daka azurtani da karuwa da wadda nake so a rayuwana ya Allah ka bamu mai albarka da tarbiya imani irin na addinin musulunci.
Kuka na kara sakawa sosai bai dai min magana ba muna gab da shiga gida ne na dakatar dashi da fadin don Allah daddy ina mai rokon ka da ka boye zancen cikin nan ga kowa don gujewa baki da fitina tsakanina da matan ka ?
Baice dani uffan ba ya danna horn maigadi ya fito da sauri ya bude muna get muka shige a lokacin magariba ya kusa bai bude motar ba sai cewan da yayi dani ya kamata ki daina wanan kukan haka don banga dalilin yin shi ba.
Sai da ya tabbatar da na daina ya bude min mota na fito ashe Hindatu da Zulfa suna tsaye suka ga fitowana ban tsaya ta kan su ba na shige abina ciki.
Gajiye da Fatima na zaune har Atika sai ganina sukayi daga sama na shigo gidan zubur suka mike Gajiye na fadin Alhamdullahi uwar dakin mu ta dawo kenan insha Allahu.
Fatima ko fadawa tayi jikina ta fashe da kuka tana cewa anty kin wuce kin barmu cikin wanan matan hankalin mu a tashe.
Daga baya na mukaji muryan shi yana cewa Fatima saketa taje daki karbi hand bag dinta kibita dashi dakin.
Ban tsaya sauraren komai ba na wuce har ya fara tafiya naji yana cewa Gajiye don Allah ki kula min da ita sosai kada ki bari tana aikin komai don tana bukatan hutu tare da ita.
Tace angama Alhaji insha Allahu, yafice suka bi bayana zuwa dakin duk maitar son kallon Fatima ranan sai na samu tv a kashe haka yasa na gane suna zaman takura ne suma a gidan.
Na dan zauna can na mike na shiga wanka na fito na tayar da sallah na dade zaune a gurin ina adduoi shiigowan Gajiye ne ya sani dakatawa ta samu wuri a kasa ta zauna tana gaidani.
Tace hajiya Rahama kin boye haka da yawa hankalin maigida yai matukar tashi sai faman fada yake da kowa a gidan nan an rasa gane kan shi dan kwana biyun nan.
Bayan tafiyan ki sun kara tafka wani fitinan da hajiya Saade sosai a kan ki har yana mata ikirarin indan kin bar gidan nan itama ta tabbatar da tabar shi ke nan .
Tace dasu hindatu kuma anyi shi ba dadi a safiyan jiya don ina ganin ta kawo mai zancen ki ne yai mata tas a kan ki.
Nace Gajiye kyale su kawai dama don su cuta min yasa matar nan tai min haka ina zaman zamana hankalina a kwamce ta sani yin wanan auren yanzu kuma ta dawo tana zargina haka ?
Gajiye tace duk ki bar wanan tunanen hakana yanzu ki rugumi mijin ki kiba banza ajiyan kowa tunda Allah ya nuna maki ai ba yau ta fara ba tun auren ki dashi suke wanan rikicin haka dashi.
Nace Gajiye kina nufin anty ta dade tana nuna min wanan halin a tare da ita tace wallahi Allah ko don shi ya zama namijin gaske ne sosai.
Ni ina ganin a zaton ta ba zaiyi rawan kafa dake ba haka yadda yakeyi ta dauka dai ta aura mashi ke ne kita mata bauta ita da diyanta kada ki gushe a garesu.
Nace koma may ye Gajiye ni da zuciya daya nake zaune da anty idan ita ta dauke ni da zuciya biyu ne na barta da Allah don Allah ba azzaluumin kowa bane ai.
Ba zan taba nuna mata wani mugun hali ba na kishi don itace sillar mayar dani haka a duniya da bata jawoni ba da ai yanzu ina kauye sai yadda Allah yayi dani.
Dama dai Allah ya riga da ya zana akwai aure a tsakanin ku kuma ta dalilin ta zaku hadu dashi kawai.
Amma hajiya ta furfura fiye da tsanmanin ki Rahama don tun tafiyan ki bata taba laiko mu ba shiyan nan balle taji halin da muke ciki.
Yaran dai ne ina ganin sato jiki suke sama sama su shigo su tambaye ki ko kina nan da ance bakyanan zasu juya da sauri su fice sukoma inda suka fito.
Murmushi nayi nace wanan ai daukan alhaki ne bayan ita ta hada ni da yaran kuma zatace yanzu zata raba mu tsakanin mu ni yaran ta basu min komai ba don haka ba zan daina kulasu ba har ta sauko.
Gajiye bata gama maganan ta ba sai ko ga yaran sun shigo dakin nawa suna lekawa suka gane ni jinior ne maimakon ya tsaya sai ya juya da gudu yabar dakin sai gasu gaba dayan su su uku sun shigo da murnan su duk suka fada min a jikina.
Mun baje sai faman surutu muke yi dasu daddy ya shigo ya samay mu a haka da gani yaji dadin yadda ya samay mu din, nan ya zauna dasu suna hira sai ga yar aikin anty ta shigo tana cewa maman ku tace na kira ku.
Ganin daddy baisa ta gaidashi ba sai yaran suka make sukaki tashi yace kice suna zuwa suna tare dani anan.
Mun kai wani lokaci a wurin tare dashi dasu ya tashi ya fice dasu daga dakin nawa naji wani irin ba dadi muna zaman mu lafiya shedan ya shigo muna a rayuwan mu.

********* ********* *********
Duk da anty tasan na dawo bata shigo ba part din ina son shiga school sai da nagama shiri na tsab na shirya na nufi ban garen ta.
Tana daga cikin daki sai yar aikin ta ke zaune a falo ga falon ya wani ya mutse man da gani bata da niyar gaida ni nima ban kula ta ba na nufi kofan dakin ta.
Sai naji matar nacewa tana kwance ne tace kowa ya shigo na fada mai ta kwanta wama zai shigo din in bani ba na fada a raina nasan kuma don ni tabar wanan sakon haka.
Sallama na fara yi har kusan sau uku sannan ta karba min da waye wai please nace nice anty na karasa shiga tana daga kwance da wayya hannun ta nace ina kwana anty tace lafiya kawai.
Nace na tafi school adawo lafiya har nakai kofa ra sake cewa dani kinga dama kin dawo daga barna min suna Rama kisa duniya ta zage ni kan gaskiya na ko may ?
Tsam na ja na tsaya nace cikin yar sirirayar murya kiyi hakkuri anty idan na bata maki amma ni ban bar gidan nan da sunan ki ba na bari ne kan abinda naga yafi sauki gare mu.
Yanzu da kika dawo waya biki can inda kika tafi din ban dai yi magana ba itama bata sake furta komai ba naja kafana na fice daga dakin kawai.
Ina fita naji ta kira Saliha matar ta amsa tace bana nace kada ki bari kowa ya shigo min daki ba na kwanta ina hutawa.
Wallahi Na fada mata bata tsaya ba ta shigo dakin kai tsaye tace ba dole ta shigo ba tasan mugun kullin da tayo min zai kare a kan ta ai.
Murmushi kawai nayi na karasa fita bayan na gama jin maganan su a wajen gidan kuma na hade da mutumiyar tawa Hindatu uwar mita da anyi ance .
Gurin da mota na yake na nufa yana aje a wanke min shi sai shaki yakeyi tun daga nesa na bude shi kafin na karaso gurin.
Kai amma dai hanne wasu matan basu san takaici ba kayi yaji ba wanda ya bika dangin miji ka kwashi kafa kadawo gidan sidau daga kai sai mijin ka an daiyi harasa kawai wallahi.
Wai ma hanne ni sai ina ganin dangin miji sun gaji da bata iri ne a gidan su kulun sai ci ana juyewa a masai babu wani shedan zama ana raya sunan ma, aikin Allah a gani.
To ba dole a dawo ba an saba da shan jan miya yanzu ba a iya zaman kauye kare ya nuna mutum.
Dole miji na zuwa a kwasa a dawo ragai ragai an gaji da kwasan kuka kulun da dawa.
Har na dan wuce ta sai na dawo baya daidai inda suke tare da hanne din yar aikin ta nace cikin murmushi.
Ashe kai yaji miji ya dauki kafan shi ya bika baka aiko ba baka turo ka takurawa dangin miji ba isa ne.
Kauye kuma suna suka tara don wasu sai dai su fadi sunan nasu amma abin kunya bai bari su taka kauyen .
Shikuma nunawa duniya kana kwana da miji ai kauyancine mijin dai shi zai nuna ka isa gareshi har yana rawan kafa.
Barin sheda kuma abune daga Allah don da wasu sun tara shedan dayawa yadda suke so kullun.
Shan kuka da dawa kuma sai naga kamar abincine ba haram ba don yafi shan giya da zina.
To wakike nufi da mazina ci ko may shan giya din nace magana ce da amsar ta ai ko laifine kuma ?
Aiko tayo kaina a, a hindatu babu gaskiya don a gabana kuka fara babu ruwan ki da miji ya bita balle gori ya biyo baya naga nan ake yaji gidan nan bai rawan kafa irin haka ?
Zulfa ce da tun safiyan jiya suke da matsala tsakanin su take bata amsa tace in kasan abin fada baka san amsan da zai dawo maka ba ai ?
Nace na dai gode anty Zulfa in tsoho baiji kunyan hawan jaki ba, shiko haki bazaiji kunyar kada tsoho ba ashe kin zube min wallahi hindatu bazan sake jin naitin ki ko kunyar ki ba agidan nan dani dake shege ka fasa a gidan nan.
Na juya nasa kai na wuce abina inajin Zulfa na fadin kin kai ga yadda kike so ai yanzu girman ki da kimar ki ya gama zubewa ke nan.
Mace kice ke kowa kina bakin cikin kiga ya rabi miji sai ke kada halan ke kadai aka halitta mashi da ya aura ne wai ?
Na ta da mota na na bar gidan abina ban tsaya binta nasu ba don sun kaurai da fada a tsakanin su ba mai jin has a cikin su .
Ina isa school Zarah ta tare ni da dariyar shakiyanci nai banza da ita bamu zauna ba muka shiga pratical ba wasa sai two muka fito sallah.
Nan muka dan samu lokacin kebewa muka dan taba hira wanda duk hiran namu akan matsalar mune da abokkan zama na mukeyi.
Mun gama break muka koma cikin asibiti ba mu fito ba sai karfe shidda dai dai muka fito koda na iso gida a gajiye.
Sashe na nanufa kai tsaye inda na samu su Fatima sun gama hada komai don ranan nice zanyi girki a gidan.
Komai ya kammala yadda nake so sai bayan da nai sallah na shirya tsab a cikin wani English wear dina mai ruwan pink da baki sai dai bakin yafi yawa a jikun kayan sosai.
Kayan abinci na dauka zuwa part din shi har na gama jera komai na dan shiga daga ciki na gyara dakin sama sama har ban dakin sai da na gyara na wanke tsab ina shirin fitowa ne ya shigo dakin don ya kimtsa.
Yace ashe kina ciki na dauka kin fita ne ai nace dakin nake gyarawa yanzu yake cewa baki dai jin komai a jikin ki ko ?
Lafiya kalau nake bana jinn komai tare da ni sai dai yawan jiri dake damuna sometime idan na mike tsaye nake yawan ji.
Yace you see ya kamata muje checkup a duba may ke yawan damuwar ki haka ne wai ?
Nace daddy ko ban tafi ba zan iya curing din kaina anan gida da sauri naji yace dani no no no gobe ki shirya mu tafi gun likita ban jaba nace Allah ya kaimu kawai.
Falo muka dawo tare ya zauna cin abinci tare ina daga gefen shi a zaune a lokacin ne matan gidan daya bayan daya suke shigowa gaida maigida.
Duk wacce ta shigo taga irin zaman da mukayi da daddy yau saman kujere daya na harde kafana daya saman kujera kusa dashi dayan na a kasan kujera gashi gaf da juna muke zaune.
Sai mai shi ta hade fuskan ta take suke nuna bacin ran su har anty na a haka ta samay mu zaune dashi.
Bata tsaya ba ta juya ta fita daga falon wanda dama da gangan na zauna hakan a kusa dashi don kawai na nuna masu lokaci yayi da zasu fahinci nima fa na iya komai ladabin kurage nake masu kawai.

ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE DON BA A YAFE BA SABODA ONLINE NOVEL NE WANAN, , , , ,
63

Bamu wani jima ba muka kwanta ranan nasha fada da nasiha sosai a gurin daddu har takai na fara kuka don jikina yai sanyi sosai ga nasihan shi.
Ban yi mamakin yadda ta gudanar dani ba a ranan don halin maza ne nuna gwaninta su a gun mace.
Washe gari muka tafi asibiti yan maganin da dama nake sha su likita yaso bani nace already dama ina amfani da su ai.
Sai da yaji likita yace wanan ba komai bane haka wasu mata suke fama kafin ciki ya zauna a jikin su da kyau hankalin daddy ya kwanta.
Tun wanan ranan nake kokarin ganin na kiyayye kowa a gidan dagani sai su Fatima da gajiye muke al, amarin mu.
A cikin wanan halin Allah ya kawo muna mama altine ko da tazo bani gidan ina school dana dawo ne Gajiye ke sanar dani zuwan mama din.
Sai da nai sallah isha,i na shiga gaida mama din da fara, anta ta tare ni nima din haka a falo na samay ta muka gaisa na tambaye ta duk mutanen gida tace suna lafiya Rukaiyya ma ta haihu na biyu.
Naji dadi sosai muna cikin hira jinior na kwance a jikina yana wasan shi Nasir na gefe na a kwance sai ga uwar ta fito daga dakin ta.
Na gaida ita irin yadda ta karba min yasa mama ta kalle ni yaran ta kalla tace dasu ban hanaku zama jikin mutum ba ashe ?
Cikin rashin sanin may ke wakana mama tace cikin dariya kai amma Saade akwaiki da wani magana kuma .
Rahama da yaran nan ai sai Allah shifa yaro kamar dabba yake inda yaga ido a nan yake ko yaushe, da basu tafi gurin wani sun mamay shi ba fuska suka gani.
Sai cewa anty tayi a, a mama bana son irin haka yanzu kowa ya tsaya matsayin shi yara dai nawa ne aiko ?
Gyara dai zancen ki Saade yara naki ne kin haife su ne kawai amma aida Rahama suka bude idanuwan su ko ?
Kai mama don Allah ki bar wanan zancen idan ta samu nata zata bude ido da su ai.
Ikon Allah inji mama Altine tace kanki daya kuwa yau Saade nifa tun zuwa na naga canji sosai a yanayin ki.
Muna murnan kin samu lafiya kuma sai sabon yanayi ya shigo gaskiya banji dadin jin wanan zancen ba dakika yi yanzu.
Ina yarinyar nan tun bata san duniya ba Allah ya hada ku tare har talai kin sadaukar da sonta a kan ki.
Anty tace ada ke nan mama ni yanzu ai an shani na warke ko na fahinci waye dan adam ka gan shi a rana kakai shi innuwa yanzu ba may kara yaudara na kuma.
To Allah ya kyauta da magana ke nan a gidan naku don naga alaman haka tun zuwa ban ga Gajiye a nan ba tun da tazo taimin sannu da zuwa sai wanan bakar matan nake gani tundazu gata bata da ko marmari kamar muguwa.
Mikewa nayi nace mama a huta gajiya zan koma sai da safe ina mikewa yaran ma suka mike wai zasu bini amma fafir uwar ta rufe ido ta hana su a gaban mama dani.
Bayan fita na mama take mata magana take cewa haba Saade ban san ki da wanan mugun rayuwan ba.
Tace mama ai dole ne ya kawo hakan nan dai takawo wa mama dalilin ta mama dai tana sauraren ta har ta gama maganan ta.
Tace amma kinyi kuskure wallahi Saade yau ina kwakwalwanki ya shiga da tunanen ki da har kike wa yarinyar da kika raina da hannun ki kika bata tarbiyan da kike so tayi koda a bayan ranki ne ?
Wanan bakin tuhumar da zargi ai wahalal da kanki kikeyi da zubarwa kanki daraja a gun yar kankanuwar yarinyar da take jin ki fiye da kowa a duniya.
Dake nan mama yanzu ai Rama ta wuce sani na don ta samu wanda suka fini ke kike daukan ta a yarinya mama.
Yarinya ce zatai kokatin rabani da mijina ta na kokarin ganin sai na koma baya gun mijina daga taimako sai abu ya koma tsiya kuma ?
Eh lalai kin ko samu matsala babba don dai ni ko ga wani ban taba tunanen haka ba a gareki balle wanan yarinyar Rahama.
Duk yadda mama taso ta kwantar mata da hankali anty taku fahinta hakan sai dai ta nuna mata bacin ran yadda take saka har da yara a cikin kishin mu .
Ganin bata da niyar yarda yasa mama tace da safe zata bar gidan idan Allah ya kaimu don bazata zauna tana ganin wanan irin
Showing 261001 words to 264000 words out of 456145 words
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22Chapter 23Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32Chapter 33Chapter 34Chapter 35Chapter 36Chapter 37Chapter 38Chapter 39Chapter 40Chapter 41Chapter 42Chapter 43Chapter 44Chapter 45Chapter 46Chapter 47Chapter 48Chapter 49Chapter 50Chapter 51Chapter 52Chapter 53Chapter 54Chapter 55Chapter 56Chapter 57Chapter 58Chapter 59Chapter 60Chapter 61Chapter 62Chapter 63Chapter 64Chapter 65Chapter 66Chapter 67Chapter 68Chapter 69Chapter 70Chapter 71Chapter 72Chapter 73Chapter 74Chapter 75Chapter 76Chapter 77Chapter 78Chapter 79Chapter 80Chapter 81Chapter 82Chapter 83Chapter 84Chapter 85Chapter 86Chapter 87Chapter 88 Chapter 89Chapter 90Chapter 91Chapter 92Chapter 93Chapter 94Chapter 95Chapter 96Chapter 97Chapter 98Chapter 99Chapter 100Chapter 101Chapter 102Chapter 103Chapter 104Chapter 105Chapter 106Chapter 107Chapter 108Chapter 109Chapter 110Chapter 111Chapter 112Chapter 113Chapter 114Chapter 115Chapter 116Chapter 117Chapter 118Chapter 119Chapter 120Chapter 121Chapter 122Chapter 123Chapter 124Chapter 125Chapter 126Chapter 127Chapter 128Chapter 129Chapter 130Chapter 131Chapter 132Chapter 133Chapter 134Chapter 135Chapter 136Chapter 137Chapter 138Chapter 139Chapter 140Chapter 141Chapter 142Chapter 143Chapter 144Chapter 145Chapter 146Chapter 147Chapter 148Chapter 149Chapter 150Chapter 151Chapter 152Chapter 153