mahaukacin da ya like maki yazo ya samu daddy ku da hauka yace koda karfin tsiya sai ya aure ki.
Duk da naji tsoro a raina amma a fili cewa nayi Allah ya fishi mugu azzalumi kawai.
Nace mata sai na dawo tace fitan zakiyi ke nan Rama ?
Nace anty saboda shi na zauna gida karatuna ya tsaya kuma ?
Tace to Allah ya tsare nace amin anty sai na dawo ke nan tace Allah yasa nafice.
Tun barin layin uguwar mu na lura da wata bakar mota dake bina a baya a guje na kwasa Allah dai ya tsare ni na isa school lafiya.
Yinin ranan a firgice na wuni har Zarah ta fahinci hakan a gareni take tambayana ko lafiya nake haka yau ?
Ban boye mata ba tace badai boy kike nufi ba dan gidan haruna daura nace kamar haka naji sunan shi fa.
Tace aiko kin shiga uku wallahi wanan dan iskan mara mutunci may zakiyi dashi ke ?
Tace abu daya zan muyi shine idan mun tashi sai ki shiga motana ni na tafi da naki gida na ko yaya kika gani ?
Nace hakan yayi ba matsala ai yadsa muka tsara haka mukayi na samu na isa gida lafiya a firgice itakuma ashe sun bita sai da sukaga ta nufi gidan ta har can suke tafito sukaga bani bace sai suka juya.
Washe gari tsohuwar motar anty na shiga basu gane ba sai da naje school suka fahinci nice a cikin motar.
Aiko suka darkakeni saida na shige wani guri na samu na isa gida lafiya haka yasa na fadawa anty halin da nake ciki.
Tace na zauna babu inda zan kara zuwa sai komai ya lafa zan fita nayi hakkuri da karatun kwana biyu.
Shiryawa tayi sai gidan mama laraba tasamu babu kowa a gidan suka gaisa da ita take cewa lafiya dai ko Saade.
Nan anty take cewa mama magana nazo muyi dake da fatan zaki saurareni ki fahinci abinda nazo maki dashi.
Nasan baban su Amira a duniyan nan babu shawaran da zaki bashi bai dauka ba kuma ya zamo mai alheri a karshe.
Tace matsala kuka samu ne dashi tace mama ba matsala bane sai dai kuma matsalar ce.
Nan dai ta kwashe abinda ke tafe da ita na neman shawara akan auren da take son yakara ya bijera mata.
Mama laraba ra dubeta da kyau tace yanzu ke Saade da kanki koke son mijin ki ya karo maki kishiya bayan wa yan nan ma da kike dasu ba wani zaman dadi kukeyi dasu ba.
Nikan Saade da zaki bi shawara na da sai nace hakan ma da kuke ya isa don kishiya fa ba dadi gareta ba.
Mama nasan da hakan amma ina sin ki fahinci manufata a hakan don samun saukin mu nan gaba dani dashi da yaran baki daya.
Mama kinga da yaje gaba a kasa rike mai diyan diyan shi yace zai dauko wata don nasan halin shi akan yaran shi.
Gara ya dauko wacce na sani kuma na yarda da ita da ya dauki fitsarariya wace zata zo ta ganawa yara mugun hali.
Umm, umm Saade dadai ki kara tunane matan yanzun ko ince mutum yanzu ba dan goyo bane wallahi.
Mama garafa da wanan din nasan ta yasan ta musan halinta kin ga yafi komai sauki a gare mu.
To ke saade dakike wanan magana Allah fa shi yai ciwo yai magani ai ciwo ba mutuwa bane don sai mai lafiya ma ya tafi yabar maiciwon a duniya.
Tace hakanane mama nidai don Allah a duba min bukatana ko za, a dace ga hakan tunda ni yaki jin magana na.
Mama tace kin ga idan har wacce kike son ya aura din batai mashu ba ko kuma ita din butulu ce fa kinga kin zalunce shi ta zalunce ki ke kuma.
Jikin anty yai sanyi a lokaci guda hankalinta ya dan tashi take kuma wani natsuwa yazo mata tace cikin kuka mama ba wata bace can daban nake son ya aura sai Rahama dake gurina.
Kin dai gane ta kinga ko nasan halinta yasan nata ai banyi tsan manin irin hakan ba daga gareta.
Salati mama Laraba ta saka tare da tafa hannunuwan ta alaman mamaki ya kashe ta lokaci guda.
Tace Rahama dai Rahama dai Sa,ade dana sani ta gurin ki anya kuwa kanki daya Saade da zakice mijin ki ya auri yar uwar ki.
Mama Rahama yar uwata ce amma bata jini ba sai girma da arzikin daya hada mu ya koma yan uwan taka a tsakanin mu yanzu.
Jikin mama laraba yai sanyi yadda taga anty na zubar da hawaye tasan irin haka ita kadai tasan abinda take ji a zuciyar ta ai banza baikai zomo kasuwa.
Idan ya duba ga maganan ta gaskiya ne don dan nata ai yana son kulla amma Allah bai hada shi da matan arziki ba ita waban mai hankali lalura ya hana ta bashi lokacin ta.
Mama Laraba ta nisa tace yanzu tunda ke da bakin ki kika bukaci hakan ai Alhamdullahi da shine yazo da maganan kinga sai muce yayi rashin hankali duk da aure ya hallata a tsakanin shi da ita.
Don haka ki barni dashi insha Allahu zamu zauna dashi kan maganan kuma da yardan Allah zai fahince ni don ban taba bukatan wani abu dashi ba bai min ba don haka wanan din ma ai bazaki ba idan na fahintar dashi.
Anty tace nagode mama da kika fahince ni haka da wuri ba kowane zai gane hakan ba sai ma ai min daukan banda hankali ban san ciwon kaina ba.
Ai maganan aure babban magana ne Saade ba ko wace mace zata iya wanan sadaukar da ran da kikayi ba haka shiyasa za, a dauka ko baki da hankaline.
Tsananin son mijin ki da yaran ki yasa har kike masu gwadayin fatan alheri a rayuwa nan gaba.
Anty tace ni har ga Allah ina ma mijina kwadayin kasancewa da wanan yarinyar koda kuwa ina da raina na ne nidai bukatana naga ya samu kwanciyan hankalin aure kaman ko wani magidan ci a gidan shi.
Naji na kuma gane manufan ki don haka banda abinda zance sai nace Allah yai maki albarka a rayuwan ki yasa a gama da duniyan nan lafiya.
Tace amin a sanya tasan takawo maganan inda za ai mata maganin shi indai mama ce don Allah ya bata sa, an dan yar uwar ta sosai.
Tace yanzu mama ba sai na sake mai magana ba ke nan ko?
Ba sai kin shiga ba Saade ki barni dashi kawai zamu zauna da shi insha Allahu.
Tai sallama da mama Laraba ta barta tana mamakin ta da tausaya mata don tana gani don kawai rashin lafiyan dake damunta ne ya kawo mata wanan danyen yanke hukuncin da taiwa kan ta.

********* ********* *********
Ance labarin gari a tambayi dan gari ashe komai nawa dadin hira yaja Gajiye har sunyi hiran da Farida.
Wanan labarin ne da sunan kauyen mu da sunan iyayyena yadda za, a samay su idan sunje garin mu kaf Farida ta fadawa soja komai.
Haka yasa yafita batun daddy a nan birni suka zagaya shi da iyayyen suka tafi har kauyen mu gurin iyayyena.
Kan sunzo nemawa dan su aure na Allah ne ya taimaka babana da maigari yakira shi kan zancen basira yazo mai yace.
A gaskiya sunan na haifi Rahama ne kawai yanzu amma uwar rikon ta da maigidan ta sunfi ni iko da ita don ko a gurin su take kun ga idan nace nai masu haka ba kyautawa zama tare ba.
Basu so jin haka ba sai cewa Alhaji haruna yayi amma kai ka haifi abinka kana da iko da ita har yanzu .
Kayi tunane akai ko nawa kada kaji komai zan zube maku shi yanzu anan basai mun tashi ba.
Babana yace adaiyi hakkuri don Allah Alhaji a bari zan ga shi marikin nata don idan nai masu haka kamar naci amanan zamane.
Don dai a rayuwa banda abinda zancewa wa yan nan mutane sai godiya ga irin alherin da suke min.
Basu so haka ba sai da maigari ya basu hakkuri akan su dawo nan da sati mai zuwa suji shawaran da aka yanke akai.
Da haka sukai sallama suka kawo alheri mai yawa na ban mamki suka babana da dama duk wani wanda ke fadan maigari a wannan lokacin.
Suka tafi sukan mutane sai gani suke ana dace nayi saa da wanan babban kamu da nayi a rayuwana.
Kafin wani lokaci bari ya karade garin ko cewa wasu masu kudi sunzo neman aure na daga birni ai.
Bayan tafiyan sune maigari yake cewa baba yadda yayi yana da kyau gara da bai biyewa abin duniya sai an tsaya anyi bincike akai.
Don irin haka karshe sai anyi abin yazo ya ya koma ciki kuma don duk auren da aka gwada mai dukiya haka baya karko.
Don gaskiya kalaman dattijon nan yasa na zargi wani abu a kasa ko.

Babana da kanshi ya tafi gurin mama altine da wanan labarin tace ikon Allah amma may zai sa su zagaye ta bayan shi Alhaji yusuf sozo nan bayan a tare suke can a gari guda.
Ai idan ma da sanin shi to tare ya kamata suzo nan ko kuma azo tare da wakilin shi nan din.
Koma may ye zan kira ita yar uwar nata da take gurinta naji na bakin ta baba yace haka yafi dai.
Ya tafi ya barta tana mamare bayan ya dan bata wani abu daga cikin abinda aka bashi yakai saura ya boye bai bari mama lauratu tasan da maganan kudin ba.
Don da zaran ta sani sunan su sorry sai taga bayan su kaf hankalinta zai kwanta da su.
Inna da ta samu labari take cewa maigidan ta ita gaskiya mutanen sun bata tsoro don hankalinta bai kwanta ba sam da wanan magana maigari yace zai sayo mata kati sai ta kirani taji may ke gudana ne wai nasan da zuwan bakin ko kuwa ?

Sakon kiran da mama laraba kewa daddy ya samay shi don da wayan ta tai amfani ta kirashi.
Amma sai aka samu akasi baya gari yake cewa mama injin dai lafiya ko tace babu komai sai alheri wani dan magana ne nake son muyi da kai kawai.
Yace ta dakance shi zai dawo nan zuwa jibi don yaji may ke gudana a gurin ta sam bai kawo wanan zancen a ran shi ba don daga shi sai Sadatun shi ke wanan rikicin dama a tsakanin su don ko ni da akeyi a kaina banda labarin hakan.
Mama Labara taje gun mahaifin daddy ba tare da sanin yar uwarta ba takai mashi shawaran da Saade ta kawo mashi.
Dama shi Abba ya dade da bada goyon bayan hakan don haka bata samu wani matsala ba gurin fahinta.
Yake cewa tunda har matar shi da kansa ta bude baki ta bukaci hakan to ya kamata aje agana da iyayyena don su san da zancen suma.
Da dare daddy ya dawo don haka bai samu zuwa gurin mama ba sai da safe bayan ya karya yatafi ansa kiran uwar goyon shi kaunar mahaifiyar shi.
A falon ta suka zauna kamar ta sani Faridan ta ta canza yanzu tace dashi su fita daga waje magana ne wanda daga shi sai ita sai Allah take son suyi shi don kada abin yazo baiyi ba abatawa saadatu sunan ta ga banza.
Suna barin gurin ya bude mota motar shi suka shiga don ya fahinci magana ce mai muhinmanci ta siri kuma da alama bata son a ji koma may ye din..
Sunan shi ta kira a hankali take cewa da fatan abinda zan fada maka bazai zazzafa ma zuciya ba zaka tausasa zuciyar ka ka fahince ni da kunnen basira.
Yace insha Allahu mama nai maki alkawari koma may ne indai bai sabawa sharia ba zan yi nazari ko na rugumi ko may ye da zuciya daya da hannu bibiyu.
Tace masha Allahu nakuma gode Allah yai maka albarka da fatan samunbalheri ga abinda zamu tatauna din yace amin.
Tace Yusufa ina son na rokeka da farko da kayi hakkuri kuma ka kara hakkuri da iyalin ka kowa da irin rayuwan da Allah ya kaddaro mai dashi.
Yusufa ina son in roke ka ba don nakai ba ko na isa ba sai don hangen alherin da abin zaizo ya haifar daga baya.
Kayi hakkuri bukatar da matar ka ke binka dashi na auren yar uwarta ka yarda ka cika mata burin ta a kan hakan.
Don ni gaskiya Saadatu duk ta sare min gwiwa na da wanan zancen don haka zancen abune na a tsaya a duba bisa ga hujjojin da takawo din.
Kaga Saadatu dai mace baza, ace bata kishin ka bane tanayi kaima ka sani abinda manufan ta ya hango ne sai an daure za a hango shi din.
Sannan kuma aure ne take kokarin kullawa aure kuma kowa yasani sunnan ma, aikine sallalahu Alaihim wassalam.
Bai kamata ki daukan shawaran ta ba tunda itace da kanta ta bukaci da ai haka din baiwa kaine ka bijiro mata da zancen ba.
Balle tace anyi mata butulci ko wani abin cin fuska da zarafi, tazo ta mutu din da take ikirari kazo kana da ka sanin rashin cika mata burin ta tun tana raye.
Ka ga idan abin yai dadi ko bayan ta zata sha addua ga wanan hadin da tayi tsakanin ka da yarinyar nan.
Idan ma bata mutum ba dai itace ta bukaci yin hakan da kanta da bakin ta ba wai wani ya tilasta mata yin hakan ba ita ta nema da kan ta.
Tazo din ta mutu yaranta dakai da take ganin zasu iya fadawa wani hali kazo kana kukan rashin yin haka daga baya.
Jikin shi ne yai sanyi don bai taba tsanmanin wanan magana bane mama Laraba ke neman shi ba dayi.
Saadatu ta bashi mamaki matuka da ta nace akan wanan magana haka har yakai tun sunayi su biyu a tsakanin su gashi yanzu takawo maganan ga magabatan shi.
Yanzu shi yaya zai iyacewa mama hakan bazai yuyu ba bayan kwararan hujjujin da ta kawo mashi yanzu a gaban shi wanda ita da Sa,adatu ke gani hujjane a garesu.
Shi fa bai taba jin son Rahama da aure ba a rayuwan shi ba asali ma dai mamakin mazan da ke ta hauka akanta yakeyi don baiga abin burgewa gareta ba gaskiya sai dai idan farar fatan ta tane ke rudin su.
Shi bayan Saadatun shi fa baitaba tsayawa kallon wata mace bata bashi sha, awa haka na ba.
Ko su wa yan nan dake gidan shi aure daine mukkadari kawai a tsakanin shi da su har yake zaune dasu don biyayya kawai.
Amma bawai don yasan wani dadin zama da mace ba may mace zata iya maka wanda zai iya saka natsuwa ko shagalta a kan ta duk shi bai san wanan abin ba.
Can dai ya nisa bayan ya fahinci mama tagama fadar abinda zata fada mai shi take saurare yanzu.
Yace mama nagode da wanan shawaran naki tunda haka take bukata da kan ta insha Allahu zan yi kokari naga na cika mata gurin ta akan hakan.
Sai dai kuma bazan so jin daga baya tadawo tana wani korafi ba da bakin ta akan yin hakan kuma don mama kin san halin mata akan kishi kuma.
Ita Saade na rasa may nene ke damun rayuwa ta data yankewa kanta wanan danyen hukuncin haka ba ?
Mama tace yanzu ai koma maye dai itace ta bukaci ganin hakan a rayuwan ta ko naka yanzu shine kayi kokari kaga ka kwatanta adalci a tsakanin matayen naka.
Don tserewa hushin ubangijin ka a gobe kiyama Allah kuma yai maka albarka ya daukaka zurianka.
Yakare muna ku daga sherin makiya da mahassada nagida da na waje sai ka jajirce sosai gurin kwantata adalci akan iyalin ka don nauyi ne mai girma ya kara hawa kan ka yanzu kuma.
Na kuma ji dadi kwarai na rokeka alfarma irin haka kuma kai min shi a take babu bata lokaci don haka yanzu abinda nake son ka dashi shine.
Kabar wanan zancen a ranka itama Saade sai dai ka shirya yanda neman auren naka zai kasance idan har Allah yayi sai dai aji kawai anyi auren.
Don baiyyana shi zai iya kawo muhawara mai karfi har takai karshe azo a samu akasi a hakan.
Yace hakane mama insha Allah zan bi al, amarin a tsanake yadda abin zaizo a cikin sauki ba tare da rayuka sun baci ba akai.
Tace hakan na da kyau Allah yai maka albarka tagi ka huta abin baka dama aanan shine maganan kawai .
Yai mata godiya tare da sallama tana ta saka mai albarka tafita yaja motan shi yana tafe yanajin wani irin abu a zuciyar shi.
Shi yanzu ma ta ina zai fara ne wai takan Saade ko ta kan wanan yarinyar da akalaka mai akai ko kuma da maganan jama, a zaiji.
Mahaifin shi dana Saade ne suka fado mashi arai dole ta kan su ne zai fara bai tafi gida ba sai da yaje kasuwa ya samu Abba suka gana dashi akan maganan.
Abba yai murna kwarai
Showing 141001 words to 144000 words out of 456145 words
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22Chapter 23Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32Chapter 33Chapter 34Chapter 35Chapter 36Chapter 37Chapter 38Chapter 39Chapter 40Chapter 41Chapter 42Chapter 43Chapter 44Chapter 45Chapter 46Chapter 47Chapter 48 Chapter 49Chapter 50Chapter 51Chapter 52Chapter 53Chapter 54Chapter 55Chapter 56Chapter 57Chapter 58Chapter 59Chapter 60Chapter 61Chapter 62Chapter 63Chapter 64Chapter 65Chapter 66Chapter 67Chapter 68Chapter 69Chapter 70Chapter 71Chapter 72Chapter 73Chapter 74Chapter 75Chapter 76Chapter 77Chapter 78Chapter 79Chapter 80Chapter 81Chapter 82Chapter 83Chapter 84Chapter 85Chapter 86Chapter 87Chapter 88Chapter 89Chapter 90Chapter 91Chapter 92Chapter 93Chapter 94Chapter 95Chapter 96Chapter 97Chapter 98Chapter 99Chapter 100Chapter 101Chapter 102Chapter 103Chapter 104Chapter 105Chapter 106Chapter 107Chapter 108Chapter 109Chapter 110Chapter 111Chapter 112Chapter 113Chapter 114Chapter 115Chapter 116Chapter 117Chapter 118Chapter 119Chapter 120Chapter 121Chapter 122Chapter 123Chapter 124Chapter 125Chapter 126Chapter 127Chapter 128Chapter 129Chapter 130Chapter 131Chapter 132Chapter 133Chapter 134Chapter 135Chapter 136Chapter 137Chapter 138Chapter 139Chapter 140Chapter 141Chapter 142Chapter 143Chapter 144Chapter 145Chapter 146Chapter 147Chapter 148Chapter 149Chapter 150Chapter 151Chapter 152Chapter 153