kwana a wahalce saida kuma tayi aiki da safen nan.
Gajiye tace nace ta bari takine hajiya sai da tayi yanzu kuma tana kwance don yau yaran ma sunga daban a gidan ta kasa kaisu bakin mota.
Tea ta hada mai kauri ta aje falo can kuryan daki ina dunkule ta samay ni ta tayar dani nazo na karya zan yi magana tace dani ban son musu fa.
Nafito na zauna a kasa tare da dunkule kafana guri daya na tsurawa shayin ido kawai tace dauki mana kisha Rama.
Na dauka na kurba kada n naji shi kamar ruwan magani yadda bakina yake komai bana son sha a lokacin.
Mama Altine ce ta shigo gida da ganin ta zakasan ba cikin hankalinta take ba a lokacin .
Mutum zai dauka ko a kano ta kwana don uban samakon da ta bugo nayi mamakin inda ta samu abin hawa haka dasafe ta bugo wanan uban sammakon haka.
Sannu da zuwa muke mata fuskanta a daure tamau dashi babu walwala a cikin sa.
Inda nake zaune a takure gaban anty ta watsa min harara tsana ne karara a idon ta da take min.
Take na soke kaina a kasa sai hawaye shar ya zubo min kaina a duke a kasa na kasa dago ido na kalle ta murya a raunane nace da ita mama sannu da zuwa.
Ta amsa min ciki ciki ba yadda muka saba ba da ita da take jina kamar itace ta haife ni a baya.
Anty ta shiga taron ta cikin nuna jin dadi da ganin ta tare da tambayan ta mama anan kika kwana ne ko kuwa ?
Tace agida na dai na kwana da yake na kwana da shirin tafiyan ne na bugo sammako mashin aka dauko ni dashi har zuwa bakin titi.
Sai lokacin nadago kaina na kalle ta nake mamakin jin wai mashin ta hawo zuwa bakin titi daga kauyen mu da wanan safiyan haka.
Ina naga sukunin zama wanan wanan mara amanan ta sakani a damuwa yadda naga dare jiya haka naga safiya ban iya runtsawa ba wallahi.
Wanan tashin hankalin da may yai kama Saade may kuke shiryawa ne haka ba tunane a cikin sa keda mijin ki da wanan ja,irar yarinyar.
Mikewa nayi zuwa dakin tabini da harara tana cewa Albasa baiyi halin ruwa ba wallahi yarinya a sakaki innuwa kice zaki kai mutum rana ke.
Haba haba mama damay yarinyar nan zataji bafa laifin Rama bane wanan maganan yadda kikaji maganan haka taji shi wallahi.
Asalima ke kin riga ta ma jin maganan don ita sai baya anyi angama nake sanar da ita.
Tun jiya a birkice take muna na rasa gane kan ta gaba daya taki kwantar da hankalinta tafahince ni.
May zata fahinta bayan tariga ta san tsiyan da ta shugawa mutane ni yanzu da wani ido zan kalli mutane dashi sai ta fashe da wani irin kuka.
Mama don Allah ki kwantar da hankali ki, ki fahince ni, may zan fahinta Saade anan mun dauko tsintarciyar mage mun saka ajikin mu.
Yau Ramane za, ace wai kishiyar ki a gidan nan komay ban taba tunanen yariyar zatayi muna wanan irin yankan kaunar ba.
Irin aibanta ni da mama yau takeyi har tana kokarin hadawa da iyayyena yasa naji duk duniyan baki daya ya kara min kunci a raina.
Mama don Allah kibar zagin yarinyar nan ni na bada wanan shawaran saboda ina da hujjan yin hakan danay ga baki dayan mu gidan nan.
Salati mama ta saka tace kina da hankali kuwa Saade yanzu har ki kalli idona kice da hannun ki da bakin ki kika saka ai maki kishiya.
Wa yan nan ma da kuke tare dasu yaya kuka iya da juna balle ki kara daukowa kanki wani sabon wahala kuma ?
Mama Rama insha Allahu alheri ne a gare mu ba yadda kike tunane bane da yardan ubangiji.
Mama tace ita kishiyar kikewa wanan shedan haka Saade yaufa duk wani so da kauna dake tsakanin ku ya koma kiyayya ke nan tunda kun zama kishiyoyin junan ku kuma.
Saade ni har mamaki kike bani wallahi waiko banza yarinyar nan tabar ki kin fasan mutum yanzu abin tsoro ne.
Mama wallahi ba abinda Rama tai min yadda kike tunane nice dai naga dacewan hakan na bada goyon bayan ayi din.
Daga daki nace a raina lalai duniya da ban mamaki yake ni wani irin so anty ke min haka har yakai takai ga hadani da mijin ta abin alfaharin rayuwan ta da kaunan ta yadda nasan zaman takewar su a cikin so da kaunan junan su suke ko yaushe.
Samun irin mata kamar anty a wanan zamanin mace ma,abociya karamci ga mazan auren su tare da jiye masu jin dadin rayuwan su don bukatan su kawai.
Samun irin su anty yanzu gaskiya sai an tona a duniya don babu macen da zata iya sadakar da rayuwan mijin ta akan wata can.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA YAR UWA DON BA, A YAFE MAKI BA, , ,
IDAN KIN TURAWA WANDA BAIBIYA BA ALLAH YA SAKA MUNA A KANKI YAR UWA, , ,
36
Ina daga daki inajin yadda mama ke ci gaba da aibantani ga anty tana fadin dama ta dade tana shakkan faruwan haka a gare mu .
Don son da kikewa yarinyar nan yai muni Saade shi so haukane da har zaki yi wanan danyen hukuncin a kanki.
Maganan Lauratu ya tabbata ke nan in ma bakine itace tai maki shi don ta furta dama tunda mukazo da ita sai tai muna abinda har mu mutu bazamu mantaba a rayuwan mu to gashi ko tayi yau.
Nan dai mama take ta aibantani da iyyena cikin daga murya yadda zan iya ji daga inda nake a dakin mu zaune a takure.
Hankalina idan yai dubu ya tashi kuka nake ni daya a daki ina fadin koma may zaki fada yau mama a kaina na cancanci hakan a gareku da duk wani nakuma.
Baku duk duniya ma na ci a zageni a zargeni a matsayin rikkakan yar cin amana a gare ku.
Shike nan yau so da kaunar da anty ke gwada min ya tashi a tutar babu tunda kaddara aure ya gitta a tsakanin mijin ta dani.
Aure aure fa waini da daddy yau wai daddy ne mijin sunna na da nake aure wanda zanyi zaman rayuwa irin wanda ma aurata ke yi a tsakanin su.
Wanan bakin auren yau yaraba tsakani na da matar data zamay min matsayin uwa da ubana a duniya tai ma rayuwa na tsaye gurin ganin ya inganta.
Yau banda wani martaba ga idon duk wanda yaji wanan kaddaran a kaina babu ma wanda zai dauke shi wai kaddara ne haka.
Mikewa nayi na fara hada kayana duk abinda nake bukata sai dai babu abinda na dauka daga cikin abinda anty da mijin ta suka saya min a gidan.
Na jawo wani dan karamin jakkar kayana na cusa a ciki na mayar na tura a karkashin gado ina mai ci gaba da sauraren maganan mama a falo da takeyi.
Gajiye ta shigo dakin ta samu ina kuka take cewa dani Rahama ashe abinda ya faru ke nan dake, yanzu nake jin haka a gurin mama da tazo ai.
Kiyi hakkuri tunda ba yin kanki bane haka Allah ya nufa dake sai dai ita mama ta bani mamaki gaskiya wanan magana da takeyi haka bayan tasan koke wacece ta san kuma abinda zaki iya da wanda baki iyawa.
Na share hawaye na a hankali cikin dakushewar murya nake cewa Gajiye bari mama ta fadi don itace silar hadani da Anty a rayuwana.
Yau kuma ga irin kaddaran daya gitta tsakanina da anty wai muna a matsayin zaman miji daya da ita.
Gajiye tace amma ai duk wanda yaji idan ya saurara yasan baki da laifi a cikin zancen nan Rahama,
Haba gajiye wanan magana wani mai hankaline ba zai konawa rai ba duk wanda yaji dole ne ya zarge ni gajiye.
Yaya zan zauna da daddy mijin anty a matsayi wai mijin sunna a gare ni sai na sake sake wani kuka mai tsuma zuciyar duk mai sauraren ta.
Ni yanzu ai tankar daidai nake da mujiya a cikin alumma don nasan duk inda na shiga Gajiye nunani za, ayi a matsayin yar cin amana.
Rahama ki daina wanan maganan haka ki zamo cikin bayi masu rungumar kaddara akan su walau mai kyau ko mara kyau.
Nace Gajiye na yadda da kaddaran auren mijin matar data rikeni kamar yar cikin ta riko irin na fisabillahi ba kisa ba munafunci a cikin sa.
Yau shine zan zauna wai a matsayin kishiya a gurin ta kema kin san hakan ai ba zai taba yuyu ba gaskiya.
Dagani har gajiye kuka muke a dakin can muka jiyo muryan anty tana kiranta a falo da sauri tamike ta fita tabarni tana share hawaye a fuskan ta a hankali.
Ganin gajiye na sharan hawaye yasa anty ta fahinci kuka mukeyi a dakin dagani har ita.
Tace ba dai kuka, kuka shiga daki kunayi ba gajiye kiramin Rama don Allah so take tajawa kan ta ciwo ko may kuma ?
Gajiye ta dawo dakin ta samay ni na daga kai sama ina kallon rufing din dakin take fada min kiran da ake min ta juya tafita daga dakin
Mama ko har lokacin bata fasa aibantani ba da iyayye sai bata hakkuri anty keyi a falon
Munan kalamai na aibanci da mama Altine ke fadi a kaina yasa na rutse ido daga inda nake kwance a daki cikin dafe bakina kada sautin kukana yafito
Bata kuma fasa fadan ba cikin daga harshen ta ta yadda zagin da maganan da takeyi zai iso gare ni.
Hankalina idan ya kai dubu ya tashi ban san lokacin da na mike ba cikin sanda na tura kofan dakin yadda bazan iya jin kalaman mama ba a kaina.
Komai da ya kasance anty ko mijin ta ne suka saya min shi ban dauka ba na boye kayan ina jiran na samu kafa ne kawai na balle daga gidan.
Kuka nake ina tunane akan rayuwana ina fadi a raina shike nan burina ba zai cika ba a rayuna nida karatu kuma sai wani ikon Allah don idan na samu nabar gidan nan har abada bazan sake waigo shi ba.
Ban taba tunanen rayuwa na zai kare a haka ba ba tare da gurina akan karatuna ya cika ba.
Gajiye ta turo kofan ta kura min ido tace ya kamata kibarwa Allah wanan alamarin haka Rahama, dafa yarda da umurnin hajiya hakan ya faru.
Gajiy asanadin mama nasan anty yau gashi an wayi gari na zamo maciyiya amana a gare su bazasu taba yarda cewa bada sani na haka ya faru a gareni ba.
Don haka ba mama ba duk wani shakiki na anty yau na zamo mai laifi ne da bakin jini a gurin shi.
Gajiye da mutuwa nayi daya fiye min ganin wanan bakin ranan a rayuna ranan da za, ace ni Rahama wai na hada mijin sunna da Anty Anty da take kamar uwa da uba a gurina.
Matar da ta rike ni rikeni riko na tsakani da Allah ba kissa ba cutarwa tsakanina da ita amma yau ga shi wai mijinta mijin sunnan tane mijina nima.
Tace to daure kije kiji kiran da hajiya take maki yanzu kinji yi hakkuri don Allah kibar kuka.
Na mike da kyat tare da gyara hijjabin dake a jikina na nufi falon idanuwa da suka sha kuka sunyi zurun zurun dasu don kukan da nasha.
Ina shiga falin daddy na fara tozali dashi ya shigo gaida mama da zuwa magana suke da mama da anty da ganin shi abuga na miji hankalin shi a kwance yake abin shi .
Yana saye cikin shadda ghalila mai ruwan danyen kore sai maiko takeyi a jikin shi yana sheki.
Sai naga ta kara min kwarjini a idanuwa na yau fiye da yadda na san shi a baya sajen fuskan shi ta kwanta lub lub a fuskan shi zakace baima taba aje mace ba a gidan shi don kurciyar shi daya fito fili.
Wani irin shock naji har cikin kaina da sauri na dukar da kaina kasa kamar na bude kasa na shige don kunya.
Da kyat na karasa gaban su tare da rusunnawa a gaban anty kamar kullun ina fadi cikin dassashiyar murya gani anty.
Tace dani bakiga mijin ki bane banji kin gaida shi ba da kwana mana ko kin gan shine yau da gari ya waye ?
Hmm naji mama tace tare da fadin ikon Allah wai in baka mutu ba baka gama ganin ikon Allah ba aduniya.
Jin abin da mama tace yasa daddy ya kai hannu a fuskan shi cikin dan furzo da iska daga bakin shi yana shafan sajen fuskan shi a hankali da hannu daya tare da dauke kan shi daga kallon mu.
Umurnin anty na bi cikin dassashiyar murya nace a hankali daddy ina kwana.
Dan gajeren murmushi yayi tare da mikewa yana fadin shi zai fita yana ganin zai isa a wudil akwai wanda yake son gani a can.
Anty tai mashi a dawo lafiya yafice daga falon ba tare da ya tsaya amsa mata ba ita ma.
Anty take cewa dani bayan fitan shi Rama kina son kijawa kan ki ciwo ne haka ko kije kiyi wanka ki gyara jikin ki don Allah ki daina wanan kukan haka mana may ye amfanin kuka hakane wai ?
Ikon Allah lalai Saade kin dauko wa kanki ruwan dafa kanki da hannun ki yanzu kamar Rahama yarinya son kowa kin wanda ya rasa kike kokarin cuna ta haka ga mijin auren ki.
Yarinya ta zauna a cikin tsofin mata tayi kishi dasu ba wani hayani shine wai har kike gwada mata yadda zatayi da mijin auren ki.
Haba dai mama mijin ta ne fa itama yanzu yadda nake da iko dashi haka itama take da iko dashi a gidan nan.
Yaya zanga abinda zai iya halakata ban lurar da ita ba hanya madaidaiciya.
Mama tace eh lalaine kuwa naga alaman hakan lalai kinyi nisa bakuajin kira yanzu kan dole sai na mike nasan abin yi akai.
Don Allah mama kada kice zakiyi wani abin kaucewa Allah anan da hankalina wallahi.
To inko da hankalinki kina bukatan addua gaskiya don abin naki bana kai sake bane an dai kaiki an baro kawai anga gurin ci.
Na hade yawu masu daci ikon Allah yau ni mama Altine ke aibantawa haka har da zargi akaina wai nakai anty gurin boka da malamai na kwace mata mijin ta.
Maimakon na shiga wanka na koma bakin gado na zauna sai sake sake nake a cikin raina ina maijin kunan rai a tare dani.
Zuwa tsawon wani lokaci na daina jin maganan su a falo haka yasa na fahinci sun shiga daga ciki ko daya ya tashi yabar daya a gurin.
Na mike na fito don na gaskanta hakan kamar zan dauki wani abu a gurin babu kowa a falon har gajiye ina gani tana ciki tana aiki a lokacin.
A hankali na nufi kofan fita daga part din na bude shi cikin sanda na fice daga part din na nufi hanyan fita get.
Gefen filawa nabi ina tsoron kada na hadu da wata daga cikin matan gidan don ina tsoron haduwa dasu yanzu saboda na zama mara gaskiya a cikin su.
Ina kaiwa bakin get maigadi na hangoni yafara washe baki yana cewa cikin jin dadi hajiya Rahama ashe wani abin arziki ne ta samay mu haka kuma ?
Sai da safen nan ai nake samun labari gurin mutanen gidan nan ban tsaya sauraren karshen maganan shi ba na bude get na fice daga gidan.
Nai saa wani mai Napep ya kawo wasu mata uguwar na tsayar dashi na dauki shata sai uguwar su Zarah na nufa.
Nayi saa zarah na gida a lokacin bata fitaba tana gani yamutse dani na hargitse takw cewa dani Rahama lafiya kike kuwa kika koma haka lokaci daya ?
Ban tsaya bata amsa ba na fada saman fogon kujeran dake falonta na shiga kuka ba kakautawa hankalin Zarah yai matukar tashi sosai tai tambayan duniyan nan a kaina babu amsa gare ni.
Sai itama ta shiga kuka don tasan akwai mugun labarin da zan fada mata wanan irin kukan haka danakeyi balafiya ba dai kan.
Sai da mukayi mai isar mu takoma tana lalashi na kuma cikin tsigar lalami da ban ki har na dan tsagaita kukan nawa.
Nace zarah na shiga uku na lalace a rayuwana na zama babban yar cin amana yau zarah ina zan sa kaina yau zarah na shiga uku zarah.
Tace don Allah don kaunarki da Annabi ki fada min may ke faruwa dake wai Rahama don Allah daina kukan nan ki fada min.
Na dago jajayen idanuwa na sauke su ga nata nace cikin kuka Zarah aure aka daura min jiya.
Tace aure aure Rahama aure dawa kuma shine kike wanan kukan kamar mutuwa wallahi na dauka wani abu ne ya samu antyn ki ko wani naki.
Nace zara dole inyi kuka zarah wanda aka daura min aure dashi ne abin kuka da tashin hankali.
Wa aka daura maki aure dashi Rahama
Showing 150001 words to 153000 words out of 456145 words
Gajiye tace nace ta bari takine hajiya sai da tayi yanzu kuma tana kwance don yau yaran ma sunga daban a gidan ta kasa kaisu bakin mota.
Tea ta hada mai kauri ta aje falo can kuryan daki ina dunkule ta samay ni ta tayar dani nazo na karya zan yi magana tace dani ban son musu fa.
Nafito na zauna a kasa tare da dunkule kafana guri daya na tsurawa shayin ido kawai tace dauki mana kisha Rama.
Na dauka na kurba kada n naji shi kamar ruwan magani yadda bakina yake komai bana son sha a lokacin.
Mama Altine ce ta shigo gida da ganin ta zakasan ba cikin hankalinta take ba a lokacin .
Mutum zai dauka ko a kano ta kwana don uban samakon da ta bugo nayi mamakin inda ta samu abin hawa haka dasafe ta bugo wanan uban sammakon haka.
Sannu da zuwa muke mata fuskanta a daure tamau dashi babu walwala a cikin sa.
Inda nake zaune a takure gaban anty ta watsa min harara tsana ne karara a idon ta da take min.
Take na soke kaina a kasa sai hawaye shar ya zubo min kaina a duke a kasa na kasa dago ido na kalle ta murya a raunane nace da ita mama sannu da zuwa.
Ta amsa min ciki ciki ba yadda muka saba ba da ita da take jina kamar itace ta haife ni a baya.
Anty ta shiga taron ta cikin nuna jin dadi da ganin ta tare da tambayan ta mama anan kika kwana ne ko kuwa ?
Tace agida na dai na kwana da yake na kwana da shirin tafiyan ne na bugo sammako mashin aka dauko ni dashi har zuwa bakin titi.
Sai lokacin nadago kaina na kalle ta nake mamakin jin wai mashin ta hawo zuwa bakin titi daga kauyen mu da wanan safiyan haka.
Ina naga sukunin zama wanan wanan mara amanan ta sakani a damuwa yadda naga dare jiya haka naga safiya ban iya runtsawa ba wallahi.
Wanan tashin hankalin da may yai kama Saade may kuke shiryawa ne haka ba tunane a cikin sa keda mijin ki da wanan ja,irar yarinyar.
Mikewa nayi zuwa dakin tabini da harara tana cewa Albasa baiyi halin ruwa ba wallahi yarinya a sakaki innuwa kice zaki kai mutum rana ke.
Haba haba mama damay yarinyar nan zataji bafa laifin Rama bane wanan maganan yadda kikaji maganan haka taji shi wallahi.
Asalima ke kin riga ta ma jin maganan don ita sai baya anyi angama nake sanar da ita.
Tun jiya a birkice take muna na rasa gane kan ta gaba daya taki kwantar da hankalinta tafahince ni.
May zata fahinta bayan tariga ta san tsiyan da ta shugawa mutane ni yanzu da wani ido zan kalli mutane dashi sai ta fashe da wani irin kuka.
Mama don Allah ki kwantar da hankali ki, ki fahince ni, may zan fahinta Saade anan mun dauko tsintarciyar mage mun saka ajikin mu.
Yau Ramane za, ace wai kishiyar ki a gidan nan komay ban taba tunanen yariyar zatayi muna wanan irin yankan kaunar ba.
Irin aibanta ni da mama yau takeyi har tana kokarin hadawa da iyayyena yasa naji duk duniyan baki daya ya kara min kunci a raina.
Mama don Allah kibar zagin yarinyar nan ni na bada wanan shawaran saboda ina da hujjan yin hakan danay ga baki dayan mu gidan nan.
Salati mama ta saka tace kina da hankali kuwa Saade yanzu har ki kalli idona kice da hannun ki da bakin ki kika saka ai maki kishiya.
Wa yan nan ma da kuke tare dasu yaya kuka iya da juna balle ki kara daukowa kanki wani sabon wahala kuma ?
Mama Rama insha Allahu alheri ne a gare mu ba yadda kike tunane bane da yardan ubangiji.
Mama tace ita kishiyar kikewa wanan shedan haka Saade yaufa duk wani so da kauna dake tsakanin ku ya koma kiyayya ke nan tunda kun zama kishiyoyin junan ku kuma.
Saade ni har mamaki kike bani wallahi waiko banza yarinyar nan tabar ki kin fasan mutum yanzu abin tsoro ne.
Mama wallahi ba abinda Rama tai min yadda kike tunane nice dai naga dacewan hakan na bada goyon bayan ayi din.
Daga daki nace a raina lalai duniya da ban mamaki yake ni wani irin so anty ke min haka har yakai takai ga hadani da mijin ta abin alfaharin rayuwan ta da kaunan ta yadda nasan zaman takewar su a cikin so da kaunan junan su suke ko yaushe.
Samun irin mata kamar anty a wanan zamanin mace ma,abociya karamci ga mazan auren su tare da jiye masu jin dadin rayuwan su don bukatan su kawai.
Samun irin su anty yanzu gaskiya sai an tona a duniya don babu macen da zata iya sadakar da rayuwan mijin ta akan wata can.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA YAR UWA DON BA, A YAFE MAKI BA, , ,
IDAN KIN TURAWA WANDA BAIBIYA BA ALLAH YA SAKA MUNA A KANKI YAR UWA, , ,
36
Ina daga daki inajin yadda mama ke ci gaba da aibantani ga anty tana fadin dama ta dade tana shakkan faruwan haka a gare mu .
Don son da kikewa yarinyar nan yai muni Saade shi so haukane da har zaki yi wanan danyen hukuncin a kanki.
Maganan Lauratu ya tabbata ke nan in ma bakine itace tai maki shi don ta furta dama tunda mukazo da ita sai tai muna abinda har mu mutu bazamu mantaba a rayuwan mu to gashi ko tayi yau.
Nan dai mama take ta aibantani da iyyena cikin daga murya yadda zan iya ji daga inda nake a dakin mu zaune a takure.
Hankalina idan yai dubu ya tashi kuka nake ni daya a daki ina fadin koma may zaki fada yau mama a kaina na cancanci hakan a gareku da duk wani nakuma.
Baku duk duniya ma na ci a zageni a zargeni a matsayin rikkakan yar cin amana a gare ku.
Shike nan yau so da kaunar da anty ke gwada min ya tashi a tutar babu tunda kaddara aure ya gitta a tsakanin mijin ta dani.
Aure aure fa waini da daddy yau wai daddy ne mijin sunna na da nake aure wanda zanyi zaman rayuwa irin wanda ma aurata ke yi a tsakanin su.
Wanan bakin auren yau yaraba tsakani na da matar data zamay min matsayin uwa da ubana a duniya tai ma rayuwa na tsaye gurin ganin ya inganta.
Yau banda wani martaba ga idon duk wanda yaji wanan kaddaran a kaina babu ma wanda zai dauke shi wai kaddara ne haka.
Mikewa nayi na fara hada kayana duk abinda nake bukata sai dai babu abinda na dauka daga cikin abinda anty da mijin ta suka saya min a gidan.
Na jawo wani dan karamin jakkar kayana na cusa a ciki na mayar na tura a karkashin gado ina mai ci gaba da sauraren maganan mama a falo da takeyi.
Gajiye ta shigo dakin ta samu ina kuka take cewa dani Rahama ashe abinda ya faru ke nan dake, yanzu nake jin haka a gurin mama da tazo ai.
Kiyi hakkuri tunda ba yin kanki bane haka Allah ya nufa dake sai dai ita mama ta bani mamaki gaskiya wanan magana da takeyi haka bayan tasan koke wacece ta san kuma abinda zaki iya da wanda baki iyawa.
Na share hawaye na a hankali cikin dakushewar murya nake cewa Gajiye bari mama ta fadi don itace silar hadani da Anty a rayuwana.
Yau kuma ga irin kaddaran daya gitta tsakanina da anty wai muna a matsayin zaman miji daya da ita.
Gajiye tace amma ai duk wanda yaji idan ya saurara yasan baki da laifi a cikin zancen nan Rahama,
Haba gajiye wanan magana wani mai hankaline ba zai konawa rai ba duk wanda yaji dole ne ya zarge ni gajiye.
Yaya zan zauna da daddy mijin anty a matsayi wai mijin sunna a gare ni sai na sake sake wani kuka mai tsuma zuciyar duk mai sauraren ta.
Ni yanzu ai tankar daidai nake da mujiya a cikin alumma don nasan duk inda na shiga Gajiye nunani za, ayi a matsayin yar cin amana.
Rahama ki daina wanan maganan haka ki zamo cikin bayi masu rungumar kaddara akan su walau mai kyau ko mara kyau.
Nace Gajiye na yadda da kaddaran auren mijin matar data rikeni kamar yar cikin ta riko irin na fisabillahi ba kisa ba munafunci a cikin sa.
Yau shine zan zauna wai a matsayin kishiya a gurin ta kema kin san hakan ai ba zai taba yuyu ba gaskiya.
Dagani har gajiye kuka muke a dakin can muka jiyo muryan anty tana kiranta a falo da sauri tamike ta fita tabarni tana share hawaye a fuskan ta a hankali.
Ganin gajiye na sharan hawaye yasa anty ta fahinci kuka mukeyi a dakin dagani har ita.
Tace ba dai kuka, kuka shiga daki kunayi ba gajiye kiramin Rama don Allah so take tajawa kan ta ciwo ko may kuma ?
Gajiye ta dawo dakin ta samay ni na daga kai sama ina kallon rufing din dakin take fada min kiran da ake min ta juya tafita daga dakin
Mama ko har lokacin bata fasa aibantani ba da iyayye sai bata hakkuri anty keyi a falon
Munan kalamai na aibanci da mama Altine ke fadi a kaina yasa na rutse ido daga inda nake kwance a daki cikin dafe bakina kada sautin kukana yafito
Bata kuma fasa fadan ba cikin daga harshen ta ta yadda zagin da maganan da takeyi zai iso gare ni.
Hankalina idan ya kai dubu ya tashi ban san lokacin da na mike ba cikin sanda na tura kofan dakin yadda bazan iya jin kalaman mama ba a kaina.
Komai da ya kasance anty ko mijin ta ne suka saya min shi ban dauka ba na boye kayan ina jiran na samu kafa ne kawai na balle daga gidan.
Kuka nake ina tunane akan rayuwana ina fadi a raina shike nan burina ba zai cika ba a rayuna nida karatu kuma sai wani ikon Allah don idan na samu nabar gidan nan har abada bazan sake waigo shi ba.
Ban taba tunanen rayuwa na zai kare a haka ba ba tare da gurina akan karatuna ya cika ba.
Gajiye ta turo kofan ta kura min ido tace ya kamata kibarwa Allah wanan alamarin haka Rahama, dafa yarda da umurnin hajiya hakan ya faru.
Gajiy asanadin mama nasan anty yau gashi an wayi gari na zamo maciyiya amana a gare su bazasu taba yarda cewa bada sani na haka ya faru a gareni ba.
Don haka ba mama ba duk wani shakiki na anty yau na zamo mai laifi ne da bakin jini a gurin shi.
Gajiye da mutuwa nayi daya fiye min ganin wanan bakin ranan a rayuna ranan da za, ace ni Rahama wai na hada mijin sunna da Anty Anty da take kamar uwa da uba a gurina.
Matar da ta rike ni rikeni riko na tsakani da Allah ba kissa ba cutarwa tsakanina da ita amma yau ga shi wai mijinta mijin sunnan tane mijina nima.
Tace to daure kije kiji kiran da hajiya take maki yanzu kinji yi hakkuri don Allah kibar kuka.
Na mike da kyat tare da gyara hijjabin dake a jikina na nufi falon idanuwa da suka sha kuka sunyi zurun zurun dasu don kukan da nasha.
Ina shiga falin daddy na fara tozali dashi ya shigo gaida mama da zuwa magana suke da mama da anty da ganin shi abuga na miji hankalin shi a kwance yake abin shi .
Yana saye cikin shadda ghalila mai ruwan danyen kore sai maiko takeyi a jikin shi yana sheki.
Sai naga ta kara min kwarjini a idanuwa na yau fiye da yadda na san shi a baya sajen fuskan shi ta kwanta lub lub a fuskan shi zakace baima taba aje mace ba a gidan shi don kurciyar shi daya fito fili.
Wani irin shock naji har cikin kaina da sauri na dukar da kaina kasa kamar na bude kasa na shige don kunya.
Da kyat na karasa gaban su tare da rusunnawa a gaban anty kamar kullun ina fadi cikin dassashiyar murya gani anty.
Tace dani bakiga mijin ki bane banji kin gaida shi ba da kwana mana ko kin gan shine yau da gari ya waye ?
Hmm naji mama tace tare da fadin ikon Allah wai in baka mutu ba baka gama ganin ikon Allah ba aduniya.
Jin abin da mama tace yasa daddy ya kai hannu a fuskan shi cikin dan furzo da iska daga bakin shi yana shafan sajen fuskan shi a hankali da hannu daya tare da dauke kan shi daga kallon mu.
Umurnin anty na bi cikin dassashiyar murya nace a hankali daddy ina kwana.
Dan gajeren murmushi yayi tare da mikewa yana fadin shi zai fita yana ganin zai isa a wudil akwai wanda yake son gani a can.
Anty tai mashi a dawo lafiya yafice daga falon ba tare da ya tsaya amsa mata ba ita ma.
Anty take cewa dani bayan fitan shi Rama kina son kijawa kan ki ciwo ne haka ko kije kiyi wanka ki gyara jikin ki don Allah ki daina wanan kukan haka mana may ye amfanin kuka hakane wai ?
Ikon Allah lalai Saade kin dauko wa kanki ruwan dafa kanki da hannun ki yanzu kamar Rahama yarinya son kowa kin wanda ya rasa kike kokarin cuna ta haka ga mijin auren ki.
Yarinya ta zauna a cikin tsofin mata tayi kishi dasu ba wani hayani shine wai har kike gwada mata yadda zatayi da mijin auren ki.
Haba dai mama mijin ta ne fa itama yanzu yadda nake da iko dashi haka itama take da iko dashi a gidan nan.
Yaya zanga abinda zai iya halakata ban lurar da ita ba hanya madaidaiciya.
Mama tace eh lalaine kuwa naga alaman hakan lalai kinyi nisa bakuajin kira yanzu kan dole sai na mike nasan abin yi akai.
Don Allah mama kada kice zakiyi wani abin kaucewa Allah anan da hankalina wallahi.
To inko da hankalinki kina bukatan addua gaskiya don abin naki bana kai sake bane an dai kaiki an baro kawai anga gurin ci.
Na hade yawu masu daci ikon Allah yau ni mama Altine ke aibantawa haka har da zargi akaina wai nakai anty gurin boka da malamai na kwace mata mijin ta.
Maimakon na shiga wanka na koma bakin gado na zauna sai sake sake nake a cikin raina ina maijin kunan rai a tare dani.
Zuwa tsawon wani lokaci na daina jin maganan su a falo haka yasa na fahinci sun shiga daga ciki ko daya ya tashi yabar daya a gurin.
Na mike na fito don na gaskanta hakan kamar zan dauki wani abu a gurin babu kowa a falon har gajiye ina gani tana ciki tana aiki a lokacin.
A hankali na nufi kofan fita daga part din na bude shi cikin sanda na fice daga part din na nufi hanyan fita get.
Gefen filawa nabi ina tsoron kada na hadu da wata daga cikin matan gidan don ina tsoron haduwa dasu yanzu saboda na zama mara gaskiya a cikin su.
Ina kaiwa bakin get maigadi na hangoni yafara washe baki yana cewa cikin jin dadi hajiya Rahama ashe wani abin arziki ne ta samay mu haka kuma ?
Sai da safen nan ai nake samun labari gurin mutanen gidan nan ban tsaya sauraren karshen maganan shi ba na bude get na fice daga gidan.
Nai saa wani mai Napep ya kawo wasu mata uguwar na tsayar dashi na dauki shata sai uguwar su Zarah na nufa.
Nayi saa zarah na gida a lokacin bata fitaba tana gani yamutse dani na hargitse takw cewa dani Rahama lafiya kike kuwa kika koma haka lokaci daya ?
Ban tsaya bata amsa ba na fada saman fogon kujeran dake falonta na shiga kuka ba kakautawa hankalin Zarah yai matukar tashi sosai tai tambayan duniyan nan a kaina babu amsa gare ni.
Sai itama ta shiga kuka don tasan akwai mugun labarin da zan fada mata wanan irin kukan haka danakeyi balafiya ba dai kan.
Sai da mukayi mai isar mu takoma tana lalashi na kuma cikin tsigar lalami da ban ki har na dan tsagaita kukan nawa.
Nace zarah na shiga uku na lalace a rayuwana na zama babban yar cin amana yau zarah ina zan sa kaina yau zarah na shiga uku zarah.
Tace don Allah don kaunarki da Annabi ki fada min may ke faruwa dake wai Rahama don Allah daina kukan nan ki fada min.
Na dago jajayen idanuwa na sauke su ga nata nace cikin kuka Zarah aure aka daura min jiya.
Tace aure aure Rahama aure dawa kuma shine kike wanan kukan kamar mutuwa wallahi na dauka wani abu ne ya samu antyn ki ko wani naki.
Nace zara dole inyi kuka zarah wanda aka daura min aure dashi ne abin kuka da tashin hankali.
Wa aka daura maki aure dashi Rahama
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22Chapter 23Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32Chapter 33Chapter 34Chapter 35Chapter 36Chapter 37Chapter 38Chapter 39Chapter 40Chapter 41Chapter 42Chapter 43Chapter 44Chapter 45Chapter 46Chapter 47Chapter 48Chapter 49Chapter 50Chapter 51 Chapter 52Chapter 53Chapter 54Chapter 55Chapter 56Chapter 57Chapter 58Chapter 59Chapter 60Chapter 61Chapter 62Chapter 63Chapter 64Chapter 65Chapter 66Chapter 67Chapter 68Chapter 69Chapter 70Chapter 71Chapter 72Chapter 73Chapter 74Chapter 75Chapter 76Chapter 77Chapter 78Chapter 79Chapter 80Chapter 81Chapter 82Chapter 83Chapter 84Chapter 85Chapter 86Chapter 87Chapter 88Chapter 89Chapter 90Chapter 91Chapter 92Chapter 93Chapter 94Chapter 95Chapter 96Chapter 97Chapter 98Chapter 99Chapter 100Chapter 101Chapter 102Chapter 103Chapter 104Chapter 105Chapter 106Chapter 107Chapter 108Chapter 109Chapter 110Chapter 111Chapter 112Chapter 113Chapter 114Chapter 115Chapter 116Chapter 117Chapter 118Chapter 119Chapter 120Chapter 121Chapter 122Chapter 123Chapter 124Chapter 125Chapter 126Chapter 127Chapter 128Chapter 129Chapter 130Chapter 131Chapter 132Chapter 133Chapter 134Chapter 135Chapter 136Chapter 137Chapter 138Chapter 139Chapter 140Chapter 141Chapter 142Chapter 143Chapter 144Chapter 145Chapter 146Chapter 147Chapter 148Chapter 149Chapter 150Chapter 151Chapter 152Chapter 153