyalin shi ko kadan tunda duk wani nauyi da hakkin daga matan har yaran shi yana saukewa kai bama iyalin shi ba har masu aikin dake karkashin shi bai barsu a baya ba dubi gajiye yadda ta koma matar mai gadi fa kawai ba wani ba can.
Kin kai nisa ai inji mama ninan fa yar uwar matarshi ce amma ji yadda yake min tankar mahaifiyan shi ce ke a gidan sau goma zai shigo sai ya shigo nan ya duba ni tare da tambayar banda matsala dai ko ?
May yafi wanan dadi Asiya a duniya ai irin mazan nan ko wace mace na fatan samun iri su a duniya.
Murmushi kawai nayi na gyara zama na araina nace wanan kuka sani ku may yafi bacin rai kullun namiji sunan kuna zaune kalau amma baida aiki sai na kadin aure.
Kamar wanda bai samun jin dadi gun iyalin shi irin wanan ma ai sai duniya ta zagi mutum don baza mu fita sai ace mune bamu gamsar dashi ga wanda bai san halin shi da raayin shi ba.
Sai naji Inna tace kinga ta nan tun dawowan ta na fahinci ba dadi tsakanin ta da shi don ko yawan shigowan da take dubamu ya rage.
A, a haba dai Rahama may kuma kike so a duniya yanzu ilimi da daukaka Allah ya baki ga miji na gwadawa tsara kin samu ga zuria dayyaba Allah yabaku a tsakani may kuma kike nema Rahama ?
In dai don wanan auren da yake yawan yi ne sai ku barshi da halin shi tunda auren nasa bawai yana takura maku bane ko wani abu.
Gaskiya in har hakane abinda uwarki ta fada baki ko kyauta ba don banga abin damuwa ba ga wanan dai.
Bafa a kan ku matan ke zama ba ke ku godewa Allah ma da ba irin mazan nan bane da idan sun dauko wata a gida ke ra gida dake da babu duk daya kuke a wurin shi.
Iya hakkuri bawan Allah nan yana dashi a gare ku iyalin shi ki duba irin tsiyar da yaran nan hindatu da zulfa ke shuka mai amma yana hakkuri yana takewa yana kuma zaune dasu lafiya.
Duk masu shigowan nan ni a ganina kaddaran aure ne a tsakanin shi dasu inba ita wanan daya aura mara tarbiyan ba bayan mutuwan diyana waya haihu dashi ?
Balle ita wanan uwar guzumar daya kwaso yanzu ai ba batun haihuwa a gare ta ma mufa a zamanin mu bamu kishin komai inba na haihuwa ba ki zuba in zuba kowa ya cika gida kuma babu wani abindake ga namiji in dai ba wanan din ba.
Nace mama ni ba wai auren shi bane ko wani abu ke damuna yanzu fa ba irin da can baya ne aure haka a zamanin nan abun tsoro ne ga namiji don zamani ya canza lafiyan mutum akewa tsoro.
Haba yar nan har ke kin fishi sanin hakan ko kin kaishi sanin abinda duniya ke cikine wai inna tace fada mata dai mai kuli yarinyar nan bata ji ne tun bata dawo kasan nan ba mukai wanan maganan da ita.
Ashe ita da manufa a zuciyar ta yanzu kinji inda ta bullo wai ita malamar lafiya dariya inna tabani nace inna ba haka bane ku baku ganewa ne shiyasa.
Bafa ganin mutum yanzu haka lafiyyaye shine lafiya ba ciwon ba a goshi ake ganin shi ba nan dai nai masu bayan komai kan irin cutar da nake gudu gare shi ga yawan auren da yakeyi.
Na kara da fadin yanzu fa ki duba waban matar da ganin ta irin yan duniyan matan nan ne dake zaman kasu a wani kasan bama a na kasan ba kawai.
Nan nake fada masu yadda mukayi da ita ranan da muka dawo garin mama tace yo ga yar iska ita kuma dashi ta shigo watse gida ko may ?
Nan dai suke min nasiha da kuma fadakar dani irin halakan da nake daukawa kaina na wanan zaman doya da manjan da mukeyi dashi a gidan.
Maganan su ba wai ya shigeni bane sosai don ina a kan bakana na sai naga takardan gwajin da sukayi da ita kafin auren su dashi.
Baya gari da ya dawo ya shigo gaida su nan yake magana akan tafiyan inna da zatayi ga jibi sai inna take cewa dashi Alhaji mun gode kwarai da kokarin ka a gare mu ko yaushe don Allah adai ta hakkuri da iyali.
Murmushi yayi yace Inna ai hakkuri ya zama dole tun da an zama daya yanzu suna dauka na ban san may nakeyi bane shi ya kawo haka kawai.
Hakkuri za ayi don mu mata dama sai hakkuri balle ga wanda ya aje mace fiye da daya ko biyu a gidan sa.
Ya mike yana fadin barsu ai mun saba in dai halin su ne komai zai wuce ne insha Allahu.
Da dare na shiga falin nashi don na fada mai ina sin ni da kaina zan mayar da inna gida idan zata tafi do ina son zuwa na duba jikin mahaifina.
Ya dago kai yana cewa dani ashe ina da darajan da za a nemi wani alfarma a guna nace ni ba wana ya kawo ni ba yanzu.
Yace ban amince ba in dai nike da wanan dokar a hannuna nace ba matsala Allah ya bashi lafiya don ban tsaya jan maganan ba .
Namike zan wuce yake cewa dani kina ganin wannan matakin da kika dauka a gare ki shine daidai ko kina min daukan mara hankali ne wai ?
Nace namay kuma nifa auren ka ba wai ya damay ni bane kawai dai magana ta daya ne a nan shine naga takardan ku na gwaji da kukayi da wanan yar duniyar matar tunda abin bana kai sake bane nake gani.
Ko makaho ai sai ya lalaba yake taka wuri ba wai tafiya yake babu lalabe ba mutum tun yana dauko abinda duniya ke iya dan kallo har ya koma dauko abinda za ai mai dariya don bakin jaraba kawai.
Na sa kai zan bar falon naji yace dani Rahama nine yau kuma jarabbabe ko may ?
Nace ai haka din ne don in ba jaraba ba banga abin gani gun wanan curarar matar daka dauko ba a gidan nan ban da magana babu abin ganewa a nan.
Yace a ganin ki ba ni abin dake min na dauko kune baku ganewa kawai nace sai kuje kuyi ta ganewa kai da ita ku da jaraba ya dama a rai.
Ina fadin haka na juya na fice daga falin dakina na nufa kai tsaye na fada saman gado siffan wanan matar dana gani mai kiba wai amarya nake tunane da yace shi yana gane abin sa.
Nace a raina to may daddy ya gani har yace mune wai bamu ganewa a nan dayake fadi ni dai banga wani tsiya ba a gunta in banda muni sai ko launin jikin ta da ya nuna mai take shafawa na zamani.
Shima na barshi can yana tunanen magana na abin ashe ya bata mai rai yace watau ke nan ina nufin baida hankali ko may da zai afkawa mace irin haka kai tsaye shiko Niima da ya aura a budurwa bata shigo gidan shi ba sai da sukai gwaji da ita.
Balle wanan dashi kan sa yasan zaman barikin da tayi a waje dama nan kasan don ba diyar kowa bace ita irin matan nan ne kawai masu sai sunyi kudi da karfin tsiya ko ta wani hanya.
Shi kan shi wani lokaci yakan yi mamakin yadda ya aure ta ba dai tsari takai ko wace mace dake gare shi a gida ba balle auren dai ne yazo masu don ta dade tana bin shi amma sai gashi haduwan su da ita a kaduna yaji yana balain sha awanta shiko ba zina ya iya ba don haka tana gabatar mai da zancen aure yaji ya amince mata da suyi din ba adauki lokaci mai tsawo ba aka daura auren.
Abinda bai sani ba sai da tai mai zaman kashi na shekaru tana aiki a kan sa duk wani shige da ficen shi ta sani a kasan shiyasa bata sha wani wahala ba wurin samo kan sa.
Namiji baida wuyan kamawa gun mace ta wanan fannin sai idan Allah ya kare shi kawai daga kaidin ta gashi ma ita kan ta da ganin Rahama hankalin ta yai balain tashi sosai don yanzu haka a cikin rikici suke da ita.
Don ya tsura ta taja waya tana fadin itafa hankalin ta ya tashi ga matar don ko diyan ta fa cewa tayi takwas dashi kawar da ita kawai zanyi don ina ganin ita ce aka fada muna dama bazan iya da ita ba a gidan a kawar min da ita kawai kowa ma ya huta.
Bai san may ake fada mata ba a wayan dago kan da zatayi sai kawai ta gan shi tsaye a bayan ta nan ta shiga kamay kamay tana fadin ai na fada maki wanan hadizan yar iskace ni maganin ta zanyi idan bata dawo min da kudi na ba.
Ta kashe wayan tana wani fadan borin kunya sai taji yace da ita a gidan nawa nake da hadizan data ci maki kudi har kike son a kawar da ita a duniya ko may ?
Tace dashi tunda ba kunya gare ta ba a gidan ka kamar ya kasan da wace nake waya ne balle kace wai a gidan ka ?
Yace ke dakata kiji duk abinda ya samu daya daga cikin iyalina kema ya samay ki don duk abinda kike fadi tun dazun a kunne na yake gaki ga matan nawa sai ki kashe ta tun yau mu gani.
Ya juya ya fita ya barta tana fadan borin kunya don duk jikin ta yai sanyi har ta tafi basu shirya ba do ta rasa gane kan shi abu ya taru yai mashi yawa a zuciya sai kuma.
Wanan shigowan nawa yanzu ya fahinci inda na dosa da zaman mu dashi da muke yar tsama tun dawowa na.
Ya nisa tare da furzo da iska daga bakin shi yanisa yace halin mace ta waye ke nan ai su wa yan nan basu ko kai zuciyar ga wanan maganan da nayi ba sai fadan kishi da ya damay su kawai.
Ban sake magana akan bin Inna ba zuwa duba mahaifina da yan uwana a gida sai da safe ina daukan waya naga text din shi yana fadin na shirya nakai ina gida tafiya ya kama shi baya samun zuwa ya maidata.
Kamar nace na fasa amma kuma sai naga wanan ne lokacin da nake dashi a yanzu kuma ko banza mahaifiya tace zan kai ba wata ba.
Don haka a gurguje na shirya tafiyan sai gashi ya shigo yi wa inna din sallama ya kawo sako envelop biyu ya bata daya takaiwa maigari dayan na mahaifina nane.
Godiya sossi inna ta shiga mashi ba laifi a gurguje nake ta shiri ya shigo dakin ya samay ni a hakan nai mashi ina kwana ya amsa ba sakin fuska kudi ya bani masu yawa akan tafiyan da zanyi din na ansa da godiya.
Nan yake fada min zancen tafiyan shi da zauyi zuwa kasan Kuwait inda zai kwana biyu a can don wani harkan mai da suke son yi a can din.
Zuwa wani kasa shi da wasu da suka hada hannu dasu nai mashi fatan alheri tare da rokon Allah ya bada saa ga tafiyan.
Bayan na gama maganan ne sai dan shiru ya biyo bayan va wanda yai magana a cikin mu can naji yana cewa dani yanzu haka zaki barni na tafi babu ko tausayawa ?
Nace kamar ta kuma aini na gama zance akai ko don na fada ma matsala kuma na zauna inda Allah ya aje ni ko.
A ina aka aje ki nace matar da bata da wani biyan bukata aji dadin ta sai na waje da ake hangowa a gare su ne hutu yake da jin dadi ko.
Wanan kuma maganan ki ne abin siri ne mai daki shi yasan inda ruwa ke yoyo ai ba wani ne yasan cikin zuciyana ba.
Auren da nake kuma kaddaran ubangiji nane wanan don haka Allah ya kaddaro min a rayuwana nace da sauri kuma da niyyan yin hakan ba.
Yace haka dai kika ce amma ai ko duniya tasan banda macen da tafi min Rahama a yanzu, in ma yin auren da nakeyi ne ai kina da kamisho a cikin sa tunda kulawan da nake samu da a wurin ki yanzu aikin ki ya hanani samun shi kamar baya.
Kin mayar da rayuwan ki akan aikin ki fiyye da bani irin kulawan da kika saba bani a baya.
Yaya kike son na zauna a gida ni kadai kulun kamar maraya babu mai bani kulawa yadda nake so ai min.
Nace ta nan kuma za a bullo min yanzu su matan dake gida ba mata bane ko ni kadai ne mace a gidan wanan maganan ma kada ka bari wani yajita don Allah don sai ai maka wani fahinta na daban can.
Mutum mai mata uku a gida zai tsaya yana fadin irin wanan maganan haka ai abin kunyane a gare ka aji hakan daga bakin ka.
Yace ga wanda baisan mai aure yake nufi ba
Showing 447001 words to 450000 words out of 456145 words
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22Chapter 23Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32Chapter 33Chapter 34Chapter 35Chapter 36Chapter 37Chapter 38Chapter 39Chapter 40Chapter 41Chapter 42Chapter 43Chapter 44Chapter 45Chapter 46Chapter 47Chapter 48Chapter 49Chapter 50Chapter 51Chapter 52Chapter 53Chapter 54Chapter 55Chapter 56Chapter 57Chapter 58Chapter 59Chapter 60Chapter 61Chapter 62Chapter 63Chapter 64Chapter 65Chapter 66Chapter 67Chapter 68Chapter 69Chapter 70Chapter 71Chapter 72Chapter 73Chapter 74Chapter 75Chapter 76Chapter 77Chapter 78Chapter 79Chapter 80Chapter 81Chapter 82Chapter 83Chapter 84Chapter 85Chapter 86Chapter 87Chapter 88Chapter 89Chapter 90Chapter 91Chapter 92Chapter 93Chapter 94Chapter 95Chapter 96Chapter 97Chapter 98Chapter 99Chapter 100Chapter 101Chapter 102Chapter 103Chapter 104Chapter 105Chapter 106Chapter 107Chapter 108Chapter 109Chapter 110Chapter 111Chapter 112Chapter 113Chapter 114Chapter 115Chapter 116Chapter 117Chapter 118Chapter 119Chapter 120Chapter 121Chapter 122Chapter 123Chapter 124Chapter 125Chapter 126Chapter 127Chapter 128Chapter 129Chapter 130Chapter 131Chapter 132Chapter 133Chapter 134Chapter 135Chapter 136Chapter 137Chapter 138Chapter 139Chapter 140Chapter 141Chapter 142Chapter 143Chapter 144Chapter 145Chapter 146Chapter 147Chapter 148Chapter 149Chapter 150 Chapter 151Chapter 152Chapter 153