ai na duba ku ko ?
Tace nasani ai ba don ni kika zo gidan nan ba don yaushe rabon da kizo gidan nan Sa, ade ?
Zama anty tayi daga gefen gadon da kyat ta zauna tare da maida numfashin ta.
Nan ta fara gaisawa da matan dake dakin ina tsaye daga gefe kofan ina kare ma matan birni kallo.
Can ta hangoni tsaye take cewa Rama zo nan mana ki zauna sai lokacin na karasa kusa da ita maijegon ke cewa zo nan ki zauna ga guri kinji donnke kawai zan tara.
Anty tace ai duk daya idan kin tari kaunana akai dariya suna kokarin mika mata baby dake nade a cikin showel fari tas dashi.
Bata jima rike dashi ba ta miko min shi gani da son yara nan na karbe shi na rugumay ina karewa taron kallo cikin sha,awa.
Sai fira suke kwasa tsakanin su inajin suna mata ba,a wai ashe ta tsofe ne haka ?
Maijegon nace masu ai kunsan ta da wayo taki bari kannen ta su samu sai ita ce mai daukewa.
Anty tace wanan kuma a tambaye ku don kune masu sawa ai bani ba inma rowa ne kukai masu rowa abin.
Aka kwashe da dariya maijegon ke cewa yanzu ko kishiyar ki ta bar nan har da gulman ki mukayi ai.
Anty tai dariya tace shine aikin ku ai dangin miji yanzu nazo shine nima zakuyi nata dani ko ?
Kai ai Zulfa yar uwa tace tace ni kuma yar uwar mijin ki ba kinga ma falo zan koma nasamu Nura muyi zumuncin mu.
Sai lokacin na fahinci mijin mai haihuwan dan uwan anty ne ke nan ita kuma matar yar uwan mijin ta.
Maijegon take cewa ai dama kuna zumuncin ne sai na damu dake dashi duk abu daya ne ba zumuncin.
Waya fada maki lokacin da muke zumutan mu a waya fada maki zaiyi ne ?
Saade baki da dama fa yanzu sabon gidan da kowa ke murnan shiga shine kika karbe masu part din da yafi kyau.
Kai ni saade na shiga uku wata sabuwa kuma ke nan yanzu wai mayye banbancin wanan part din da nasu Aisha ?
Su shi suke so ai, anty tace nikuma shi mijina ya zaba min na zauna ciki sai yaya kw nan.
Sai lokacin wata daga cikin mata ukun da muka samu tai magana tace kaji gaskiya haka nake son namijin da yasan kan shi a samu tare a mutu tare.
Anty tace kin san su matan yanzu su samay ka da mijinka suce sun fika iyawa ne in bashi ba gidan dai ai duk gidan ne ko ?
Maijegon tace barsu kawai indai bros ne karamin aikin shine ya mayar dasu tsihon gidan idan sun matsa ai na fada masu gaskiya, don kowan su sai cika take tana batsewa .
Ji min fa don Allah ijin matar dake zaune tace wai da may suke nufi don kina ta ffarko su amare sai ya fifita su ke nan ko?
Aini yaya yai min daidai wallahi don bai daukan raini ga kan shi da matar shi ba don haka na da wa yan nan da kike gani ko mu yan uwan shi sai munyi da gaske mu shiga gidan shi.
Yanzu dai kuka fada ai da bakin ku inji anty saade tana dariya
Maijego tace ni hajiya na rasa may yasa take son saka kanta cikin irin wanan magana ranan naje gida baba ya kirata ina jin suna case din dashi akan maganan.
Anty ce ta kawar da zancen dacewa yauwa fatima dama ina son ganin ki wallahi don wanan kaunan tawa nake son tayi joining din school din ku.
Matar da ta kira da fatima tai saurin kallona tace har ta gama secondry ne wanan din ?
Tagama almost two years ke nan yanzu masha Allahu inji matar tace karama da ita haka ?
Tace yanzu zan mata kokari tasamu matric ta jona sai tayi jam idan lokaci yayi mugani.
Nan dai sukai ta magana yadda za, ayi kan karatuna ina sauraren su duk dadi ya kamani cikin raina tace wa matar zata turo da komai nawa a kawo mata insha Allahu.
Bamu jima ba mukai masu sallama anty ta ciro kudi mai yawa ta dora saman gefen showel din da baby ke ciki tace asaya mai pant dashi.
Muna tafe ba wanda yai magana sai zuwa can take cewa zan tura ki da hamza gobe ai browsing din takardan ki mu gani sai ai amfani dashi.
Wani shago ta tsayar da mota muka shiga abubuwan amfanin mu da babu a gida ta saya masu yawa ina kallon yadda ake komai har biya muka dawo gida .
A falo muka zube mun samu yara sun dawo daga schools lokacin nan muka shiririce dasu don sunyo kaina muna hira na cire masu uniform din su na saka masu kayan gida na basu abincin su .
Shi Nasir nasan halin shi don haka na koma kusa dashi ina da yake na zauna yana ci muna dan hira har na samu ya dan ci abincin nasa.
Duk abinda mukeyi anty tana kallon mu a fakaice tana yabawa da irin hikimar da nake wa yaran wanda ko ita uwar su bata da lokacin masu hakan da nake masu.
Suna gamawa muka fara shirmayn karatun mu ina biye masu kafin lesson teacher din yazo.
Sai ga hanifa yar gurin Zulfa ta shigo inda muke ko uniform ba a cire mata ba lokacin ta zauna tare da mu ana ta wasa da karatu a lokaci daya.
Bata fi minti ko goma da shigowa ba sai ga wata mata badai tsohuwa bace can ta shigo da sallama tana ganin mu hankalin ta yana kan hanifa dake wasa da Amira take cewa hajiya barka da hutawa .
Anty ta karba mata tace hanifa wai kizo inji maman ki sai yarinyar tace bazata je ba nan matar ta shiga lalashin yarinyar amma fir taki bin matar.
Nace ki tafi ki barta mana tunda tace bata zuwa matar ta marairaice tace idan na tafi bada ita ba fada hajiya zatayi min .
Da kyat na lalashi yarinyar nace yanzu zamu hadu a gurin lesson da ita ta tafi kawai amma yarinyar taki binta.
Matar ta juya ta fita sai lokacin anty dake kishingide tana kallon mu tai magana tace ai yanzu dawowa zatayi don bazasu barta nan ba.
Suna ganin idan sun barta cuta mata za, ayi ne don haka ki lalashe ta ta tafi don Allah Rama rarashe ta tafi please.
Kafin anty takai aya ga maganan ta sai ga matan da dawo falon fuskan ta ba dadin gani da gani an mata fada ne sosai tana zuwa ta sukkuci yarinyar a kafadan ta tana ihu tana kuka ta fita da ita daga falon namu.
Anty tace may na fada maki ai basu bari yarinyar ta zauna a nan zuwan ki ne ma har take shigowa inda muke dan zaman da kukayi da ita ta dan saba da nan din.
Baifi minti uku ba Nasir na saman kaina wai yana min fakin ina zaune na ishishire kafana zaune saman ties .
Maigidan ne ya shigo rike da hannun yarinyar dake kuka suna shigowa ta sake hannun ta da rikon uban tayo kaina tana dariya da cewa itama zatai min kitso ne.
Anty na ganin su take cewa kadawo da ita ne kuma yace a hannun wanan bakuwar matar na ganta tana kuka wai ance ta dauko ta da karfi ta maida ita part din su.
Nikan ina ganin ya shigo ina kokatin tashi nabar falon kamar hadin baki yaran duk suka haye min jiki wai kitso zasuyi min dukkan su sai kokuwa suke kowa nason ya rike min kai na.
Kallon mu iyayyen keyi anty tace kaga shirmay da take so don Rama na biye masu suna yadda suke so da ita.
Yace ai yaro haka yake so dama shi ko yaushe yana inda yake ganin fuska ne shi amma su basu ganewa don kishin tsiya.
Muryan Zulfane a falon a fusace take cewa oya Hanifa come to mummy what are you doing here.
Yarinyar ta bata rai tare makewa a jiki na tana cewa mummy ki barni gurin anty please.
Zulfa get out kafin raina ya baci idan ba haka ba yanzu ranki zai baci ga hukuncin da zan yake a kan ki.
Wani kallo tai mashi sai dai yadda taga fuskan shi yasa takasa fadin abinda take da niyar fadi a lokacin.
Ta juya har takai kofa take cewa wanan ai rashin adalci ne yaya za aiwa mutum dole kan dan shi kowa ai yana da nasa yarinke abinsa mana.
Idan kai an mai dakai mijin tace ai ba zaka mayar damu muma sai yadda akayi damu ba da diyan mu a gidan kafin ta ci gaba da magana.
Ya kara fadi a hasale ba ita da akaiwa ba har mu dake falon sai da muka kadu idon shi ya kade yai ja yace get out i said
Da sauri tabar part din ranta a bace shima yabi bayan ta ba tare da yai magana ba.
Gaba dayan mu hankalin mu ya koma kansu kaina na sadda a kasa don sun bani tsoro gaba dayan su.
Mama tace ikon Allah zamanin nan ina zaki damu ne wai haka ni na taba ganin irin haka gida daya ace yaro ba zaiyi yadda yake so ba.
Anty tai murmushi tace gani suke yadda zukatan su yake akaina hakan ne nima zan aikatawa nasu diyan .
Niko yaro koba dan mijina bane ina son shi balle dan da mijina ya haifa yan uwan haihuwa diyana.
Allah dai ya kara haushe ki kan su kawai za, ace don sunyi nisa sai addua ai kishi ba hauka bane.
Murmushi anty tayi ta mayar da hankalin ta inda muke zaune muna sha, anin mu hankalin a kwance ba abinda ya damay mu.
Shaawan mu ne yakamata yadda taga na kwantar da hankalina kamar ba abinda ya taba faruwa dani a baya.
Gashi yanzu na kwantar da hankalina a gurin ta na gyagije kamar ba wani damuwa a tare dani.
Lesson teacher ne yazo muka fita zuwa lesson gaba dayan mu, nan muka hade da yar gurin hindatu itama a kusa dani tazo ta zauna tana ta zuba min surutu.
Uban daga inda yake mu bamu ganin shi yana kallon yadda yaran ke ta shige min a jikina.
Mamaki yakeyi yadda yaran sukai saurin sabawa dani haka sosai har Nasir da ke da tsauri a cikin su amma yana yarda dani haka.
Yana matukar tausayawa anty saade amma yanzu ya fahinci amun wanan yarinyar a kusa da ita ya sa ta dan samu sakewa sosai.
Don ko yawan tashi da jikin ta keyi yanzu ta daina yin haka sosai gashi mahaifiyar shi ta matsa kan sai yasa saade ta sallami wanan yarinyar don yaki yarda da hankan ne yasa sauran matan nashi dauko wasu suma su zauna dasu abinda bayaso a gidan shi amma babu yadda ya iya don samun lafiyan matar tashi ya yarde da hakan badon yaso ba.
Yanzu gashi a dalilin haka yaran shi na zama guri daya suyi wasan su da dariya wanda hakan zai kawo masu shakuwa a tsakanin su.
****** ********* ******
Zaune take a dan dakin da aka gyara mata dakin tsoho ne baida fadi sosai rufin shi duk ya tsofe sosai .
Tana gefe daya a takure cikin damuwa abinda tsohon nan yai mata a daren jiya tana ganin shi kamar baida karfi amma yafita karfi sosai yadda ya makureta ya nuna mata karfin maza duk ihu da shure shuren da takeyi sai da ya kai gareta.
Ga gari ya waye sai wani dan guntu kunu mai sanyj aka kawo mata duk kasari a cikin sa babu ko dadin ganin shi.
Ga yunwa yanzu yana damun ta ga wanan abin da take tunane da ya tsaya mata a rai idanuwan ta na kallon kofan dakin.
A inda take a zaune taga an bankado kofan dakin da karfi wata dattijuwa tagani a tsaye a kanta tana mata kallon banza tace da ita.
Ke may kike nufi da bazaki fito ki yi ko shara ba ko kin samu wurin mike kafa ne sai dare yayi ki cika mutane da ihu irin najiya kamar kanki aka fara aure.
Ban masan ihun dakikeyiwa mutane ba kamar sabon abu a gareki bayan kin gama ba yan kwararo kanki a garka.
An dai ji kunya wallahi wai budurwa a haka nakashe babu abin kai gida anan duk bakin tallan da ku kai wa uwar ku ta kasa sai maki ko yar katifan kada kizo dashi.
Ta karewa dakin kallo tana cewa ni ban maga wani abin kishi ba anan don dake da yar sadaka mai gindin banza duk daya kuke a gidan nan.
Kai koma sadaka aka bashi ke ai yafi nan kishi da wanan abin kunyan haka.
Indai da kwadai da wullakanci maza ki fito ga sharan gida nan idan kin gama ki wanke kwanukan da aka bata jiya.
Daga inda lawisa take zaune ta watso mata kallo tace ni ba zama nazo yi da tsohon mijin ku ba balle ki ce kin samu yar aiki don haka ki nemi mai maki wanan aiki.
Har ta kai kofa ta dawo baya tace towoo mara kunya dama nasan da halinki ba yau ba to ki sani kin samu tsohuwar zamani don zamuyu daidai dake ne a gidan nan.
Lawisa tace ai bana tsoron muyi daidai din ko kashe ni zakuyi keda mijin naku sai dai ku kashe ni amma bazan taba ko kara ba a gidan nan .
Muzuba dake ai jiki magayi wallahi ni dake a gidan nan kafin su ci gaba sukaji muryan su Rukaiyya ga maigidan a bayan su tafe cikin hasala shima.
Tana ganin yan uwan ta ta mike tsaye Rukaiyya tace maza tazo su tafi gida yau wanan bakin auren ya mutu ke nan.
Kofan Jatau ya tsaya yace sai yaga inda zasu fita da ita a gidan shi don babu shegen da zai fitar mai da matar shi.
Kudin shi yasa ya auro ta don haka basu isa su fitar da ita gidan nan ba nan suka shiga zagi suzaga ya zaga.
Rukaiya na ganin zai bata masu lokaci ta bangaje shi suka kwasa a guje yan gidan suka biyo su suna atare atare suka samu suka fice daga gidan.
Da kyat Jatau ya mike sai sannu yara da mata ke mashi don har ya gurje a gwiwan hannun shi.
Gidan maigari ya nufa a hasale yana zuwa ya labarta masu abinda ke faruwa a gidan shi.
Nan aka saka salati maigari ya tura aje azo da baba da mama lokacin yaran na mayar mata da yadda sukayi da Jatau a gidan sa da mutanen gidan.
Sukaji sallaman yaron maigari Rukaiyya ce ta fita don ganin mai sallama Lawisa sai kuka take wiwi tana Allah ya isa ga iyayyen ta da suka cuce ta suka kaita gidan wanan bakin tsohon kazami.
Rukaiyya ta dawo take fada masu ai yaron maigari ne yazo gidan yake neman mahaifin su.
Mama tace yafita ya tafi kasuwan kauye akace ance azo da mama nan mama tace babu inda zata sai mijin ta ya dawo.
Dole yaron maigari ya koma ya fadi sakon ta akace tana da gaskiya Jatau yayi hakkuri har lokacin da baba ya dawo sai a zauna.
Nan suka wuni mama da yaranta suna kulla abinda zasu yi idan sun je gurin maigari don sun san baba ba zai dauki wani matakin da ya dace ba ita ko ta sha alwashin sai ta debi wani abu gun Jatau da zata gyara dakin diyan ta dashi ta fitar da ita kunyan daki.
Sai yamma lis baba ya dawo gidan kamar kullun bai ko kai zama cin abinci ba yaron maigari ya sallama mashi yafita gurin shi.
Can ya dawo yana kwadawa mama kira tun a kofan gida tasan da maganan tafito cikin shirin ta tana cewa lafiya yake mata wanan kiran haka ?
Yace may Lawisa ta dawo yi gidan nan bayan an kaita gidan mijin ta don yanzu yaron maigari yazo yana sanar dashi halin da ake ciki.
Mama tace eh tana gida ita ta tura a dauko mata yar ta tunda yazo wa mutane da rashin mutunci har gida saboda yaji dafin ta bashi yarta ai dama kudin bazawara ya bayar bana auren budurwa ba.
Yanzu ko bata mayar mai da yarta sai ya zube mata kudin auren budurwa zata bari lawisa ta koma gidan nan nan.
Baba yace wai lauratu may kike so ne a duniyan nan wanan abin fa duk kece kika jawo shi ba wani ba don da baki karbi kudin shi ba ba zai saka mu a gaba ba hakan nan.
Wanan ma ai rufin asirin ki ne da yar ki don in bashi din ba da ya aure ta ya rufa mata asiri wayazo ya taya ta a gidan da sunan aure.
Tace dama ai bazaka ga laifin yarka da ta tsale ke ra gudu zuwa birni ba ita da aka biya kudin kan ta.
Don Rahama da uwarta sunfi karfin ka shine zaka ce dani haka ita Rahaman har wani farin jini ne da ita da tsufi ke zuwa neman ta gidan nan da zakaiwa diya na gorin aure.
Ko dai tsufi ne ke zuwa ta daifi wa yanda ke zaune gida suna aikata
Showing 66001 words to 69000 words out of 456145 words
Tace nasani ai ba don ni kika zo gidan nan ba don yaushe rabon da kizo gidan nan Sa, ade ?
Zama anty tayi daga gefen gadon da kyat ta zauna tare da maida numfashin ta.
Nan ta fara gaisawa da matan dake dakin ina tsaye daga gefe kofan ina kare ma matan birni kallo.
Can ta hangoni tsaye take cewa Rama zo nan mana ki zauna sai lokacin na karasa kusa da ita maijegon ke cewa zo nan ki zauna ga guri kinji donnke kawai zan tara.
Anty tace ai duk daya idan kin tari kaunana akai dariya suna kokarin mika mata baby dake nade a cikin showel fari tas dashi.
Bata jima rike dashi ba ta miko min shi gani da son yara nan na karbe shi na rugumay ina karewa taron kallo cikin sha,awa.
Sai fira suke kwasa tsakanin su inajin suna mata ba,a wai ashe ta tsofe ne haka ?
Maijegon nace masu ai kunsan ta da wayo taki bari kannen ta su samu sai ita ce mai daukewa.
Anty tace wanan kuma a tambaye ku don kune masu sawa ai bani ba inma rowa ne kukai masu rowa abin.
Aka kwashe da dariya maijegon ke cewa yanzu ko kishiyar ki ta bar nan har da gulman ki mukayi ai.
Anty tai dariya tace shine aikin ku ai dangin miji yanzu nazo shine nima zakuyi nata dani ko ?
Kai ai Zulfa yar uwa tace tace ni kuma yar uwar mijin ki ba kinga ma falo zan koma nasamu Nura muyi zumuncin mu.
Sai lokacin na fahinci mijin mai haihuwan dan uwan anty ne ke nan ita kuma matar yar uwan mijin ta.
Maijegon take cewa ai dama kuna zumuncin ne sai na damu dake dashi duk abu daya ne ba zumuncin.
Waya fada maki lokacin da muke zumutan mu a waya fada maki zaiyi ne ?
Saade baki da dama fa yanzu sabon gidan da kowa ke murnan shiga shine kika karbe masu part din da yafi kyau.
Kai ni saade na shiga uku wata sabuwa kuma ke nan yanzu wai mayye banbancin wanan part din da nasu Aisha ?
Su shi suke so ai, anty tace nikuma shi mijina ya zaba min na zauna ciki sai yaya kw nan.
Sai lokacin wata daga cikin mata ukun da muka samu tai magana tace kaji gaskiya haka nake son namijin da yasan kan shi a samu tare a mutu tare.
Anty tace kin san su matan yanzu su samay ka da mijinka suce sun fika iyawa ne in bashi ba gidan dai ai duk gidan ne ko ?
Maijegon tace barsu kawai indai bros ne karamin aikin shine ya mayar dasu tsihon gidan idan sun matsa ai na fada masu gaskiya, don kowan su sai cika take tana batsewa .
Ji min fa don Allah ijin matar dake zaune tace wai da may suke nufi don kina ta ffarko su amare sai ya fifita su ke nan ko?
Aini yaya yai min daidai wallahi don bai daukan raini ga kan shi da matar shi ba don haka na da wa yan nan da kike gani ko mu yan uwan shi sai munyi da gaske mu shiga gidan shi.
Yanzu dai kuka fada ai da bakin ku inji anty saade tana dariya
Maijego tace ni hajiya na rasa may yasa take son saka kanta cikin irin wanan magana ranan naje gida baba ya kirata ina jin suna case din dashi akan maganan.
Anty ce ta kawar da zancen dacewa yauwa fatima dama ina son ganin ki wallahi don wanan kaunan tawa nake son tayi joining din school din ku.
Matar da ta kira da fatima tai saurin kallona tace har ta gama secondry ne wanan din ?
Tagama almost two years ke nan yanzu masha Allahu inji matar tace karama da ita haka ?
Tace yanzu zan mata kokari tasamu matric ta jona sai tayi jam idan lokaci yayi mugani.
Nan dai sukai ta magana yadda za, ayi kan karatuna ina sauraren su duk dadi ya kamani cikin raina tace wa matar zata turo da komai nawa a kawo mata insha Allahu.
Bamu jima ba mukai masu sallama anty ta ciro kudi mai yawa ta dora saman gefen showel din da baby ke ciki tace asaya mai pant dashi.
Muna tafe ba wanda yai magana sai zuwa can take cewa zan tura ki da hamza gobe ai browsing din takardan ki mu gani sai ai amfani dashi.
Wani shago ta tsayar da mota muka shiga abubuwan amfanin mu da babu a gida ta saya masu yawa ina kallon yadda ake komai har biya muka dawo gida .
A falo muka zube mun samu yara sun dawo daga schools lokacin nan muka shiririce dasu don sunyo kaina muna hira na cire masu uniform din su na saka masu kayan gida na basu abincin su .
Shi Nasir nasan halin shi don haka na koma kusa dashi ina da yake na zauna yana ci muna dan hira har na samu ya dan ci abincin nasa.
Duk abinda mukeyi anty tana kallon mu a fakaice tana yabawa da irin hikimar da nake wa yaran wanda ko ita uwar su bata da lokacin masu hakan da nake masu.
Suna gamawa muka fara shirmayn karatun mu ina biye masu kafin lesson teacher din yazo.
Sai ga hanifa yar gurin Zulfa ta shigo inda muke ko uniform ba a cire mata ba lokacin ta zauna tare da mu ana ta wasa da karatu a lokaci daya.
Bata fi minti ko goma da shigowa ba sai ga wata mata badai tsohuwa bace can ta shigo da sallama tana ganin mu hankalin ta yana kan hanifa dake wasa da Amira take cewa hajiya barka da hutawa .
Anty ta karba mata tace hanifa wai kizo inji maman ki sai yarinyar tace bazata je ba nan matar ta shiga lalashin yarinyar amma fir taki bin matar.
Nace ki tafi ki barta mana tunda tace bata zuwa matar ta marairaice tace idan na tafi bada ita ba fada hajiya zatayi min .
Da kyat na lalashi yarinyar nace yanzu zamu hadu a gurin lesson da ita ta tafi kawai amma yarinyar taki binta.
Matar ta juya ta fita sai lokacin anty dake kishingide tana kallon mu tai magana tace ai yanzu dawowa zatayi don bazasu barta nan ba.
Suna ganin idan sun barta cuta mata za, ayi ne don haka ki lalashe ta ta tafi don Allah Rama rarashe ta tafi please.
Kafin anty takai aya ga maganan ta sai ga matan da dawo falon fuskan ta ba dadin gani da gani an mata fada ne sosai tana zuwa ta sukkuci yarinyar a kafadan ta tana ihu tana kuka ta fita da ita daga falon namu.
Anty tace may na fada maki ai basu bari yarinyar ta zauna a nan zuwan ki ne ma har take shigowa inda muke dan zaman da kukayi da ita ta dan saba da nan din.
Baifi minti uku ba Nasir na saman kaina wai yana min fakin ina zaune na ishishire kafana zaune saman ties .
Maigidan ne ya shigo rike da hannun yarinyar dake kuka suna shigowa ta sake hannun ta da rikon uban tayo kaina tana dariya da cewa itama zatai min kitso ne.
Anty na ganin su take cewa kadawo da ita ne kuma yace a hannun wanan bakuwar matar na ganta tana kuka wai ance ta dauko ta da karfi ta maida ita part din su.
Nikan ina ganin ya shigo ina kokatin tashi nabar falon kamar hadin baki yaran duk suka haye min jiki wai kitso zasuyi min dukkan su sai kokuwa suke kowa nason ya rike min kai na.
Kallon mu iyayyen keyi anty tace kaga shirmay da take so don Rama na biye masu suna yadda suke so da ita.
Yace ai yaro haka yake so dama shi ko yaushe yana inda yake ganin fuska ne shi amma su basu ganewa don kishin tsiya.
Muryan Zulfane a falon a fusace take cewa oya Hanifa come to mummy what are you doing here.
Yarinyar ta bata rai tare makewa a jiki na tana cewa mummy ki barni gurin anty please.
Zulfa get out kafin raina ya baci idan ba haka ba yanzu ranki zai baci ga hukuncin da zan yake a kan ki.
Wani kallo tai mashi sai dai yadda taga fuskan shi yasa takasa fadin abinda take da niyar fadi a lokacin.
Ta juya har takai kofa take cewa wanan ai rashin adalci ne yaya za aiwa mutum dole kan dan shi kowa ai yana da nasa yarinke abinsa mana.
Idan kai an mai dakai mijin tace ai ba zaka mayar damu muma sai yadda akayi damu ba da diyan mu a gidan kafin ta ci gaba da magana.
Ya kara fadi a hasale ba ita da akaiwa ba har mu dake falon sai da muka kadu idon shi ya kade yai ja yace get out i said
Da sauri tabar part din ranta a bace shima yabi bayan ta ba tare da yai magana ba.
Gaba dayan mu hankalin mu ya koma kansu kaina na sadda a kasa don sun bani tsoro gaba dayan su.
Mama tace ikon Allah zamanin nan ina zaki damu ne wai haka ni na taba ganin irin haka gida daya ace yaro ba zaiyi yadda yake so ba.
Anty tai murmushi tace gani suke yadda zukatan su yake akaina hakan ne nima zan aikatawa nasu diyan .
Niko yaro koba dan mijina bane ina son shi balle dan da mijina ya haifa yan uwan haihuwa diyana.
Allah dai ya kara haushe ki kan su kawai za, ace don sunyi nisa sai addua ai kishi ba hauka bane.
Murmushi anty tayi ta mayar da hankalin ta inda muke zaune muna sha, anin mu hankalin a kwance ba abinda ya damay mu.
Shaawan mu ne yakamata yadda taga na kwantar da hankalina kamar ba abinda ya taba faruwa dani a baya.
Gashi yanzu na kwantar da hankalina a gurin ta na gyagije kamar ba wani damuwa a tare dani.
Lesson teacher ne yazo muka fita zuwa lesson gaba dayan mu, nan muka hade da yar gurin hindatu itama a kusa dani tazo ta zauna tana ta zuba min surutu.
Uban daga inda yake mu bamu ganin shi yana kallon yadda yaran ke ta shige min a jikina.
Mamaki yakeyi yadda yaran sukai saurin sabawa dani haka sosai har Nasir da ke da tsauri a cikin su amma yana yarda dani haka.
Yana matukar tausayawa anty saade amma yanzu ya fahinci amun wanan yarinyar a kusa da ita ya sa ta dan samu sakewa sosai.
Don ko yawan tashi da jikin ta keyi yanzu ta daina yin haka sosai gashi mahaifiyar shi ta matsa kan sai yasa saade ta sallami wanan yarinyar don yaki yarda da hankan ne yasa sauran matan nashi dauko wasu suma su zauna dasu abinda bayaso a gidan shi amma babu yadda ya iya don samun lafiyan matar tashi ya yarde da hakan badon yaso ba.
Yanzu gashi a dalilin haka yaran shi na zama guri daya suyi wasan su da dariya wanda hakan zai kawo masu shakuwa a tsakanin su.
****** ********* ******
Zaune take a dan dakin da aka gyara mata dakin tsoho ne baida fadi sosai rufin shi duk ya tsofe sosai .
Tana gefe daya a takure cikin damuwa abinda tsohon nan yai mata a daren jiya tana ganin shi kamar baida karfi amma yafita karfi sosai yadda ya makureta ya nuna mata karfin maza duk ihu da shure shuren da takeyi sai da ya kai gareta.
Ga gari ya waye sai wani dan guntu kunu mai sanyj aka kawo mata duk kasari a cikin sa babu ko dadin ganin shi.
Ga yunwa yanzu yana damun ta ga wanan abin da take tunane da ya tsaya mata a rai idanuwan ta na kallon kofan dakin.
A inda take a zaune taga an bankado kofan dakin da karfi wata dattijuwa tagani a tsaye a kanta tana mata kallon banza tace da ita.
Ke may kike nufi da bazaki fito ki yi ko shara ba ko kin samu wurin mike kafa ne sai dare yayi ki cika mutane da ihu irin najiya kamar kanki aka fara aure.
Ban masan ihun dakikeyiwa mutane ba kamar sabon abu a gareki bayan kin gama ba yan kwararo kanki a garka.
An dai ji kunya wallahi wai budurwa a haka nakashe babu abin kai gida anan duk bakin tallan da ku kai wa uwar ku ta kasa sai maki ko yar katifan kada kizo dashi.
Ta karewa dakin kallo tana cewa ni ban maga wani abin kishi ba anan don dake da yar sadaka mai gindin banza duk daya kuke a gidan nan.
Kai koma sadaka aka bashi ke ai yafi nan kishi da wanan abin kunyan haka.
Indai da kwadai da wullakanci maza ki fito ga sharan gida nan idan kin gama ki wanke kwanukan da aka bata jiya.
Daga inda lawisa take zaune ta watso mata kallo tace ni ba zama nazo yi da tsohon mijin ku ba balle ki ce kin samu yar aiki don haka ki nemi mai maki wanan aiki.
Har ta kai kofa ta dawo baya tace towoo mara kunya dama nasan da halinki ba yau ba to ki sani kin samu tsohuwar zamani don zamuyu daidai dake ne a gidan nan.
Lawisa tace ai bana tsoron muyi daidai din ko kashe ni zakuyi keda mijin naku sai dai ku kashe ni amma bazan taba ko kara ba a gidan nan .
Muzuba dake ai jiki magayi wallahi ni dake a gidan nan kafin su ci gaba sukaji muryan su Rukaiyya ga maigidan a bayan su tafe cikin hasala shima.
Tana ganin yan uwan ta ta mike tsaye Rukaiyya tace maza tazo su tafi gida yau wanan bakin auren ya mutu ke nan.
Kofan Jatau ya tsaya yace sai yaga inda zasu fita da ita a gidan shi don babu shegen da zai fitar mai da matar shi.
Kudin shi yasa ya auro ta don haka basu isa su fitar da ita gidan nan ba nan suka shiga zagi suzaga ya zaga.
Rukaiya na ganin zai bata masu lokaci ta bangaje shi suka kwasa a guje yan gidan suka biyo su suna atare atare suka samu suka fice daga gidan.
Da kyat Jatau ya mike sai sannu yara da mata ke mashi don har ya gurje a gwiwan hannun shi.
Gidan maigari ya nufa a hasale yana zuwa ya labarta masu abinda ke faruwa a gidan shi.
Nan aka saka salati maigari ya tura aje azo da baba da mama lokacin yaran na mayar mata da yadda sukayi da Jatau a gidan sa da mutanen gidan.
Sukaji sallaman yaron maigari Rukaiyya ce ta fita don ganin mai sallama Lawisa sai kuka take wiwi tana Allah ya isa ga iyayyen ta da suka cuce ta suka kaita gidan wanan bakin tsohon kazami.
Rukaiyya ta dawo take fada masu ai yaron maigari ne yazo gidan yake neman mahaifin su.
Mama tace yafita ya tafi kasuwan kauye akace ance azo da mama nan mama tace babu inda zata sai mijin ta ya dawo.
Dole yaron maigari ya koma ya fadi sakon ta akace tana da gaskiya Jatau yayi hakkuri har lokacin da baba ya dawo sai a zauna.
Nan suka wuni mama da yaranta suna kulla abinda zasu yi idan sun je gurin maigari don sun san baba ba zai dauki wani matakin da ya dace ba ita ko ta sha alwashin sai ta debi wani abu gun Jatau da zata gyara dakin diyan ta dashi ta fitar da ita kunyan daki.
Sai yamma lis baba ya dawo gidan kamar kullun bai ko kai zama cin abinci ba yaron maigari ya sallama mashi yafita gurin shi.
Can ya dawo yana kwadawa mama kira tun a kofan gida tasan da maganan tafito cikin shirin ta tana cewa lafiya yake mata wanan kiran haka ?
Yace may Lawisa ta dawo yi gidan nan bayan an kaita gidan mijin ta don yanzu yaron maigari yazo yana sanar dashi halin da ake ciki.
Mama tace eh tana gida ita ta tura a dauko mata yar ta tunda yazo wa mutane da rashin mutunci har gida saboda yaji dafin ta bashi yarta ai dama kudin bazawara ya bayar bana auren budurwa ba.
Yanzu ko bata mayar mai da yarta sai ya zube mata kudin auren budurwa zata bari lawisa ta koma gidan nan nan.
Baba yace wai lauratu may kike so ne a duniyan nan wanan abin fa duk kece kika jawo shi ba wani ba don da baki karbi kudin shi ba ba zai saka mu a gaba ba hakan nan.
Wanan ma ai rufin asirin ki ne da yar ki don in bashi din ba da ya aure ta ya rufa mata asiri wayazo ya taya ta a gidan da sunan aure.
Tace dama ai bazaka ga laifin yarka da ta tsale ke ra gudu zuwa birni ba ita da aka biya kudin kan ta.
Don Rahama da uwarta sunfi karfin ka shine zaka ce dani haka ita Rahaman har wani farin jini ne da ita da tsufi ke zuwa neman ta gidan nan da zakaiwa diya na gorin aure.
Ko dai tsufi ne ke zuwa ta daifi wa yanda ke zaune gida suna aikata
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22Chapter 23 Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32Chapter 33Chapter 34Chapter 35Chapter 36Chapter 37Chapter 38Chapter 39Chapter 40Chapter 41Chapter 42Chapter 43Chapter 44Chapter 45Chapter 46Chapter 47Chapter 48Chapter 49Chapter 50Chapter 51Chapter 52Chapter 53Chapter 54Chapter 55Chapter 56Chapter 57Chapter 58Chapter 59Chapter 60Chapter 61Chapter 62Chapter 63Chapter 64Chapter 65Chapter 66Chapter 67Chapter 68Chapter 69Chapter 70Chapter 71Chapter 72Chapter 73Chapter 74Chapter 75Chapter 76Chapter 77Chapter 78Chapter 79Chapter 80Chapter 81Chapter 82Chapter 83Chapter 84Chapter 85Chapter 86Chapter 87Chapter 88Chapter 89Chapter 90Chapter 91Chapter 92Chapter 93Chapter 94Chapter 95Chapter 96Chapter 97Chapter 98Chapter 99Chapter 100Chapter 101Chapter 102Chapter 103Chapter 104Chapter 105Chapter 106Chapter 107Chapter 108Chapter 109Chapter 110Chapter 111Chapter 112Chapter 113Chapter 114Chapter 115Chapter 116Chapter 117Chapter 118Chapter 119Chapter 120Chapter 121Chapter 122Chapter 123Chapter 124Chapter 125Chapter 126Chapter 127Chapter 128Chapter 129Chapter 130Chapter 131Chapter 132Chapter 133Chapter 134Chapter 135Chapter 136Chapter 137Chapter 138Chapter 139Chapter 140Chapter 141Chapter 142Chapter 143Chapter 144Chapter 145Chapter 146Chapter 147Chapter 148Chapter 149Chapter 150Chapter 151Chapter 152Chapter 153