Rama yadda kika saba yi muna wanan dawainiyar kina kula dani da yaran nan da zuciya daya ina gujewa ranan da zakice zaki bar mu wallahi.
Shiyasa nake kokarin ganin baki barmu ba har abada mu zauna dake cikin farin ciki da jin dadi amma bazaki gane ba ke yanzu.
Shima din da yake ganin yaran kina ahagwaba su ai bai ganewa ne yanzu ne suke samun kulawa irun na uwa daya dace yaro ya samu.
Yaushe suka samu kula irin haka a gurina kullun yau ciwo gobe lafiya nake sai in share watan ni ma basu ganni ba suna zaune ana gwada masu ukuba gurin kishiya.



ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE, ,


IDAN KIN BIYA KIKA TURAWA WANDA BAI BIYA BA HAKKIN AMANA YANA KAN KI DON ALLAH NA GANIN KI YAR UWA, , , , ,

29
Bukin sallah akeyi don haka gidan bai rabuwa da baki ta ko ina shigowa akeyi wanda kusan yan uwan dangin mai gidan ne ke shigowa yawon barka da sallah gidan.
Farida kan washe garin sallah ta hada abin arzikin ta sai ganin ta mukayi tana cewa anty ni zan tafi gida.
Anty take cewa yau din nan Farida babu ko magana ta da yi murmushi tana gyara jakar kayan ta dake kafadan tana cewa akwai friends dina da muke yawon sallah tare dasu sune suke ta damuna da kira tun jiya.
Daga inda nake zaune ina mata murmushi nace yanzu kina nufin tafiya zakiyi ki barni gashi munce zamu gida Zarah yawon sallah.
Tace tafiyan ta kama ne nayi shi ai Idan ta tafi saina rakaki Rahma inji Gajiye nace shike nan kuwa Gajiye mu dawo idan kin zo mu baki labari ai.
Namike na rakata har bakin get da kayan ta Hamza driver ne ya tafi da ita gida a lokacin .
Na dawo na samu gajiye na magana da anty take cewa tun jiya da dare take fushi ban san may akai mata ba dai.
Ranan dai ce min tayi wai ita da take yar uwar maigidan ma ba, a kulata kamar yadda ake kula Rahma a gidan nan.
Anty tace kyale mahaukaci kune baku gane may take nufi ba fa ita adole wurin nan daddy ku take so.
Lokaci daya mukace ita Faridan ke son daddy anty tayi yaya da daddy idan ma yace yana son ta.
Kai amma Farida bata da kunya mutum mai mata haka kamar daddy zatace wai tana kyarkyaran shi a gaban matan shi.
Gajiye Tace yau she ma zai so mace haka kamar Farida wanda keda mata irin haka a gida.
Anty tace kada kuce haka ita rayuwan duniya haka take dama kuma Allah yafimu sanin abin daya dace a rayuwan mu don haka idan da aure a tsakanin shi da wata a gidan nan cikin ku sai ayi ai.
Kallon mamaki naiwa anty wai ita anty wata irin mace ce mai saukin kai ne irin haka ?
Hakan fa ranan da Hindatu tai muna kazafi sai budan baki tayi wai zatai farin ciki idan daddy ya aure ni.
Ko wace mace na kishin mijin ta karara a fili amma ita anty sam bata nuna kishin mijin ta irin na sauran mata da sukeyi.
Gajiye tace haba hajiya ina Farida ina shiga tsakiyan ku kishi yaushe ma Alhaji zai tsaya kallon wata Farida can.
Anty tace kai Gajiye akwai ki da wani magana wallahi ai kamar yadda yaro yake dan son jiki zagi ko duka bai sawa yaro natsuwa haka na miji yake shima.
Namiji da zaran mace ta iya tattalin shi tasan takon halaiyan shi shike nan idan tana da hakkuri ta gama da namiji yi nayi bari na bari sai kiji zama ya dore ana wance ta asirce mijin ta sai abinda tace da shi.
Yanzu ki duba fadan daddy akan Nasir da Amira duk wanda ke gidan nan yaran nan basu saba dashi ba kamar Rama a gidan don may don ita ta zauna da yan uwanta a gida tasan ta ja yaro a jikin tw baki taba jin Rama ta zagi yaro ko tai fada dashi a gidan nan.
Sai dai ta nuna masu soyayya da cusa masu tsoron Allah ta hanyan yi masu nasiha idan sunyi abinda ba daidai ba tare da basu labarin da zai tsoratar dasu bazasu sake maimaita abin da sukayi ba.
Kin ga ai ta taimaka muna sosai gurin gyara tarbiyan yaran nan da basu samu ba a gare mu a baya da yaushe yaron gidan nan zai tsaya gaida babba can.
Ni kinga in ba yanzu dana dan samu lafiya ba gajiye bana zama a kasan nan haka ko yaushe nike nan bin jirgi zuwa ganin likitana a waje.
Gajiye tace hajiya wai may ke damun kin ne hakana don Allah ?
Murmushi anty tayi yanayin ta ya juye a lokaci daya batare da tai magana ba tace gani nan dai gajiye abin sai Allah kawai yau ace wanan gobe ace wanan ke damuna.
Yanzu haka ko azumin da na dan yi ne tun jiya nake jin alaman ciwon nan na son taso min wallahi.
Da sauri nace subbahanallahi anty ai gara kije asibiti kagin ya matsa maki don Allah tai murmushi tace Rama ai nasha magani koda safen nan shine na dan ji saukin shi ai.
Nayi shiru ina tunanen matsalan anty na mace mai kawaici da karamci irin anty samun ta a wanan zamanin sai an tona .
Ku shirya anjima ina son muje gaida Abbana da sallah don yana gida yanzu nasan bai fara fita ba tunda sallah ne.
Bana son zuwa gida idan Abba baya gida saboda yadda ake min a gidan shiya kikaga bai faye zuwa ba idan ba wani dalili mai karfi ba zai kaini gidan.
Gajiye ce ke cewa matan gidan fa ba suna nan ba tai murmushi tace sunan Gajiye kin san muna cikin lokacin da kowa nasa ya sani yanzu.
Ba kowane zai iya kula dan kishiya ba ni ko zama ma basu yi da uwata ba amma sun dauki tsanan duniya sun saka min a rayuwan su.
Don hanin da sukayi Abba na tausaya min rashin uwar da na taso ban dashi a gidan har yakai shi kan shi Abban ya fahinci basu kaunana ko kadan a gidan.
Zarah ce kawai nake dan hurda da ita cikin yan uwana duk sun hurewa diyan su kunne akaina wallahi.
Mikewa nayi zan shige anty ke cewa ina kuma zaki Rama nace naji kin ce zamu gaida daddy shine zan hada mashi cake da wani abin.
Tace ikon Allah yaya kika san Abba yana son cake sosai Rama nace ranan naji yana magana an mashi cake ba dadi ai.
Nan na shige na fara hada cake din na kuma gasa mai nama na peppeying din shi da kyau na hada fruits salad mai dadi na sa a fridge zuwa azahar har na kammala na shiga wanka ina wanka nake tunanen maganan anty akan Farida.
Lalai biri yai kama da mutum don ko motan da daddy ya saya min sai da tai fushi sosai a kan shi tama dauke kafan ta a gidan a lokacin sai daga baya ta dawo kuma.
Idan muna zaune da ita takama magana ke nan Rahama mutum ya samu miji irin daddy ai ya more rayuwan shi tun dai idan matan shi sukai mai wani abu.
Ta shiga tsaki da korafi ke nan sai nai mata magana nace ina ruwan ki mutum da matan sa ke may ya shafe ki a ciki.
Baki ganewa ne Rahma ita anty Zulfau tana ganin kamar tafi kowa cikin dangine da ya aure ta inba aure mukkadari ba ina ita ina shi mace haka kamar uwarta ba kiba ba wani zati da za, a gani ace wai matar shi ce.
A lokacin sai nake dauka don tana yar uwarsu ce take jin haushin abin da ake mashi ashe ita abin ba haka yake ba a gurin ta.
Nafito na shiga da yaran na kara yi masu wanka bamu fito ba sai dana gyara su tsab muka fito na samu ita anty bata ma shirya ba tana kwance da taimakona ta samu ta shirya ina shirya jinior take cewa daddy yace shi zai kai mu ai.
Ban ji dadin haka ba naso mu fita da ita kawai don mu dan yi yawo saboda mu ga gari da bukin sallah da akeyi.
Na fito da kayan dana hada tana gani tace ikon Allah Rahama ashe yau zaki saka Abba cikin farin ciki dama yana min korafin nabar kawo mai abinda nake mashi a da can baya.
Muna fitowa dauke da basket biyu ni na dauki dayan Gajiye ta dauko dayan yana cikin mota mu yake jira ya bude buth din motan na saka kayan a ciki.
Na koma na karbo jinior dake hannun anty suna fitowa kamar kullun motar shi bakajin komai sai sautin tashin kira, a a cikin sa ta tsaya ta rufe kofan shiga part din mu ta miko min keys din na kada a handbag dina.
Tana gaba nida gajiye da yaran muna baya nan muka gaida shi ya amsa muna kamar dole.
Yaja mota muka fara tafiya suna hira shi da matar shi nima a baya yaran sun matsa min sai da nai magana dasu har nabiye masu muna hira muma da gajiye.
Uguwar su anty tsohon gari ne don gidajen dake unguwar zaka fahinci haka dagani suma gidan nasu daga baya akai mai kwaskwarima na zamani .
Sai gidan ya haska uguwar sosai dashi da wasu gidaje daga cikin unguwar.
Nan dai muka fito muka shiga ciki a falo muka samu Abban yana tare da wasu dattawa a zaune yan uwan shi.
Muka zube kasa har daddy muna gaida shi yake cewa Alhaji Yusuf ka dawo ne kuma Allah dai yai maka albarka kin gane shi nan idan har yana garin nan sai yazo ya gaidani wallahi jiya nan yake da yaran nan sun zo gaidani da sallah.
Yafi min sauran mazan yan uwan ki sau dubu wallahi shiyasa nake jin shi kamar ni na haifi abina Saade don yanzu ma kusan ya karbe maki nine ai .
Tace kai haba Abba akwai wanda ya isa ya karbe min kai kuwa yace to tsaya kiyi wasa nan dai yaja yan jikokin shi yana wasa dasu wasan jika da kaka.
Nan yake fada masu cewa kwana biyu ba, a karasa azumi dashi ba ai don jikin nashi ya motsa mai.
Anty tace dashi ai Abba nima haka nake tun jiya wallahi tafiyan nan ma dai na karfin hali nayi don nasan yanzu ne ake samun ka a gida.
Daddy yace amma Abba da ka daure idan zamu fita atafi dakai kaga likita kaima a can yace kai haba wani likita zan je gani har waje Allah dai ya yayye kawai za, ace yanzu.
Rama baki ba Abba tsara ban ki ba mana sai lokacin na dan motsa shima Abban ya kallo inda yaji an ambaci sunana yace au itace yarinyar da kuke rikicin akan ta ke nan ko ?
Rikici kuma nace a raina sai kuma nake cewa killa zan cen fitinan su hindatu ne a kaina yakawo ga kunnen Abba din.
Abba itace fa kagan ta nan amma shine wai yake daukan magana a shirmay nakeyi yin shi daddy ne yace damu ku dan bamu guri Gajiye mu gana da Abba haka yasa nafi kowa saurin mikewa na bar gurin muka shiga daga ciki don dama nasan gidan muna zuwa da anty wani lokaci.
Dakin wacce nake ganin ita ce uwar gida a gidan muka fara shiga muka gaida ita sai dayan dakin don su biyu ne a gidan.
Kamar sauran gidaje su ma da alama ba wani zaman hadin kai kamar sauran gidajen da ake tsara akidar kishi a ciki.
Muna barin gurin daddy yace ban san abinda ke damun saade ba ta matsa min akan maganan yarinyar nan har tana kokarin ganin mun samu sabani a tsakanin mu.
Murmushin manya Abba yayi tare da jawo basket din abincin da mu kazo dashi a gaban shi yana dan budewa.
Yace in ban da abinka Alhaji Yusuf yo tunda kaji har mace ta bude baki da kanta tace ka aura mata kishiya ai tana da hujjan yin hakan.
Ai sai ka bari mu saurari hujjan ta muji yanzu ko anty ta nisa tace hujja na akan haka daddy ba wani dalili bane sai ganin da nayi rayuwan yarinyar ya cancan ci hakan a gare mu.
Kamar yaya Saade inji Abban ya tambaye ta sai hawaye ya fara zubo mata a idon ta a hankali tace dashi.
Abba idan kai la, akari da yadda yanayi yake yau ciwo gobe lafiya yarana suna bukatan taimako suna bukatan kasancewa tare da mai son su tsakani da Allah.
Shi kan shi ai yana bukatan kwanciyan hankali tare dashi wanda kwata kwata tunda na fara ciwon nan babu shi a tare dashi.
Amma idan ya auri Rahama ko bayan bani ina da yakinin yarana dashi suna da mai rike min su a tsakani da Allah kuma ai Abba wanan abin da nake son yayi kamar taimakon kan mu da kan mu ne za, a yi shi.
Ni dai take jiyewa nikuma wallahi harga Allah na yafe ma ya auri yarinyar nan ta zauna damu babu komai a raina na burbushin kishin ta a tare dani sai kuka ya kubce mata a take a gurin .
A, a a haba Saade may yakawo kuka kuma ana magana na fahinta anan magana zaki tsaya ayi a fahinci juna ko ?
Abba ya kasa fahintar manufata akan yin wanan shawaran danayi ni kuma ina jiyewa makomar bayana ne a gidan.
Haba Saade ai ciwo bashine mutuwa ba ga yadda wa yancan likitocin naku masu jajjayen kunnuwa sukace a baya wa ya dauka zaki kai wanan lokacin.
Bagashi Allah da hikimar shi ba har da rabon haihuwa kin samu a hakan kuma aikwai may yine bayan Allah.
Ki kwantar da hankalinki kiyi nazarin abin da kike kokarin shiryawa kada daga baya kuma kizo abin ya damay ki .
Aure ne fa shi sha, ani na aure ana son kwanciyan hankali da natsuwa a cikin sa kada kuma ayi garaje abu yazo ya koma maki ciki daga baya.
Abba na riga nai nazari sosai akan halaiyar yarinyar babu wani matsalan da za, a samu a ciki da yardan ubangiji.
To maji ita yarinyar tasan da wanan magana ne a yanzu haka ga abin da kike shirin yi a kan ta ?
Tace cikin girgiza kan ta bata sani ba Abba don ina son ne shi mu daidaita dashi kafin na tun kare ta da zancen tukun.
Don insha Allahu Rahma mai kaunata ce bazata ki abin da nake so da ita ba tunda taimako na zatayi ga hakan.
Murmushi Abban ya dan karayi yace kai Saade ban taba ganin mace maitaushi kamar ki ba don taushin ki har yafi na mahaifiyar ki baki rageta da komai ba a duniyan nan.
Yanzu kai Alhaji Yusuf kaji hujjan ta dabara ta rage naka tun da ita ke bukatan yin hakan gareta.
Daddy ya numfasa da karfi yace Abba kaji abinda take fadi wai hujjata ke nan a koda yaushe.
Ita burin ta ke nan shiyasa take kokarin hasasa muna rashin zaman lafiya akan wanan magana da ta a ranta don nata manufan kawai.
Tace eh shine burina don ni abinda zai fishe mu nan gaba nakewa bawai son zuciya ba.
Hakan ne naga yafi dacewa ayi don samun mafita a rayuwan mu shiya kaji na matsa da maganan.
Abba yace wanan shine abin da ake fadi idan kana son kama uwa to kaso dan ta da zuciya daya shine nan.
Ita wanan yarinyar na lura ta yi amfani da imanin ki ne gurin gwadawa diyan ki son da take masu da zuciya daya amma baki ganin idan ta shiga ta samu nata watarana zata iya watsar da naki yaran ta kama nata.
Daddy yace hakane Abba ba wani abu takewa wanan ba nikuma ban dauke shi a hujjju da zata sani abin da ban da niyya ba akan shi.
Yanzun dai da ita da kai kuje ku kara sasanta kan ku a kan zancen amma ni Alhaji yusuf ai naga wanan kamar kai aka taimakawa.
Don hujjan Saade gaskiya abin dubawa ne kaje kai nazari zanji daga gareka yadda kuka kaya daga baya.
Allah ya tabbatar da Alherin sa Allah kuma yau maku albarka yasa wa zuria albarka dayyaba.
Suka karba da amin Abba daddy yace amma ni Abba naso ne ai mata magana ta fita wanan zancen don Allah kada mu samu matsala akan shi nan gaba.
Abba ya daga mai hannu yace na fahinci manufar hikiman saadatu ga hakan kaje kai nazarin maganan ta da basira ko zaka fahinci manufarta anan.
Sukai sallama ta mike tashiga gida gaida gaida mutanen gidan kamar kullun babu wani kyakyawan taro da ta samu garesu sun dai gaisa da ita kadaran kada ham tai masu barka da sallah tare da fatan Allah ya maimaita muna takawo kudi ta basu barka da sallah sukakarba da godiya babu addua a kai mata kin shi sai su don kishi harda matatta.
Muna dakin sister din ta murja don school din mu daya da ita muna dan mutnci a school da
Showing 114001 words to 117000 words out of 456145 words
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22Chapter 23Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32Chapter 33Chapter 34Chapter 35Chapter 36Chapter 37Chapter 38Chapter 39 Chapter 40Chapter 41Chapter 42Chapter 43Chapter 44Chapter 45Chapter 46Chapter 47Chapter 48Chapter 49Chapter 50Chapter 51Chapter 52Chapter 53Chapter 54Chapter 55Chapter 56Chapter 57Chapter 58Chapter 59Chapter 60Chapter 61Chapter 62Chapter 63Chapter 64Chapter 65Chapter 66Chapter 67Chapter 68Chapter 69Chapter 70Chapter 71Chapter 72Chapter 73Chapter 74Chapter 75Chapter 76Chapter 77Chapter 78Chapter 79Chapter 80Chapter 81Chapter 82Chapter 83Chapter 84Chapter 85Chapter 86Chapter 87Chapter 88Chapter 89Chapter 90Chapter 91Chapter 92Chapter 93Chapter 94Chapter 95Chapter 96Chapter 97Chapter 98Chapter 99Chapter 100Chapter 101Chapter 102Chapter 103Chapter 104Chapter 105Chapter 106Chapter 107Chapter 108Chapter 109Chapter 110Chapter 111Chapter 112Chapter 113Chapter 114Chapter 115Chapter 116Chapter 117Chapter 118Chapter 119Chapter 120Chapter 121Chapter 122Chapter 123Chapter 124Chapter 125Chapter 126Chapter 127Chapter 128Chapter 129Chapter 130Chapter 131Chapter 132Chapter 133Chapter 134Chapter 135Chapter 136Chapter 137Chapter 138Chapter 139Chapter 140Chapter 141Chapter 142Chapter 143Chapter 144Chapter 145Chapter 146Chapter 147Chapter 148Chapter 149Chapter 150Chapter 151Chapter 152Chapter 153