da jin wanan labarin yake cewa yai matukar farin ciki da jin haka aiko ba komai Saadatu tayi jahadi babba anan, don aure ta hada don farin cikin ka.
Yasan Alhajin shi na gona a wanan lokacin don haka ya juya akalar motar shi zuwa gida inda ya nufo gidan cike da natsuwa da karin imani a zuciyar shi.
Don maganan da mahaifin Saade yai mashi a yanzu ya kara sa jikin shi yin sanyi ga ala, marin kowa na fada mashi cewa aure ne yayi kawai.
Yana shigowa gida ya nufi part din shi duk da sanyin Ac daya kunna a falon bai hana shi jin zafi ba a jikin shi.
Zama yayi tare da mike kafafuwan shi saman dan table din dake a tsakiyan falon.
Ya dafe kan shi da hannun shi daya yana jin kan nashi na matukar sara mashi a lokacin.
Shidai Allah ya gani wanan auren yafi ko wani zo mashi da rikici a rayuwan shi yanzu shi dawani ido zai kalli Saade ko dawani ido zai kalli Rahama wai a matsayin matar auren shi da zasu raya sunna a tare zaman aure fa ba zaman wasa bane anya kuwa Saaden shi tayi la, akari da wanan abin kuwa a yadda yasan mata da kishin tsiya.
Yanzu dai zaiga Saadatun don yaji ta ina zasu fara bullowa zancen don komai yanzu yana hannun ta ita da ta kawo maganan.
Zai danka mata komai ta gudanar yadda take bukata shi nashi idone kawai yaga iya gudun ta.
Yana zancen zuci Zulfa ta shigo falon da ganin yanayinta kasan bata da lafiya a lokacin .
Jin an shigo falon ne yasa shi bude idanuwan shi dake a lumshe ya sauke a kan ta.
Yace da ita lafiya yau kike kuwa ta samu guri ta zauna daga gefen shi tana cewa yau tunda safe a kwance nake na rasa gane kan jikin nan nawa duk kwanakin nan.
Yake cewa ki shirya muje asibiti yanzu adan kara dubaki muji may likitan zaice akai.
Ta mike da kyat tana fadi bari naje na dan kimtsa kafin ka gama sai na fito.
Tana barin gurin yake cewa a ranshi bari ya shiga gun Saade ya ganta tunda hakkanta ya cin ma ruwa ta kai ga yadda take son ganin su.
Fitina kawai take son kirkiro mashi yana fama da fitinan wasu takara saka shi ga wani sabo.
Yamike zuwa part din na anty muna zaune sai kwasan dariya muke Jinior ne ke bin mu yana cizo wai hakoran shi na kaikayi inji anty.
Ganin daddy ya shigo falon muka shiga gaidashi tare da kokarin mikewa mu bar falon don su gana inda nake zaune nake gaida sai baima tsaya falon ba ya nufi bedroom din ta yana fadin ke may ya hanaki zuwa school yau ko ba a karatu ne yau din.
Ta bi yan shi tana fadin ina zata fita mahaukacin soja ya saka security's dinshi akan ta ko ina tabi binta sukeyi yi
Yace binta kuma garin yaya haka ya faru ban sani ba kuma ke baki sanar dani abinda ake ciki ba tace yanzu haka kai nake jira ka shigo nai maka maganan ai.
Don ashe wai har can kauyen su ya tafi gurin iyayyenta ya nuna masu kudi nan dai tana zama take labarta mai abinda ke faruwa take cewa dashi yanzu haka ita duk a rude take ta rasa yaya za, a bullowa zancen don ta fahinci wanan sojan ba karamin tantiri bane gaskiya kamar aure dole ne ga mata a gari ko ina amma ya nace wa mace daya haka ?
Yace yanzu ma zancen ta ya kawo ni gurin ki ai bukatan ki ya biya tunda har kina son hadani da mamana fada.
Yace daga gurin mama furin Abba na nufa na fada mashi kina akan bukatan ki sai dai ki sani ba korafi ko wani magana akan hakan daga baya.
Don bani na bukaci yin hakan ba kece da hujjan ki mara tushe kin samu mama kin mata dadin baki ta hau ta zauna nai magana tace ban yi mata biyayya ba kuma don haka yanzu dabara ya saura gareku.
Sai ki san yadda zaki tsara tunda kece kika hada abinki da kan ki ba wani ya hada maki ba.
Tace Alhamdullahi Allah nagode ma dajin wanan labarin farin cikin hakika Rahama alheri ce a gare mu besty ba zaka gane manufana ba sai bayan anyi abin idan Allah ya tabbatar insha Allahu.
Idan har kana tunanen zan tsaya kishi da Rama a rayuwana kayi kuskure ni don ka nai wanan hadin amma ka kasa fahintana cikin saukin kai.
Kaima kasan abinda mata kewa bakin kishi ai abu daya ne ko toni ina iya hadawa danawa da nata duk ta kwashe na bar mata ita kadai in wanan ne?
In dai har zakai muna wanan alfarman ni da ita don ni may yarage gare ni banda bautan Allah kuma yanzu.
Wani kallo yai mata yace kada ki soma wanan maganan idan ba haka ba wallahi yanzu nace na fasa tace rufa min asiri idan ka kara botse min kuma wa na san zai taro min kai kuma ?
Ban ni dai yanzu nasan yadda zan bullowa wannan yar butsar din tawa don nasan akwai rikici babba tsakani na da Rama nan gaba.
Baki ya tabe yace wanan matsalar kune ni dama ban dauka aka ba balle ku tsanmani zan saka maku baki ga zancen ku.
Tace ai wallahi dole ka saka don kaine ma zakai jagora gurin lalashin abinka don yanzu ta tashi daga Rama ta koma Raman besty kuma.
Haushin zancen ta yake ji fita yayi daga dakin ba tare da ya iya bata amsa ba don haushin maganan yakeji.

********* ********* *********
Duk kwanakin nan biyu idan mun zauna da anty bata da wani zance sai muna huduban yadda zama da miji yake da abinda ya dace mace ta dinga yiwa mijin ta.
Sai nake ganin don Gajiye mai son yin aure ita da maigadi takeyin maganan don zancen su yayi nisa sosai kowa yasan shi zai auri gajiye yanzu.
Don har daddy yasa a gyara masu can baya inda aka gina wa masu aikin gida ba kowa ke zama ciki ba sai shi maigadin da yan komatsen shi keciki dama.
Don haka wani lokaci idan anty na magana har naka yiwa Gajiye dariya mu saka mata wakan shakiyan ci nida su Amira taita murmushi tana jin dadi.
Don haka nakan zauna nai ta sauraren yadda anty ke faman mata nasiha kan hakkin da ya rataya akan mata dakuma namiji daya rataya akan shi ga matar shi.
Nidai har nagaji dajin hudubar anty akan aure da sun fara zan kunna game muyu ta bugawa nida Nasir muna ihun mu ban tsayawa sauraren su .
Ranan Jumma,a da safe daddy yashigo muna falo muna karyawa yana saye cikin wani shadda yaci aiki mai ruwan dark blue sai maiko shaddan ke yi.
Anty tace dakyau nawa sai goga na Ram, , , sai kuma tai shiru tanacewa Allah ya bada saan tafiya aje lafiya a dawo lafiya mukuma ji alheri.
Ya dan dubeta cikin tsiga maikama da harara yake cewa shi zai tafi sai sun dawo kenan, Anty ke cewa tana gaida mutanen gida idan sun tafi.
Bayan ya fitan shi na dago kaina inacewa anty ina daddy zai tafi yau haka aha wanan kwalliya irin haka gashi ko kayan sun matukar karban jikin shi sosai wallahi.
Tace da gaske Rama kayan sun karbe shi nace aikema anty kin gani bana gkina ta murmushi ba sunyi maki kyau ke nan kema.
Gajiye kece hajiya garin su zai tafi ne ko may dariya tayi tace Gajiye shi ai haifafen dan garin nan ne kowa nasa na cikin garin nan gaba daya yan uwan shi ta uwa ta uba.
Unguwa dai zai tafi nan ba nisa bane kwarai nake gani zai tafi a tare muke fadin Allah ya tsare hanya tace amin na mike na kwashi kayan zuwa kitchen ina mai jin haushin rashin shiga na school da wanan fitinanen sojan ya haddasa min kwana biyu ga zarah har gida ta biyo ni kan rashin ganina da batayi kwana biyu.
Ban fito ba sai da na wanke kayan na tsane su na dawo falon na samu Gajiye na gyara gurin na samu kujera na haye tare da kwantawa na mike flat tare da lumshe idanuwana a hankali ina jin raina ba dadi ko kadan a lokacin.
Yar aikin Zulfa ce tashigo tana tambaye gajiye wai tana da goro ta san ma uwar dakin ta gajiye ta ballo goro cikin wani leda tabara tafice daga falon namu.
Gajiye ke cewa nikan hajiya kodai da zaki samune ko ya xon kwanan duk sai matar nan ta aiko neman goro gurina.
Anty tace hakanake gani gajiye kamar ciki Zulfa ta samu shine take wahal da ita haka wallahi.
Daga yadda nake kwance na mike da sauri ina fadin Ciki kega anty Zulfa Allah sarki har nayi mata murna wallahi tun mutuwan hanifa dama bata sake sake jiku ba a gidan nan kamar yadda take a baya.
Keko mutuwar da fa akwai zafi Rama balle irin Zulfa data sawa yar ta rai a gidan nan kamar ikon Allah.
Murmushi nayi don nasan ko ita anty ba baya ba ai gurin son yara sai dai na wani yafi na wani ne don ita tana kawaici akan yaran ta.
Waya anty ta dauka sai naga ta mike tashiga daki tajima a ciki sai tafito jikin ta duk yayi sanyi a lokacin.



ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU

.
IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKIN WASU PLEASE IDAN KIN YI GANGANCI KARANTAWA NA BARKI GA ALLAH.


IDAN KIN BIYA KIKA TURAWA WANDA BAI BIYA BA ALLAH YABI MIN HAKKINA AKAN KI DON HAKA CIN AMANA NE KI KULA YAR UWA PLEASE, , ,

YA ALLAH DUK WACCE KE FITAR MIN DA LITTAFINA HAR TAI MAI NOMBA ALLAH NAKAI KUKA NA GARE KA DAUKAN MIN FANSA ACIKIN GAGAWA AKAN KO WACCE YA NA KAI KUKANA GARE KA DUK MAI KOKARIN YI MIN ZAGON KASA TANA FITAR MIN DA KAYA BA BISA KAIDA BA ALLAH KA DAUKAN MIN FASAN CIN AMANA AKAN TA YA ALLAH, , ,
35
Mota biyu sukai amfani dashi zuwa gurin iyayyen na wanda Abban anty Saade ne ke jagoran tafiyan nasu a lokacin.
Dama daddy yasan gidan mama Altine don haka basu sha wahala ba gurin meman gidan maigari kamar yadda anty tace su tafi can ai masu iso gidan mu.
Batan gaisuwa da su ka da yi na dan lokaci mai gari dake zaune cikin shan jinin jikin shi ganin baki daga birni sun shigo mai lokacin yasa yake ganin kamar wani magana ne ya kawo su kan garin shi.
Cikin natsuwa maigari bayan an gaisa yake cewa sai dai bamu shedaku ba gaskiya.
Abba yai dan dariya irin ma manya yace hakane amma ba Jibo bane nake gani nan kanin Dauda gayu.
Maigari yace kwarai kuwa nine Alhaji amma sai dai ni ban gane ka ba ai amma ina ganin idin kamar wanda na taba sani a baya.
Abba ya yai murmushi sai ya tuna mai da kikrarin da suke mai idan yazo hira gurin mahaifiyar anty Saade da tai zama gurin mama Altine itace ta tayar da ita su biyu ne gun iyayyen su haka yasa da mama Altine zatai aure tazo da yar uwar ta inda ta hadu da wani yaron Alhajin birni dake shigowa da tasa da atamfa da tangaran na mata suna yawo kauye kauye
Nan yaga maman anty tana budurwa lokacin sai dai ta, taso irin bata faye rigima ba ta faye zama shiru shiru da ita sosai.
Abba yace Ali na Aliya ikon, Allah da sauri maigari ya nuna shi da yatsa yace hadin Allah ba hadin bawa ba.
Yace Alhaji Aliyu kaine nake gani yau a gabana ko may Allahu Akbar ashe da rabon zamu kara ganin junan mu.
Yace garin naku ne bana son zuwan shi saboda zuwan shi na min fami da yawa a zuciya na.
Ina tuna marigayiya Aliya Allah ya kai rahamarsa gareta aka karba gurin da amin.
Nan dai aka dan dawo da dogon labari gamay da baya ana hira ana dariya.
Abba ke fada masu ai suna zuwa kauyen mu sosai suna kawo tallah tasa da kumbu da tangaran sai atamfa da sauran kayan amfanin mata a lokaci.
Karramawa sosai maigari yai masu bayan sun natsune yake tambayan ko lafiya suka gan su a garin.
Abba yace sai alheri don ko yanzu tarihi ne ke son maimaita kan shi don yaron nan nawa mu kazo nemawa auren yar ku.
Nan dai Abba ya kawo maganan daluln zuwa su ya fada sunzo ne nemawa dan aure na a gurin su mai gari yai murya yake sai dai bani keda haihuwan yarinyar nan ba amma bari a kira mahaifinta muji na bakin sa duk da dai duk irin hukuncin dana zarta ya dauku akan ta ke nan.
Tsawon dan lokaci kada mahaifina ya iso kana ganin shi kaga tallaka tilis dashi wando daban riga daban yadin roba har ya dan takure daga kasa ga hular kanshi duk zaren shi ya zare baiko daukan sitaci don tsufa.
Yana zuwa ya na zuwa ya furfa na yana gaida da duk jama, an daya samu a gurin cikin mutunci da girmamawa.
Ya samu guri ya zauna tare da lan kwashe kafafuwan shi cikin ladabi ga maigari da jama,an dake gurin a lokacin.
Maigari ne yaiwa baba bayanin abinda ke tafe da bakinsu a kan yar shi sai lokacin ya dago kai yana dan kallon su ba bakin da suka zo wancan satin bane yagani.
Yace amma dai ba wanda suka zo bane satin can don gaskiya hankalina bai kwanta da su ba.
Abba ne yai magana yace malam ka saurarari bayani na da kyau, asali dai nine mahaifin yarinyar da yar ka gurin ta ma, ana marikiyar yar ka a kano.
Wanan da kake gani ya nuna daddy, shine maigidan yar tawa da take aure Alhaji Yusuf Sada Rano.
Wanan dattijon kuma shine mahaifin shi sai wa yannan aminan mu ne da sukai muna rakiya zuwa nan nemawa dan mu Yusuf Rano auren yar ka.
Gaba daya fadan kan su ya daure da maganan Abba din ya fahinci haka garesu yai dan murmushi yace.
Nasan zakuyi mamakin jin hakan da nai maku bayani yanzu to hakan duk mun sani a nan bai sabawa addini ba yin hakan.
Munzo nan da kokon baran auren yar ku ne bisa tsarin ita marikiyar nata watau ya ta ma, ana matar ita mai son auren diyar taku yanzu.
Bukatane mukazo dashi da kokon baran nema iri daga gurin da fatan zaku fahince mu da kunnen basira ba sai an tsaya wani tone tone ba ga yin hakan.
Sai fatan alheri ga yin hakan don ni kaina ga irin mutuncin dake tsakani na da mutanen garin nan da kuma zaman yarinyar a hannun mu acan.
Zan iya daura mata aure kan mutunci da zumuntan dake tsakanina daku tun a baya gaba daya a ka dauka da hakana ne gaskiya baba na yace ai ko mijin hajiya Saade na da ikon yiwa Rahama aure Alhaji balle kai da kan ka dake da iko da abinka.
Amma idan nai haka hankalin abokan tafiya nawa zaifi kwanciya ne idan munzo nan gaban ku ai komai a tare da ku.
Gaskiya ne Alhaji maganan ka dutse zaka iya zartar da komai akan Rahama don tazama yar ka halal malak.
Maigari ya gyara yake cewa Alhaji sai dai mu abinda ya daure muna kai shine jin wanan mijin hajiya Saade shine yazo neman auren yarinyar nan Rahama.
Abba yace hakane nasan zakuji maganan wani banbarakwai haka to amna tunda kuka ganin ni maihaifin Saade ai ya kamata ku san da sanin ta ake komai kuma bukata yin hakan daga gurin ta ya samo asali.
Nan dai Abba ya kara masu bayani yadda zasu fahinta da zancen akansu nan dai aka shiga yin kuskus akan maganan gurin ya rude da nazarin maganan.
Karshe Abba da mai gari ne suka yanke shawaran cewa tunda har sunce mutanen can da suka fara zuwa su dawo to kamata yayi koda zasu dawo su samu an aiwatar da kwakwaran hujja da zai sa su jaye.
Don haka kai Alhaji Yusuf tunda kazo da magaba tan may zai hana ayita takare yanzu a daura auren anan a take.
Da sauri daddy dake zaune cikin su shida bashir tunzuwa ba abinda suka furta a zancen ya dago kai yana kallon maigari.
Maigari yaci gaba da fadin yin haka shine zai kawo saukin wani fitina don naga wa yan nan mutane akwai aki ga al, amarin su basu zo da saukin kai ba gaskiya.
Nan dai aka tsayar da magana cewa za, a daura aure a take a firin wanda Abba ne ya bada sadaki naira dubu dari cif daga aljihun shi .
Atake mai shela ya fita ya sanar akwai daurin aure yanzu a kofan gidan maigari ga wanda Allah yaba ikon zuwa.
Kafin wani lokaci gurin ya cika da jama, a dan su sheda don haka al, adan kauye yake
Showing 144001 words to 147000 words out of 456145 words
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22Chapter 23Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32Chapter 33Chapter 34Chapter 35Chapter 36Chapter 37Chapter 38Chapter 39Chapter 40Chapter 41Chapter 42Chapter 43Chapter 44Chapter 45Chapter 46Chapter 47Chapter 48Chapter 49 Chapter 50Chapter 51Chapter 52Chapter 53Chapter 54Chapter 55Chapter 56Chapter 57Chapter 58Chapter 59Chapter 60Chapter 61Chapter 62Chapter 63Chapter 64Chapter 65Chapter 66Chapter 67Chapter 68Chapter 69Chapter 70Chapter 71Chapter 72Chapter 73Chapter 74Chapter 75Chapter 76Chapter 77Chapter 78Chapter 79Chapter 80Chapter 81Chapter 82Chapter 83Chapter 84Chapter 85Chapter 86Chapter 87Chapter 88Chapter 89Chapter 90Chapter 91Chapter 92Chapter 93Chapter 94Chapter 95Chapter 96Chapter 97Chapter 98Chapter 99Chapter 100Chapter 101Chapter 102Chapter 103Chapter 104Chapter 105Chapter 106Chapter 107Chapter 108Chapter 109Chapter 110Chapter 111Chapter 112Chapter 113Chapter 114Chapter 115Chapter 116Chapter 117Chapter 118Chapter 119Chapter 120Chapter 121Chapter 122Chapter 123Chapter 124Chapter 125Chapter 126Chapter 127Chapter 128Chapter 129Chapter 130Chapter 131Chapter 132Chapter 133Chapter 134Chapter 135Chapter 136Chapter 137Chapter 138Chapter 139Chapter 140Chapter 141Chapter 142Chapter 143Chapter 144Chapter 145Chapter 146Chapter 147Chapter 148Chapter 149Chapter 150Chapter 151Chapter 152Chapter 153