ita yace Hausatu kada kice komai hakan ma yafi min komai dadi daga yau kowa ta girka nata da diyan ta ita kuma Rahama ta girka wanda zataci can shiyan ta.
Dama ba yau ba kike min korafin sai nasa sarakaina suna girkin gidan nan naki biye maki amma yanzu tunda haka kike so hakan yai min dadi wallahi.
Sai dai kada ki manta ba leken tallen kowa ba kuma wani zancen na wance yafi nawa na kashe wanan korafin a gidan nan.
Yarinyar na kuma ba ruwan ki da ita ko irin habaicin da nake ji kinawa yar mutane kada na kara jin shi a gidan nan.
Idan ba haka ba wallahii rai zai baci don haka ke Kulu da hausi ga amanan wanan yarinyar gare ku da diyan ku na danka maku don Allah ku tayani bata tarbiya yadda ya dace.
Sukace insha Allahu Alhaji mu yarinyar nan bata tsare muna komai ba wallahi har yaran mu tunda tasan darajan mu.
Ko yaran nan suka dawo kasuwa har kofan su takee binsu tai masu sannu da kasuwa yaran su kuma tana haba haba dasu .
To yaron da yasan haka may zakace akan shi kuma sai fatan alheri yadda muma muka haifa itama Allah ya bata nata tasaka a cikin mu ba shi ke nan ba.
Yace nako gode dama nasan bazaku ki duk wani abinda na koso ba gidan nan indai har alheri ne da jin dadi na don haka Allah yai maku albarka suka ce amin a lokaci daya.
Yace ke kuma Rahama tarbiyan nan da iyayyen ki sukai maki ina son kici gaba dashi don shine tubalin zaman ki gidan nan.
Can sabuwa tace muma da ba a saka muna ba Allah yai muna shi sannan yaya zancen namu kayan dakin daka saya mata.
Cikin mamaki yace kayan daki kuma nine ma na saya mata kayan dakin nata ke nan.
Tace idan ba kai ka saya mata ba uban waya basu kudin sayen wanan kayan haka giredi masu kyau ?
Yace toni wallahi ko ku yarda ko kada ku yarda ban san komai ba akan wanan zancen.
Ita bata da mahaifa ne da zasuyi mata ban san lokacin da nace nikan anty na ta birni ce tai min komai ba wani ba.
Yace to kinji tai wani irin murguda baki tace haka dai akace kawai amma wata anty gare ta na birni da zatai mata wanan.
Yace to yanzu dai kowa yaji kowa ya tsaya a matsayin shi babba ya rike girman shi karami ma ya rike nashi.
Yace ku tashi ku tafi na gama magana na ni ban son wani abu kuma ya biyo baya.
Bayan fitan su sai ni ban fice daga dakin ba mama tace Rahama tashi zuwa dakin ki kinji.
Nace mama ni anan zan kwana tsoro nake ji ni daya a dakin nan kada sabuwa ta kashe ni.
Subbahanallahi inji su suna hada baki ita da mijin ta yace kin gani ko ta riga da ta tsorata a gidan nan da sabuwa.
Mama hausi tace kinga tashi na sa zuwaira ta tayaki kwana a dakin naki ba shi ke nan ba.
Daga ranan muka fara kwana ni da zuwaira a dakina kafin mu kwanta mukan yi hira na ta karanta muna labarai a littatafai.
Idan nace ina da wani matsala kuma nai karya girkin abinda zanci ma sai na so don idan su mama sunyi nasu suna saka min wani lokaci naci wani sain kuma nace na koshi.
Gashi ban gajiya gurin kama masu aiyukan su tun suna hanawa har sun gaji sun kyale ni ina yi da zuciya daya don yadda uwa da yar ta suke haka nake dasu su biyun.
Idan girki ya zo kaina a dadafe cikin takura nakeyin shi don Alhaji kan min nauyi a dakina har yanzu na kasa sake jikina dashi.
Sai ma kwana da zuwaira yafi min ace shine zai kwana a dakin duk da ba komai yake min ba sai lalashi da ban hakkuri wanda ni ban fahinci na maye ba.
Nayi kyau dani haskena yafito har dan kiba na kara gani shar fes dani idan kin gan ni.
Har kirjina dake a shafe sun fara tasowa yanzu sai dai duk wanan dadin da nake ci hankalina yana gurin Innata ko yaushe don yanzu ban san wake dibar mata ruwa ba wake mata talla wake mata aiki don kanni na duk yan maza ne.
Kaunata mace yar karama ce sosai ita aka yaye ba a haifi wani ba bayan ta ko may yasa inna bata kara haihuwa ba oho ?
Sallaman wani yaro ne a kofana rike da dakwalen kaji guda biyu a hannun shi sai kayan miya a wani leda mai yawa yace Alhaji ne yace ya kawo min.
Na karba yaron zai tafi nake cewa ya tsaya nazo na shiga daki na dauko mai biscuit na bashi har ya fara tafiya yace.
Amarya Alhaji ko na tsaya na taya ki gyaran kajin ?
Nace to shi ke nan dauki kaje a yanka bari na sa ruwan zafi kafin ka dawo ya juya dasu yafita.
Daidai lokacin da sabuwa tafito daga daki yaran ta sun fada mata an kawo kaji a sashe na yanzu sai ko ga yaron tafe dasu za, a yanka.
Tabi kajin da kallo har yaron ya fice daga gidan tanisa tace hum, umm ashe akwaita ke nan ?
Tare da yaron muka gyara ya kama min nayanka na zauka na shuga jajagen kayan miya kafin wani lokaci har guri ya dauki kamshi.
Miya ya kammalu na sauke na dora tuwo duk tare da yaron nan da yace min sunan shi habib ne dan gidan mai faci.
Sai yamma Alhaji ya shigo gidan daga shiyana ina zubawa yaron abinci naji muryan sabuwa tana cewa yau wani sabon cin amana ne da muna funci ya taso a gidan nan kuma ?.
Kamar yaya kuma ya tambaya tace duk munafuncin da kake a gidan nan nabawa yarinyar nan kayan dadi taci don ta yarda dakai ta kwantar da hankalin ta ka murje ra yadda kake so nagane ka.
Mu sai ka tura muna tuwo ita ko daga shinkafa sai taliya kake bata bata taba cin tuwo a gidan nan.
Ga kowa yai cirko cirko yana sauraren ta yace cikin daka tsawa ke sabuwa ban son sheri ni kike kira da munafuki yau.
In ma har munafunci ne ai ake nakeyi don ke ce munafukan kullun a gidan nan ba mai bani bani sai ke, ke, kenan kullun yin karya da ciwon yara ba ranan da zan fita baki karbi kwabona ba a gidan nan karyan yau daban na gobe daban.
Kaji kuma na sayo mata don itace mai girki su nake son ci shiyasa na sayo ke ranan da zan sayo bacewa kikiyi wai nabaki kufin ba ki sayo da kanki dana baki na dawo cewa kikayi n sace kudin ai.
Nawa nake ba wanan yarinyar a gidan nan ko bata nayi yadda nake bata sai dai tace na sayo mata duk abin da ya dace idan na fita.
Sabuwa nan ta hau borin kunya akan wai Allah dai ya kama ka yau kila ma har gashin dare kake kawo mata kai a dole gaka mijin yarinya ko ?
Sabuwa yau dai na gaji da sherin ki a gidan don haka na fada maki akan yarinyar nan zan iya saba maki kifice min daga gida.
Ahayye nanaye abin kunya wai aure da mara kwabo yace balle da kwabona ko kin manta kwabon kika gani a baya kika lake min da aike da komai har na yarda kika shigo gidan don haka yau ko wayai maki tsaye a gidan nan wallahi baki kwana min a gida.
Maimakon ta ci gaba da gudan da takeyi sai kuma jikin ta yai matukar sanyi sosai don tasan takan mashi fiye da haka amma bai taba yanke irin wanan hukuncin ba a kan ta sai yau kuma akan yar karamar yarinya.
Nan dai mama hausi ta saka bakin ta tace asha Alhaji da baka biye mata ba halin sabuwa ne kuma bako a gare ka yau.
Yace bari hausatu nagaji da sherin yarinyar nan yau ta kaini kat ne ita bata ji kunyan yaudara na ba sai nine zanji kunyan ta.
Ina kazan nan a kowan ku da yai girki sai da na saya mai aka girka min naci amma don wanan yarinyar na da girki na sayo zatai min sheri tace ai ba biyu ka saya muna ba kamar nata.
Bai kula ta ba ya shige dakin ta da kan shi ya kwaso kayan shi na kwan ciya ya fito daga dakin nata.
Hankali yai matukar tashi sosai a lokaci don nasan halin kauyen mu yazu labari zai sha banban ace daga shiga na na fara watsa matan gidan da na samu.
Hakana jiki ba kwari na dinga aiken wanan yaron da Allah ya hadani dashi yau yana kai wa kowa miyan duk sai da na kusa rabe naman don yawan gidan.
Mama hausi dake zaune tare da sarakan ta matan diyan ta su uku ta ce kungani ba yanzu ga naman ma karshen ta duk ta rabe shi gare mu.
Har ya fita zuwa sallah ya dawo bata bar gidan ba kamar yadda ya bukata haka yasa shi zuwa har kofanta ya daga labulen dakin yace.
Sabuwa may kike jira ne a gidan nan wai ai tunda gidan nan bana ubanki bane yau na fada maki wallahi baki kwana min a gida ki tafican gidan ku kikarata can.
Idan kuma kin ki fita yanzu na turo masu karfi aja min ke da karfin tsiya har waje.
Ganin haka tasan kuma da gaske yake yi yasa ta fara tattara kayan ta tana kuka wai saboda karamar yarinyar da kokwai bai aje da ita zai koreta gidan shi ita dake da yara bakwai a gidan.
Haka tafice daga gidan bakin ta bai mutu ba ta nufi gidan su a cikin dare kowana na kallon ta a wullakance.
Sai bayan tafiyan tane na fahinci ashe halinta ya ishi kowa agidan sai fadin aibunta kowa keyi.
Nan naji abubuwa da dama akan halinta ashe shiyasa take ganin an auro ni zan karbe mata power da take dashi a gidan da gurin mijin su.
****** ********* ******
Washegari tunda safe na shiga gurin mama bayan na gama aikin da nakeyi na kwashi kayan wankin ta sai aune tayi dani ina wanke tufafin ta.
Ta saka salati tana cewa haba amarya ai sai kina ace muna bautar dake ko iyayyen ki suka samu labari bazasu ji dadi ba gaskiya.
Nace daidai danta babba yana shigowa gidan dauke da dan karamin yaron shi a kafadan shi haba mama don nai maki wanki shine za, ace kina bautar dani kefa uwatace mama ba kishiya ba kamar yadda naji ana fada.
Ko a gida nike wankewa su innata har da mama kayan su idan yai dauda don wanan kayan da baida yawa ma.
Girgiza kan shi yayi yana cewa a ranshi ikon Allah yanzu baba wanan karamar yarinyar daya kwaso kurciya zalla haka may zai gane a gurin ta ne wai.
Nan dai dole uwar ta barni da wankin na wanke su fes na shanya na koma dakina ina jiran su bushe na kwashe mata.
Yaron nata mai suna yaya sani ya shigo dakin mahaifiyar tashi ya samu guri ya zauna daga gefen ta yace.
Mama dazun sai nake jin ki da amaryan ku a bakin rijiya kuna gaddama kuma akan wanki.
Tace bari kaidai ni kurciyar yarinyar na ya fara daure min kai wallahi bata tasan kyashi ba ko hassada a rayuwan ta komai haka zata zage tayi shi tsakani da Allah.
Yace haka naji nima sai dai mama gaskiya sai kunyi da gaske gurin rike amana tun da dai ba sanin ciwon kan ta tayi ba yarinyar gashi uwarta tai mata tarbiyan da ya dace duk uwa ta gari taiwa yarta.
Tace insha Allahu haka nake kokarin ganin nayi yo har ma may mutum zai cuta a wanan gurin kuma ?
Nan dai sukai ta zancen su har suka fado kan maganan sabuwa da irin hallin gallaza masu data dinga yi a zamanin ta a gidan.
Mama hausatu tace don yaran ai ayi hakkuri ta dawo dakin ta gashi kuma bazan so ace don wanan yarinyar tabar gidan nan ba.
Kada azo a shafa wa yar mutane labbo bata ci ba tasha akama zarginta ga banza kasan haln mutanen yanzu da dauka su dagwarawa kan su maganan da bata shafe su ba.
Dan nata yace hakan yana da kyau mama indai wanan mara mutuncin ne aiko ta dawo ba dainawa zatayi ba.
Gara dai tadawo dakin ta din zaifi don kaga yanzu idan tafice gidan nan nauyin diyan ta duk akaina zai dawo gasu ba tarbiya ke garesu ba.
Yadda mama hausatu tai shawara da danta haka akayi da yamma da Alhaji yadawo gida ta sanya shi a gaba tana bashi baki akan yayi hakkuri ya daure sabuwa ta dawo dakin ta hakana ko don yaranta.
Yace wai hausatu ke ce ke auren ta ko ni da zaki isheni naje nayo bikon ta ina indai sabuwa ce koke bata bari a gidan da tsufanki kuwa ?
Mama hausatu tace kadai yi hakkuri Alhaji kodan yaran ta ta dawo taci gaba da duba abinta.
Yace yara ai bada su tazo ba anan ta samay su kuma a gidan iban su suke ko ?
Ya ja tsaki ya dauki buta ya fice daga gidan.
Gaba daya yaran Sabuwa sun ishi matan gidan da rashin kunya idan ka cire shi Alhajin da basuyi a gaban shi don tsaye yake akan iyalin shi.
Don haka shi zaman su ma babu uwar su a gidan ko a kwallan shi bai taba damuwan shi ba don dan ficewan ta har ya samu natsuwa tare dashi.
Satin ta daya shiru babu labarin dawowan ta gidan har wanan lokacin ganin maganan wasa zai zama gaskiya yasa.
Mama hausatu samun wani dan uwan Alhaji kuma amin shi akan zancen sabuwa din don yaran sun ishesu ba hutu gareta.
Bayan sun gaisa ne tayi mashi bayanin komai akan matsalan da ake ciki tsakanin sabuwa da Alhajin.
Malam shehu yace a gaskiya ba yau ba Alhaji hakkuri yake da al, amarin sabuwa ke ma kin sani .
Don ko jiya muna tare nan dashi yake min bayanin komai don iyayyen ta da yan uwan ta sun damay ni da zariya agida.
Amma tunda kinzo ba komai insha Allahu anjima zan samay shi muyi magana idan ya dawo.
Mama tace don Allah malam a taimaka a sa baki ga alamarin a gyara tun bai baci ba kodon yara.
Daga haka sukai sallama ta tafi tana godiya don sun saba dashi sosai akan matsalar gidan su.
Duk yadda ya raya da Alhaji akan yai hakkuri Sabuwa ta dawo dakin ta yaki yarje mashi.
Don haka ya kyale shi malam shehu ya nemi wani amin shi da magariba suka shirya sai gidan wan sabuwa inda take zaune.
Lokacin da suka isa gidan sun samu wan nata baya gida dole suka dan jira shi don ba nisa ya tafi ba.
Bayan sun gaisa ne suke cewa da shi dama mun biyo bayan sabuwa ne don Allah ayi hakkuri ta koma dakin ta hakana.
Don sabani akasamu kuma yanzu kowa ya gane kuresa don ko tsakanin harshe da hakori ana samun sabani balle mutum da mutum don gaskiya iya hakkuri kukan ku kun sani Alhaji garbati yana iya hakkurin shi da sabuwa a gidan shi.
Yayan nata yace hakane amma naso ace shi Alhajin ne yazo nan da kan shi don na kara bashi hakkuri saboda nima dan zaman ta cikin iyalina nasan yana hakkuri sosai.
Malam shehu ya jinjina kan shi yace hakane amma da zuwan Alhajin da namu duk kusan guda ne don a madadin shi muka zo mu.
Koma may nene ai yanzu ta san ta fara kaishi bango don baka kallon babban mutum kamar Alhaji garba tsakiya iyalin shi tace mai munafuki.
Yayan nata yace don Allah akara bashi hakkuri kafin nazo har gidan na bashi.
Yayan yace kafin ku tafi bari na kirata taji da kan ta don ku kara ja mata kunne mace da girman ta kamar Sabuwa ace wai ta saura yaji don rashin hakkuri irin nata.
Bai jima ba suka fito a tare yana gaba tana bayan shi ta samu guri daga gefe ta tsugun na.
Yayan nata yace sabuwa ga malam shehu nan sunzo bikon auren ki a madadin maigidan ki.
Ta dukar da kai cikin kunya da nauyi zatayi magana malam shehu yace da ita.
Haba Sabuwa yanzu lokaci yayi da za, a san girma ya kama a daina wasu halaiya kuma.
Don Alhaji ya auro wanan yarinyar bai kamata ace daga gareki ne ba a samu zaman lafiya ba idan kin yi tunanen irin zaman da kukayi ke dashi har takai kina ci masa mutunci a tsakiyan sarakan shi hakana.
Don haka idan kin koma dakin ki da fatan komai zai sauya daga gareki yanzu shiga ki dauko kayan ki basai gobe ba mutafi na mayar dake dakin ki.
Zatai magana yayan nata dake zaune a gefe yace ya katseta cikin bacin rai da cewa .
Kin sani sarai bana son tashin tashin kije ki shiryo ku tafi.
Ba don taso ba ta tashi ta shiga ciki can sai gata tafito da lulubinta dauke da dan ledan kayan ta suka kama hanya.
Ko da suka iso gidan sun samu Alhaji a kofan gida shi da baba salla zaune suna hira.
Yacewa Sabuwa shiga gida
Showing 27001 words to 30000 words out of 456145 words
Dama ba yau ba kike min korafin sai nasa sarakaina suna girkin gidan nan naki biye maki amma yanzu tunda haka kike so hakan yai min dadi wallahi.
Sai dai kada ki manta ba leken tallen kowa ba kuma wani zancen na wance yafi nawa na kashe wanan korafin a gidan nan.
Yarinyar na kuma ba ruwan ki da ita ko irin habaicin da nake ji kinawa yar mutane kada na kara jin shi a gidan nan.
Idan ba haka ba wallahii rai zai baci don haka ke Kulu da hausi ga amanan wanan yarinyar gare ku da diyan ku na danka maku don Allah ku tayani bata tarbiya yadda ya dace.
Sukace insha Allahu Alhaji mu yarinyar nan bata tsare muna komai ba wallahi har yaran mu tunda tasan darajan mu.
Ko yaran nan suka dawo kasuwa har kofan su takee binsu tai masu sannu da kasuwa yaran su kuma tana haba haba dasu .
To yaron da yasan haka may zakace akan shi kuma sai fatan alheri yadda muma muka haifa itama Allah ya bata nata tasaka a cikin mu ba shi ke nan ba.
Yace nako gode dama nasan bazaku ki duk wani abinda na koso ba gidan nan indai har alheri ne da jin dadi na don haka Allah yai maku albarka suka ce amin a lokaci daya.
Yace ke kuma Rahama tarbiyan nan da iyayyen ki sukai maki ina son kici gaba dashi don shine tubalin zaman ki gidan nan.
Can sabuwa tace muma da ba a saka muna ba Allah yai muna shi sannan yaya zancen namu kayan dakin daka saya mata.
Cikin mamaki yace kayan daki kuma nine ma na saya mata kayan dakin nata ke nan.
Tace idan ba kai ka saya mata ba uban waya basu kudin sayen wanan kayan haka giredi masu kyau ?
Yace toni wallahi ko ku yarda ko kada ku yarda ban san komai ba akan wanan zancen.
Ita bata da mahaifa ne da zasuyi mata ban san lokacin da nace nikan anty na ta birni ce tai min komai ba wani ba.
Yace to kinji tai wani irin murguda baki tace haka dai akace kawai amma wata anty gare ta na birni da zatai mata wanan.
Yace to yanzu dai kowa yaji kowa ya tsaya a matsayin shi babba ya rike girman shi karami ma ya rike nashi.
Yace ku tashi ku tafi na gama magana na ni ban son wani abu kuma ya biyo baya.
Bayan fitan su sai ni ban fice daga dakin ba mama tace Rahama tashi zuwa dakin ki kinji.
Nace mama ni anan zan kwana tsoro nake ji ni daya a dakin nan kada sabuwa ta kashe ni.
Subbahanallahi inji su suna hada baki ita da mijin ta yace kin gani ko ta riga da ta tsorata a gidan nan da sabuwa.
Mama hausi tace kinga tashi na sa zuwaira ta tayaki kwana a dakin naki ba shi ke nan ba.
Daga ranan muka fara kwana ni da zuwaira a dakina kafin mu kwanta mukan yi hira na ta karanta muna labarai a littatafai.
Idan nace ina da wani matsala kuma nai karya girkin abinda zanci ma sai na so don idan su mama sunyi nasu suna saka min wani lokaci naci wani sain kuma nace na koshi.
Gashi ban gajiya gurin kama masu aiyukan su tun suna hanawa har sun gaji sun kyale ni ina yi da zuciya daya don yadda uwa da yar ta suke haka nake dasu su biyun.
Idan girki ya zo kaina a dadafe cikin takura nakeyin shi don Alhaji kan min nauyi a dakina har yanzu na kasa sake jikina dashi.
Sai ma kwana da zuwaira yafi min ace shine zai kwana a dakin duk da ba komai yake min ba sai lalashi da ban hakkuri wanda ni ban fahinci na maye ba.
Nayi kyau dani haskena yafito har dan kiba na kara gani shar fes dani idan kin gan ni.
Har kirjina dake a shafe sun fara tasowa yanzu sai dai duk wanan dadin da nake ci hankalina yana gurin Innata ko yaushe don yanzu ban san wake dibar mata ruwa ba wake mata talla wake mata aiki don kanni na duk yan maza ne.
Kaunata mace yar karama ce sosai ita aka yaye ba a haifi wani ba bayan ta ko may yasa inna bata kara haihuwa ba oho ?
Sallaman wani yaro ne a kofana rike da dakwalen kaji guda biyu a hannun shi sai kayan miya a wani leda mai yawa yace Alhaji ne yace ya kawo min.
Na karba yaron zai tafi nake cewa ya tsaya nazo na shiga daki na dauko mai biscuit na bashi har ya fara tafiya yace.
Amarya Alhaji ko na tsaya na taya ki gyaran kajin ?
Nace to shi ke nan dauki kaje a yanka bari na sa ruwan zafi kafin ka dawo ya juya dasu yafita.
Daidai lokacin da sabuwa tafito daga daki yaran ta sun fada mata an kawo kaji a sashe na yanzu sai ko ga yaron tafe dasu za, a yanka.
Tabi kajin da kallo har yaron ya fice daga gidan tanisa tace hum, umm ashe akwaita ke nan ?
Tare da yaron muka gyara ya kama min nayanka na zauka na shuga jajagen kayan miya kafin wani lokaci har guri ya dauki kamshi.
Miya ya kammalu na sauke na dora tuwo duk tare da yaron nan da yace min sunan shi habib ne dan gidan mai faci.
Sai yamma Alhaji ya shigo gidan daga shiyana ina zubawa yaron abinci naji muryan sabuwa tana cewa yau wani sabon cin amana ne da muna funci ya taso a gidan nan kuma ?.
Kamar yaya kuma ya tambaya tace duk munafuncin da kake a gidan nan nabawa yarinyar nan kayan dadi taci don ta yarda dakai ta kwantar da hankalin ta ka murje ra yadda kake so nagane ka.
Mu sai ka tura muna tuwo ita ko daga shinkafa sai taliya kake bata bata taba cin tuwo a gidan nan.
Ga kowa yai cirko cirko yana sauraren ta yace cikin daka tsawa ke sabuwa ban son sheri ni kike kira da munafuki yau.
In ma har munafunci ne ai ake nakeyi don ke ce munafukan kullun a gidan nan ba mai bani bani sai ke, ke, kenan kullun yin karya da ciwon yara ba ranan da zan fita baki karbi kwabona ba a gidan nan karyan yau daban na gobe daban.
Kaji kuma na sayo mata don itace mai girki su nake son ci shiyasa na sayo ke ranan da zan sayo bacewa kikiyi wai nabaki kufin ba ki sayo da kanki dana baki na dawo cewa kikayi n sace kudin ai.
Nawa nake ba wanan yarinyar a gidan nan ko bata nayi yadda nake bata sai dai tace na sayo mata duk abin da ya dace idan na fita.
Sabuwa nan ta hau borin kunya akan wai Allah dai ya kama ka yau kila ma har gashin dare kake kawo mata kai a dole gaka mijin yarinya ko ?
Sabuwa yau dai na gaji da sherin ki a gidan don haka na fada maki akan yarinyar nan zan iya saba maki kifice min daga gida.
Ahayye nanaye abin kunya wai aure da mara kwabo yace balle da kwabona ko kin manta kwabon kika gani a baya kika lake min da aike da komai har na yarda kika shigo gidan don haka yau ko wayai maki tsaye a gidan nan wallahi baki kwana min a gida.
Maimakon ta ci gaba da gudan da takeyi sai kuma jikin ta yai matukar sanyi sosai don tasan takan mashi fiye da haka amma bai taba yanke irin wanan hukuncin ba a kan ta sai yau kuma akan yar karamar yarinya.
Nan dai mama hausi ta saka bakin ta tace asha Alhaji da baka biye mata ba halin sabuwa ne kuma bako a gare ka yau.
Yace bari hausatu nagaji da sherin yarinyar nan yau ta kaini kat ne ita bata ji kunyan yaudara na ba sai nine zanji kunyan ta.
Ina kazan nan a kowan ku da yai girki sai da na saya mai aka girka min naci amma don wanan yarinyar na da girki na sayo zatai min sheri tace ai ba biyu ka saya muna ba kamar nata.
Bai kula ta ba ya shige dakin ta da kan shi ya kwaso kayan shi na kwan ciya ya fito daga dakin nata.
Hankali yai matukar tashi sosai a lokaci don nasan halin kauyen mu yazu labari zai sha banban ace daga shiga na na fara watsa matan gidan da na samu.
Hakana jiki ba kwari na dinga aiken wanan yaron da Allah ya hadani dashi yau yana kai wa kowa miyan duk sai da na kusa rabe naman don yawan gidan.
Mama hausi dake zaune tare da sarakan ta matan diyan ta su uku ta ce kungani ba yanzu ga naman ma karshen ta duk ta rabe shi gare mu.
Har ya fita zuwa sallah ya dawo bata bar gidan ba kamar yadda ya bukata haka yasa shi zuwa har kofanta ya daga labulen dakin yace.
Sabuwa may kike jira ne a gidan nan wai ai tunda gidan nan bana ubanki bane yau na fada maki wallahi baki kwana min a gida ki tafican gidan ku kikarata can.
Idan kuma kin ki fita yanzu na turo masu karfi aja min ke da karfin tsiya har waje.
Ganin haka tasan kuma da gaske yake yi yasa ta fara tattara kayan ta tana kuka wai saboda karamar yarinyar da kokwai bai aje da ita zai koreta gidan shi ita dake da yara bakwai a gidan.
Haka tafice daga gidan bakin ta bai mutu ba ta nufi gidan su a cikin dare kowana na kallon ta a wullakance.
Sai bayan tafiyan tane na fahinci ashe halinta ya ishi kowa agidan sai fadin aibunta kowa keyi.
Nan naji abubuwa da dama akan halinta ashe shiyasa take ganin an auro ni zan karbe mata power da take dashi a gidan da gurin mijin su.
****** ********* ******
Washegari tunda safe na shiga gurin mama bayan na gama aikin da nakeyi na kwashi kayan wankin ta sai aune tayi dani ina wanke tufafin ta.
Ta saka salati tana cewa haba amarya ai sai kina ace muna bautar dake ko iyayyen ki suka samu labari bazasu ji dadi ba gaskiya.
Nace daidai danta babba yana shigowa gidan dauke da dan karamin yaron shi a kafadan shi haba mama don nai maki wanki shine za, ace kina bautar dani kefa uwatace mama ba kishiya ba kamar yadda naji ana fada.
Ko a gida nike wankewa su innata har da mama kayan su idan yai dauda don wanan kayan da baida yawa ma.
Girgiza kan shi yayi yana cewa a ranshi ikon Allah yanzu baba wanan karamar yarinyar daya kwaso kurciya zalla haka may zai gane a gurin ta ne wai.
Nan dai dole uwar ta barni da wankin na wanke su fes na shanya na koma dakina ina jiran su bushe na kwashe mata.
Yaron nata mai suna yaya sani ya shigo dakin mahaifiyar tashi ya samu guri ya zauna daga gefen ta yace.
Mama dazun sai nake jin ki da amaryan ku a bakin rijiya kuna gaddama kuma akan wanki.
Tace bari kaidai ni kurciyar yarinyar na ya fara daure min kai wallahi bata tasan kyashi ba ko hassada a rayuwan ta komai haka zata zage tayi shi tsakani da Allah.
Yace haka naji nima sai dai mama gaskiya sai kunyi da gaske gurin rike amana tun da dai ba sanin ciwon kan ta tayi ba yarinyar gashi uwarta tai mata tarbiyan da ya dace duk uwa ta gari taiwa yarta.
Tace insha Allahu haka nake kokarin ganin nayi yo har ma may mutum zai cuta a wanan gurin kuma ?
Nan dai sukai ta zancen su har suka fado kan maganan sabuwa da irin hallin gallaza masu data dinga yi a zamanin ta a gidan.
Mama hausatu tace don yaran ai ayi hakkuri ta dawo dakin ta gashi kuma bazan so ace don wanan yarinyar tabar gidan nan ba.
Kada azo a shafa wa yar mutane labbo bata ci ba tasha akama zarginta ga banza kasan haln mutanen yanzu da dauka su dagwarawa kan su maganan da bata shafe su ba.
Dan nata yace hakan yana da kyau mama indai wanan mara mutuncin ne aiko ta dawo ba dainawa zatayi ba.
Gara dai tadawo dakin ta din zaifi don kaga yanzu idan tafice gidan nan nauyin diyan ta duk akaina zai dawo gasu ba tarbiya ke garesu ba.
Yadda mama hausatu tai shawara da danta haka akayi da yamma da Alhaji yadawo gida ta sanya shi a gaba tana bashi baki akan yayi hakkuri ya daure sabuwa ta dawo dakin ta hakana ko don yaranta.
Yace wai hausatu ke ce ke auren ta ko ni da zaki isheni naje nayo bikon ta ina indai sabuwa ce koke bata bari a gidan da tsufanki kuwa ?
Mama hausatu tace kadai yi hakkuri Alhaji kodan yaran ta ta dawo taci gaba da duba abinta.
Yace yara ai bada su tazo ba anan ta samay su kuma a gidan iban su suke ko ?
Ya ja tsaki ya dauki buta ya fice daga gidan.
Gaba daya yaran Sabuwa sun ishi matan gidan da rashin kunya idan ka cire shi Alhajin da basuyi a gaban shi don tsaye yake akan iyalin shi.
Don haka shi zaman su ma babu uwar su a gidan ko a kwallan shi bai taba damuwan shi ba don dan ficewan ta har ya samu natsuwa tare dashi.
Satin ta daya shiru babu labarin dawowan ta gidan har wanan lokacin ganin maganan wasa zai zama gaskiya yasa.
Mama hausatu samun wani dan uwan Alhaji kuma amin shi akan zancen sabuwa din don yaran sun ishesu ba hutu gareta.
Bayan sun gaisa ne tayi mashi bayanin komai akan matsalan da ake ciki tsakanin sabuwa da Alhajin.
Malam shehu yace a gaskiya ba yau ba Alhaji hakkuri yake da al, amarin sabuwa ke ma kin sani .
Don ko jiya muna tare nan dashi yake min bayanin komai don iyayyen ta da yan uwan ta sun damay ni da zariya agida.
Amma tunda kinzo ba komai insha Allahu anjima zan samay shi muyi magana idan ya dawo.
Mama tace don Allah malam a taimaka a sa baki ga alamarin a gyara tun bai baci ba kodon yara.
Daga haka sukai sallama ta tafi tana godiya don sun saba dashi sosai akan matsalar gidan su.
Duk yadda ya raya da Alhaji akan yai hakkuri Sabuwa ta dawo dakin ta yaki yarje mashi.
Don haka ya kyale shi malam shehu ya nemi wani amin shi da magariba suka shirya sai gidan wan sabuwa inda take zaune.
Lokacin da suka isa gidan sun samu wan nata baya gida dole suka dan jira shi don ba nisa ya tafi ba.
Bayan sun gaisa ne suke cewa da shi dama mun biyo bayan sabuwa ne don Allah ayi hakkuri ta koma dakin ta hakana.
Don sabani akasamu kuma yanzu kowa ya gane kuresa don ko tsakanin harshe da hakori ana samun sabani balle mutum da mutum don gaskiya iya hakkuri kukan ku kun sani Alhaji garbati yana iya hakkurin shi da sabuwa a gidan shi.
Yayan nata yace hakane amma naso ace shi Alhajin ne yazo nan da kan shi don na kara bashi hakkuri saboda nima dan zaman ta cikin iyalina nasan yana hakkuri sosai.
Malam shehu ya jinjina kan shi yace hakane amma da zuwan Alhajin da namu duk kusan guda ne don a madadin shi muka zo mu.
Koma may nene ai yanzu ta san ta fara kaishi bango don baka kallon babban mutum kamar Alhaji garba tsakiya iyalin shi tace mai munafuki.
Yayan nata yace don Allah akara bashi hakkuri kafin nazo har gidan na bashi.
Yayan yace kafin ku tafi bari na kirata taji da kan ta don ku kara ja mata kunne mace da girman ta kamar Sabuwa ace wai ta saura yaji don rashin hakkuri irin nata.
Bai jima ba suka fito a tare yana gaba tana bayan shi ta samu guri daga gefe ta tsugun na.
Yayan nata yace sabuwa ga malam shehu nan sunzo bikon auren ki a madadin maigidan ki.
Ta dukar da kai cikin kunya da nauyi zatayi magana malam shehu yace da ita.
Haba Sabuwa yanzu lokaci yayi da za, a san girma ya kama a daina wasu halaiya kuma.
Don Alhaji ya auro wanan yarinyar bai kamata ace daga gareki ne ba a samu zaman lafiya ba idan kin yi tunanen irin zaman da kukayi ke dashi har takai kina ci masa mutunci a tsakiyan sarakan shi hakana.
Don haka idan kin koma dakin ki da fatan komai zai sauya daga gareki yanzu shiga ki dauko kayan ki basai gobe ba mutafi na mayar dake dakin ki.
Zatai magana yayan nata dake zaune a gefe yace ya katseta cikin bacin rai da cewa .
Kin sani sarai bana son tashin tashin kije ki shiryo ku tafi.
Ba don taso ba ta tashi ta shiga ciki can sai gata tafito da lulubinta dauke da dan ledan kayan ta suka kama hanya.
Ko da suka iso gidan sun samu Alhaji a kofan gida shi da baba salla zaune suna hira.
Yacewa Sabuwa shiga gida
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10 Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22Chapter 23Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32Chapter 33Chapter 34Chapter 35Chapter 36Chapter 37Chapter 38Chapter 39Chapter 40Chapter 41Chapter 42Chapter 43Chapter 44Chapter 45Chapter 46Chapter 47Chapter 48Chapter 49Chapter 50Chapter 51Chapter 52Chapter 53Chapter 54Chapter 55Chapter 56Chapter 57Chapter 58Chapter 59Chapter 60Chapter 61Chapter 62Chapter 63Chapter 64Chapter 65Chapter 66Chapter 67Chapter 68Chapter 69Chapter 70Chapter 71Chapter 72Chapter 73Chapter 74Chapter 75Chapter 76Chapter 77Chapter 78Chapter 79Chapter 80Chapter 81Chapter 82Chapter 83Chapter 84Chapter 85Chapter 86Chapter 87Chapter 88Chapter 89Chapter 90Chapter 91Chapter 92Chapter 93Chapter 94Chapter 95Chapter 96Chapter 97Chapter 98Chapter 99Chapter 100Chapter 101Chapter 102Chapter 103Chapter 104Chapter 105Chapter 106Chapter 107Chapter 108Chapter 109Chapter 110Chapter 111Chapter 112Chapter 113Chapter 114Chapter 115Chapter 116Chapter 117Chapter 118Chapter 119Chapter 120Chapter 121Chapter 122Chapter 123Chapter 124Chapter 125Chapter 126Chapter 127Chapter 128Chapter 129Chapter 130Chapter 131Chapter 132Chapter 133Chapter 134Chapter 135Chapter 136Chapter 137Chapter 138Chapter 139Chapter 140Chapter 141Chapter 142Chapter 143Chapter 144Chapter 145Chapter 146Chapter 147Chapter 148Chapter 149Chapter 150Chapter 151Chapter 152Chapter 153