zaune yana fama da laptop a gaban shi na shigo da sallama dauke da kayan abinci na dire a kasa gaban shi sai dana aje na samu wuri nai mashi sannu da zuwa.
Ya dago kai ya dan kalle ni yana fadin ashe kin san na shigo nace dashi yara ke fada min don dazun na tambaye su suka ce dani baka dawo ba.
Gidan naku ne naga ya cika da jama, a ko ba zan iya shiga wurin ku ba nace aikuwa mata ne dam a gidan namu.
Dama ku ai buki ne harkan ku a taru ana gulman kayan jikin ko wace da ta saka ba wani abin yi sai wanan din.
Dariya nayi na gyara zamana ina fadin ga abin tabawa nan ka dan taba ko kadan ne baiki ba naga ya ture kayan da yake aiki dasu a gefe daya.
Ya sauko don ya fara cin abincin dana kawo mashi din ganin haka yasa nai saurin saukowa daga kujeran na fara zuba mai a plate.
Ina gap da gama zuba mai ne naji yana cewa naga wurin Zulfa a bude mana ko yau ne zata dawo din ?
Murmushi nayi nace yallabai ai kai zan tanbaya wanan don kai ne mai yuka a hannu a gidan.
Don nima a wurin hindatu nake ji wai taga ana gyaran wurin Zulfa din yai murmushi yana cewa daidai yana daukan spoon a hannun shi.
Ashe shiyasa naga tana shan toka a fuskan ta da na shigo gidan wanan ne dalilin nata ashe ?
Murmushi nayi kawai ya fara cin abinci nace dashi ita Niima fa daddy yaushe zata dawo gidan don yakamata ai mata hakkuri itama.
Dakatawa yayi daga kai abincin da ya diba zai kai bakin shi tare da watso min Wani irin kallo yana fadin waike Rahama wani irin zuciya ne gare ki haka ?
To kiji bana son jin zancen yarinyar nan daga yau a gidan nan don nike zama da ita ba wani ba, har yakai spoon din kamar zai dibi abincin ya sake cewa dani wai ke yanzu don rashin zuciya irin naki har zaki ce wai yarinyar nan ta dawo gidan nan da zama ?
Wai kin san ko wacece Niiman da kike magana a kanta ni nasan irin hakkurin da nayi da zama da yarinyar nan a gidan nan don bana son mutum mai zalama da yawan korafi.
Ya debi abincin ya kai bakin shi tare da kada kan shi yace hakkuri nayi dama don bana son wani abinda zai hada ta da wani har yakai mu ga samun sabani da ita.
Kinga hakkurina yaci akan diyana zata iya kallon idona tace wai na fifita su da ita ita har yaushe ta shigo gidan da zata iya fada min hakan.
Ko ku dake gidan yau akwai wacce ta isa tace don may zanwa yarana gata da nai niyar yi ita kuma wanan munafukar har da biye mata su zauna suna wanan irin maganan haka ?
Ko ita taci albarkacin iyayye da diyan ta ne a gare ni da duk wani makircin ku na bani hakkuri haka ba zai taba tasiri a kaina ba.
Nace cikin marairai cewa daddy mu mata sai hakkuri yanzu ai ta gane kuren ta ba dadi ne ace anyi aure ko shekara ba a kaiba an rabu.
Yace ke za a zaga ko ni Rahama zama da wanan yarinyar mai jiran cin gado na nagama shi don dama ni nasan abinda nake zama dashi ba wani ba.
A daiyi hakkuri daddyn mu ai mata afuwan hakana har ta sake bai tankani ba yaci gaba da cin abincin shi ba tare da yai wani magana ba kuma.
Can ina dai zaune shiru naji yace dani mutanen gidan su Saade sun shigo kuwa gidan nan don naji suna korafi wai ba akai masu Amira din ba wurin su.
Nace suna da gaskiya ai daddy shiyasa nace dakai tun zuwan mu a bari taje ta dan kwana masu biyu can su gan ta.
Sai daya kurba ruwan dake aje a gefen shi cikin cup yace dani, wurin wa kike ganin zan iya turata cikin su ?
Mutanen da suka nuna basu ma san da zaman yaran ba a duniya wa kika taba gani ya wanko kafan shi yazo gidan nan da sunan yazo duba su cikin su.
Nace wanan kuma ruwan su ai tunda sune sukai watsi da zumunci don basu san falalan shi ba su da basu bar diyan yar uwar su data bari a duniya ba sun yi watsi dasu don wata manufa dake gare su.
Yace wani manufa ina dai kan su rike ita Amira din ne nikuma sun san ba yarda zanyi da hakan ba itace ma dai ba yar goyo ba.
Don ba don ke ba waye zai iya rike ta irin yadda taso mayar da kan ta a baya abin ya damay ni sosai a lokacin ban da yadda zanyi ne kawai idan nagan ta a lokacin.
Ba laifin ta bane nace dashi akwai kurciya da kuma zugi ana fada mata maganganun da ba zasu fisheta ba ita a ganin ta ta dauka so ne.
Yanzu ai ta gane gaskiya ita da bakinta ranan naji suna hira da mama Altine irin maganganun da sukai ta fada mata ba don Allah ya gyara ba ai lalata suka so yi kawai.
Amma shi yaro ina yasan wanan irin raayin da sukai ta koya mata kan taki ubanta da yan uwan ta.
Nifa shiyasa Nasir da jinior har gobe nake son rayuwan su don tun uwar su na raye basu taba nuna min ko diyana wani banbanci ba dama shi da namiji haka rayuwan shi yake sai kalilan ne ake samu da wani halin na daban.
Bar ni dasu ai zasu sha mamakina don koda ita marigayiyar take a raye may suka mayar da ita a cikin su in ba suna son abin hannun ta ba zasu zagayo ta.
Daddy ba zamu bi ta nasu ba azama daya zan kaita anjima idan an gama kamu sai ta kwana a wurin su zuwa gobe ko jibi ta dawo kaga ai an dai wuce wurin ba shike nan ba.
Yace idan kinga hakan ba matsala shike nan amma ni naso ne kawai a share su, nace kada ku zama daya dasu daddy bari dai kawai nakaita da dare gidan anty Amina sai gobe kuma na tura taje can babban gidan ta wuni masu.
Yace yayi idan ba zai kawo matsala ba nace insha Allahu ba komai shigowan hindatu falon ya dan katse hiran da mukeyi taje cewa ashe kina nan ne nace da ita eh kawai.
Na fara tattara kayan da yaci abincin don na basu wuri sai naji tace ashe yau zulfa zata dawo gidan shine ba a fada muna ba.
Hindatu kina da hankali kuwa ko kuwa raini ne ya kawo hakan tsakanin mu matana don zata dawo zaki ce wai sai na fada maki ke lokacin da kika tafi wana fadawa cewa zaki dawo gidan.
Ko akwai wace ta biya min sadakin wata a cikin ku ne fice min daga falin yar rainin wayon banza kawai.
Ni dai ficewa nayi ina jin yadda yake zagin ta a raina nace wanan kuma ta daukowa kan ta wani sabon fitina a zaune kalau.
Na koma na samu wasu bakin sun shigo gidan nan muka baje ana hira su Zarah na ta faman shirin buki da za ayi da karfe biyar na yamma ranan.
Mun kai wani lokaci sai ga su anty Amina da anty maryam sun shigo nan muka tare su a cikin mutunci na sa Gajiye ta kawo masu abin tabawa.
Barshi inji maryam ta fada cikin rashin damuwa nace a dai kawo masu su taba anty Amina yau fa a gidan ki Amira zata kwana nace da ita.
Tace cikin ya tsune fuska ai mu darajan mu bai kai ace za a kawo muna yar mu gare mu ba don yanzu kin fi iko da ita ai.
Nace haba anty nina isa don dai kawai bamu kusa ne kin san aikina ba lokaci ke gare shi ba ita kuma Amiran tana karatune kun sani.
Yanzu dai bashi ba mun zo ne muji abinda ake ciki tunda mu matsayin mu baikai na anemay mu ba mu san komai akai.
Mun ga idan mun kyale ki zakiyi muna rufarufa ba zurfine ki rubda ciki ga komai don kina ganin kin fi kowa wayau.
Nace haba dai anty may yai zafi haka kuma ai abin baikai can ba duk abinda ake ciki ina kiran anty Asamau na fada mata komai balle ni ai komai shiya saya da kan shi ya kuma tura a gyara mata dakin ta can bauchi.
Bakaji ba ina ruwan an haifa maki jari ashe har jere kin saka ai mata bamu sani ba mu inji anty maryam ?
Tace anty ai saiki tashi mu tafi don wanan ta riga da ta mamaye komai ba komai zamu gane ba sai dai shi may gidan ya kamata mu gani.
Sai dai ki sani duk cin amanan da kikewa yaran nan a kunnuwar mu yake in zalunci abinyi ne sai ki hau ki zauna ga yaran nan kinwa uwar su ma data kafaki balle mu din.
Wasu hawaye ne suka zubo min nace cikin kuka haba anty maryam ban taba zaton irin wanan sakamakon a gareku ba wallahi.
Muryan Zarah ne naji tana fadin may ye na kuka a nan doctor da har zaki tsaya kina zubar da hawayen ki ga banza diyan da aka bari ai ba a ke kadai aka bari ba.
Wa ya nuna nashine har yasan da zaman su a gun ki sai yanzu ne da ake ganin sun zama mutane aka san dasu ko may da za a zo ana fadawa mutane wani magana can mara tushe.
Ke kuma a suwa wai wakike a cikin maganan ko karan kada miya baki kai ba ga zancen nan don haka ki ja bakin ki kiyi shiru ga maganan nan.
Aikuwa nan fada ya tashi a tsakani sai ga suwaiba ta fito daga daki itama ta saka baki aja su aja su anty Amina din fada suke sosai da gori a tsakanin su.
Sai ga Amira ta fito da abokan ta don jin hayaniyar da yai yawa tana ganin ina kuka ta nufe ni bata nufe su ba tana fadin.
Mummy may ya samay ki may my ya faru hakane kuma ina dazun nan kike cewa zan tafi gidan su na kwana.
Sai nace ba komai Amira ina share hawayen dake fuskana ba komai kamar ya uwayen ki ne sukazo suna zargin ta wai ta kakace komai ta hana su shiga har kan bukin ki inji suwaibana take fadin hakana a hasale.
Kamar ya ta daga kai tana kallon inda suke tsaye suna fada take cewa dama wa ake son yai min wani abu bayan mummy ina da wata uwace data fi min mummy ne yanzu.
Nifa yanzu ba zan yarda ba don yanzu ba irin da bane da ake fadawa mutum magana yana yarda amma may mummy ta rage mu dashi a duniya ni da yan uwa na ?
Ke rufa muna baki shanyayun banza kawai daku da uban naku duk an shanye ku baku dana fadi a kan ku.
Duk dukiyar uwar ku da ta bar mai an handamay wama ya sani ko yanzu babu komai da ya saura gare ku.
Haba mama Amina wanan bai dace ba gaskiya kudin dama kuke magana ai ba a hannun ta yake ba kuje ku samu daddy mana shi da komai ke gurin shi amma za a zo a saka mum a gaba da wanan magana haka ?
Kai kai wai may ke faruwa haka ne a nan anyi taron arziki za a kawo muna fitina kuma ana zaune kalau wai may ke faruwa ne wai ?
Gasu nan gara dai da ka shigo don wannan abin baiyi ba gaskiya yarinya tana iya kokarin ta da yara amma babu kunya kuzo muna da zancen wai dukiyan yara idan an baku dukiyan may zakuyi dashi baku za a yi ku rike ko may ?
Mama Altine ne da ranta ya baci take fadin wanan maganan cikin bacin rai da damuwa daddy ya juya gun su yace dukiya wani dukiya kuma ?
Maryam tace na yaran mana da mukaji ance wai an fitar masu kwanaki shine muke son ji idan wanan mai wawason bata wawaahe masu ba ?
Ke kuma tsohuwar munafuka Altine da kike wanan magana don an shan ye ki an gama daku ana baki na goro idon ki ya rufe har kike wai ana zaune kalau.
Kai ku dakata don Allah ba wacce zata shigo min har cikin gidana tazo taba son ciwa iyalina mutunci a zauna kalau.
Dama ai na fada maki keda kike daukan su wasu tsiya ko yar uwar nasu dake da rai yaya ta kare dasu sai yanzu ne kuka san ta bar baya a duniya ?
Wa ya taba zuwa da sunan yazo gidan nan don ya ga yaran da ta bari sai yanzu to bari kuji na fada maku.
Idan ba girma da arziki ne zai kawo ku wurin wanan sha a nin ba na rokeku da ku zauna a gidajen ku daga yau idan yaran suna so zasu tafi inda kuke amma ba a gidana ba .
Ku fice min gida idan fitina ya kawo ku ai akwai hukuma sai kukai karana a can ina jiran sanmacin ku.
Ya nuna masu hanya da su fice mai a gida nan suka fara sake mai bakaken maganganu suka fice daga gidan a fusace.
Suna fita hajiyan harka tana shigowa nan take samun labarin abinda ke faruwa a gidan tace kayya ai dama ace tana gidan haka ya faru da sun ji magana.
Wa ya hanavzaman lafiya a tsakanin marigayiya da Rahama ba su ba ta kasa gane va son ta suke tsakani da Allah ba a kullun cikin zuga ta suke da tai rashin mutunci a dakin ta don suna hassada da bakin ciki da samun ta cikin su.
Ina kafin ta mutu ta gane gaskiya nan ta mutu ba kunya suka wawashe abin da ta bari a dakin ta yanzu kuma sun dawo dan abinda ya saura ga yaran su kuma wawashe shi a tsakanin su.
Nace wallahi hajiya ni ban taba kai zuciyana a irin wanan abin ba a rayuwana duk abinda zanwa yaran tsakanina da Allah nake masu don ina kwadayin samun lada a kan su balle Allah na tuba har anty zata bar baya na ce ni Rahama wai na gaji dasu ko na watsar dasu don ina butulu ko may.
Kuma duk abinda zanyi fa tare da sanin anty Asamau nakeyin shi gidan nan don kafa sheda irin haka dama.
Ko ba sheda fa Rahama sai makiyin Allah zai ce ga sherin ki akan yaran nan a gidan nan wallahi.
Sai da lokacin fita yayi aka sasauta maganan daidai lokacin kuma hajiyan daddy ta shigo gidan kan maganan ita ma tace zata tafi har gida ta samay su tai masu tas yara dai nasu ne su da yar uwar su ta mutu suka kasa rikewa har suna da bakin zuwa yin wani magana yanzu don basu da kunya ko may ?
An dai bata hakkuri na hada mata duk wani abinda za a raba gun kamun a ka kai mata a mota suka tafi.
Ko ba komai dai naji dadi don dani kadai suka sama ba wani abin da zan iya yi a lokaci sai kuka don takaici amma Allah ya rufa min asiri a gaban mutane suka zo min kuma sunji magana sosai ranan.
Anyi kamu anci ansha komai yayi kyau yadda ya dace ayi an tafi da dadin rai a gidan an barmu yan gida muna ta kawar da kayan da aka fitar.
Da dare misalin karfe tara sai ga su anty Asmau sun shigo gidan sunzo bada hakkurin abinda ya faru don ashe daddy ta tafi wurin wani kanin mahaifin su ya fada mai.
Shine ya kira su daya bayan daya yana masu kashedi akan gida daddy tare da fada masu abinda su anty Amina suka zo sukayi.
Sun bani hakkuri nace babu komai ai zama tare ne ya kawo hakan take cewa don Allah abawa daddy hakkuri don tana ma jin nauyin shi da kunya su hada ido don basu da bakin magana akan zancen din an riga da an bata zance ko.
Da haka dai da zasu tafi suke cewa sunji ance za a taimaka akai masu amarya ta kwana don Allah kada abi ta zancen nasu.
Na aika aka kira Amira tazo sai dai tana zuwa ta nuna bazata tafi ba da lalashi da komai ta shirya suka tafi da ita.
Su suwaiba na fadin wai don may zan bari a tafi da ita yin haka kamar na nuna jin tsoron su ne ai, nace haba hakan ai ba komai bane diyar suce fa a barta ta san iyayen ta ta san darajan su tun yanzu don yan uwan uwa ba wasa bane.
Dama sune suka watsar da yaran har haka yakai ga faruwa amma ai tasan anty Asamau don idan muna waya tana kusa nakan bata su gaisa da ita ta dan tambaye ta wasu abu gamay da rayuwan su .
Sai gashi kuma bayan tafiyab su da yarinyar washegari daddy ya samay ni da nashi fadan don may zan tura Amiira wurin su tunda basu da mutunci.
Hakkuri na fara bashi nace daddy yar su ce
Showing 438001 words to 441000 words out of 456145 words
Ya dago kai ya dan kalle ni yana fadin ashe kin san na shigo nace dashi yara ke fada min don dazun na tambaye su suka ce dani baka dawo ba.
Gidan naku ne naga ya cika da jama, a ko ba zan iya shiga wurin ku ba nace aikuwa mata ne dam a gidan namu.
Dama ku ai buki ne harkan ku a taru ana gulman kayan jikin ko wace da ta saka ba wani abin yi sai wanan din.
Dariya nayi na gyara zamana ina fadin ga abin tabawa nan ka dan taba ko kadan ne baiki ba naga ya ture kayan da yake aiki dasu a gefe daya.
Ya sauko don ya fara cin abincin dana kawo mashi din ganin haka yasa nai saurin saukowa daga kujeran na fara zuba mai a plate.
Ina gap da gama zuba mai ne naji yana cewa naga wurin Zulfa a bude mana ko yau ne zata dawo din ?
Murmushi nayi nace yallabai ai kai zan tanbaya wanan don kai ne mai yuka a hannu a gidan.
Don nima a wurin hindatu nake ji wai taga ana gyaran wurin Zulfa din yai murmushi yana cewa daidai yana daukan spoon a hannun shi.
Ashe shiyasa naga tana shan toka a fuskan ta da na shigo gidan wanan ne dalilin nata ashe ?
Murmushi nayi kawai ya fara cin abinci nace dashi ita Niima fa daddy yaushe zata dawo gidan don yakamata ai mata hakkuri itama.
Dakatawa yayi daga kai abincin da ya diba zai kai bakin shi tare da watso min Wani irin kallo yana fadin waike Rahama wani irin zuciya ne gare ki haka ?
To kiji bana son jin zancen yarinyar nan daga yau a gidan nan don nike zama da ita ba wani ba, har yakai spoon din kamar zai dibi abincin ya sake cewa dani wai ke yanzu don rashin zuciya irin naki har zaki ce wai yarinyar nan ta dawo gidan nan da zama ?
Wai kin san ko wacece Niiman da kike magana a kanta ni nasan irin hakkurin da nayi da zama da yarinyar nan a gidan nan don bana son mutum mai zalama da yawan korafi.
Ya debi abincin ya kai bakin shi tare da kada kan shi yace hakkuri nayi dama don bana son wani abinda zai hada ta da wani har yakai mu ga samun sabani da ita.
Kinga hakkurina yaci akan diyana zata iya kallon idona tace wai na fifita su da ita ita har yaushe ta shigo gidan da zata iya fada min hakan.
Ko ku dake gidan yau akwai wacce ta isa tace don may zanwa yarana gata da nai niyar yi ita kuma wanan munafukar har da biye mata su zauna suna wanan irin maganan haka ?
Ko ita taci albarkacin iyayye da diyan ta ne a gare ni da duk wani makircin ku na bani hakkuri haka ba zai taba tasiri a kaina ba.
Nace cikin marairai cewa daddy mu mata sai hakkuri yanzu ai ta gane kuren ta ba dadi ne ace anyi aure ko shekara ba a kaiba an rabu.
Yace ke za a zaga ko ni Rahama zama da wanan yarinyar mai jiran cin gado na nagama shi don dama ni nasan abinda nake zama dashi ba wani ba.
A daiyi hakkuri daddyn mu ai mata afuwan hakana har ta sake bai tankani ba yaci gaba da cin abincin shi ba tare da yai wani magana ba kuma.
Can ina dai zaune shiru naji yace dani mutanen gidan su Saade sun shigo kuwa gidan nan don naji suna korafi wai ba akai masu Amira din ba wurin su.
Nace suna da gaskiya ai daddy shiyasa nace dakai tun zuwan mu a bari taje ta dan kwana masu biyu can su gan ta.
Sai daya kurba ruwan dake aje a gefen shi cikin cup yace dani, wurin wa kike ganin zan iya turata cikin su ?
Mutanen da suka nuna basu ma san da zaman yaran ba a duniya wa kika taba gani ya wanko kafan shi yazo gidan nan da sunan yazo duba su cikin su.
Nace wanan kuma ruwan su ai tunda sune sukai watsi da zumunci don basu san falalan shi ba su da basu bar diyan yar uwar su data bari a duniya ba sun yi watsi dasu don wata manufa dake gare su.
Yace wani manufa ina dai kan su rike ita Amira din ne nikuma sun san ba yarda zanyi da hakan ba itace ma dai ba yar goyo ba.
Don ba don ke ba waye zai iya rike ta irin yadda taso mayar da kan ta a baya abin ya damay ni sosai a lokacin ban da yadda zanyi ne kawai idan nagan ta a lokacin.
Ba laifin ta bane nace dashi akwai kurciya da kuma zugi ana fada mata maganganun da ba zasu fisheta ba ita a ganin ta ta dauka so ne.
Yanzu ai ta gane gaskiya ita da bakinta ranan naji suna hira da mama Altine irin maganganun da sukai ta fada mata ba don Allah ya gyara ba ai lalata suka so yi kawai.
Amma shi yaro ina yasan wanan irin raayin da sukai ta koya mata kan taki ubanta da yan uwan ta.
Nifa shiyasa Nasir da jinior har gobe nake son rayuwan su don tun uwar su na raye basu taba nuna min ko diyana wani banbanci ba dama shi da namiji haka rayuwan shi yake sai kalilan ne ake samu da wani halin na daban.
Bar ni dasu ai zasu sha mamakina don koda ita marigayiyar take a raye may suka mayar da ita a cikin su in ba suna son abin hannun ta ba zasu zagayo ta.
Daddy ba zamu bi ta nasu ba azama daya zan kaita anjima idan an gama kamu sai ta kwana a wurin su zuwa gobe ko jibi ta dawo kaga ai an dai wuce wurin ba shike nan ba.
Yace idan kinga hakan ba matsala shike nan amma ni naso ne kawai a share su, nace kada ku zama daya dasu daddy bari dai kawai nakaita da dare gidan anty Amina sai gobe kuma na tura taje can babban gidan ta wuni masu.
Yace yayi idan ba zai kawo matsala ba nace insha Allahu ba komai shigowan hindatu falon ya dan katse hiran da mukeyi taje cewa ashe kina nan ne nace da ita eh kawai.
Na fara tattara kayan da yaci abincin don na basu wuri sai naji tace ashe yau zulfa zata dawo gidan shine ba a fada muna ba.
Hindatu kina da hankali kuwa ko kuwa raini ne ya kawo hakan tsakanin mu matana don zata dawo zaki ce wai sai na fada maki ke lokacin da kika tafi wana fadawa cewa zaki dawo gidan.
Ko akwai wace ta biya min sadakin wata a cikin ku ne fice min daga falin yar rainin wayon banza kawai.
Ni dai ficewa nayi ina jin yadda yake zagin ta a raina nace wanan kuma ta daukowa kan ta wani sabon fitina a zaune kalau.
Na koma na samu wasu bakin sun shigo gidan nan muka baje ana hira su Zarah na ta faman shirin buki da za ayi da karfe biyar na yamma ranan.
Mun kai wani lokaci sai ga su anty Amina da anty maryam sun shigo nan muka tare su a cikin mutunci na sa Gajiye ta kawo masu abin tabawa.
Barshi inji maryam ta fada cikin rashin damuwa nace a dai kawo masu su taba anty Amina yau fa a gidan ki Amira zata kwana nace da ita.
Tace cikin ya tsune fuska ai mu darajan mu bai kai ace za a kawo muna yar mu gare mu ba don yanzu kin fi iko da ita ai.
Nace haba anty nina isa don dai kawai bamu kusa ne kin san aikina ba lokaci ke gare shi ba ita kuma Amiran tana karatune kun sani.
Yanzu dai bashi ba mun zo ne muji abinda ake ciki tunda mu matsayin mu baikai na anemay mu ba mu san komai akai.
Mun ga idan mun kyale ki zakiyi muna rufarufa ba zurfine ki rubda ciki ga komai don kina ganin kin fi kowa wayau.
Nace haba dai anty may yai zafi haka kuma ai abin baikai can ba duk abinda ake ciki ina kiran anty Asamau na fada mata komai balle ni ai komai shiya saya da kan shi ya kuma tura a gyara mata dakin ta can bauchi.
Bakaji ba ina ruwan an haifa maki jari ashe har jere kin saka ai mata bamu sani ba mu inji anty maryam ?
Tace anty ai saiki tashi mu tafi don wanan ta riga da ta mamaye komai ba komai zamu gane ba sai dai shi may gidan ya kamata mu gani.
Sai dai ki sani duk cin amanan da kikewa yaran nan a kunnuwar mu yake in zalunci abinyi ne sai ki hau ki zauna ga yaran nan kinwa uwar su ma data kafaki balle mu din.
Wasu hawaye ne suka zubo min nace cikin kuka haba anty maryam ban taba zaton irin wanan sakamakon a gareku ba wallahi.
Muryan Zarah ne naji tana fadin may ye na kuka a nan doctor da har zaki tsaya kina zubar da hawayen ki ga banza diyan da aka bari ai ba a ke kadai aka bari ba.
Wa ya nuna nashine har yasan da zaman su a gun ki sai yanzu ne da ake ganin sun zama mutane aka san dasu ko may da za a zo ana fadawa mutane wani magana can mara tushe.
Ke kuma a suwa wai wakike a cikin maganan ko karan kada miya baki kai ba ga zancen nan don haka ki ja bakin ki kiyi shiru ga maganan nan.
Aikuwa nan fada ya tashi a tsakani sai ga suwaiba ta fito daga daki itama ta saka baki aja su aja su anty Amina din fada suke sosai da gori a tsakanin su.
Sai ga Amira ta fito da abokan ta don jin hayaniyar da yai yawa tana ganin ina kuka ta nufe ni bata nufe su ba tana fadin.
Mummy may ya samay ki may my ya faru hakane kuma ina dazun nan kike cewa zan tafi gidan su na kwana.
Sai nace ba komai Amira ina share hawayen dake fuskana ba komai kamar ya uwayen ki ne sukazo suna zargin ta wai ta kakace komai ta hana su shiga har kan bukin ki inji suwaibana take fadin hakana a hasale.
Kamar ya ta daga kai tana kallon inda suke tsaye suna fada take cewa dama wa ake son yai min wani abu bayan mummy ina da wata uwace data fi min mummy ne yanzu.
Nifa yanzu ba zan yarda ba don yanzu ba irin da bane da ake fadawa mutum magana yana yarda amma may mummy ta rage mu dashi a duniya ni da yan uwa na ?
Ke rufa muna baki shanyayun banza kawai daku da uban naku duk an shanye ku baku dana fadi a kan ku.
Duk dukiyar uwar ku da ta bar mai an handamay wama ya sani ko yanzu babu komai da ya saura gare ku.
Haba mama Amina wanan bai dace ba gaskiya kudin dama kuke magana ai ba a hannun ta yake ba kuje ku samu daddy mana shi da komai ke gurin shi amma za a zo a saka mum a gaba da wanan magana haka ?
Kai kai wai may ke faruwa haka ne a nan anyi taron arziki za a kawo muna fitina kuma ana zaune kalau wai may ke faruwa ne wai ?
Gasu nan gara dai da ka shigo don wannan abin baiyi ba gaskiya yarinya tana iya kokarin ta da yara amma babu kunya kuzo muna da zancen wai dukiyan yara idan an baku dukiyan may zakuyi dashi baku za a yi ku rike ko may ?
Mama Altine ne da ranta ya baci take fadin wanan maganan cikin bacin rai da damuwa daddy ya juya gun su yace dukiya wani dukiya kuma ?
Maryam tace na yaran mana da mukaji ance wai an fitar masu kwanaki shine muke son ji idan wanan mai wawason bata wawaahe masu ba ?
Ke kuma tsohuwar munafuka Altine da kike wanan magana don an shan ye ki an gama daku ana baki na goro idon ki ya rufe har kike wai ana zaune kalau.
Kai ku dakata don Allah ba wacce zata shigo min har cikin gidana tazo taba son ciwa iyalina mutunci a zauna kalau.
Dama ai na fada maki keda kike daukan su wasu tsiya ko yar uwar nasu dake da rai yaya ta kare dasu sai yanzu ne kuka san ta bar baya a duniya ?
Wa ya taba zuwa da sunan yazo gidan nan don ya ga yaran da ta bari sai yanzu to bari kuji na fada maku.
Idan ba girma da arziki ne zai kawo ku wurin wanan sha a nin ba na rokeku da ku zauna a gidajen ku daga yau idan yaran suna so zasu tafi inda kuke amma ba a gidana ba .
Ku fice min gida idan fitina ya kawo ku ai akwai hukuma sai kukai karana a can ina jiran sanmacin ku.
Ya nuna masu hanya da su fice mai a gida nan suka fara sake mai bakaken maganganu suka fice daga gidan a fusace.
Suna fita hajiyan harka tana shigowa nan take samun labarin abinda ke faruwa a gidan tace kayya ai dama ace tana gidan haka ya faru da sun ji magana.
Wa ya hanavzaman lafiya a tsakanin marigayiya da Rahama ba su ba ta kasa gane va son ta suke tsakani da Allah ba a kullun cikin zuga ta suke da tai rashin mutunci a dakin ta don suna hassada da bakin ciki da samun ta cikin su.
Ina kafin ta mutu ta gane gaskiya nan ta mutu ba kunya suka wawashe abin da ta bari a dakin ta yanzu kuma sun dawo dan abinda ya saura ga yaran su kuma wawashe shi a tsakanin su.
Nace wallahi hajiya ni ban taba kai zuciyana a irin wanan abin ba a rayuwana duk abinda zanwa yaran tsakanina da Allah nake masu don ina kwadayin samun lada a kan su balle Allah na tuba har anty zata bar baya na ce ni Rahama wai na gaji dasu ko na watsar dasu don ina butulu ko may.
Kuma duk abinda zanyi fa tare da sanin anty Asamau nakeyin shi gidan nan don kafa sheda irin haka dama.
Ko ba sheda fa Rahama sai makiyin Allah zai ce ga sherin ki akan yaran nan a gidan nan wallahi.
Sai da lokacin fita yayi aka sasauta maganan daidai lokacin kuma hajiyan daddy ta shigo gidan kan maganan ita ma tace zata tafi har gida ta samay su tai masu tas yara dai nasu ne su da yar uwar su ta mutu suka kasa rikewa har suna da bakin zuwa yin wani magana yanzu don basu da kunya ko may ?
An dai bata hakkuri na hada mata duk wani abinda za a raba gun kamun a ka kai mata a mota suka tafi.
Ko ba komai dai naji dadi don dani kadai suka sama ba wani abin da zan iya yi a lokaci sai kuka don takaici amma Allah ya rufa min asiri a gaban mutane suka zo min kuma sunji magana sosai ranan.
Anyi kamu anci ansha komai yayi kyau yadda ya dace ayi an tafi da dadin rai a gidan an barmu yan gida muna ta kawar da kayan da aka fitar.
Da dare misalin karfe tara sai ga su anty Asmau sun shigo gidan sunzo bada hakkurin abinda ya faru don ashe daddy ta tafi wurin wani kanin mahaifin su ya fada mai.
Shine ya kira su daya bayan daya yana masu kashedi akan gida daddy tare da fada masu abinda su anty Amina suka zo sukayi.
Sun bani hakkuri nace babu komai ai zama tare ne ya kawo hakan take cewa don Allah abawa daddy hakkuri don tana ma jin nauyin shi da kunya su hada ido don basu da bakin magana akan zancen din an riga da an bata zance ko.
Da haka dai da zasu tafi suke cewa sunji ance za a taimaka akai masu amarya ta kwana don Allah kada abi ta zancen nasu.
Na aika aka kira Amira tazo sai dai tana zuwa ta nuna bazata tafi ba da lalashi da komai ta shirya suka tafi da ita.
Su suwaiba na fadin wai don may zan bari a tafi da ita yin haka kamar na nuna jin tsoron su ne ai, nace haba hakan ai ba komai bane diyar suce fa a barta ta san iyayen ta ta san darajan su tun yanzu don yan uwan uwa ba wasa bane.
Dama sune suka watsar da yaran har haka yakai ga faruwa amma ai tasan anty Asamau don idan muna waya tana kusa nakan bata su gaisa da ita ta dan tambaye ta wasu abu gamay da rayuwan su .
Sai gashi kuma bayan tafiyab su da yarinyar washegari daddy ya samay ni da nashi fadan don may zan tura Amiira wurin su tunda basu da mutunci.
Hakkuri na fara bashi nace daddy yar su ce
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22Chapter 23Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32Chapter 33Chapter 34Chapter 35Chapter 36Chapter 37Chapter 38Chapter 39Chapter 40Chapter 41Chapter 42Chapter 43Chapter 44Chapter 45Chapter 46Chapter 47Chapter 48Chapter 49Chapter 50Chapter 51Chapter 52Chapter 53Chapter 54Chapter 55Chapter 56Chapter 57Chapter 58Chapter 59Chapter 60Chapter 61Chapter 62Chapter 63Chapter 64Chapter 65Chapter 66Chapter 67Chapter 68Chapter 69Chapter 70Chapter 71Chapter 72Chapter 73Chapter 74Chapter 75Chapter 76Chapter 77Chapter 78Chapter 79Chapter 80Chapter 81Chapter 82Chapter 83Chapter 84Chapter 85Chapter 86Chapter 87Chapter 88Chapter 89Chapter 90Chapter 91Chapter 92Chapter 93Chapter 94Chapter 95Chapter 96Chapter 97Chapter 98Chapter 99Chapter 100Chapter 101Chapter 102Chapter 103Chapter 104Chapter 105Chapter 106Chapter 107Chapter 108Chapter 109Chapter 110Chapter 111Chapter 112Chapter 113Chapter 114Chapter 115Chapter 116Chapter 117Chapter 118Chapter 119Chapter 120Chapter 121Chapter 122Chapter 123Chapter 124Chapter 125Chapter 126Chapter 127Chapter 128Chapter 129Chapter 130Chapter 131Chapter 132Chapter 133Chapter 134Chapter 135Chapter 136Chapter 137Chapter 138Chapter 139Chapter 140Chapter 141Chapter 142Chapter 143Chapter 144Chapter 145Chapter 146Chapter 147 Chapter 148Chapter 149Chapter 150Chapter 151Chapter 152Chapter 153