ta ban samu zama ba don yara na dake damuna suna fama da lolayin ciki kowan su.
Idan na gama da wanan wanan zata kirani da nata korafin kuma haka suka raba min hankali ga aikin da ya taso min a gabana kuma ban da hutu ta ko ina a kaina.
Ranan jumma,a maigidan zai dawo kasan don haka a bangaren kowan mu sai shirin taron maigidan akeyi kowa na nuna nata bajin ta akan dawowan shi kamar yadda ko wani gida haka mata keyi idan miji ya dan yi nisan balaguro da gida na kwana biyu.
Ashe mu duk shirmay mukeyi a bangaren mu bamu sani ba sai ranan ds zai dawo yai waya zasu iso da karfe sha biyun rana yakuma ce ba sai mun je taron shi ba da yan aikin su yake tare.
Ina dakina ina shiri Atika ta shigo tana ce wa dani ga Anty Amira da Aisha sunzo na ce kai sunzo min da matsalan su ke nan daga mai miyau sai amai a cikin su dariya tayi ta fita daga dakin.
Sai gasu sun shigo tun daga kofa suke kwala min kira da mummy mummy nace ya salam wanan kiran fa na tashin hankali haka fa for god sake ?
Suka fada min a jiki da murnan su muka shiga gaisawa dasu nan Amira take cewa dani mummy wani buki kukeyi ne a gidan yau naga gidan ya cika da motoci mana haka barkatai.
Cikin mamaki nace motoci kuma a ina na mike tare da leka window dakina aiko matane na hango suna shige da fice a bangaren amaryan daddy din.
Nace kun san mun samu yan bidi,a a gidan yanzu kila wani abin sukeyi kuma a nan ashe ni ban sani ba wai duk dawowan daddy akewa wanan shirin haka .
Sai isowan shi gidan ne mukajiyo hayaniya ta ko ina a gidan da shewa wai suna mai sannu da zuwa.
Sai dai kamar hadin baki don babu ko mutum daya daga cikin mu mamaki wanan abin ya bashi don haka yayi zaune a cikin mota yaki fitowa daga ciki.
Suna tsaye sai iskanci suke zubawa irin na manyan mata yan duniya suna wani girgije girgijen jikin su.
Waya ya daga ya kira mu dashi yana fada wai ban mu san ya iso bane kuma wani haukane haka mata suka taru muna a gida haka suna wanan iya shegen haka ?
Nace a gidan nan to banda ma saniya a kan su amma ganinan fitowa yanzu ai.
A tare mu uku muka dinga fitowa daga part din mu nice ta karshe tare da yarana gaba dayan su muka fito shigan mu ma kawai ya isa mutum ya tsaya kallon mu don kowan mu ya kure a dakan sa sosai rike nake da hannun anty da daddy da suka sha irin nasu adon nan kuma kallo ya koma a kan mu duk wanan iya shegen da suke zubawa a wurin.
Motar har lokacin yana rufe haka muka ratsa su har bakin motar daidai lokacin ne ya bude motan tare da sako kafar shi daya waje.
Sai na karasa bude motar tare da rankwafawa gare shi na dan kamo shi da saurin ta ta karaso bakin motar tana bangaje yaran dake murnan ganin mahaifin su har anty na buga bakin ta a kofar motar wai tana kamo shi.
Wani tsawa ya daka mata tare da karasa fitowa daga cikin motar gaba daya yana kama yarinyar yake fadin kina haukane haka komay da zaki ture min yarinya kina gani.
Jaye min daga nan please ya juya gun matan da suka dandazo a gaban mu yana fadin wa yan nan fa kuma daga ina haka suke su ya busu da wani irin matsiyacin kallo na takaici hindatu ta fada jikin shi ya rugumay ta haka ma zulfa tai mashi ban tafi ba shi da kan shi ya jawoni izuwa jikin shi ya kama hannun su jinior muka shiga cikin gidan yana rungumay dani a jikin shi .
Nan muka barsu tsaye cikin takaici da mamakin wannan irin cin fuskan da daddy nuna masu a fili gava kowa don su suna ganin duk a inda yar wanan kungiyar take dole tana da razara da matan da ta samu a gidan don zaman su hamshakan mata a gari masu kafafen kungiya na kan su.
Wata da take itace hanshakiya a cikin su ce ta fara magana da cewa asha samira banji dadin ganin haka daga gare ki ba ashe kin san baki shirya ba kika taramu a nan don ganin wanan bakin cikin haka ?
Yanzu wanan cin fuskan da mijin nan naku yai muna kinga kin kyauta muna ke nan ko may da har zai dubemu haka a wullakance yaja iyalin shi ya barmu kamar wasu marasa galihu a gurin.
Daga haka bata sake magana ba ta nufi motar ta sauran ma ganin shugaban kungiya ta nufi hanyan fita suka fara sake magana suna fita daga gidan daya bayan daya cikin kunar rai wai an masu wullakanci an nakasa su.
Hankalin Samira yai matukar tashi sosai daga ita sai kawaywn ta biyu aka watse aka barsu a wurin nan suka shiga magana a kaina.
Na yarda da cewan da malam baushe keyi da neman tsari na jiki idan bana sheri bane yana da amfani sosai ga mutum watarana.
Ga yadda irin zamani ya koma a yanzu duk da malamai na fadakarwa amma zuciyan wasu sai kara bushewa yake wurin aikata aikin kaucewa Allah.
Don dai kawai wani buri ko bukata na duniya akan su irin haka ne ga wanan matan don su a nasu ganin kamar duk wata mace a duniya zasu iya shiga da fice su takata yadda ransu ke so a gidan miji idan sun samay ta.
Don koda mijin da baida mata daya su ta aura haka mai shi zai tabbata a duniya ba wata mace sai su haka kuma idan kishiya ko kishiyoyi suka samu ba zasu dauki lokaci a gidan basu watsi da wanan macen ko matar da suka tarar a gidan ba.
Sai dai duk da haka ba wai kullun ne suke nasara akan ko wace mace da suka sama a gida ba akwai wa yanda kan dan fi karfin su a zauna aita fafatawa dasu a gidan Allah ya tsare mu daga sherin irin wa yan nan mata masu mugun hali na rashin tsoron Allah.
Nasan ba komai daddy yakewa wanan rawan kafa haka ba sai yadda zai ga komai ya daidaita a tsakanina dashi wanan karon.
Yayin da su kuma sauran kishiyoyina suke ganin ai asiri ne nai mashi tare kuma da ilimi da kyau din dake gare ni yake min wanan rayuwan haka.
Wanda nina san ba haka bane alamarine na Allah, sai farko idan ka samu daukaka gun Allah sai ya tsare ka ga komai.
Ke dai yar uwa maida al, amarin ki a gun ubangiji a koda yaushe sai Allah ya tsare ki daga duk wani abin ki a gare ki.
Duk wanda ya nufe ki da sheri Allah yana tare da ke sai ya koma a kan mai shi duk wanan aikin dake gabana bai hana ni kullun tsaida dare abokin hirana ba wurin mika koke na ga ubangijina akoda yaushe.
Rana ce kawai nakan dan samu lokacin aiwatar da rayuwana na duniya a cikin sa don shi tashin dare wani alamari ne dake tafiya da sabo da saka abin a zuciyar bawa.
Fitina ce sosai a tsakanin Samira da maigidan yayin da mu kuma sauran iyalin nashi muke a cikin farin ciki da dawowan shi don mun godewa Allah yadda taso taga mun nakasa a kan shi hakan bai samu ba a gare ta don bai shiga guntaba ma balle ta aiwatar da duk wani shiri nata akan shi balle abin yai tasiri gareshi yadda take so.
Don ba karamin gagarumin shiri tayi ba kamar yadda mata da yawa suke wanan irin shirin ga maigida idan ya kwana biyu baya cikin iyalin shi.
Wanan baiwan ne daga Allah don badon Allah yaba tsare bayin sa ba da wata irin shirin da kishiya take a kanta ko daga kai miji baya iya yi ya kalle ka da suna wai abokiyar zaman ta.
Amma da yake abin daga Allah sai kaga ubangiji yana kare bayin sa masu dogaro a kan shi suna yawan kai kukan su a gareshi ko da yaushe.
A nan Allah ya taimakeni a kan Samira don haushin ba nawa bane ni kadai don ya shafi kowan mu saboda ta shiga wurin shi ta samay shi tare da zulfa suna soyewan su washegari da ta koma kuma ta sake samun shi tare da hindatu .
Sai haushin nawa ya rage ya koma a kan su take cewa da kawarta dama hakane ana zaton wuta a makera sai a samayta a masaka.
Don haka tai muna bugun dan kade gaba dayan mu tace mune mukai mata wani sihiri miji ke ganin bakin ta haka daga dawowan shi.
Ranan da girki ya dawo a kaina ne muka kwasa da daddy din don har lokacin ina a kan bakana na rashin yarda dashi da banayi.
Ya kirani a waya yake fadin nazo na samay shi ya dawo nan na shirya na samay shi a falon wuri na samu na zauna daga nesa kada dashi tare da gaida shi da dawowan shi.
Ya amsa min ba tare da ya dago kan shi ba yace maman Jinior ke nan wai ni ban fahinta ba ya fadi yana kokarin rufe takardan dake a hannun shi.
Ya dago yana mai kallona cikin mamaki nake cewa dashi na may fa ke nan daddy don da zaran ya kirani da wanan sunan na maman jinior nasan da akwai magana ke nan daya taso a kaina.
Yace wai har yanzu kina nan akan bakarki ne na kina guduna ina da cuta ko may ?
Nace ni bance kana da cuta ba daddy kawai dai don na fahinta da irin auren nan da kake a yanzu ko a kai tsaye ne ko da binciki gama yadda duniyar nan ta mu ta koma a yanzu.
Murmushi yayi yace dani yayi shine har yakai bana samun kulawan da aka saba bani ko kadan kamar baya.
Nace ba haka bane wanan kawai dai dorowa ne don ni ban ma san ka dawo ba gidan ai.
Yace dani karbi wanan na mika hannuna na karba a cikin ladabi tare da budewa sai naga ai form ne na wani makaran ta a kasan saudiya dake garin madina.
Ga kuma sunayen yarana a jere a ciki su hudu a form din na gani da dan wurin zulfa guda, da sauri na dago kai cikin mamaki ina kallon shi tare da son jin na may ye wanan form din kuma daddy ?
Yace dani kin karan ta aiko ?
Nace na karanta sai dai ban fahinta ba yace ok yaran nan nake son akai su can suyi karatu dukkan su.
Nace dukkan su daddy yace ko baki ra, ayin hakan ne ke nace a, a ni may zance abinda ka zartan ai shine nawa.
Yace good ina da raayin yarana su fahinci addini sosai a rayuwan su tunda Ubangiji ya hore min abinda zan iya daukan nauyin su a hakan dashi.
Masha Allahu nace dashi yace na gama komai akai saura tafiyan su idan lokaci yayi Allah ya kaimu nace tare da fatan Alheri ga wanan tsarin.
Yace haka nake son ji wanan halin naki yasa nake kara son ki a raina ko yaushe Rahama don biyayyan ki a gare ni sai dai kuma gashi ana yabon ki ga sallah kina son kasa yin salati kuma.
Nai murmushi nace ni din kuma daddy may kuma nayi baiyi magana ba ya miko min wani takarda dake gefen shi again yace karan ta wanan mu gani kuma.
Na karba na bude sai naga takardane na test da aikai masu shida Samira din wata shidda da suka wuce a baya.
Hakan na nufin ayi test din ne kafin su daura auren su dashi kuma a sibitin mu ne akai masu wanan gwaji din da nake son gani.
Ina kai karshen takardan na sauke ajiyan zuciya tare da dago kaina na dan kalle shi ina kokarin mika mai takardan.
Ya karba tare da fadin kin gansu da haja yanzu ko akwai sauran wani abinda kike son ji kuma don naga kina daukana ban san abin da nakeyi ba ne ko ?
To ki sani ni jarabar tawa bata kaini ga har na dinga yin abu a ido rufe ba haka yadda kike nufi nakeyi din.
Na dan musguta zamana kadan cikin jin nauyi da kunya ina cewa dashi ni abinda doka ya tabadar nake magana a kai, bawai nace kakai ga hakan bane ai.
Ya ware hannaye shi tare da fadin what ever d case dai yanzu kin gani a zahiri dama na kyale kine naga iya gudun ki.
Murmushin yake nayi tare da dan dagawa na kara mika mai takardan nace abinci fa akawo yanzu ne ko sai anjima.
Yace idan an tausaya min abani don tun karyawan safe danayi ne a cikin nan nawa har yanzu.
Mikewa nayi da nufin zuwa dauko mai abincin nasa sai naji yace dani ki turo min zulfa tazo idan kin tafi na ansa da to na fice falon.
Sai da na shiga guri ta na nufi nawa bangaren inda na fara hada mai kayan abincin da na shirya mai da kaina.
Koda na koma na samay su baram baram da ita tace bata yarda da zancen zuwa danta wani kasa ba naji tana cewa ita ba yaran ke gunta da yawa ba da za, a dauke mata dan ta daya akai wata kasa wai karatu.
Ban tanka su ba na shiga shirin abinda nake a gaban shi tare da sauraren maganganun su din.
A cikin fushi ta bar falon sai lokacin nace dashi tunda kaga hankalinta bai kwanta ba don Allah daddy a bar zancen yaron kawai.
A harzuke yake cewa dani akan may itakeda iko dashi ko ni da zance ga abinda nake so har ta tsaya musanta min ga hakan.
Ni naja bakina na shiru daga hakan shima din shirun yayi na dan wani lokaci kada na juya gare shi tare da fadin bisimillah ga abincin nan.
Komai ya koma muna normal a tsakanin mu dashi ba sauran fitina sai dana fita girki Samira ta karba wanda nake gani a ranan ne ma ta dawo gari.
Mu dai da asuba muke jin kururuwan fitina a gidan wanda tun lokacin ban kara biyewa akan su ba.
Ban kuma sake jin duriyar Samira din ba ma a gidan da sannu loiacin tafiya yara na yayi sai naga ashe ba da dan wurin zulfa za ayi ba ashe.
Sai da na kai su kano sukai sallama da iyayyen mu mukai tafiyan da hajiyan daddy da za a kai asibiti saudiya sai ihisan da muka tafi da ita da Atika.
Makaran ta ba laifi a wurin tsaruwa kuma yaro baya dawowa sai idan ya sauka yayi hadda za, a bari yazo gida ya kwana biyu idan yana da bukatan ci gaba da karatu sai ta koma yaci gaba dayi wasu littafai da kuma fannin boko watau secondary di su har digree.
Abin yai matukar bani shaawa sosai don nasan insha Allahu idan Allah ya raya min su nan gaba kadan zanyi alfahari da su, bani ba har da kasata baki daya da yan uwa.
Bayan mun barsu ne mun dawo masauki nakewa daddy godiya da kuma fatan alheri ga yin hakan da yayi.
Akwai kewa amma da yake karuwa ne ga kowa daurewa nayi ga abin na fitar dasu a raina baki daya.
Bayan mun dawo ne nake samun labarin wai ashe ba karanin fitina akayi da zulfa dashi ba har takai gun iyayye yasa ya janye maganan tafiyan yaron nata.
Ga kuma labarin Samira da tazo har gida tai masu tas har tana ikirarin wai sai mun gani da baki dayan mu abinda zatai muna kamar yadda mukai mata.
Amira da Aisha suka haifi diya su duka maza muka sha buki sosai na suna Nasir ya gama karatun shi shima yafito da aninin shi na su na soja.
Zama dai ne na hakkuri har lokacin a tsakanin mu don ba wai an daina zaman kishin bane a tsakanin mu.
Shekara takwas yarana maza sun zama hazifai na addini tako wani fanni sun zo gida kowan su ya girma sosai.
Ida na kalle su sai naga tankar ba nice na haife su ba da cikina mahaifin su ya zama don sosai yanzu kafan shi ya kama kasa ga arziki ga kuma yara sun girma.
Haka yasa ya bukaci da na aje aikin gwaunatin da nake na zauna gida a cikin iyalina ban yi mashi mussun hakan ba na aje kamar yadda ya bukata na zauna gida ina dan duba asibitin daya bude a kano duk da haka ida aiki ya taso muna zaga jahohi muna aiki da gwaunati din don kwarewar mu ga aikin .
Hajiyan daddy ta rasu don haka muka kwasa sai kano a lokacin yarana duk suna gida baki dayan su kowa ya gan mu sai ya yaba muna.
Mun dawo daga gidan hajiya ta gan mu yaba tsaye tare da wasu mutane a kofan gida suna magana mu gaidasu zamu shiga naji mutumin na
Showing 453001 words to 456000 words out of 456145 words
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22Chapter 23Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32Chapter 33Chapter 34Chapter 35Chapter 36Chapter 37Chapter 38Chapter 39Chapter 40Chapter 41Chapter 42Chapter 43Chapter 44Chapter 45Chapter 46Chapter 47Chapter 48Chapter 49Chapter 50Chapter 51Chapter 52Chapter 53Chapter 54Chapter 55Chapter 56Chapter 57Chapter 58Chapter 59Chapter 60Chapter 61Chapter 62Chapter 63Chapter 64Chapter 65Chapter 66Chapter 67Chapter 68Chapter 69Chapter 70Chapter 71Chapter 72Chapter 73Chapter 74Chapter 75Chapter 76Chapter 77Chapter 78Chapter 79Chapter 80Chapter 81Chapter 82Chapter 83Chapter 84Chapter 85Chapter 86Chapter 87Chapter 88Chapter 89Chapter 90Chapter 91Chapter 92Chapter 93Chapter 94Chapter 95Chapter 96Chapter 97Chapter 98Chapter 99Chapter 100Chapter 101Chapter 102Chapter 103Chapter 104Chapter 105Chapter 106Chapter 107Chapter 108Chapter 109Chapter 110Chapter 111Chapter 112Chapter 113Chapter 114Chapter 115Chapter 116Chapter 117Chapter 118Chapter 119Chapter 120Chapter 121Chapter 122Chapter 123Chapter 124Chapter 125Chapter 126Chapter 127Chapter 128Chapter 129Chapter 130Chapter 131Chapter 132Chapter 133Chapter 134Chapter 135Chapter 136Chapter 137Chapter 138Chapter 139Chapter 140Chapter 141Chapter 142Chapter 143Chapter 144Chapter 145Chapter 146Chapter 147Chapter 148Chapter 149Chapter 150Chapter 151Chapter 152 Chapter 153