dayan su ba wanda yai magana sai hajiya ce can tai karfin halin cewa .
Don bamu san yadda ka samu ba shine zai hana mu yin magana idan kayi rashin adalci ko may ?
Yace hajiya may ye rashin adalci anan don na bawa uwargidana zabi akan girman da Allah ya bata a gidana.
Nakuma bata zabi amatsayin ta wacce ta taimaka ma rayuwana tun ban san ko mai ba na hanyan neman kudi har yakai ta fara lurar dani yadda zan zamo mai dogaro da kaina har zuwa wanan lokacin.
A fusace hajiyan shi, take cewa kace ma da kudin ta ka zama haka a yau.
A gadarance yace kusan hakane gaskiya don kudin ta da nawa ne muka hada nasai form na sai sauran abubuwan da ya sace nayi kafin na samu na kai ga appointment dina.
A lokacin hajiya ke kin sani Abba bai yarda da zancen aikin da nake nema ba yafi da son na kama kasuwanci kawai.
Ashe don haka hajiya yau komay nai ma sa,adatu kaman ma ban mata komai bane daga cikin gudun mawan da tai min a rayuwana.
Don haka yau hajiya a gaban ki ina son kowacen su ta sani cewa Sa, ade da suke gani ba abin da zanyi wasa ko sakaci da ita bane arayuwa na.
Don haka wace zata iya zama dani da mata ta zauna don a tare kuka gan mu da ita auren mu va zai sa na watsar da mata na mai tausayina mai sona da kauna na wace ta san zafina da tausayawa rayuwana.
Hajiya ta cabe da cewa ai ka karasa kace wace ta haife ka ta san zafin cikin ka da goyon ka.
Aa hajiya bata kai can ba amma dai ina son su fahinci darajan ta a guri na yafi karfin yadda suke tsanmani a yanzu don naga suna son su wuce limite din su agidan nan.
Duk wace bata iya zama a gurin da na ajeta hanya a bude yake gareta zata iya komawa inda tafito don babu dole a gareta.
Matata dai ce ba zan taba wullakanta taba akan ko wacen su insha Allahu.
Kuma ina son ku sani hajiya da kuke kai karana kona matana a gare ta ga hajiya ga ku duk wace ta kara kai karan dayan mu gurin hajiya a gidan nan kan al,amarin da ya shafe ni ko Sa,ade.
Mace ta sani kuma ta rike a kanta zan bata mamaki kwarai ga irin matakin da zan dauka akan ko wacece a gidan.
Haka ya isa please ban san may kuke so dani ba kowacen ku nan tasan zamana da matana tun farko haka kuma kuka amince da zaku iya zama damu a hakan da muke ban auro ku don na wulakanta matana ba don ina son abina kowan ku kuma ta sab da hakan ta amice don haka yanzu kune kma kuke son bi ta hanyan mahaifiyana don ku cuta mata kuma cutawa mahaifiya don Alhakin yarinyar mutane ya haukan magaifiyana.
Saboda may zakuyi muna wana mugun sakkaiyan hakan kuna amfani da mahaifa na don ganin an cutatawa yar mutane saboda hakkurin ta.
Kada kuyi tsanmani ban san abubuwan dake gudana a gidan nan ba na bar kowa tana abinda ta ga dama a gidana.
Akwai watarana yaba tafe ranan da zan dauki mataki daidai da laifin kowan ku amma dai ina mai kara ja maku kune ga abu biyu zuwa uku.
Na farko shine mai son zaman lafiya ya bar hadani da matata da iyayye na fada.
Sai kuma ina gargadin ku da ku daina shiga harkan Sa,ade ku barta taji da lalurar da Allah ya jarrabe ta da shi.
Don haka zance shiya da kuke cewa ta zaba ta bar maku wanda bakwa so zaku iya komawa can dakunan ku da kuka fito don yau idan Sa, ade tace min bata bukatan zama da kowacen ku a cikin gidan nan ya ya tabbata hakan a gare ni.
Aiko na hajiyan shi ta amshe da cewa tau issahe akan wanan figagan matar naka mutu kwakwai rai kwakwai kake wanan magana.
May yarinyar nan tai maka hakane har idon ka da zuciyar ka ya rufe yau a gabana kake wanan magana.
Lalai Sa,adatu kin gwada min ki kai kin kai matakin daba naki ba a gidan nan tunda har yau Alhaji karami ya rufe idon shi a gabana yake wanan magana haka.
Hajiya ya kamata ki sani yau idan haka ya kasance a gidajen auren yan uwan mu mata ba zaki ji dadi haka ba, muma ba zamuji dadi ba don may hajiya ba zaki daina wanan halin ba ko don kwanciyan hankalin diyan ki mata dake gidan mazajen su suna aure.
Au to lalai abin har yakai zakaiwa yan uwanka mata baki akan matar son ka duk ka haukace min yau don na taba ko.
Ai kafin kayi naka, naga wata fitsararar yarinyar da matar ka ta dauko ta aje a gidan don isa da mallaka ra fara nuna min fitsara don samun wuri.
Ta juya gurin antyna tana cewa ban son ganin wanan yarinyar a gidan nan ta gagawan barin gidan nan tun ban dauki mataki ba a kan ta ?
Hajiya wanan yarinyar yar uwar Saade ce nina bada bakin ta dauko ta nan don ta samu mai taimaka mata ga halin da take ciki tana bukatan taimako ?
Kafin suci gaba da magana sai ga maigidan ta ya kirata yana tambayan ta tana inane wai.?
Ta kasa bashi amsa don tasan ya hanata zuwa gidan dan nata saboda wanan halin da take zuwa tayi.
Kwata kwata bata kaunan zaman Sa,ade da danta don acewan ta kullun wai ta girmay wa mijin nata shi yasa take masu wayo.
Ta manta cewa itama tana da diya mata dake aure a wanu gidan har su uku bata tunanen cewa abinda take wa yar mutane zai iya faruwa akan diyan ta.
Mata bamu tunanen cewa mu uwaye ne masu diya duk abinda ka shuka shine kake girma a rayuwan ka.
Muryan mijin nata ne ke fada mata cewa tazo gida ga Aisha, yar su ta dawo gida da matsala.
Wanan maganan da taji ne yasa ta dafe kirjin ta tana cewa zata tafi amma zata dawo don bata karasa maganan da ya kawo ta ba.
****** ********* ******
******
Tun da farar safiya muryan Jatau ne ya tayar da mutanen gidan da balain da yazo masu.
Yake cewa mama tafito bazai yarda ba tasan yarta honko ne ta dauka takai mashi gidan shi don an raina shi.
Shi za, aiwa wullakanci ko may da za, a dauko honkon akawo maigida don an mai dashi tsoho.
Gaban mama ne yai mugun faduwa haka ta daure tafito zani na faduwa mata gashi har mutane sun fara taruwa don gulma.
Tace a ranta bari ta rufe ido tai mai na mahaukaci kawai a wuce gurin gaba daya.
Ta na lekowa take cewa kai Jatau kada ka dauka ko tsoron ka ake ji duk haukan da kakeyi kyaleka na keyi.
Mata kace kana so mata kuma na baka banga dalilin da zaka taso tsofai tsofai dakai ba kazo muna kana wanan magana abin kunya.
Tace ankai maka honko din sai ka turo min yata yau din nan na fasa auren bazata zauna ba a gidan ka.
Da Jatau yaga mama ta fishi iskanci da hauka dole ya kwantar da nashi haukan yace baki da hurimin daukan min mata, don mata zamana take yanzu.
Matar ka da kace honko ce ai daga yau ta gama zama dakai a gidan ka don dama kudin bazawara ka biya bana budurwa ba.
Yace a shekeke yo ina budurwan take anan kin kai min hinkon diyar ki aiko sai ga su Rukaiyya sun fito daga cikin gida.
Mama ta juya garesu tana cewa maza kuje kuzo min da Lawisa gidan nan yanzun nan.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE, ,
IDAN KIN BIYA KIKA TURAWA WANI NA BARKI DA NAUYIN AMANA A KAN KI YAR UWA
18
Anty na barin falon ta dawo part din ta samay mu zaune inda ta bar mu ganin yanayin mu kawai zai sa kagane rayukan mu a bace yake dagani har mama Altine a lokacin.
A kasa nake zaune kusa da dima diman kujerun dake a falon ta samu kujeran dake daf dani ta zauna .
Sai bayan ta zaunane ta dafa ni a hankali tare da ambatan sunana ta riko min hannuwa na ta hade da nata guri daya.
Jin ta ambaci sunana da irin rikon da taimin yasa na mayar da hankalina gare ta tare da kura mata ido ina sauraren ta.
Rama ina son ki kwantar da hankalinki ki dinga nazarin kowa na gidan da idon basira.
Kamar yadda kiia san duk wani gida mai iyali akwai irin kalubalin da gidan ke fuskan ta hakane ma ko a wanan gidan namu.
Don gaba daya matan gidan da iyayyen gidan kalubalin su akaina yake wanda ba komai ne yakawo haka ba sai ganin Allah ya dorani kan mijina da kuma su baki daya a gidan.
Wanda ba komai ya kawo min shi ba sai hakkurina da kuma halaiyana na gari yasa na cin ma wanan falalan haka.
Rama ina so daga yau ki kasance mai hakkuri ga al, amarin gidan nan don zaki ji ko kiga abubuwa da dama na cin fuska a gamay dani amma dole sai kin daure ki kawar da kan ki ga hakan.
Babu inda zaki muna nan tare da ke har lokacin da Allah zai nufa ki kara yin wani aure idan Allah ya yarda.
Don haka kada ki jefa kanki cikin fitina da rigigimun gidan nan a kaina.
Nasan dazu ranki ya baci yadda hajiya bata ji nauyi idon ku ba a matsayin ku na yan uwana tana tozarta ni a gaban ku yadda taso ta saba da yi min hakan ne tun farkon aurena da danta.
Amma duk wanan ni bai taba damuna don dai nasan Allah kadai yakai ya rabani da heart beat ba wai wani mahaluki ba.
Nan dai taita min nasiha mai tsuma zuciya akan rayuwa har naji gaba daya ma zaman duniya ba dadi a cikin sa.
Washe gari kafin wani lokaci na gama gyaran ko ina inda ya dace a gyara sai na dora girki guri ya kaure da kamshi.
Ina gamawa na shiga nai wanka na saka daya daga cikin dogayen rigunan da aka sayo min na gyara na fito tsab dani.
Na dade a gaban mirro ina kallon yadda halintan jikina ya nuna min sura na a wanan lokacin.
Gaba daya dan lokaci guda na sauya nayi matukar kyawo na zama wata young fresh dani .
Dakin Anty na nufa don na tambaye ta ko zata ci abinci dana gama dafawa a lokacin.
Zaune na samay ta a saman sallaya da alama ta idar da sallah ne a lokacin .
Jin shigowana da yasa ta dan mayar da hankalinta ga kofan ido ta tsura min har na karaso inda take zaune durkusawa nayi daidai inda take zaune ina gaida da ita.
A daidai lokacin da ta shafa ta dago kai tana min murmushi take cewa dani dama yanzu nake son kiranki don zamu dan fita zuwa unguwa sai dai ba mai nisa bane .
Na sharada zamu tafi gidan sister din maigidan ta haihu yau kwana hudu ke nan.
Sai da na tabbatar da ta gama magana nake cewa Allah ya raya tare da cewa dama nazo na fada maki na gama abinci ko zakici yanzu ?
Tace da hakan nayi zaifi min don ina dan jin yunwa dama kin ga sai na fita da nauyi.
Dama fitan nawa kamar fitan dole zanyi shi kin san alamarin dangin miji yadda yake rashin zuwa zai iya jawo min matsala.
Kallon ta nayi ta bani tausayi ga cikin ta ya girma kwarai a lokacin gashi tana matukar karfin hali sosai a lokacin.
Abincin na kawo mata ta zauna nan inda take zaune a kasa taci sai dai ba sosai ba don yanayin ta ba dadi gare ta.
Na tace mu fasa fita sai zuwa gobe idan ta dan kara jin sauki amma sai gashi ina idar da Sallah ta shigo inda muke tana ce min na zo mu tafi mu samu mu dawo in time.
Da sauri na mike tare da dan gyara fuskana na saka hijjab a jikina sai naga anty taja ta tsaya tana kallona wani irin.
Nima dai din kallonn ta nake don ban san wanan kallon da take min ba sai na ga tayi murmushi ta nufo ni tare da daukan gyalen rigan dake jikina tana mika min take cewa haba ko dai ni macen aure ai kinga shigan dake jikina ko.
Dole ba don naso ba na cire hijjab din na yafa gyalen kayan a kaina na fito kamar wata yar birni dani don ni kaina nasan na canza sosai.
Tana gaba ina biye da ita a bayan ta rike da hand bag din ta muna fitowa haraban gidan ne mukai kicibis da maigidan wanda da alama dawowan shi ke nan daga wani guri a lokacin.
Yana ganin ta ya dan ja ya yatsaya tare da jingina jikin shi a jikin motar daya fito daga ciki.
Jikin shi na saye da wani yadin maza mai laushe da daukan ido fari kal zaka iya gano yar farar singlet din ke ta cikin jikin shi
Da sauri na basu guri zuwa gurin motan da nake tunane itace motar ta da muka taba fita da ita.
Volvo ce yafito daga ciki ban san yaya akayi ina can tsaye dan nesa kadan dasu na kurawa kasa ido ina faman tunanen yadda in mota tashigo kauyen mu zamu dinga binta har zuwa kofan gidan da mai shi zai tsaya.
Sai muryan tane ya katse na dago da sauri ina kallon inda suke tsaye gaba dayan su shi da ita sun tsura min ido inda nake tsaye ina tunane.
Tace zo a wanan zamu tafi , zaifi muna saukin tafiya ai da sauri na dago na nufo inda suke tsaye yana kokarin jayewa ya bata guri ta shiga motan ne nake cewa cikin yar murya ina wuni.
Kamar baijini ba don bai amsa min ba sai kokari yake yaga matar shi ta zauna da kyau a cikin motan yana fadin don Alkah ki ja sannu ban son gudu ko sauri tace ina naga lafiyan gudu yanzu heart beat.
Tace zagayo ki zauna mu tafi da sauri na kara na shiga motan da ta bude min dayan gefen na shiga.
Ina jin tana mashi horn a inda yake tsaye hannayen shi harde cikin dan uwa yana kallon yadda take jan motan.
Daga inda nake na dan saci kallon su naga yadda suke nunawa juna tsatsan kauna zalla tsakanin su.
Wani kamshi da sayin ne suka ziyarci hanci na da jikina a lokaci guda wanda ban san lokacin da na sake sanyayan ajiyan zuciya ba don yanayin da naji.
Tace yaya dai Rama na naga tun dazu sai faman tunane kike yi may ke faruwa ne wai ?
Idanuwa na lunshe tare da sake dan murmushi nake cewa anty sauyin rayuwa ne kawai nake tunane da ina kauye yaushe zan taba wanan sabon rayuwan da nake ciki.
Murmushi tayi tare dayiwa wata mota da naji tai mata horn ita ta mayar masu da horm din tana cewa ya dauka ko maigidan ne da kan sa a ciki .
Yanzu ke har kin ganki a wani rayuwa ke nan Rama naji ta tambaye ni ta sake wancan maganan da take na motar da ta wuce gaban mu.
Nace anty idan da nayi auren gidan Jatau ai da ko jaki sai nayi shekara ban gani don ba fita ake a gidan shi ba.
Dariya anty tasa tace kai ai da jin sunan shi kasan mutanen dauri ne ba na yanzu ba wai Jatau.
Wani gida ta tsaya tana horn aka bude mata gidan ta danna kan motar ta zuwa cikin gidan.
Kishiryata zulfa ce tsaye da wata suka kuro muna idon su har muka kawo inda suke basu daina kallin mu ba suna son ganin ko maigidan ne a motar.
Can ta fito daga ciki sai naga sun kawar da kan su ga kallon su basu dade ba naga Zulfa ta juya tana kokarin shiga motar ta.
Muna kawowa wace suke tare tsaye bata da niyya muna magana naji Anty na cewa Samira yaya yau ?
A, a uwargida yau kece da kanki a motar oga wani kaya sai amali ke nan ?
Murmushi anty tayi mata muka sa kai zuwa cikin gidan gidan ya kaure da hayani zaka fahinci akwai mutane a gidan.
Wani daki muka nufa inda nake zaton nan ne dakin matar gidan da muka zo gayarwa din.
Da sallama muka sa kai a dakin yayin da matan dake dakin suka kuro muna ido su.
Matar suna da matukar kama da mijin anty sosai dagani basai anfada ma ba don jini yana aiki sosai.
Tun ba su gaisa ba take cewa a, a matar mulki an samu fitowa ke nan dai ai na dauka mulkin ba zai barki zuwa ganin baby ba ai.
Tace ai kin san ko don nazo naga dana zan zo
Showing 63001 words to 66000 words out of 456145 words
Don bamu san yadda ka samu ba shine zai hana mu yin magana idan kayi rashin adalci ko may ?
Yace hajiya may ye rashin adalci anan don na bawa uwargidana zabi akan girman da Allah ya bata a gidana.
Nakuma bata zabi amatsayin ta wacce ta taimaka ma rayuwana tun ban san ko mai ba na hanyan neman kudi har yakai ta fara lurar dani yadda zan zamo mai dogaro da kaina har zuwa wanan lokacin.
A fusace hajiyan shi, take cewa kace ma da kudin ta ka zama haka a yau.
A gadarance yace kusan hakane gaskiya don kudin ta da nawa ne muka hada nasai form na sai sauran abubuwan da ya sace nayi kafin na samu na kai ga appointment dina.
A lokacin hajiya ke kin sani Abba bai yarda da zancen aikin da nake nema ba yafi da son na kama kasuwanci kawai.
Ashe don haka hajiya yau komay nai ma sa,adatu kaman ma ban mata komai bane daga cikin gudun mawan da tai min a rayuwana.
Don haka yau hajiya a gaban ki ina son kowacen su ta sani cewa Sa, ade da suke gani ba abin da zanyi wasa ko sakaci da ita bane arayuwa na.
Don haka wace zata iya zama dani da mata ta zauna don a tare kuka gan mu da ita auren mu va zai sa na watsar da mata na mai tausayina mai sona da kauna na wace ta san zafina da tausayawa rayuwana.
Hajiya ta cabe da cewa ai ka karasa kace wace ta haife ka ta san zafin cikin ka da goyon ka.
Aa hajiya bata kai can ba amma dai ina son su fahinci darajan ta a guri na yafi karfin yadda suke tsanmani a yanzu don naga suna son su wuce limite din su agidan nan.
Duk wace bata iya zama a gurin da na ajeta hanya a bude yake gareta zata iya komawa inda tafito don babu dole a gareta.
Matata dai ce ba zan taba wullakanta taba akan ko wacen su insha Allahu.
Kuma ina son ku sani hajiya da kuke kai karana kona matana a gare ta ga hajiya ga ku duk wace ta kara kai karan dayan mu gurin hajiya a gidan nan kan al,amarin da ya shafe ni ko Sa,ade.
Mace ta sani kuma ta rike a kanta zan bata mamaki kwarai ga irin matakin da zan dauka akan ko wacece a gidan.
Haka ya isa please ban san may kuke so dani ba kowacen ku nan tasan zamana da matana tun farko haka kuma kuka amince da zaku iya zama damu a hakan da muke ban auro ku don na wulakanta matana ba don ina son abina kowan ku kuma ta sab da hakan ta amice don haka yanzu kune kma kuke son bi ta hanyan mahaifiyana don ku cuta mata kuma cutawa mahaifiya don Alhakin yarinyar mutane ya haukan magaifiyana.
Saboda may zakuyi muna wana mugun sakkaiyan hakan kuna amfani da mahaifa na don ganin an cutatawa yar mutane saboda hakkurin ta.
Kada kuyi tsanmani ban san abubuwan dake gudana a gidan nan ba na bar kowa tana abinda ta ga dama a gidana.
Akwai watarana yaba tafe ranan da zan dauki mataki daidai da laifin kowan ku amma dai ina mai kara ja maku kune ga abu biyu zuwa uku.
Na farko shine mai son zaman lafiya ya bar hadani da matata da iyayye na fada.
Sai kuma ina gargadin ku da ku daina shiga harkan Sa,ade ku barta taji da lalurar da Allah ya jarrabe ta da shi.
Don haka zance shiya da kuke cewa ta zaba ta bar maku wanda bakwa so zaku iya komawa can dakunan ku da kuka fito don yau idan Sa, ade tace min bata bukatan zama da kowacen ku a cikin gidan nan ya ya tabbata hakan a gare ni.
Aiko na hajiyan shi ta amshe da cewa tau issahe akan wanan figagan matar naka mutu kwakwai rai kwakwai kake wanan magana.
May yarinyar nan tai maka hakane har idon ka da zuciyar ka ya rufe yau a gabana kake wanan magana.
Lalai Sa,adatu kin gwada min ki kai kin kai matakin daba naki ba a gidan nan tunda har yau Alhaji karami ya rufe idon shi a gabana yake wanan magana haka.
Hajiya ya kamata ki sani yau idan haka ya kasance a gidajen auren yan uwan mu mata ba zaki ji dadi haka ba, muma ba zamuji dadi ba don may hajiya ba zaki daina wanan halin ba ko don kwanciyan hankalin diyan ki mata dake gidan mazajen su suna aure.
Au to lalai abin har yakai zakaiwa yan uwanka mata baki akan matar son ka duk ka haukace min yau don na taba ko.
Ai kafin kayi naka, naga wata fitsararar yarinyar da matar ka ta dauko ta aje a gidan don isa da mallaka ra fara nuna min fitsara don samun wuri.
Ta juya gurin antyna tana cewa ban son ganin wanan yarinyar a gidan nan ta gagawan barin gidan nan tun ban dauki mataki ba a kan ta ?
Hajiya wanan yarinyar yar uwar Saade ce nina bada bakin ta dauko ta nan don ta samu mai taimaka mata ga halin da take ciki tana bukatan taimako ?
Kafin suci gaba da magana sai ga maigidan ta ya kirata yana tambayan ta tana inane wai.?
Ta kasa bashi amsa don tasan ya hanata zuwa gidan dan nata saboda wanan halin da take zuwa tayi.
Kwata kwata bata kaunan zaman Sa,ade da danta don acewan ta kullun wai ta girmay wa mijin nata shi yasa take masu wayo.
Ta manta cewa itama tana da diya mata dake aure a wanu gidan har su uku bata tunanen cewa abinda take wa yar mutane zai iya faruwa akan diyan ta.
Mata bamu tunanen cewa mu uwaye ne masu diya duk abinda ka shuka shine kake girma a rayuwan ka.
Muryan mijin nata ne ke fada mata cewa tazo gida ga Aisha, yar su ta dawo gida da matsala.
Wanan maganan da taji ne yasa ta dafe kirjin ta tana cewa zata tafi amma zata dawo don bata karasa maganan da ya kawo ta ba.
****** ********* ******
******
Tun da farar safiya muryan Jatau ne ya tayar da mutanen gidan da balain da yazo masu.
Yake cewa mama tafito bazai yarda ba tasan yarta honko ne ta dauka takai mashi gidan shi don an raina shi.
Shi za, aiwa wullakanci ko may da za, a dauko honkon akawo maigida don an mai dashi tsoho.
Gaban mama ne yai mugun faduwa haka ta daure tafito zani na faduwa mata gashi har mutane sun fara taruwa don gulma.
Tace a ranta bari ta rufe ido tai mai na mahaukaci kawai a wuce gurin gaba daya.
Ta na lekowa take cewa kai Jatau kada ka dauka ko tsoron ka ake ji duk haukan da kakeyi kyaleka na keyi.
Mata kace kana so mata kuma na baka banga dalilin da zaka taso tsofai tsofai dakai ba kazo muna kana wanan magana abin kunya.
Tace ankai maka honko din sai ka turo min yata yau din nan na fasa auren bazata zauna ba a gidan ka.
Da Jatau yaga mama ta fishi iskanci da hauka dole ya kwantar da nashi haukan yace baki da hurimin daukan min mata, don mata zamana take yanzu.
Matar ka da kace honko ce ai daga yau ta gama zama dakai a gidan ka don dama kudin bazawara ka biya bana budurwa ba.
Yace a shekeke yo ina budurwan take anan kin kai min hinkon diyar ki aiko sai ga su Rukaiyya sun fito daga cikin gida.
Mama ta juya garesu tana cewa maza kuje kuzo min da Lawisa gidan nan yanzun nan.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE, ,
IDAN KIN BIYA KIKA TURAWA WANI NA BARKI DA NAUYIN AMANA A KAN KI YAR UWA
18
Anty na barin falon ta dawo part din ta samay mu zaune inda ta bar mu ganin yanayin mu kawai zai sa kagane rayukan mu a bace yake dagani har mama Altine a lokacin.
A kasa nake zaune kusa da dima diman kujerun dake a falon ta samu kujeran dake daf dani ta zauna .
Sai bayan ta zaunane ta dafa ni a hankali tare da ambatan sunana ta riko min hannuwa na ta hade da nata guri daya.
Jin ta ambaci sunana da irin rikon da taimin yasa na mayar da hankalina gare ta tare da kura mata ido ina sauraren ta.
Rama ina son ki kwantar da hankalinki ki dinga nazarin kowa na gidan da idon basira.
Kamar yadda kiia san duk wani gida mai iyali akwai irin kalubalin da gidan ke fuskan ta hakane ma ko a wanan gidan namu.
Don gaba daya matan gidan da iyayyen gidan kalubalin su akaina yake wanda ba komai ne yakawo haka ba sai ganin Allah ya dorani kan mijina da kuma su baki daya a gidan.
Wanda ba komai ya kawo min shi ba sai hakkurina da kuma halaiyana na gari yasa na cin ma wanan falalan haka.
Rama ina so daga yau ki kasance mai hakkuri ga al, amarin gidan nan don zaki ji ko kiga abubuwa da dama na cin fuska a gamay dani amma dole sai kin daure ki kawar da kan ki ga hakan.
Babu inda zaki muna nan tare da ke har lokacin da Allah zai nufa ki kara yin wani aure idan Allah ya yarda.
Don haka kada ki jefa kanki cikin fitina da rigigimun gidan nan a kaina.
Nasan dazu ranki ya baci yadda hajiya bata ji nauyi idon ku ba a matsayin ku na yan uwana tana tozarta ni a gaban ku yadda taso ta saba da yi min hakan ne tun farkon aurena da danta.
Amma duk wanan ni bai taba damuna don dai nasan Allah kadai yakai ya rabani da heart beat ba wai wani mahaluki ba.
Nan dai taita min nasiha mai tsuma zuciya akan rayuwa har naji gaba daya ma zaman duniya ba dadi a cikin sa.
Washe gari kafin wani lokaci na gama gyaran ko ina inda ya dace a gyara sai na dora girki guri ya kaure da kamshi.
Ina gamawa na shiga nai wanka na saka daya daga cikin dogayen rigunan da aka sayo min na gyara na fito tsab dani.
Na dade a gaban mirro ina kallon yadda halintan jikina ya nuna min sura na a wanan lokacin.
Gaba daya dan lokaci guda na sauya nayi matukar kyawo na zama wata young fresh dani .
Dakin Anty na nufa don na tambaye ta ko zata ci abinci dana gama dafawa a lokacin.
Zaune na samay ta a saman sallaya da alama ta idar da sallah ne a lokacin .
Jin shigowana da yasa ta dan mayar da hankalinta ga kofan ido ta tsura min har na karaso inda take zaune durkusawa nayi daidai inda take zaune ina gaida da ita.
A daidai lokacin da ta shafa ta dago kai tana min murmushi take cewa dani dama yanzu nake son kiranki don zamu dan fita zuwa unguwa sai dai ba mai nisa bane .
Na sharada zamu tafi gidan sister din maigidan ta haihu yau kwana hudu ke nan.
Sai da na tabbatar da ta gama magana nake cewa Allah ya raya tare da cewa dama nazo na fada maki na gama abinci ko zakici yanzu ?
Tace da hakan nayi zaifi min don ina dan jin yunwa dama kin ga sai na fita da nauyi.
Dama fitan nawa kamar fitan dole zanyi shi kin san alamarin dangin miji yadda yake rashin zuwa zai iya jawo min matsala.
Kallon ta nayi ta bani tausayi ga cikin ta ya girma kwarai a lokacin gashi tana matukar karfin hali sosai a lokacin.
Abincin na kawo mata ta zauna nan inda take zaune a kasa taci sai dai ba sosai ba don yanayin ta ba dadi gare ta.
Na tace mu fasa fita sai zuwa gobe idan ta dan kara jin sauki amma sai gashi ina idar da Sallah ta shigo inda muke tana ce min na zo mu tafi mu samu mu dawo in time.
Da sauri na mike tare da dan gyara fuskana na saka hijjab a jikina sai naga anty taja ta tsaya tana kallona wani irin.
Nima dai din kallonn ta nake don ban san wanan kallon da take min ba sai na ga tayi murmushi ta nufo ni tare da daukan gyalen rigan dake jikina tana mika min take cewa haba ko dai ni macen aure ai kinga shigan dake jikina ko.
Dole ba don naso ba na cire hijjab din na yafa gyalen kayan a kaina na fito kamar wata yar birni dani don ni kaina nasan na canza sosai.
Tana gaba ina biye da ita a bayan ta rike da hand bag din ta muna fitowa haraban gidan ne mukai kicibis da maigidan wanda da alama dawowan shi ke nan daga wani guri a lokacin.
Yana ganin ta ya dan ja ya yatsaya tare da jingina jikin shi a jikin motar daya fito daga ciki.
Jikin shi na saye da wani yadin maza mai laushe da daukan ido fari kal zaka iya gano yar farar singlet din ke ta cikin jikin shi
Da sauri na basu guri zuwa gurin motan da nake tunane itace motar ta da muka taba fita da ita.
Volvo ce yafito daga ciki ban san yaya akayi ina can tsaye dan nesa kadan dasu na kurawa kasa ido ina faman tunanen yadda in mota tashigo kauyen mu zamu dinga binta har zuwa kofan gidan da mai shi zai tsaya.
Sai muryan tane ya katse na dago da sauri ina kallon inda suke tsaye gaba dayan su shi da ita sun tsura min ido inda nake tsaye ina tunane.
Tace zo a wanan zamu tafi , zaifi muna saukin tafiya ai da sauri na dago na nufo inda suke tsaye yana kokarin jayewa ya bata guri ta shiga motan ne nake cewa cikin yar murya ina wuni.
Kamar baijini ba don bai amsa min ba sai kokari yake yaga matar shi ta zauna da kyau a cikin motan yana fadin don Alkah ki ja sannu ban son gudu ko sauri tace ina naga lafiyan gudu yanzu heart beat.
Tace zagayo ki zauna mu tafi da sauri na kara na shiga motan da ta bude min dayan gefen na shiga.
Ina jin tana mashi horn a inda yake tsaye hannayen shi harde cikin dan uwa yana kallon yadda take jan motan.
Daga inda nake na dan saci kallon su naga yadda suke nunawa juna tsatsan kauna zalla tsakanin su.
Wani kamshi da sayin ne suka ziyarci hanci na da jikina a lokaci guda wanda ban san lokacin da na sake sanyayan ajiyan zuciya ba don yanayin da naji.
Tace yaya dai Rama na naga tun dazu sai faman tunane kike yi may ke faruwa ne wai ?
Idanuwa na lunshe tare da sake dan murmushi nake cewa anty sauyin rayuwa ne kawai nake tunane da ina kauye yaushe zan taba wanan sabon rayuwan da nake ciki.
Murmushi tayi tare dayiwa wata mota da naji tai mata horn ita ta mayar masu da horm din tana cewa ya dauka ko maigidan ne da kan sa a ciki .
Yanzu ke har kin ganki a wani rayuwa ke nan Rama naji ta tambaye ni ta sake wancan maganan da take na motar da ta wuce gaban mu.
Nace anty idan da nayi auren gidan Jatau ai da ko jaki sai nayi shekara ban gani don ba fita ake a gidan shi ba.
Dariya anty tasa tace kai ai da jin sunan shi kasan mutanen dauri ne ba na yanzu ba wai Jatau.
Wani gida ta tsaya tana horn aka bude mata gidan ta danna kan motar ta zuwa cikin gidan.
Kishiryata zulfa ce tsaye da wata suka kuro muna idon su har muka kawo inda suke basu daina kallin mu ba suna son ganin ko maigidan ne a motar.
Can ta fito daga ciki sai naga sun kawar da kan su ga kallon su basu dade ba naga Zulfa ta juya tana kokarin shiga motar ta.
Muna kawowa wace suke tare tsaye bata da niyya muna magana naji Anty na cewa Samira yaya yau ?
A, a uwargida yau kece da kanki a motar oga wani kaya sai amali ke nan ?
Murmushi anty tayi mata muka sa kai zuwa cikin gidan gidan ya kaure da hayani zaka fahinci akwai mutane a gidan.
Wani daki muka nufa inda nake zaton nan ne dakin matar gidan da muka zo gayarwa din.
Da sallama muka sa kai a dakin yayin da matan dake dakin suka kuro muna ido su.
Matar suna da matukar kama da mijin anty sosai dagani basai anfada ma ba don jini yana aiki sosai.
Tun ba su gaisa ba take cewa a, a matar mulki an samu fitowa ke nan dai ai na dauka mulkin ba zai barki zuwa ganin baby ba ai.
Tace ai kin san ko don nazo naga dana zan zo
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22 Chapter 23Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32Chapter 33Chapter 34Chapter 35Chapter 36Chapter 37Chapter 38Chapter 39Chapter 40Chapter 41Chapter 42Chapter 43Chapter 44Chapter 45Chapter 46Chapter 47Chapter 48Chapter 49Chapter 50Chapter 51Chapter 52Chapter 53Chapter 54Chapter 55Chapter 56Chapter 57Chapter 58Chapter 59Chapter 60Chapter 61Chapter 62Chapter 63Chapter 64Chapter 65Chapter 66Chapter 67Chapter 68Chapter 69Chapter 70Chapter 71Chapter 72Chapter 73Chapter 74Chapter 75Chapter 76Chapter 77Chapter 78Chapter 79Chapter 80Chapter 81Chapter 82Chapter 83Chapter 84Chapter 85Chapter 86Chapter 87Chapter 88Chapter 89Chapter 90Chapter 91Chapter 92Chapter 93Chapter 94Chapter 95Chapter 96Chapter 97Chapter 98Chapter 99Chapter 100Chapter 101Chapter 102Chapter 103Chapter 104Chapter 105Chapter 106Chapter 107Chapter 108Chapter 109Chapter 110Chapter 111Chapter 112Chapter 113Chapter 114Chapter 115Chapter 116Chapter 117Chapter 118Chapter 119Chapter 120Chapter 121Chapter 122Chapter 123Chapter 124Chapter 125Chapter 126Chapter 127Chapter 128Chapter 129Chapter 130Chapter 131Chapter 132Chapter 133Chapter 134Chapter 135Chapter 136Chapter 137Chapter 138Chapter 139Chapter 140Chapter 141Chapter 142Chapter 143Chapter 144Chapter 145Chapter 146Chapter 147Chapter 148Chapter 149Chapter 150Chapter 151Chapter 152Chapter 153