wanan yarinyar bata san arziki ba ina hakkuri don darajan mahaifinta amma ita duk bata san da hakan ba .
Uwarta kuma ta biyewa son zuciyar yar ta bata iya kwaba mata sai yadda take so zasuyi yanzu gata ga yar nata zance ya kare.
Wasu uwanyen haka suke dama basu san su kwaba wa yaron abinda yake ba daidai ba balle ita da ta saba zama ita kadai gun mijinta kunga yanzu yarta na auren mai mata dole ne su dinga ganin ana cuta masu su basu ganin nasu laifin ko kadan.
Mama laraba ce ke wanan magana ni dai ban yi magana ba don tun ranan da na bashi hakkuri yai cikinada fada kamar zai cinye ni danya ban kara magana ba kan zancen.
Ya juyo inda nake nai shiru cikin damuwa yace ina yaran nan suke su duba min store may kuke bukata a sayo maku zan kira sani yazo ya samay ni yanzu.
Nace ina ganin nama da kifi za, a sayo don akwai komai yace su dai duba akaro bana son wani abu ya kare ba sayo wani ba.
Aisha na kira tazo ta fadi abubuwan da za, a karo muna can naji yana waya da Hamza yace aje a sayo kayan abinci nasan suma zai saya masu ne don akwaishi da kokarin kulawa da abin abincin gidan shi sosai.
Tun fitan shi bai dawo ba sai hudu da rabi nafito falo na zauna ba kowa falon ban dade da zama ba.
Sai ga mama tafito falon tace ashe kin fito Rahama nace eh mama sannun ku da zama tace bari ke dai takai zaune tana cewa dani.
Har yanzu yaron nan baidawo bane ni har ranan da ba aiki ma bai zama a gida ya dan huta ne wai ?
Nace cikin murmushi mama ai wani lokaci sai dare yake dawowa shi ko yaushe aikine gareshi kin san dan kasuwa baida hutu ko kadan.
Tace bakaji ba suko sauran na ganin kina nan dashi ne kuna holewan ku ashema har gara can in yana can yana dan zama a gida aganshi.
Nace mama haka abin yake ai zatone kawai irin na dan Adam amma danan da can duk daya ne tace ai basu ganewa ne.
Amma dan banbancin kadan ne kawai mama ni fa duk abinda zace su ta fada duk mai zuwa tazo ai ga wurin nan tunda ba saman kaina mace zata zauna ba tana wurinta ina wurina.
Tace da sauri na raba ki yar nan hakan dai yafi nisa da nisa amma matan nan bar su kawai inda kika gan su ba dadi garesu ba don bakiga yadda sukayi ba ranan da zamu zo ko ?
Nace mama ni abin yana daure min kai ma wallahi zamane dai na kazo nazo sai a zauna afahinci juna a zauna lafiya bashi ke nan ba.
Tace ke kika san wanan ai kinga ita zulfa yanzu tagane mai goya masu bayan ta san gaskiya kin ga ta kama kan ta da wuya aji sunan ta yanzu ga wani matsalan.
Muna nan zaune ina gyara hular rigar dake a jikina sai gashi ya shigo gidan da sallaman shi.
Nan muka shiga gaidashi ya samu wuri ya zauna yace kun gani sai yanzu ko mama haka nake wallahi banda wani lokacin kaina ko kadan yanzu ma wanan meeting din da mukayi ban san dashi ba sai bayan fitana.
Ai maganan da muke yi da Rahama ke nan nace su wa yan can suna can suna ganin kana nan like da ita ne ko wani lokaci kuna tare kamar wani dadi kuke ji anan din.
Yace mama sun san komai hali ne dai irin na mata su sani su take ai ina tafiya da ko wacen su sun san abinda ke wakana ai.
Nace ga abinci can a table yana jiran ka tun dazun yace kai Rahama bar abincin nan bana jin cin komai yanzu hutu kawai nake so nagaji sosai wallahi.
Mikewa yayi zuwa dakin shi mama tace ikon Allah abincin ma mutum bai zama yaci don kan shi wanan neman kudi da wahala yake wallahi.
Wanda bai sani ba sai aga ai masu kudi dadin su kawai suke ji ba wani wahala a tare dasu irin haka nace mama ai neman na kai wahala ne dashi.
Na kai wani lokaci na mike na samay shi a dakin na dauka zan samay shi a kwance amma sai na samay shi ya saka laptop din shi a gaba yana aiki a ciki.
A hankali na karasa inda yake zaune na zauna daga bakin gafon nace a sanyaye daddy na dauka hutun kake ashe aki ka tsiro yi kuma.
Ya dago ya dan kalle ni yace ina fa hutu Rahama abinda ya kaini spain ne ya fito shine kikaga mun wuni yau muna aiki kan sa haka.
Nace Allah ya taimaka ya bada saa yace amin yace wallahi naso weekend din nan mu dan shiga mu samo kayan haihuwan ki tunda ban samu saye a waje ba yadda na saba.
Nace kada ka damu daddy Allah dai ya sauke makani lafiya shine a gaba ai ba za, a rasa wanda za ai amfani dashi ba a wurina don na dan saya ko.
Ya dago tare da sauke idon shi a kaina yace amna in ke baki so kin san shi baby hakkina ne na saya mai kaya da kudina ko ?
Shiru nayi yace ki shirya ki daure ki ku tafi da Aisha ko wata kawar ki ku dan zabo nayiwa matar Abdulkarim waya da zasu dawo ta sayo muna acan dama ina tunanen kagin su dawo din ko kin haihu ne.
Nace ai da, yace kin daiji magana na ke nan ki shirya ku tafi ya jawo briefcase din shi dake gefe kudi masu yawa ya fitar ya aje min a gabana yace idan basu isa ba sai ki fada min na kara maki.
Kallon yawan kudi nakeyi ina mamaki may zan saya haka da wanan kudin masu yawa har yana fadin wai idan basu isa ba saina fada mai ya kara.
Nace ni daddy may zan saya da wanan kudin bayan kace ka bada sauti a sayo muna a waje kuma ya dago idanuwa shi da wahala yasa sukai ja yacehaba Rahama wai bakiga abinda nakeyi bane na fa riga na fada maki yadda nake so.
Shiru nayi can na mika hannu na dauki kudin daya zube min a gefenshi tare da cewa nagode Allah ya saka da alherin sa .
Don dai nasan ba wai ya bani wanan kudin masu yawa bane kan sayen kayan haihuwa kawai sai dai alherine zuwa gare ni tsakanina da shi.
Koda na koma daki na zauna na kirga sai naga har dubu dari biyar cur din su nace cikin mamaki ikon Allah wanan kyautan na daddy da yawa yake gashi kuma ya hanani yin ko magana a gaban shi.
Yadda yace hakan mukayi don Faiza kawata da muka hadu wurin aiki muna shiri da ita, na dauka washegari muka tafi shopping din tare itace ta zabo kaya masu kyau na baby mu ka dawo gida niki niki dasu.
A dakina Aisha ta zube kayan don ko ita saida na sayawa duk wanda ke gidan abinda zai amfane shi din.
Ban dade da dawowa ba ya shigo ina zaune a kasa na saka kayan a gaba muna kallo sai gashi ya shigo dakin idanuwan shi akan kayan.
Yace har an sayo kayan ke nan nace eh daddy yabi kayan da kallo ya sauke idon shi ga wasu set din rigunan yara unicef dake hade wuri daya har guda uku ya dan taba yace kai amma kayan nada kyau wanan kaya haka nasan an biyo ni kudi ko ?
Da sauri nace a, a daddy kadai biyoni don ga canji ka nan ko rabi ban kashe ba ma wallahi yace kinyiwa baby na keta ke nan ashe ke nan nida nace ki saya aita saka mata ko shi shine zaki ma mai shi keta Rahama.
Daddy duk wanan uban kayanay zanyi dashi haka sunyi yawa wallahi yace yanzu saura naki ke nan aban zaki saya ko a ina ?
Nace cikin bata rai daddy ni daka barshi ina da kaya yace hakkin kine fa Rahama don may zaki tauye ni haka ne wai ?
Kina son na zamo cikin mazan dake tauye hakkin matan su ne ko iyalin su wanan ne fa kadai abinda zan maku har kuji dadin zama dani cikin ko wani irin hali nake don Allah ki bari.
Ni ban iya yiwa mace alhetu ba idan ba ita ta bukata ba don ban saba da yin hakan ba a rayuwana amma ke kuma ba tambaya kike ba idan an maki kuma ki kama korafi.
Nafa san may nake a gaba dayan ku kada ki dauka neman kudine kawai a gabana haka.
Ayi hakkuri yallabai kasan ni yar tallakawa ne kuma yar kauye yace baki saba da riya ba ke nan ko , ?
Nace ba haka nake nufi ba daddy gani nayi dai kamar zan takura ma ne kawai da yin hakka yai dan murmushi ya lakoto kumatuna kadan yace Rahama ina ganin har yanzu baki san waye mijin ki ba ko ?
Nace na sani mana daddy na gashi a gaba na kuma ubana mijina na ko ba kaine ba yace to idan kin sani da baki fadi hakan ba yau.
Ko bani auren ki ni may kashe maki kudi ne balle yau ni mijin ki ne kuma mai kaunar ki don haka kibar min haka please ?
Zuria fa zamu tara ni dake mun ma tara din don may zaki dinga mayar da kanki baya ne wai ?
Ke fa Rahama matar manya ce ba matar yara ba shiyasa nake son ki gane shigar ki fitar ki wani kimane da daukaka na a idon jama,a.
Nace angama daddy haka nake so dake amma baki bari kinji dadi ba balle na tare dake suma suji dadin ki.
Har ya kai kofa ya juyo yace zan shiga kano idan zan dawo akwai yaran da zan dawo maki dasu nan don karatun su daga ciki akwai ihisan don haka ki sani ba sai sunzo ba ki gan su.
Nace daddy kana ganin iyayyen su zasu yarda da wanan hukuncin daka yanke kuwa akan diyan su kafa san yadda nake dadu duk da sun san bazan taba cuta masu ba amma abune mai wuya hakan ya kasance ai.
Babu ruwan ki ni keda gida na yadda nake so zan tsara abina ba ra, ayin wani zanbi ba.
Yaficr ya barni a zaune a gurin a hankali na jingina jikina da gado .
Ina tunanen wanan sabon fitina da daddy ke son kuma dauko min ba a gama wani ba zai jawo min wani again.
Ranan da daddy ya wuce zuwa kano tunda safe yai muna sallama sai dai kafin ya tafi sai da yajika kowa na gidan da kudi masu yawa.
Tun da ya tafi na koma daki ban fito ba ina ciki kumshe barci nake a cikin barcin na fara jin canjin yanayi na falka da wani irin ciwon mara mai rikitarwa.
Ban daki na shiga tun a can na fahinci labour yazo min ke na gaba na ya fadi sosai na fito na fara tana dar duk wani abinda zan bukata a tare dani.
Naso na gwada haihuwa ni kadai sai dai kuma yaya zanyi ga yan tsofin da aka kawo min don irin haka amma may zance dasu bazan iya ba gaskiya.
Zarah na kira ta dauki waya ta fara surutun ta nace ke wallahi yau yau ne fa don abin boye nason fita fili.
Tace da magana ke nan nace wallahi tace yanzu yaya za, ayi nace shinr na kiraki ai muji nan dai ta fara min bayanin yadda ya dace nayi.
Amma ina bazan iya ba na daga waya na kira Faiza sai ko gata bata bata lokaci ba na sha wuya wanan katon don ba irin haihuwan baba bane da nagani da sauki.
Da taimakon Allah Allah ya kawo min sauki na sullubo katon da baki dashi kamar uban shi komai na daddy yaton nadashi a jikin shi shima.
Sai sannu Faiza ke min har ta gama gyara mu tace barin fadawa tsofin nan naki kada suga ba ai masu daidai ba nace kyalesu tukun har mu kimtsa.
Sai da ta gama komai na kira Aisha da waya nace ta fadawa su mama na haihu ashe tare suke a falo tace kin haihu anty gaba daya suka dauka ta haihu fa ?
Wanan wani irin haihuwa ne a sauki haka sai gasu koda suka shigo Faiza na tsaye tana gyara yaron da taiwa wanka ta nade shi a showel.
Sai faman mamaki sukeyi nan suka shigo da murnan su suna fafin Alhamdullahi Allah abin godiya Allah ya raya muna.
May aka samu mama tana tambaya Faiza tace kin samu maigida mama sai dai bakine ba kamar dana ba cewa baba.
Tace gida ya biyo dama gidan su bakake ne koshi wanan farin ai satowa yayi wurin uwar shi amma ai komai na gidan su ne.
Waya na dake gefe yai kara na dauka daddy ne ina dauka nai mai sallama yace hayaniyar may kuke haka ne wai nace dashi suna gaisawa da babyn kane da ya kore ka ya fito.
Yace what tsaya don Allah wai da gaske kin haihu ne nace ga mama na mikawa mama din waya ta karba tana fadin sai kaji an haihu bayan ka ko ?
Yace yanzu shi nake ji tace aikuwa gamu nan da mai kama da kai sak wallahi kamar ma har ya baci wallahi Allah yasa dai yayo halin ka.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE DON BA A YAFE BA ONLINE NOVEL NE, , , ,
75
Zaune daddy yake a falon shi yayin da ya kira wayan Zulfa na zaune a gefen tana hada mai abinci don ranan a gunta ya sauka.
Jin maganan da yake ta fahinci nice na haihu duk da taji wani iri a ranta amma a fili cewa tayi dashi Rahama ce ta haihu ?
Yace itace wai lafiya na barta fa sai gashi yanzu na kira tana cewa ta haihu Zulfa tace ikon Allah ai yafi da nan may muka samu ne ?
Yace yaro ta haifa,
Masha Allahu Allah ya raya muna ta fada tace ashe shiga Abuja ya kama mu ke nan satin nan suna ?
Bai bata amsa ba yace barin fadawa su hajiya yanzu nan ya shiga buga waya yana shedawa mutane zancen.
Mun gama waya da shi nace Faiza ta kira min layin Anty ta kira bugu daya biyu gana uku ta dauka gaida ita na farayi bayan sallama.
A ranta sai tana dauka wani kilibibi ne yasa na kira layin nata don naga daddy ya shigo kano ranan.
Nace ya kwana biyu tace Alhamdullahi ya kuke nan ya su mama kuma nace gasu suna gaida ke nace anty kin yi bako fa yau.
Tace bako kuma azaton ta dai zancen mijin ta ne nake mata harta fara tanadin amsan da zata bani lokacin.
Sai nace da ita na haihu yanzu ga baby yana gaida uwar shi, tace au haihuwa kikayi ne Rama ke nan bayan tafiyan mijin ki kika haihu ko ?
Nace yanzun nan na haihu ai bayan shi ma sosai na sauka tace to Allah ta raya nace amin mukai sallama na kashe waya na kit.
Murmushi na sauke don nayi arziki an min magana mai dadi a lokacin sai dai bata tambaya ba ko may na haifa din.
Na kira Zarah inna ta da duk wani wanda ya dace ya san da haihuwan ta bangare na, Faiza bata dade sosai ba ta koma gidan ta don yamma ya soma a lokacin.
Kashe waya na nayi don ina bukatan hutu sosai a lokacin don haka na kashe waya ranan da wuri nai barci na bar su mama da dawainiyar yaron da sauran alamuran gida.
Daddy sai bayan ya gama abinda yake ya shiga gun anty yace da ita kin ji Rahama ta haihu baya na ko ?
A getsire tace dashi eh ta bugo min waya dazun tana sanar dani Allah ya raya akan sunna yace da ita amin ya fita don ya lura da yadda ta daure fuska tun zuwa shi.
Don haka baiba da wani kafan da zata tsiyaye mashi abinda ke kwance a zuciyar ta ba.
Ranan barci na nayi hankali kwance don ban falka ba sai da asuba na kara gyara kwanciya na na tusa wani sabon barci sai da mama dake kwance gefe ta gama abinda takeyi ta tayar dani nai wanka misalin shidda da rabi na safe na tashi.
Ina fitowa kuma na samu ta hada min tea mai kauri tace na sha kafin na shafa mai ya turiri haka na daure na shanye shi duka.
Sai na gyara jikina sai faman zufa nakeyi kwaliya nayi sosai Aisha na shigowa nace ta dan shiga makwabtan mu ta fada masu duk da ba wani hurda nake da su ba amma ya dace nabasu hakkin makwabtakan da ya rataya a kan mu tsakanin mu da su.
Aiko zuwa rana sai gasu suna shigowa gidan ganin baby ikon Allah kamar kada yaron ya sha iskan duniya sai gashi ya fara haske.
Yadda duk ya dace a kula da maijego hakana
Showing 300001 words to 303000 words out of 456145 words
Uwarta kuma ta biyewa son zuciyar yar ta bata iya kwaba mata sai yadda take so zasuyi yanzu gata ga yar nata zance ya kare.
Wasu uwanyen haka suke dama basu san su kwaba wa yaron abinda yake ba daidai ba balle ita da ta saba zama ita kadai gun mijinta kunga yanzu yarta na auren mai mata dole ne su dinga ganin ana cuta masu su basu ganin nasu laifin ko kadan.
Mama laraba ce ke wanan magana ni dai ban yi magana ba don tun ranan da na bashi hakkuri yai cikinada fada kamar zai cinye ni danya ban kara magana ba kan zancen.
Ya juyo inda nake nai shiru cikin damuwa yace ina yaran nan suke su duba min store may kuke bukata a sayo maku zan kira sani yazo ya samay ni yanzu.
Nace ina ganin nama da kifi za, a sayo don akwai komai yace su dai duba akaro bana son wani abu ya kare ba sayo wani ba.
Aisha na kira tazo ta fadi abubuwan da za, a karo muna can naji yana waya da Hamza yace aje a sayo kayan abinci nasan suma zai saya masu ne don akwaishi da kokarin kulawa da abin abincin gidan shi sosai.
Tun fitan shi bai dawo ba sai hudu da rabi nafito falo na zauna ba kowa falon ban dade da zama ba.
Sai ga mama tafito falon tace ashe kin fito Rahama nace eh mama sannun ku da zama tace bari ke dai takai zaune tana cewa dani.
Har yanzu yaron nan baidawo bane ni har ranan da ba aiki ma bai zama a gida ya dan huta ne wai ?
Nace cikin murmushi mama ai wani lokaci sai dare yake dawowa shi ko yaushe aikine gareshi kin san dan kasuwa baida hutu ko kadan.
Tace bakaji ba suko sauran na ganin kina nan dashi ne kuna holewan ku ashema har gara can in yana can yana dan zama a gida aganshi.
Nace mama haka abin yake ai zatone kawai irin na dan Adam amma danan da can duk daya ne tace ai basu ganewa ne.
Amma dan banbancin kadan ne kawai mama ni fa duk abinda zace su ta fada duk mai zuwa tazo ai ga wurin nan tunda ba saman kaina mace zata zauna ba tana wurinta ina wurina.
Tace da sauri na raba ki yar nan hakan dai yafi nisa da nisa amma matan nan bar su kawai inda kika gan su ba dadi garesu ba don bakiga yadda sukayi ba ranan da zamu zo ko ?
Nace mama ni abin yana daure min kai ma wallahi zamane dai na kazo nazo sai a zauna afahinci juna a zauna lafiya bashi ke nan ba.
Tace ke kika san wanan ai kinga ita zulfa yanzu tagane mai goya masu bayan ta san gaskiya kin ga ta kama kan ta da wuya aji sunan ta yanzu ga wani matsalan.
Muna nan zaune ina gyara hular rigar dake a jikina sai gashi ya shigo gidan da sallaman shi.
Nan muka shiga gaidashi ya samu wuri ya zauna yace kun gani sai yanzu ko mama haka nake wallahi banda wani lokacin kaina ko kadan yanzu ma wanan meeting din da mukayi ban san dashi ba sai bayan fitana.
Ai maganan da muke yi da Rahama ke nan nace su wa yan can suna can suna ganin kana nan like da ita ne ko wani lokaci kuna tare kamar wani dadi kuke ji anan din.
Yace mama sun san komai hali ne dai irin na mata su sani su take ai ina tafiya da ko wacen su sun san abinda ke wakana ai.
Nace ga abinci can a table yana jiran ka tun dazun yace kai Rahama bar abincin nan bana jin cin komai yanzu hutu kawai nake so nagaji sosai wallahi.
Mikewa yayi zuwa dakin shi mama tace ikon Allah abincin ma mutum bai zama yaci don kan shi wanan neman kudi da wahala yake wallahi.
Wanda bai sani ba sai aga ai masu kudi dadin su kawai suke ji ba wani wahala a tare dasu irin haka nace mama ai neman na kai wahala ne dashi.
Na kai wani lokaci na mike na samay shi a dakin na dauka zan samay shi a kwance amma sai na samay shi ya saka laptop din shi a gaba yana aiki a ciki.
A hankali na karasa inda yake zaune na zauna daga bakin gafon nace a sanyaye daddy na dauka hutun kake ashe aki ka tsiro yi kuma.
Ya dago ya dan kalle ni yace ina fa hutu Rahama abinda ya kaini spain ne ya fito shine kikaga mun wuni yau muna aiki kan sa haka.
Nace Allah ya taimaka ya bada saa yace amin yace wallahi naso weekend din nan mu dan shiga mu samo kayan haihuwan ki tunda ban samu saye a waje ba yadda na saba.
Nace kada ka damu daddy Allah dai ya sauke makani lafiya shine a gaba ai ba za, a rasa wanda za ai amfani dashi ba a wurina don na dan saya ko.
Ya dago tare da sauke idon shi a kaina yace amna in ke baki so kin san shi baby hakkina ne na saya mai kaya da kudina ko ?
Shiru nayi yace ki shirya ki daure ki ku tafi da Aisha ko wata kawar ki ku dan zabo nayiwa matar Abdulkarim waya da zasu dawo ta sayo muna acan dama ina tunanen kagin su dawo din ko kin haihu ne.
Nace ai da, yace kin daiji magana na ke nan ki shirya ku tafi ya jawo briefcase din shi dake gefe kudi masu yawa ya fitar ya aje min a gabana yace idan basu isa ba sai ki fada min na kara maki.
Kallon yawan kudi nakeyi ina mamaki may zan saya haka da wanan kudin masu yawa har yana fadin wai idan basu isa ba saina fada mai ya kara.
Nace ni daddy may zan saya da wanan kudin bayan kace ka bada sauti a sayo muna a waje kuma ya dago idanuwa shi da wahala yasa sukai ja yacehaba Rahama wai bakiga abinda nakeyi bane na fa riga na fada maki yadda nake so.
Shiru nayi can na mika hannu na dauki kudin daya zube min a gefenshi tare da cewa nagode Allah ya saka da alherin sa .
Don dai nasan ba wai ya bani wanan kudin masu yawa bane kan sayen kayan haihuwa kawai sai dai alherine zuwa gare ni tsakanina da shi.
Koda na koma daki na zauna na kirga sai naga har dubu dari biyar cur din su nace cikin mamaki ikon Allah wanan kyautan na daddy da yawa yake gashi kuma ya hanani yin ko magana a gaban shi.
Yadda yace hakan mukayi don Faiza kawata da muka hadu wurin aiki muna shiri da ita, na dauka washegari muka tafi shopping din tare itace ta zabo kaya masu kyau na baby mu ka dawo gida niki niki dasu.
A dakina Aisha ta zube kayan don ko ita saida na sayawa duk wanda ke gidan abinda zai amfane shi din.
Ban dade da dawowa ba ya shigo ina zaune a kasa na saka kayan a gaba muna kallo sai gashi ya shigo dakin idanuwan shi akan kayan.
Yace har an sayo kayan ke nan nace eh daddy yabi kayan da kallo ya sauke idon shi ga wasu set din rigunan yara unicef dake hade wuri daya har guda uku ya dan taba yace kai amma kayan nada kyau wanan kaya haka nasan an biyo ni kudi ko ?
Da sauri nace a, a daddy kadai biyoni don ga canji ka nan ko rabi ban kashe ba ma wallahi yace kinyiwa baby na keta ke nan ashe ke nan nida nace ki saya aita saka mata ko shi shine zaki ma mai shi keta Rahama.
Daddy duk wanan uban kayanay zanyi dashi haka sunyi yawa wallahi yace yanzu saura naki ke nan aban zaki saya ko a ina ?
Nace cikin bata rai daddy ni daka barshi ina da kaya yace hakkin kine fa Rahama don may zaki tauye ni haka ne wai ?
Kina son na zamo cikin mazan dake tauye hakkin matan su ne ko iyalin su wanan ne fa kadai abinda zan maku har kuji dadin zama dani cikin ko wani irin hali nake don Allah ki bari.
Ni ban iya yiwa mace alhetu ba idan ba ita ta bukata ba don ban saba da yin hakan ba a rayuwana amma ke kuma ba tambaya kike ba idan an maki kuma ki kama korafi.
Nafa san may nake a gaba dayan ku kada ki dauka neman kudine kawai a gabana haka.
Ayi hakkuri yallabai kasan ni yar tallakawa ne kuma yar kauye yace baki saba da riya ba ke nan ko , ?
Nace ba haka nake nufi ba daddy gani nayi dai kamar zan takura ma ne kawai da yin hakka yai dan murmushi ya lakoto kumatuna kadan yace Rahama ina ganin har yanzu baki san waye mijin ki ba ko ?
Nace na sani mana daddy na gashi a gaba na kuma ubana mijina na ko ba kaine ba yace to idan kin sani da baki fadi hakan ba yau.
Ko bani auren ki ni may kashe maki kudi ne balle yau ni mijin ki ne kuma mai kaunar ki don haka kibar min haka please ?
Zuria fa zamu tara ni dake mun ma tara din don may zaki dinga mayar da kanki baya ne wai ?
Ke fa Rahama matar manya ce ba matar yara ba shiyasa nake son ki gane shigar ki fitar ki wani kimane da daukaka na a idon jama,a.
Nace angama daddy haka nake so dake amma baki bari kinji dadi ba balle na tare dake suma suji dadin ki.
Har ya kai kofa ya juyo yace zan shiga kano idan zan dawo akwai yaran da zan dawo maki dasu nan don karatun su daga ciki akwai ihisan don haka ki sani ba sai sunzo ba ki gan su.
Nace daddy kana ganin iyayyen su zasu yarda da wanan hukuncin daka yanke kuwa akan diyan su kafa san yadda nake dadu duk da sun san bazan taba cuta masu ba amma abune mai wuya hakan ya kasance ai.
Babu ruwan ki ni keda gida na yadda nake so zan tsara abina ba ra, ayin wani zanbi ba.
Yaficr ya barni a zaune a gurin a hankali na jingina jikina da gado .
Ina tunanen wanan sabon fitina da daddy ke son kuma dauko min ba a gama wani ba zai jawo min wani again.
Ranan da daddy ya wuce zuwa kano tunda safe yai muna sallama sai dai kafin ya tafi sai da yajika kowa na gidan da kudi masu yawa.
Tun da ya tafi na koma daki ban fito ba ina ciki kumshe barci nake a cikin barcin na fara jin canjin yanayi na falka da wani irin ciwon mara mai rikitarwa.
Ban daki na shiga tun a can na fahinci labour yazo min ke na gaba na ya fadi sosai na fito na fara tana dar duk wani abinda zan bukata a tare dani.
Naso na gwada haihuwa ni kadai sai dai kuma yaya zanyi ga yan tsofin da aka kawo min don irin haka amma may zance dasu bazan iya ba gaskiya.
Zarah na kira ta dauki waya ta fara surutun ta nace ke wallahi yau yau ne fa don abin boye nason fita fili.
Tace da magana ke nan nace wallahi tace yanzu yaya za, ayi nace shinr na kiraki ai muji nan dai ta fara min bayanin yadda ya dace nayi.
Amma ina bazan iya ba na daga waya na kira Faiza sai ko gata bata bata lokaci ba na sha wuya wanan katon don ba irin haihuwan baba bane da nagani da sauki.
Da taimakon Allah Allah ya kawo min sauki na sullubo katon da baki dashi kamar uban shi komai na daddy yaton nadashi a jikin shi shima.
Sai sannu Faiza ke min har ta gama gyara mu tace barin fadawa tsofin nan naki kada suga ba ai masu daidai ba nace kyalesu tukun har mu kimtsa.
Sai da ta gama komai na kira Aisha da waya nace ta fadawa su mama na haihu ashe tare suke a falo tace kin haihu anty gaba daya suka dauka ta haihu fa ?
Wanan wani irin haihuwa ne a sauki haka sai gasu koda suka shigo Faiza na tsaye tana gyara yaron da taiwa wanka ta nade shi a showel.
Sai faman mamaki sukeyi nan suka shigo da murnan su suna fafin Alhamdullahi Allah abin godiya Allah ya raya muna.
May aka samu mama tana tambaya Faiza tace kin samu maigida mama sai dai bakine ba kamar dana ba cewa baba.
Tace gida ya biyo dama gidan su bakake ne koshi wanan farin ai satowa yayi wurin uwar shi amma ai komai na gidan su ne.
Waya na dake gefe yai kara na dauka daddy ne ina dauka nai mai sallama yace hayaniyar may kuke haka ne wai nace dashi suna gaisawa da babyn kane da ya kore ka ya fito.
Yace what tsaya don Allah wai da gaske kin haihu ne nace ga mama na mikawa mama din waya ta karba tana fadin sai kaji an haihu bayan ka ko ?
Yace yanzu shi nake ji tace aikuwa gamu nan da mai kama da kai sak wallahi kamar ma har ya baci wallahi Allah yasa dai yayo halin ka.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE DON BA A YAFE BA ONLINE NOVEL NE, , , ,
75
Zaune daddy yake a falon shi yayin da ya kira wayan Zulfa na zaune a gefen tana hada mai abinci don ranan a gunta ya sauka.
Jin maganan da yake ta fahinci nice na haihu duk da taji wani iri a ranta amma a fili cewa tayi dashi Rahama ce ta haihu ?
Yace itace wai lafiya na barta fa sai gashi yanzu na kira tana cewa ta haihu Zulfa tace ikon Allah ai yafi da nan may muka samu ne ?
Yace yaro ta haifa,
Masha Allahu Allah ya raya muna ta fada tace ashe shiga Abuja ya kama mu ke nan satin nan suna ?
Bai bata amsa ba yace barin fadawa su hajiya yanzu nan ya shiga buga waya yana shedawa mutane zancen.
Mun gama waya da shi nace Faiza ta kira min layin Anty ta kira bugu daya biyu gana uku ta dauka gaida ita na farayi bayan sallama.
A ranta sai tana dauka wani kilibibi ne yasa na kira layin nata don naga daddy ya shigo kano ranan.
Nace ya kwana biyu tace Alhamdullahi ya kuke nan ya su mama kuma nace gasu suna gaida ke nace anty kin yi bako fa yau.
Tace bako kuma azaton ta dai zancen mijin ta ne nake mata harta fara tanadin amsan da zata bani lokacin.
Sai nace da ita na haihu yanzu ga baby yana gaida uwar shi, tace au haihuwa kikayi ne Rama ke nan bayan tafiyan mijin ki kika haihu ko ?
Nace yanzun nan na haihu ai bayan shi ma sosai na sauka tace to Allah ta raya nace amin mukai sallama na kashe waya na kit.
Murmushi na sauke don nayi arziki an min magana mai dadi a lokacin sai dai bata tambaya ba ko may na haifa din.
Na kira Zarah inna ta da duk wani wanda ya dace ya san da haihuwan ta bangare na, Faiza bata dade sosai ba ta koma gidan ta don yamma ya soma a lokacin.
Kashe waya na nayi don ina bukatan hutu sosai a lokacin don haka na kashe waya ranan da wuri nai barci na bar su mama da dawainiyar yaron da sauran alamuran gida.
Daddy sai bayan ya gama abinda yake ya shiga gun anty yace da ita kin ji Rahama ta haihu baya na ko ?
A getsire tace dashi eh ta bugo min waya dazun tana sanar dani Allah ya raya akan sunna yace da ita amin ya fita don ya lura da yadda ta daure fuska tun zuwa shi.
Don haka baiba da wani kafan da zata tsiyaye mashi abinda ke kwance a zuciyar ta ba.
Ranan barci na nayi hankali kwance don ban falka ba sai da asuba na kara gyara kwanciya na na tusa wani sabon barci sai da mama dake kwance gefe ta gama abinda takeyi ta tayar dani nai wanka misalin shidda da rabi na safe na tashi.
Ina fitowa kuma na samu ta hada min tea mai kauri tace na sha kafin na shafa mai ya turiri haka na daure na shanye shi duka.
Sai na gyara jikina sai faman zufa nakeyi kwaliya nayi sosai Aisha na shigowa nace ta dan shiga makwabtan mu ta fada masu duk da ba wani hurda nake da su ba amma ya dace nabasu hakkin makwabtakan da ya rataya a kan mu tsakanin mu da su.
Aiko zuwa rana sai gasu suna shigowa gidan ganin baby ikon Allah kamar kada yaron ya sha iskan duniya sai gashi ya fara haske.
Yadda duk ya dace a kula da maijego hakana
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22Chapter 23Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32Chapter 33Chapter 34Chapter 35Chapter 36Chapter 37Chapter 38Chapter 39Chapter 40Chapter 41Chapter 42Chapter 43Chapter 44Chapter 45Chapter 46Chapter 47Chapter 48Chapter 49Chapter 50Chapter 51Chapter 52Chapter 53Chapter 54Chapter 55Chapter 56Chapter 57Chapter 58Chapter 59Chapter 60Chapter 61Chapter 62Chapter 63Chapter 64Chapter 65Chapter 66Chapter 67Chapter 68Chapter 69Chapter 70Chapter 71Chapter 72Chapter 73Chapter 74Chapter 75Chapter 76Chapter 77Chapter 78Chapter 79Chapter 80Chapter 81Chapter 82Chapter 83Chapter 84Chapter 85Chapter 86Chapter 87Chapter 88Chapter 89Chapter 90Chapter 91Chapter 92Chapter 93Chapter 94Chapter 95Chapter 96Chapter 97Chapter 98Chapter 99Chapter 100Chapter 101 Chapter 102Chapter 103Chapter 104Chapter 105Chapter 106Chapter 107Chapter 108Chapter 109Chapter 110Chapter 111Chapter 112Chapter 113Chapter 114Chapter 115Chapter 116Chapter 117Chapter 118Chapter 119Chapter 120Chapter 121Chapter 122Chapter 123Chapter 124Chapter 125Chapter 126Chapter 127Chapter 128Chapter 129Chapter 130Chapter 131Chapter 132Chapter 133Chapter 134Chapter 135Chapter 136Chapter 137Chapter 138Chapter 139Chapter 140Chapter 141Chapter 142Chapter 143Chapter 144Chapter 145Chapter 146Chapter 147Chapter 148Chapter 149Chapter 150Chapter 151Chapter 152Chapter 153