ta shige simi simi ciki shi kuma ya tsaya wajen su Alhaji dake kallon shi a cikin mamaki.
Nan ya zauna ya dinga bashi baki akan yayi hakkuri ya taushi zuciyar shi akan iyalin shi.
Yace babu komai tunda taci albarkacin shi zai kula ya saka ido ga komai a gidan insha Allahu.
Muna zaune kofan mama gaba dayan mu gidan ga hasken farin wata ya haske ko ina anyi gungu gungu ana hira.
Sai ganin shigowan ta kawai mukayi gidan da kumshin kayan ta babu ko sallama.
Kowa ido ya saka mata wasu sun gane cewa itane musanman ma yara ta da suka hau ihu eh mama mama da murnan su.
Nan dai duk da batai sallama ba aka shiga gaida ita tana amsawa cikin basarwa ta shiga dakin ta.
Ganin akwai duhu a dakin sai gata tafito tana cewa mama yaya ara min fitilar ki na haska naga guri don Allah.
Mama tace a dauko mata ta amsa fuuuu ta juya zuwa dakin nata daya daga cikin sarakan mama tace bisimillahi Allah matsala ta dawo ke nan kuma.
Kowa nan suke fadin albarkacin bakin su akan dawowan nata kuskus kus daya bayan daya muka watse gurin kowa ya kama gaban shi.
Da daddare can sai gashi ya shigo gidan dakina ya nufo don nice da girki a ranan.
Ya samu kujeran da yake zama kafin ya kwanta ya zauna na gaida shi da dawowa yace.
Amarya kinga wanan fitinanan ta dawo gidan ko ?
Nace wa wai maman Suwaiba ?
Yace ita ,
Don haka abinda nake so dake kikama kan ki daga gareta daga ita har yaranta ba tarbiya ne dasu ba.
Nace insha Allahu zanyi kamar yadda kace Alhaji bazan shiga tsabagan taba ko na diyan ta a gidan nan.
Ashe sabuwa tun shigowan shi gidan tana hankalece wai ita a zaton ta tunda ta dawo ranan a dakin ta zai kwana don haka takeyi wa sauran matan nashi a baya.
Tana ganin ya wuce zuwa dakina wani tukukin bakin ciki da kishi ya rufe mata zuciyar ta a lokaci daya.
Don haka tafito fuuu zuwa dakin mama hausatu tafada mata daki tana haki tace yaya kinga wanan mutumin baya son a zauna lafiya a gidan nan ko ?
Mama tace da akayi may kuma Sabuwa ?
Tace amma ai yasan na dawo amma ya iya wucewa ko dakina bai leko ba yana nufin cewa yarinyar nan itace zatai girki ko may ?
Ke sabuwa wai yaushe zakiyi hankali ne ke ki san jiya ba fa yau bane ?
Idan mu dacan kin samu kina muna yadda ran ki yaso yanzu baki tunanen cewa wata tazo gidan ne.
Gara ki rufawa kan ki asiri ki zauna dakin ki ki dubi yaran ki zai fi maki sauki wallahi .
Aiko da dakike muna hakan idan kin dawo kema kin san ba hakkin ki bane yin hakan don dai a zauna lafiya muke saka maki ido kawai.
Yanzu kuma wata tazo yarinya danya sharaf kice zaki tauye mata nata incin kinga haka zaiyuyu kuwa.
Gara ki kama kan ki da mutunci ki a gidan nan tun bakija wa kan ki raini ba ga yar diyar cikin ki da ko uwarta kin girma ga haihuwa.
Nan dai taga ba ci idan tace zata ja gashi da kyat ta samu tadawo dakin ta tun ba, a kwana ba kuma ace wani matsala ya taso a gareta haka ?
Ta juya cikin kwafa zuwa dakin ta tana faman mita da ace tasan zaman da muke da mijin nata da take ganin na anshe mata data bawa kanta lafiya.
Don idan tace taja wani fitina da daren nan wani sabon tonon asirin ta ne zai a bainan jama, a don yanzu maigidan nasu akan yar karamar yarinya baijin ass.
Don a dole banda yadda zanyi nake zaune gidan gashi har takai iyanzu na saba da komai ina zamana hankali a kwance tunda ba takura.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE, , ,
IDAN KIN BIYA KIKA TURAWA WA WANDA BAI BIYA BA ALLAH NA GANIN KI DON AMANA NE, , ,
8
Izuwa yanzu komai na gidan ba matsala saboda kakausar kashedin da manyan diyan Alhaji suka taru a tsakar gida sukayi.
Kan abar masu mahaifin su ya samu lafiyan shi don yawan futinan da aje saka shi zai iya jawo mai wani sabon matsala kuma.
Sunyi barazanan daukan mataki akan duk wace take kawo masu yawan tashin hankali a gida.
Wanan dalilin yasa gidan ya samu kwanciyan hankali na kwana biyu.
Gashi dai zan iya cewa Alhaji yana cikin mazan dake kokarin ganin yaba iyalin shi kulawa don bai make aljihun shi ga iyalin shi.
Kwanciyan hankalin da na samu ba fitina ba tsangwama yasa na sake murjewa nai kyau nai haske sosai.
Nan kan kula da yanayin Alhaji idan yana dakina sai naga ya tsura min ido kawai can naji ya sauke ajiyan zuciya a sanyaye.
Ban daukan wanan a komai sai dai naga kamar wani abune ya shige mai a duhu yake saka shi a tunane.
Ban sani ba ashe tausayina ne yake ji yana ganin kamar ya shiga hakkina da yawa.
Yakawo ni gida ya girke ba biyan bukatan komai a kaina bai san ni haka wani gata ne Allah yai min ba da hakan.
Allah bai barin bawan shi mai hakkuri ya tabe banza a duk inda yake watarana sai kaci riban hakkurin ka insha Allahu mudfin kayi shi da zuciya daya.
Ranan na tashi da safe na shiga nai wanka bayan na gama yan aiyuka na sai ganin nayi jini yana zubo min a gabana.
Tun ina bini bini kewayawa na wanke har tsoro ya fara kamani gashi naki sakin jikina ko cikin gida naki shiga na taya su aikin komai a ranan.
Sai bayan sallah azahar da naji kowa ya shige dakin shi na idar da sallah na nufi gurin mama hausatu.
Na samu ta idar da sallah tana zaune tana lazumi ita kadai a daki tana ganina tai dan murmushi a fuskan ta tana cewa Amarya .
Yanzun fa nake zancen ki a zuciyana yinin yau banga kin fito ba tun safe da muka gaisa nake cewa ko dai lafiya kuwa ?
Nakai zaune tare da cewa wallahi mama yau banda lafiya akwai matsala shine nazo na fada maki.
Cikin sauri tace subbahanallahi may ya samay ki kuma yar nan ?
Shiru nayi ban san may zance da ita ba a lokacin sai dai kaina dana sada a kasa kawai.
Tace may yafaru amarya gaya min mana nifa ban dauke ki a kishiya ba matsayi diya ta ta cikina nake daukan ki.
Na kara dukar da kaina a kasa nace mama dama sai nai shiru can kuna na dago na kara cewa a sanyaye dama yaune naga jini kawai yana ta zuwa min a karkashina tun safe da na tashi ga marata sai ciwo yake min.
Nace barin fada maki ko zanga likitane tun cutar bai min yawa ba ?
Tace cikin mamaki ikon Allah Rahama dama baki fadi bane sai yan zu ?
Na dago kai da sauri na dan kalle ta tace wanan ne karo na farko da kikaga haka ko may ?
Nace mata a sanyaye eh mama.
Tace to ki saurare ni kiji da kyau wanan abin da yazo maki zan iya cewa ba cutane ba kuma cuta bane alama ce ta girma yazo maki da hankali da samun natsuwa.
Duk ko wace mace da kike gani tana yin wanan abin a rayuwan ta wace bata yi kuma to tana da matsala kuwa babba.
Wani irin ajiyan zuciya na sauke taci gaba da fadin kada ki tsorata da hakan nan tafara yi min bayanin yadda zan kama kaina a lokacin da nake cikin wanan laluran na fashin sallah.
Kamar yadda uwa zatai wa yarta bayani haka ta zauna tai min bayani sai daga karshe tace da zaran kin gama zakiyi wanka kamar yadda kike yin wankan janaba.
Nace wankan janaba mama tace eh idan kin kwana da mijin ki ba kikan yi wankan tsarki ba ?
Nace eh kawai ba tare dana fahinci may take nufi ba tace to shima hakan zakiyi sai dai gurin niyya ya banbanta ne wacan janaba zaki ce wanan kuma haila.
Nan dai ta kara koyar dani komai nace nagane mama a makarantan boko dana islamiya duk an koya muna shi na kuma rike.
Nace mama dama wanan jinin shine jinin hailan da ake nufi tace shine amarya sai jinin haihuwa shima tai min bayani da kwanakin da ake son mace tayi ta fara yin tsarkin shi.
Na gamsu sosai da bayanin mama akarshe take ce min sirina ne daga ni sai mijina kawai daya zama dole ya sani ake son ya sani idan ma ina fashin sallah naga kowa ya tafi sallah na shige daki nima kada na zauna a waje kowa ya fahinci ban salla don siri ne babba ga mace.
Nai mata godiya tare da mikewa na wuce zuwa dakina na kimtsa jikina kamar yadda tai min bayani nayi.
Ina fita na bata tausayi sosai sai dai bata ga laifina ba sai na iyayyena dake da alhakin haka akaina.
Gashi yar karama dani a wanan zamanin an min auren cushe ga miji, mijin kuma babban mu kamar alhaji gashi ashe ko hankalina ban gama mallaka ba.
Kamar yadda mama ta fadakar dani hakan ne nayi na gyara jikina tsab mai makon na ma dinga shiga mutane sai kawai na dinga nisanta kaina da jama, a baki daya gani one two one ta na kewaya na gyara jikina.
Da maigidan ya shigo gida ne mama ke fada mashi cewa ashe amarya sai yanzu ta fadi yau ta samay ni cikin damuwa take fada min don bata san kaiba.
Shima yai mamaki kwarai jin sai a lokacin na fadi ashe kuma ban san komai ba akan faduwa hakan na nufin ke nan har yanzu ina a matsayina na cikakkan budurwa as a virgin .
Tausayi na ne ya kara kamashi a lokacin ne yai daya sani shiga rayuwa na da yayi da wuri haka nan.
Ke nan zancen da kishiyar mahaifiyana ta fada mai nacewa gara ma da yazo nema don ni watsatsace ban da kamun kai na san maza ko zan iya zama dashi ai ban ganin tsufan shi tunda maza nake so a rayuwana.
Wanan magana babu inda ya hango kamshin gaskiya a cikin sa don dai halin rayuwa na ya nuna mai ta ko ina ni yarinya ce mai mutunci da kima nasan darajan kaina da iyayyena.
Don haka dole ne yai min adalci akan zaman da nake dasu don ya fahinci yarinya ce ni sharaf ban san komai ba na duniya.
Wanan dalilin ne yasa ya kara jawo ni jikin shi sai naga yana haba haba dani fiye ma da farko da yake min.
Mutanen gidan ganin kwana biyu bana yawan fitowayasa suke shigowa daya bayan daya suna tambayana may ke faruwa dani ne wai ?
Sai cewa masu nake banda lafiya ne bana jin dadin jikina na ne shiyasa.
Su daukan su na samu cikine, wai, sai naji suna cewa Allah ya ingata ya kawo muna mai albarka.
Jin haka yasa Sabuwa ta fara dan sake magana tana fadin an dai ji kunya wallahi .
Karshen muna funci ya baiyyana ace muna ba, a da lafiya amma sai ga shi an iya labewa da karamar yarinya har ana dirka mata ciki.
Abin kunya girma ya zube kamar wanan yar yarinyar za, a ce wai ta samu ciki da mutum irin Alhaji wanda kewa iyalin shi ikirarin baida lafiya bai iya komai da mace amma ya takure a gidin yarinya karama to ga abin boye ya fito fili ai kowa ya gani yanzu gaskiya ya baiyyana.
****** ********** ******
Tun lokacin da na fara period naga gaba daya na sauya wani girma ya zo min ga kayan dadin da nake samu ina ci iri iri gwagwadon halin yan kauye irin dadin su na kauye.
Wani lokaci sai nayi kyauta da wani abin ma na rabawa yaran cikin gida su ci don ban iya ci ni don ban saba da yawan ciye ciye ba a rayuwana.
Zaune nake a saman kujeran dakina nayi tagumi da hannuna na hagu na zurfafa ga tunane.
Sai ganin shi nayi ya shigo dakin na bishi da idanu kamar shima yadda ya bini da kallo don ganin yanayi na a cikin damuwa.
Guri ya samu ya zauna a bakin gado yana kokarin cire babban rigar dake jikin shi.
Yace may kuma ya faru na gan ki haka amarya, murmushin kake nayi wanda bai kai ciki ba a fuska na.
Yake cewa wai may ke faruwa ne ko anyi wani abin ne kuma bayan fita na ?
Nace babu komai tashi yayi daga inda yake ya dawo kusa dani ya zauna saman kujera two seater dani kai a zaune.
Yake cewa fada min mana may akayi ne wai naga yanayin ki ya nuna min kina a cikin damuwa.
Nace ba komai Alhaji tunane Inna ta kawai nakeyi.
Yace wani abu ya samu inna din ne kuma ?
Kai na girgiza mai alaman a, a.
Murmushi yayi tare da riko min hannuwa na wani irin yar naji har cikin zuciyana tare da jin nauyin shi na ganin ya taba min jikina karo na farko zamana dashi.
Ban kai ga karasa mamakina na ba naji ni ya kwantar dani a saman jikin shi yana dan shafana a hankali.
A take naji yanayina na neman gagarana zama a gurin da nake zaman tsara dashi.
Yace ki kwantar da hankalinki insha Allahu akwai shawaran da nakeyi akan ki idan har nakai karshe wata kila ma zaki koma gurin Inna din da zama na dindindin.
Da sauri na dago kai ina duban shi yace ki dai kara hakkuri kinji Rahama dan bani lokaci kadan.
Nace ni ban son komawa gidan mu gurin inna ta, zama na nan yafi muna komawa gidan su Inna yanzu hankalin ta a kwance yake don mama bata gani na balle ta tayarwa Inna da hankalinta .
Ni nan zan zauna gurin ka kana kula dani fiye da Inna ta da baba na ban cikin matsin mama kuma yanzu.
Dukar da kan shi naga yayi a kasa sai naga hawaye suna zubo mai sannu a hankali.
Cikin mamaki nai zubur na mike daga inda nake a zaune tare da dawowa gaban shi na tsugun na ina cewa .
Don Allah Alhaji idan har na fadi wani abinda ba daidai bane kayi hakkuri kayafe min naji zan koma gidan mu gurin Innata muyi ta hakkuri da rayuwan da zamu tsunta agurin mama.
Ji nayi ya tallafo ni daga gurin da nake a tsugune zuwa jikin shi ya rugumay ni yana dan shafa min bayana tare da fadin ya isa haka kiyi shiru babu inda zaki tafi kina nan tare da mu insha Allahu.
Wanan ranan ne muka fara kwanciya saman gado daya da Alhaji sai dai yana gefe ina gefe a kwance har gari ya waye .
Abinda ban sani ba ranan shi gare shi ko runtsawa bai yi ba sai faman tunanen duniya yakeyi.
Ya so it a mayar dani gidan mu gurin iyayyena don yana ganin yana kuntatawa rayuwa na sosai, amma kuma sai gashi ni da bakina nake fadin wanan zaman yafiye min zaman gidan iyayyena dadi.
Haka yasa ya fahinci daga ni har innata muna wani rayuwa ne na zaman ukuba a gidan.
Dole yabar wanan yarinyar yaga abinda Allah zaiyi akai don Allah kadai yasan dalilin wanan auren don shi baki sa,ata ba ko wace tafini shekaru bai da nufin karawa a rayuwan shi.
Sai gashi a lokaci daya Allah ya jarabce shi da kara aurena auren kuma yazo da kaddaran rayuwa gare shi.
Yadda na samu kwanciyan hankali na mirje nai kyau dani haka yasa Sabuwa tayar da hankalin ta duk ta fige tayi wani baki da ita.
Gashi ta sa a ranta cewa cikine a jikina yasa na koma haka dani lokaci daya.
Akwana a tashi hasaran mai rai yau nakai wata takwas da aure har lokacin ban sheda nayi aure ba a rayuwa na.
Iyakata naci na sha na kwanta nai kwana idan naso na shiga na taya matan gidan aikin su.
Ba mama da mama hauwa ba kawai nake tayawa aiki har sarakan su idan aiki yai yawa nakan kama masu.
Ban hakkura da zancen zuwa islamiya ba na kara tunawa Alhaji da kyat na samu ya yarda na tafi sai gashi ya sawo min hijjab har uku maya har kasa da nikaf na rufe fuskana.
Ranan da zan fara fita nasha sheri gurin matan gidan wai ni yar izzala ce shiyasa nake da mugun tsabta ashe.
Na dai yi murmushi nai masu sai na dawo nafice daga gidan dama Alhaji ya riga yai min register komai a school din.
Don haka ban sha wani wahala ba na gane ajina gwajin farko ya fahinci na dan yi nisa aka mayar dani ajin manya.
Sosaina dage ga karatu na ba wasako a gida nake banda abinyi sai karatu da yan aiyuka na.
****** ********* ******
A bangare Alhaji ya samu sauki sosai don tsare dokokin da yayi na likita har anfasa zancen yi mashi aikin da akace za, ayi da farko.
Hakan da yake ji yasa yake ganin ya samu sauki ya shiga kokarin gwada sa,anshi ya gani .
Ranan a cikin barci na dinga jin wani bakon al,amari ya na
Showing 30001 words to 33000 words out of 456145 words
Nan ya zauna ya dinga bashi baki akan yayi hakkuri ya taushi zuciyar shi akan iyalin shi.
Yace babu komai tunda taci albarkacin shi zai kula ya saka ido ga komai a gidan insha Allahu.
Muna zaune kofan mama gaba dayan mu gidan ga hasken farin wata ya haske ko ina anyi gungu gungu ana hira.
Sai ganin shigowan ta kawai mukayi gidan da kumshin kayan ta babu ko sallama.
Kowa ido ya saka mata wasu sun gane cewa itane musanman ma yara ta da suka hau ihu eh mama mama da murnan su.
Nan dai duk da batai sallama ba aka shiga gaida ita tana amsawa cikin basarwa ta shiga dakin ta.
Ganin akwai duhu a dakin sai gata tafito tana cewa mama yaya ara min fitilar ki na haska naga guri don Allah.
Mama tace a dauko mata ta amsa fuuuu ta juya zuwa dakin nata daya daga cikin sarakan mama tace bisimillahi Allah matsala ta dawo ke nan kuma.
Kowa nan suke fadin albarkacin bakin su akan dawowan nata kuskus kus daya bayan daya muka watse gurin kowa ya kama gaban shi.
Da daddare can sai gashi ya shigo gidan dakina ya nufo don nice da girki a ranan.
Ya samu kujeran da yake zama kafin ya kwanta ya zauna na gaida shi da dawowa yace.
Amarya kinga wanan fitinanan ta dawo gidan ko ?
Nace wa wai maman Suwaiba ?
Yace ita ,
Don haka abinda nake so dake kikama kan ki daga gareta daga ita har yaranta ba tarbiya ne dasu ba.
Nace insha Allahu zanyi kamar yadda kace Alhaji bazan shiga tsabagan taba ko na diyan ta a gidan nan.
Ashe sabuwa tun shigowan shi gidan tana hankalece wai ita a zaton ta tunda ta dawo ranan a dakin ta zai kwana don haka takeyi wa sauran matan nashi a baya.
Tana ganin ya wuce zuwa dakina wani tukukin bakin ciki da kishi ya rufe mata zuciyar ta a lokaci daya.
Don haka tafito fuuu zuwa dakin mama hausatu tafada mata daki tana haki tace yaya kinga wanan mutumin baya son a zauna lafiya a gidan nan ko ?
Mama tace da akayi may kuma Sabuwa ?
Tace amma ai yasan na dawo amma ya iya wucewa ko dakina bai leko ba yana nufin cewa yarinyar nan itace zatai girki ko may ?
Ke sabuwa wai yaushe zakiyi hankali ne ke ki san jiya ba fa yau bane ?
Idan mu dacan kin samu kina muna yadda ran ki yaso yanzu baki tunanen cewa wata tazo gidan ne.
Gara ki rufawa kan ki asiri ki zauna dakin ki ki dubi yaran ki zai fi maki sauki wallahi .
Aiko da dakike muna hakan idan kin dawo kema kin san ba hakkin ki bane yin hakan don dai a zauna lafiya muke saka maki ido kawai.
Yanzu kuma wata tazo yarinya danya sharaf kice zaki tauye mata nata incin kinga haka zaiyuyu kuwa.
Gara ki kama kan ki da mutunci ki a gidan nan tun bakija wa kan ki raini ba ga yar diyar cikin ki da ko uwarta kin girma ga haihuwa.
Nan dai taga ba ci idan tace zata ja gashi da kyat ta samu tadawo dakin ta tun ba, a kwana ba kuma ace wani matsala ya taso a gareta haka ?
Ta juya cikin kwafa zuwa dakin ta tana faman mita da ace tasan zaman da muke da mijin nata da take ganin na anshe mata data bawa kanta lafiya.
Don idan tace taja wani fitina da daren nan wani sabon tonon asirin ta ne zai a bainan jama, a don yanzu maigidan nasu akan yar karamar yarinya baijin ass.
Don a dole banda yadda zanyi nake zaune gidan gashi har takai iyanzu na saba da komai ina zamana hankali a kwance tunda ba takura.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE, , ,
IDAN KIN BIYA KIKA TURAWA WA WANDA BAI BIYA BA ALLAH NA GANIN KI DON AMANA NE, , ,
8
Izuwa yanzu komai na gidan ba matsala saboda kakausar kashedin da manyan diyan Alhaji suka taru a tsakar gida sukayi.
Kan abar masu mahaifin su ya samu lafiyan shi don yawan futinan da aje saka shi zai iya jawo mai wani sabon matsala kuma.
Sunyi barazanan daukan mataki akan duk wace take kawo masu yawan tashin hankali a gida.
Wanan dalilin yasa gidan ya samu kwanciyan hankali na kwana biyu.
Gashi dai zan iya cewa Alhaji yana cikin mazan dake kokarin ganin yaba iyalin shi kulawa don bai make aljihun shi ga iyalin shi.
Kwanciyan hankalin da na samu ba fitina ba tsangwama yasa na sake murjewa nai kyau nai haske sosai.
Nan kan kula da yanayin Alhaji idan yana dakina sai naga ya tsura min ido kawai can naji ya sauke ajiyan zuciya a sanyaye.
Ban daukan wanan a komai sai dai naga kamar wani abune ya shige mai a duhu yake saka shi a tunane.
Ban sani ba ashe tausayina ne yake ji yana ganin kamar ya shiga hakkina da yawa.
Yakawo ni gida ya girke ba biyan bukatan komai a kaina bai san ni haka wani gata ne Allah yai min ba da hakan.
Allah bai barin bawan shi mai hakkuri ya tabe banza a duk inda yake watarana sai kaci riban hakkurin ka insha Allahu mudfin kayi shi da zuciya daya.
Ranan na tashi da safe na shiga nai wanka bayan na gama yan aiyuka na sai ganin nayi jini yana zubo min a gabana.
Tun ina bini bini kewayawa na wanke har tsoro ya fara kamani gashi naki sakin jikina ko cikin gida naki shiga na taya su aikin komai a ranan.
Sai bayan sallah azahar da naji kowa ya shige dakin shi na idar da sallah na nufi gurin mama hausatu.
Na samu ta idar da sallah tana zaune tana lazumi ita kadai a daki tana ganina tai dan murmushi a fuskan ta tana cewa Amarya .
Yanzun fa nake zancen ki a zuciyana yinin yau banga kin fito ba tun safe da muka gaisa nake cewa ko dai lafiya kuwa ?
Nakai zaune tare da cewa wallahi mama yau banda lafiya akwai matsala shine nazo na fada maki.
Cikin sauri tace subbahanallahi may ya samay ki kuma yar nan ?
Shiru nayi ban san may zance da ita ba a lokacin sai dai kaina dana sada a kasa kawai.
Tace may yafaru amarya gaya min mana nifa ban dauke ki a kishiya ba matsayi diya ta ta cikina nake daukan ki.
Na kara dukar da kaina a kasa nace mama dama sai nai shiru can kuna na dago na kara cewa a sanyaye dama yaune naga jini kawai yana ta zuwa min a karkashina tun safe da na tashi ga marata sai ciwo yake min.
Nace barin fada maki ko zanga likitane tun cutar bai min yawa ba ?
Tace cikin mamaki ikon Allah Rahama dama baki fadi bane sai yan zu ?
Na dago kai da sauri na dan kalle ta tace wanan ne karo na farko da kikaga haka ko may ?
Nace mata a sanyaye eh mama.
Tace to ki saurare ni kiji da kyau wanan abin da yazo maki zan iya cewa ba cutane ba kuma cuta bane alama ce ta girma yazo maki da hankali da samun natsuwa.
Duk ko wace mace da kike gani tana yin wanan abin a rayuwan ta wace bata yi kuma to tana da matsala kuwa babba.
Wani irin ajiyan zuciya na sauke taci gaba da fadin kada ki tsorata da hakan nan tafara yi min bayanin yadda zan kama kaina a lokacin da nake cikin wanan laluran na fashin sallah.
Kamar yadda uwa zatai wa yarta bayani haka ta zauna tai min bayani sai daga karshe tace da zaran kin gama zakiyi wanka kamar yadda kike yin wankan janaba.
Nace wankan janaba mama tace eh idan kin kwana da mijin ki ba kikan yi wankan tsarki ba ?
Nace eh kawai ba tare dana fahinci may take nufi ba tace to shima hakan zakiyi sai dai gurin niyya ya banbanta ne wacan janaba zaki ce wanan kuma haila.
Nan dai ta kara koyar dani komai nace nagane mama a makarantan boko dana islamiya duk an koya muna shi na kuma rike.
Nace mama dama wanan jinin shine jinin hailan da ake nufi tace shine amarya sai jinin haihuwa shima tai min bayani da kwanakin da ake son mace tayi ta fara yin tsarkin shi.
Na gamsu sosai da bayanin mama akarshe take ce min sirina ne daga ni sai mijina kawai daya zama dole ya sani ake son ya sani idan ma ina fashin sallah naga kowa ya tafi sallah na shige daki nima kada na zauna a waje kowa ya fahinci ban salla don siri ne babba ga mace.
Nai mata godiya tare da mikewa na wuce zuwa dakina na kimtsa jikina kamar yadda tai min bayani nayi.
Ina fita na bata tausayi sosai sai dai bata ga laifina ba sai na iyayyena dake da alhakin haka akaina.
Gashi yar karama dani a wanan zamanin an min auren cushe ga miji, mijin kuma babban mu kamar alhaji gashi ashe ko hankalina ban gama mallaka ba.
Kamar yadda mama ta fadakar dani hakan ne nayi na gyara jikina tsab mai makon na ma dinga shiga mutane sai kawai na dinga nisanta kaina da jama, a baki daya gani one two one ta na kewaya na gyara jikina.
Da maigidan ya shigo gida ne mama ke fada mashi cewa ashe amarya sai yanzu ta fadi yau ta samay ni cikin damuwa take fada min don bata san kaiba.
Shima yai mamaki kwarai jin sai a lokacin na fadi ashe kuma ban san komai ba akan faduwa hakan na nufin ke nan har yanzu ina a matsayina na cikakkan budurwa as a virgin .
Tausayi na ne ya kara kamashi a lokacin ne yai daya sani shiga rayuwa na da yayi da wuri haka nan.
Ke nan zancen da kishiyar mahaifiyana ta fada mai nacewa gara ma da yazo nema don ni watsatsace ban da kamun kai na san maza ko zan iya zama dashi ai ban ganin tsufan shi tunda maza nake so a rayuwana.
Wanan magana babu inda ya hango kamshin gaskiya a cikin sa don dai halin rayuwa na ya nuna mai ta ko ina ni yarinya ce mai mutunci da kima nasan darajan kaina da iyayyena.
Don haka dole ne yai min adalci akan zaman da nake dasu don ya fahinci yarinya ce ni sharaf ban san komai ba na duniya.
Wanan dalilin ne yasa ya kara jawo ni jikin shi sai naga yana haba haba dani fiye ma da farko da yake min.
Mutanen gidan ganin kwana biyu bana yawan fitowayasa suke shigowa daya bayan daya suna tambayana may ke faruwa dani ne wai ?
Sai cewa masu nake banda lafiya ne bana jin dadin jikina na ne shiyasa.
Su daukan su na samu cikine, wai, sai naji suna cewa Allah ya ingata ya kawo muna mai albarka.
Jin haka yasa Sabuwa ta fara dan sake magana tana fadin an dai ji kunya wallahi .
Karshen muna funci ya baiyyana ace muna ba, a da lafiya amma sai ga shi an iya labewa da karamar yarinya har ana dirka mata ciki.
Abin kunya girma ya zube kamar wanan yar yarinyar za, a ce wai ta samu ciki da mutum irin Alhaji wanda kewa iyalin shi ikirarin baida lafiya bai iya komai da mace amma ya takure a gidin yarinya karama to ga abin boye ya fito fili ai kowa ya gani yanzu gaskiya ya baiyyana.
****** ********** ******
Tun lokacin da na fara period naga gaba daya na sauya wani girma ya zo min ga kayan dadin da nake samu ina ci iri iri gwagwadon halin yan kauye irin dadin su na kauye.
Wani lokaci sai nayi kyauta da wani abin ma na rabawa yaran cikin gida su ci don ban iya ci ni don ban saba da yawan ciye ciye ba a rayuwana.
Zaune nake a saman kujeran dakina nayi tagumi da hannuna na hagu na zurfafa ga tunane.
Sai ganin shi nayi ya shigo dakin na bishi da idanu kamar shima yadda ya bini da kallo don ganin yanayi na a cikin damuwa.
Guri ya samu ya zauna a bakin gado yana kokarin cire babban rigar dake jikin shi.
Yace may kuma ya faru na gan ki haka amarya, murmushin kake nayi wanda bai kai ciki ba a fuska na.
Yake cewa wai may ke faruwa ne ko anyi wani abin ne kuma bayan fita na ?
Nace babu komai tashi yayi daga inda yake ya dawo kusa dani ya zauna saman kujera two seater dani kai a zaune.
Yake cewa fada min mana may akayi ne wai naga yanayin ki ya nuna min kina a cikin damuwa.
Nace ba komai Alhaji tunane Inna ta kawai nakeyi.
Yace wani abu ya samu inna din ne kuma ?
Kai na girgiza mai alaman a, a.
Murmushi yayi tare da riko min hannuwa na wani irin yar naji har cikin zuciyana tare da jin nauyin shi na ganin ya taba min jikina karo na farko zamana dashi.
Ban kai ga karasa mamakina na ba naji ni ya kwantar dani a saman jikin shi yana dan shafana a hankali.
A take naji yanayina na neman gagarana zama a gurin da nake zaman tsara dashi.
Yace ki kwantar da hankalinki insha Allahu akwai shawaran da nakeyi akan ki idan har nakai karshe wata kila ma zaki koma gurin Inna din da zama na dindindin.
Da sauri na dago kai ina duban shi yace ki dai kara hakkuri kinji Rahama dan bani lokaci kadan.
Nace ni ban son komawa gidan mu gurin inna ta, zama na nan yafi muna komawa gidan su Inna yanzu hankalin ta a kwance yake don mama bata gani na balle ta tayarwa Inna da hankalinta .
Ni nan zan zauna gurin ka kana kula dani fiye da Inna ta da baba na ban cikin matsin mama kuma yanzu.
Dukar da kan shi naga yayi a kasa sai naga hawaye suna zubo mai sannu a hankali.
Cikin mamaki nai zubur na mike daga inda nake a zaune tare da dawowa gaban shi na tsugun na ina cewa .
Don Allah Alhaji idan har na fadi wani abinda ba daidai bane kayi hakkuri kayafe min naji zan koma gidan mu gurin Innata muyi ta hakkuri da rayuwan da zamu tsunta agurin mama.
Ji nayi ya tallafo ni daga gurin da nake a tsugune zuwa jikin shi ya rugumay ni yana dan shafa min bayana tare da fadin ya isa haka kiyi shiru babu inda zaki tafi kina nan tare da mu insha Allahu.
Wanan ranan ne muka fara kwanciya saman gado daya da Alhaji sai dai yana gefe ina gefe a kwance har gari ya waye .
Abinda ban sani ba ranan shi gare shi ko runtsawa bai yi ba sai faman tunanen duniya yakeyi.
Ya so it a mayar dani gidan mu gurin iyayyena don yana ganin yana kuntatawa rayuwa na sosai, amma kuma sai gashi ni da bakina nake fadin wanan zaman yafiye min zaman gidan iyayyena dadi.
Haka yasa ya fahinci daga ni har innata muna wani rayuwa ne na zaman ukuba a gidan.
Dole yabar wanan yarinyar yaga abinda Allah zaiyi akai don Allah kadai yasan dalilin wanan auren don shi baki sa,ata ba ko wace tafini shekaru bai da nufin karawa a rayuwan shi.
Sai gashi a lokaci daya Allah ya jarabce shi da kara aurena auren kuma yazo da kaddaran rayuwa gare shi.
Yadda na samu kwanciyan hankali na mirje nai kyau dani haka yasa Sabuwa tayar da hankalin ta duk ta fige tayi wani baki da ita.
Gashi ta sa a ranta cewa cikine a jikina yasa na koma haka dani lokaci daya.
Akwana a tashi hasaran mai rai yau nakai wata takwas da aure har lokacin ban sheda nayi aure ba a rayuwa na.
Iyakata naci na sha na kwanta nai kwana idan naso na shiga na taya matan gidan aikin su.
Ba mama da mama hauwa ba kawai nake tayawa aiki har sarakan su idan aiki yai yawa nakan kama masu.
Ban hakkura da zancen zuwa islamiya ba na kara tunawa Alhaji da kyat na samu ya yarda na tafi sai gashi ya sawo min hijjab har uku maya har kasa da nikaf na rufe fuskana.
Ranan da zan fara fita nasha sheri gurin matan gidan wai ni yar izzala ce shiyasa nake da mugun tsabta ashe.
Na dai yi murmushi nai masu sai na dawo nafice daga gidan dama Alhaji ya riga yai min register komai a school din.
Don haka ban sha wani wahala ba na gane ajina gwajin farko ya fahinci na dan yi nisa aka mayar dani ajin manya.
Sosaina dage ga karatu na ba wasako a gida nake banda abinyi sai karatu da yan aiyuka na.
****** ********* ******
A bangare Alhaji ya samu sauki sosai don tsare dokokin da yayi na likita har anfasa zancen yi mashi aikin da akace za, ayi da farko.
Hakan da yake ji yasa yake ganin ya samu sauki ya shiga kokarin gwada sa,anshi ya gani .
Ranan a cikin barci na dinga jin wani bakon al,amari ya na
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11 Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22Chapter 23Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32Chapter 33Chapter 34Chapter 35Chapter 36Chapter 37Chapter 38Chapter 39Chapter 40Chapter 41Chapter 42Chapter 43Chapter 44Chapter 45Chapter 46Chapter 47Chapter 48Chapter 49Chapter 50Chapter 51Chapter 52Chapter 53Chapter 54Chapter 55Chapter 56Chapter 57Chapter 58Chapter 59Chapter 60Chapter 61Chapter 62Chapter 63Chapter 64Chapter 65Chapter 66Chapter 67Chapter 68Chapter 69Chapter 70Chapter 71Chapter 72Chapter 73Chapter 74Chapter 75Chapter 76Chapter 77Chapter 78Chapter 79Chapter 80Chapter 81Chapter 82Chapter 83Chapter 84Chapter 85Chapter 86Chapter 87Chapter 88Chapter 89Chapter 90Chapter 91Chapter 92Chapter 93Chapter 94Chapter 95Chapter 96Chapter 97Chapter 98Chapter 99Chapter 100Chapter 101Chapter 102Chapter 103Chapter 104Chapter 105Chapter 106Chapter 107Chapter 108Chapter 109Chapter 110Chapter 111Chapter 112Chapter 113Chapter 114Chapter 115Chapter 116Chapter 117Chapter 118Chapter 119Chapter 120Chapter 121Chapter 122Chapter 123Chapter 124Chapter 125Chapter 126Chapter 127Chapter 128Chapter 129Chapter 130Chapter 131Chapter 132Chapter 133Chapter 134Chapter 135Chapter 136Chapter 137Chapter 138Chapter 139Chapter 140Chapter 141Chapter 142Chapter 143Chapter 144Chapter 145Chapter 146Chapter 147Chapter 148Chapter 149Chapter 150Chapter 151Chapter 152Chapter 153