maki ranan da kikaiwa yarinyar nan wullakanci a gaban kowa don tace kawai key baya hannuta yana hannun maigidan.
Nan fa faban bakinta kika rufe ido kina mata cin mutunci son ran ki ashe ke da wani manufa kika sa sai a bude maki dakin duk da hanakin da mukayi.
Tace mama aiba ni kadai keda key din ba sherine kawai aka kulla min don a bata min suna kawai wallahi amma ni ina ruwana da kayan shi.
Yace kina nufin Rahama ce ta shigo ta daukar min abu bayan sun dade a wurin bata dauka ba sai yanzu.
Mama tace kai amma Zulfa baki biyo nono ba wallahi sai dai a yabe mu da fada amma ba mugun hali ba dan hannu.
Ta juya rai a bace inda mama take tace mama may kike nufi kema satan zaki dafa min ko may ?
Yace rashin kunya zaki mata yanzu ko may tace ba rashin kunya sai gaskiya tunda dai dama kowa yasan yanzu mama don anga Rahama na nan sai wani shishige mata akeyi don ana zaton itace mai shi.
Ihsan da suke dakin ta ta kumaji plan din su ta fito tace a a anty ba ruwa little mum ga maganan ku naafaji hiran ku ranan da kike basu labarin kinga white gold a dakin daddy masu yawa.
Akace ki diba sai yanzun kuma zakice wai ba ke bace tai salati tace yanzu ihisan ni zakiwa sheri abin naki har yakai can ashe ?
Nan dai duk gidan yai tsit ana sauraren fitinar su sai dai ba wanda ya fito sai sauraren su da akeyi kawai a sauran dakunan kamar yadda muma muke sauraren su din a inda muke zaune.
Duk yadda daddy ya buga taki fito mai da kayan shi su mama sukace ya kyaleta Allah ya tona asirin mai shi bai so ba haka ya yarda yabar zancen rai bace mai.
Ni dai a bangare na Allah ya fitar min da hakkin kazafin da taimin ya hau kai ba tare daya bincika ba gashi abinda ya wakana a tsakanin su yanzu.
Washe gari tunda safe suka bar garin tare da sauran bakin da suka zo sai gidan ya koma muna tsit iyamu aka bari dasu mama kawai agidan.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE DON BA A YAFE BZ ONLINE NOVEL NE, , , ,
76
Tun tafiyan bakin mu su Aisha suka gyara min gida ko ina ya rage daga ni sai yara dasu mama da zasu zauna har zuwa lokacin da zanyi arbain kafin su wuce.
Har wanan lokacin iyakana da daddy ina kwana ko shi daga kofa zan tsaya na gaida dashi na bar dakin wani lokaci ma a falo zamu hade ko ina barci zai fice daga gidan sai in yadawo nai mai sannu da zuwa daga inda nake.
Ban bin shi baya balle na daukowa kaina magana ko wani sabon fitina, nayi hakane don na kama kaina akan komai dama sati biyu aka bani a wurin bautar kasa na don haka lokaci kawai nake jira na koma.
Banda matsala da yaran da ya kawo min sosai Jinior dai ne da Ihisan keda dan matsala kuma basu wuni a gida in sun fita tun safe acan zasu wuni sai shidda na yamma zasu iso gida.
Ina ganin shiru ya dan damay shi ne ko yaya ban sani ba dama can shi dai ba gwanin zama bane ai hira dashi don ko yaushe zaka samay shi busy ne.
Na kan yi mamakin yadda yakan samu lokaci a baya yana hira da hindatu ko don yawan nacin ta ne tafi mu nacewa ban sani ba.
Case din shi da Zulf sai da iyayye suka sa masu baki daya je gida tafito mai da dutsen shi don yasan cewa ita ta dauke su.
Tasha fada sosai a gurin iyayyen su sai datace ba itace ta dauko da hannun ta ba Rafia ce kaunar ta data shiga dakin tana ciki ta dauka aka kuma bincika haka din ne sannan ta samu sasauci a gurin shi.
********* ********* *********
Tun bayan haihuwa na ban faye fitowa falo ba ina dakina ko barci ko wani abin tunda bana sallah a lokacin.
Ina kwance a dakina don tun yamma dana dan leka su mama a falo na dawo daki kafin magariba ban sake fitowa ba har tara da wani abu na dare.
Yanayin rayuwa ta tun haihuwa na gaba daya ya sake min bana son yawan hayaniya haka kuma bana yawan zama cikin mutane sosai.
Dama da yara nafi sakewa ko a baya ban faye shiga cikin manya ba ina zama ana suraitai don nakan rasa may zan fada wani lokacin .
Kwance nake sai dai ba barci nakeyi ba idona kawai na rufe na dora tsintsiyar hannuna a fuskana.
Idanuwa dake rufe bai hanani sanin ya shigo dakin nawa ba don kamshin turaren shi dana shaka a lokacin .
A hankali na bude idanuwa na da suke rufe da farko yana saye da hannuwan shi duka biyu a cikin aljihun wandon shi dake jikin shi.
Yana ganin na bude idanuwa sai ya karasa takowa zuwa inda nake kwance tare da kura min idanuwan shi duka biyu a inda nake kwancen.
"Rahama,
Na amsa da naam ba tare da ko na motsa jikina ba daga yadda ya samay ni a kwance din da farko saman gado.
May kike nufi ne da yin hakan da kika dauko yi a gidan nan yanzu bayan kin san duk wanda ke gidan nan a katshin ki yake zama sai ki shige daki ki bar mutane a falo suna zama.
Na fahinci tun ranan da akai maganan nan da Zulfau kika dauki bakin rai kika sawa zuciyar ki haka kada kice ko ban fahinci may kike nufi bane fa ?
Kin daina kulani kin daina kula duk wani wanda ke gidan nan yanzu kamar yadda kikeyi a baya can ?
Wasu kwalla ne masu zafi suka silalo a idanuwana, na tuna yadda ya rufe idon shi yai min tas ranan akan gaskiya na a gaban matar shi.
Idan kuwa ban kama kaina na tsaya a matsayina ba ai wata rana zan iya kai kaina inda Allah bai kaini ba wurin karanbani na.
Lafiyan ki ana magana baki bani amsa ba sai ki kama zubar min da hawaye haka kamar wacee akaiwa wani abu daga magana kawai.
A hankali na iya bude bakina da kyat nace don Allah daddy ka barni a matsayi na a dakina wanda ka bani agidan nake zaune bana son shiga hakkin da banawa ba ni kadai a gidan mutane.
Yace haka kikace ko nace hakan aka fada min ai koka mantane ranan abinda ka fada min a gaban matar ka akan na tsaya a matsayina kuma banfi kowa iko da gidan ba.
Yace wanan ne hujjan ki dama na sani sai dai kina da aiki idan kikace ke baki mantuwa da sabani idan anyi.
Ba rashin mantuwa bane sai tunatar dani wani matsayin da nake ciki wanda naso na manta shi a baya can.
Yace cikin kada kan shi ok yayi kyau tunda haka kikace ba matsala yasa kai ya fita na bishi da kallo har yabace min da gani na share kwallan fuskana tare da gyara kwanciya na.
Ina kwancen ban daga ba sai gashi ya sake shigowa dakin a karo na biyu wanan lokacin ya sauya kayan dake jikin shi zuwa rigar barci.
Take kuma ganin shi yasa gabana ya soma halbawa a hankali, da kyat na tatara natsuwa na wuri daya har ya karaso inda nake kwance.
Muryan shi naji yana fadin Rahama kin ban matukar mamaki da kalaman da kika fada min a yanzu kafin na fita.
Bayan aure na dake sai nake daukan zan samu natsuwa da kwanciyan hankali a gare ki ganin irin tarbiyan dake gare ki.
Sai kuma irin yadda rashin kwanciyan hankali ya yawaita a tsakanin ki da abokan zaman ki daya biyo baya musanman ma Saade da Allah kadai yasan sirin ku a baya sai ga sabani yazo yana yawan shiga a tsakanin ku kuma.
Wanan dalilin yasa naga gara na raba ku ko za, a samu zaman lafiya da kowan ku shine dalilin da nai dubaran dauko ki zuwa nan garin na kawo ki inda babu kowa naki ko nawa sai abokan arzikin da Allah ya hada mu dasu anan.
Duk da hakan da nayi Rahama ke nan na kasa sama muna farin ciki gayin haka don gashi har yakai a gaban iyayyen mu kina son su fahinci akwai wani matsala a tsakani dake a yadda kike yi din nan.
Kina nufin ko nuna masu ni na kasa sama maki farin ciki da kwanciyar hankalin da mutane suke hasashen kina a cikin sa a nan din.
Jin yayi shiru yasa nace dashi, daddy ni bakai min komai ba fa kuma ba wai nayi wani abu bane a sani kawai dai na kama kaina ne ga tunin da akai min a matsayina.
Yace tuni akan may yanzu ke kinga yadace a yadda zulfa ta gaya min anyi na tsaya nagoyi bayan ki batare da na dauki mataki ba ai sai ace dani gaskiya ne nafi karkata akan ki kamar yarda ake fadi din.
Nace aini da kai mun san fadi ne kawai amma may akai min wanda su ba ai masu shi ba sai dai suce ina nan garin a tare da kai ni kuma ban hana kowa zuwa ba ai tunda suma gidan mijin su ne nan din.
Murmushi yayi yace keda bakin ki don bacin rai kike fadin wai wata tazo ku zauna da ita anan din ?
Nace in Allah yayi akwai wacce zata zo mu zauna dani dakai ai duk bamu isa mu hana ba daddy .
Daddy Allah ne fa mai tsarawa bawan sa rayuwan da zai yi a duniya ba wai tsarin bawa bane duk mai zama tazo mu zauna mana.
Don ka ne nake ganin wa yan nan abubuwan daddy baka tsaya bincike ba ka rufe idanuwan ka ka sauke min masifa akaina yadda kake so don kawai ka gyarawa matar ka rai.
Dariya magana na ya bashi yace idan na san yadda ake tsayawa gyarawa mace rai ai kin fi kowa sanin hakan gare ni ke dai kice matsalana daukan mataki batare da na tsaya bincike ba kawai.
Nace ni ko may ye yanzu ai ya wuce sai dai ka sani Allah ya na tare da mai gaskiya ko yaushe banga dalilin da da hannun ka ka rufe kofan ka ba da zata zo ita tace na bude mata dakin dan na kowa ne.
Yace yanzu dai komai ya wuce ai Allah ya wanke ki banga abin tsayawa bata rai ba anan tunda zancen ya wuce.
Nace ai kaine duk wani sanadin fitina na dasu ina son in tabbatar ma daddy zan jure ko wani irin hali da zan shiga dasu akan ka nakuma jure hakan na zama jaruma a wurin su, don na tabbatar masu da kai kan ka cewa ni zama nake da kowan ku tsakani da Allah.
Insha Allahu daddy bazaka taba danasanin aure na da kayi ba indai ta wurina matsala zai fito har mu saba maka.
A hankali ya karasa takowa inda nake yakai zaune tare da min kiss a goshina yace nagode da kika kara tabbatar min da hakan da bakin ki Rahama.
Na dade da sanin kina gujewa bacin zuciyan wasu ki hade shi a ran ki ni kaina nazo nayi nadaman yadda nai maki gama yadda Allah yai saurin nuna min kuskuren abinda nayi da wuri.
Wani sanyi naji ya lulubeni a lokaci daya atake kuma hawayen nadama suka soma zubo min don nasan nayi kuskuren daukan zafin da nayi da kowa bayan Allah ya wanke ni ga maganan ko.
Yace ina son daga yau ki saki ranki da kowa ki koma normal batare da su mama sun fahinci akwai matsala a tsakanin mu ba.
Nace in sha Allahu ya wuce zanyi yadda kace tunda haka kake so amma ni kawai dama dan hutawa nake kafin na koma bakin aikina.
Yace ai ban ki hutun ba nima ina son hakan amma a rika dan kula mutane aba kowa hakkin shi don Allah.
Ya fice daga dakin bayan mun samu fahintar junan mu nace a raina dama ance matan yanzu a dakin su suke yaji ba sai wani yaji ba.
Gashi mun samu matsala kuma mun shirya a tsakanin mu batare da tsofin dake gidan sun fahince mu ba.
Tun washe gari na dan fara shiga mutane in dan zauna sai dai ban jin dadi sosai saboda dana zauna zan fara barci a gurin.
Har sai nake tunanen ko dai wani ciwo ne ya shigeni haka na barci na san dai dana haihu duk wani treatment din daya dace aimin a asibiti Faiza tai min shi a gida.
Ashe ba haka bane gajiya ne kawai yake sani barcin bayan kwana biyu sai na murmure har na fara zuwa gun aikina yadda ya dace don saura wata daya da kwanaki mu gama bautar kasan namu ko .
Haka yasa na dage sosai ga aiyukana na gidan mijina dana wurin bauta ma kasa don kada na samu matsala a ko wani ban gare.
Daddy yakan yi kwana goma zuwa sha daya ko sha biyu sai ya leka kano yai kusan kwanakin da yayi muna ya dawo.
Har nai arbain wanda yazo daidai kuma da gama bautan kasa na a asibitin da nakewa aiki din.
Sun karbi takatdun mu mu hudu sunce zasu iya neman mu anty time idan bukatan hakan ya taso garesu.
An bamu kyaututuka na yabo kamar kada a rabu muka barsu suna jin kewar mu sai kuma gida gasu mama na shirin komawa gida don yanzu hankalin su ya koma gida sosai sun gaji da zama wuri daya.
Daddy yaban kudi masu yawa mukaje dasu sukai sayayya saura kwana uku su tafi sai shirin tafiyan su akeyi don shi zai mayar dasu gida da kan shi.
Naso zuwa amma daddy ya hana yace na bari idan sallah yazo sai mu tafi can muyi sallah tunda ya gabato su ma don azumi suke son komawa dakunan su.
Ranan da zasu tafi kusan duk mun nuna damuwan mu don bamu son su tafi saboda suna da dadin zama sosai.
Bayan tafiyan su sai gidan ya koma muna shiru kamar ba kowa dama ance bako Rahama ne ga wuri.
Shirun da gidan yayi yasa muna shirin kwanciya ranan saiga Ihisan cikin kayan barcin ta take cewa wai ita bazata iya kwana dakin ta ba tsoro take ji.
Nace a, a Ihisan in banda abinki ai ba yau kika fara kwana dakin ba kuma kefa kika matsa da abaki wanan dakin ke shi kike so.
Don haka kiyi hakkuri ki koma dakin ki ki kwanta kiyi addua Allah zai tsare ki tace itafa atabau sai dai in Atika zata zo su dinga kwana a tare.
Atika tace wa ni wallahi bazan tafi ba keda kike fada a school din mu cewa ba baban mu daya mu yan aikin gidan ku ne anty mu ta karbewa mamakin miji shine mukewa mutane sallon banza kika sa akai min dariya.
Wani iri naji ba dadi a raina amma na daure nace haba Atika don kawai tace ki tayata kwana shine zaki mata sheri haka ?
Tace wallahi anty ba sheri bane ai mama Laraba ce tai muna sharia da muka dawo gida tace kuma nayi hakkuri kada na fada maki.
To ai yanzu gashi duk da anbaki hakkuri kin fada naji tace ai haushi naji wallahi ni ba zan tafi ba na juya inda Ihisan take da alama dai tsoro take ji din nakoma lalashin Atika din tace muje amma kinci arzikin anty wallahi nace nagode.
Na juya wurin Ihisan nace da ita haba ihisan ai ba sai kin tozarta dan uwan ki ba zakiji dadi kowa ma ai yasan cin arziki mukazo gidan ku shi mutum rana gare shi da kike ganin shi don akwai ranan da zai taimaka maka.
Tace Iam sorry mummy bazan sake ba ai mamanace tace dama idan sun min tsiya na fada masu hakana amma na bari tun ranan da grandma tai min fadan hakan.
Nace good girl haka ake son yaro ya dauki fadan manya dama ki bari kinji a zauna lafiya da mai kudi da tallaka ai duk Allah yayi shi ko.
Suka wuce zuwa dakin nace kada a manta ayi addua dai idan za a kwanta suka insha Allahu.
Bayan tafiyan su mamakine fal a zuciyana yadda mace zata zaunar da karamar yarinya haka tana koya mata kissa da kisisina Allah kadai yasan irin hudubar da taiwa yarinya da zatazo ko idan sunyi waya.
Don haka zan bi yarinyar sannu a hankali na fahinci komai da take kullawa agidan don idan nai sakaci zata iya min wani kulli da ba zan iya fitar da kaina a ciki ba wata rana.
Sai da na samu kebewa da Atika nai mata fada mai kama da jan kunne akan ta sani ba daya suke ba da Ihisan don kada wata rana taga tayi abu tace ita ma zatayi sosai naja mata kunne Alhamdullahi kuma yarinyar ta fahinci maface ni sosai.
********* ********* *********
Bayan daddy ya isa gida ya kai su mama Laraba gidan ta inda anan Attu zata kwana sai
Showing 306001 words to 309000 words out of 456145 words
Nan fa faban bakinta kika rufe ido kina mata cin mutunci son ran ki ashe ke da wani manufa kika sa sai a bude maki dakin duk da hanakin da mukayi.
Tace mama aiba ni kadai keda key din ba sherine kawai aka kulla min don a bata min suna kawai wallahi amma ni ina ruwana da kayan shi.
Yace kina nufin Rahama ce ta shigo ta daukar min abu bayan sun dade a wurin bata dauka ba sai yanzu.
Mama tace kai amma Zulfa baki biyo nono ba wallahi sai dai a yabe mu da fada amma ba mugun hali ba dan hannu.
Ta juya rai a bace inda mama take tace mama may kike nufi kema satan zaki dafa min ko may ?
Yace rashin kunya zaki mata yanzu ko may tace ba rashin kunya sai gaskiya tunda dai dama kowa yasan yanzu mama don anga Rahama na nan sai wani shishige mata akeyi don ana zaton itace mai shi.
Ihsan da suke dakin ta ta kumaji plan din su ta fito tace a a anty ba ruwa little mum ga maganan ku naafaji hiran ku ranan da kike basu labarin kinga white gold a dakin daddy masu yawa.
Akace ki diba sai yanzun kuma zakice wai ba ke bace tai salati tace yanzu ihisan ni zakiwa sheri abin naki har yakai can ashe ?
Nan dai duk gidan yai tsit ana sauraren fitinar su sai dai ba wanda ya fito sai sauraren su da akeyi kawai a sauran dakunan kamar yadda muma muke sauraren su din a inda muke zaune.
Duk yadda daddy ya buga taki fito mai da kayan shi su mama sukace ya kyaleta Allah ya tona asirin mai shi bai so ba haka ya yarda yabar zancen rai bace mai.
Ni dai a bangare na Allah ya fitar min da hakkin kazafin da taimin ya hau kai ba tare daya bincika ba gashi abinda ya wakana a tsakanin su yanzu.
Washe gari tunda safe suka bar garin tare da sauran bakin da suka zo sai gidan ya koma muna tsit iyamu aka bari dasu mama kawai agidan.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE DON BA A YAFE BZ ONLINE NOVEL NE, , , ,
76
Tun tafiyan bakin mu su Aisha suka gyara min gida ko ina ya rage daga ni sai yara dasu mama da zasu zauna har zuwa lokacin da zanyi arbain kafin su wuce.
Har wanan lokacin iyakana da daddy ina kwana ko shi daga kofa zan tsaya na gaida dashi na bar dakin wani lokaci ma a falo zamu hade ko ina barci zai fice daga gidan sai in yadawo nai mai sannu da zuwa daga inda nake.
Ban bin shi baya balle na daukowa kaina magana ko wani sabon fitina, nayi hakane don na kama kaina akan komai dama sati biyu aka bani a wurin bautar kasa na don haka lokaci kawai nake jira na koma.
Banda matsala da yaran da ya kawo min sosai Jinior dai ne da Ihisan keda dan matsala kuma basu wuni a gida in sun fita tun safe acan zasu wuni sai shidda na yamma zasu iso gida.
Ina ganin shiru ya dan damay shi ne ko yaya ban sani ba dama can shi dai ba gwanin zama bane ai hira dashi don ko yaushe zaka samay shi busy ne.
Na kan yi mamakin yadda yakan samu lokaci a baya yana hira da hindatu ko don yawan nacin ta ne tafi mu nacewa ban sani ba.
Case din shi da Zulf sai da iyayye suka sa masu baki daya je gida tafito mai da dutsen shi don yasan cewa ita ta dauke su.
Tasha fada sosai a gurin iyayyen su sai datace ba itace ta dauko da hannun ta ba Rafia ce kaunar ta data shiga dakin tana ciki ta dauka aka kuma bincika haka din ne sannan ta samu sasauci a gurin shi.
********* ********* *********
Tun bayan haihuwa na ban faye fitowa falo ba ina dakina ko barci ko wani abin tunda bana sallah a lokacin.
Ina kwance a dakina don tun yamma dana dan leka su mama a falo na dawo daki kafin magariba ban sake fitowa ba har tara da wani abu na dare.
Yanayin rayuwa ta tun haihuwa na gaba daya ya sake min bana son yawan hayaniya haka kuma bana yawan zama cikin mutane sosai.
Dama da yara nafi sakewa ko a baya ban faye shiga cikin manya ba ina zama ana suraitai don nakan rasa may zan fada wani lokacin .
Kwance nake sai dai ba barci nakeyi ba idona kawai na rufe na dora tsintsiyar hannuna a fuskana.
Idanuwa dake rufe bai hanani sanin ya shigo dakin nawa ba don kamshin turaren shi dana shaka a lokacin .
A hankali na bude idanuwa na da suke rufe da farko yana saye da hannuwan shi duka biyu a cikin aljihun wandon shi dake jikin shi.
Yana ganin na bude idanuwa sai ya karasa takowa zuwa inda nake kwance tare da kura min idanuwan shi duka biyu a inda nake kwancen.
"Rahama,
Na amsa da naam ba tare da ko na motsa jikina ba daga yadda ya samay ni a kwance din da farko saman gado.
May kike nufi ne da yin hakan da kika dauko yi a gidan nan yanzu bayan kin san duk wanda ke gidan nan a katshin ki yake zama sai ki shige daki ki bar mutane a falo suna zama.
Na fahinci tun ranan da akai maganan nan da Zulfau kika dauki bakin rai kika sawa zuciyar ki haka kada kice ko ban fahinci may kike nufi bane fa ?
Kin daina kulani kin daina kula duk wani wanda ke gidan nan yanzu kamar yadda kikeyi a baya can ?
Wasu kwalla ne masu zafi suka silalo a idanuwana, na tuna yadda ya rufe idon shi yai min tas ranan akan gaskiya na a gaban matar shi.
Idan kuwa ban kama kaina na tsaya a matsayina ba ai wata rana zan iya kai kaina inda Allah bai kaini ba wurin karanbani na.
Lafiyan ki ana magana baki bani amsa ba sai ki kama zubar min da hawaye haka kamar wacee akaiwa wani abu daga magana kawai.
A hankali na iya bude bakina da kyat nace don Allah daddy ka barni a matsayi na a dakina wanda ka bani agidan nake zaune bana son shiga hakkin da banawa ba ni kadai a gidan mutane.
Yace haka kikace ko nace hakan aka fada min ai koka mantane ranan abinda ka fada min a gaban matar ka akan na tsaya a matsayina kuma banfi kowa iko da gidan ba.
Yace wanan ne hujjan ki dama na sani sai dai kina da aiki idan kikace ke baki mantuwa da sabani idan anyi.
Ba rashin mantuwa bane sai tunatar dani wani matsayin da nake ciki wanda naso na manta shi a baya can.
Yace cikin kada kan shi ok yayi kyau tunda haka kikace ba matsala yasa kai ya fita na bishi da kallo har yabace min da gani na share kwallan fuskana tare da gyara kwanciya na.
Ina kwancen ban daga ba sai gashi ya sake shigowa dakin a karo na biyu wanan lokacin ya sauya kayan dake jikin shi zuwa rigar barci.
Take kuma ganin shi yasa gabana ya soma halbawa a hankali, da kyat na tatara natsuwa na wuri daya har ya karaso inda nake kwance.
Muryan shi naji yana fadin Rahama kin ban matukar mamaki da kalaman da kika fada min a yanzu kafin na fita.
Bayan aure na dake sai nake daukan zan samu natsuwa da kwanciyan hankali a gare ki ganin irin tarbiyan dake gare ki.
Sai kuma irin yadda rashin kwanciyan hankali ya yawaita a tsakanin ki da abokan zaman ki daya biyo baya musanman ma Saade da Allah kadai yasan sirin ku a baya sai ga sabani yazo yana yawan shiga a tsakanin ku kuma.
Wanan dalilin yasa naga gara na raba ku ko za, a samu zaman lafiya da kowan ku shine dalilin da nai dubaran dauko ki zuwa nan garin na kawo ki inda babu kowa naki ko nawa sai abokan arzikin da Allah ya hada mu dasu anan.
Duk da hakan da nayi Rahama ke nan na kasa sama muna farin ciki gayin haka don gashi har yakai a gaban iyayyen mu kina son su fahinci akwai wani matsala a tsakani dake a yadda kike yi din nan.
Kina nufin ko nuna masu ni na kasa sama maki farin ciki da kwanciyar hankalin da mutane suke hasashen kina a cikin sa a nan din.
Jin yayi shiru yasa nace dashi, daddy ni bakai min komai ba fa kuma ba wai nayi wani abu bane a sani kawai dai na kama kaina ne ga tunin da akai min a matsayina.
Yace tuni akan may yanzu ke kinga yadace a yadda zulfa ta gaya min anyi na tsaya nagoyi bayan ki batare da na dauki mataki ba ai sai ace dani gaskiya ne nafi karkata akan ki kamar yarda ake fadi din.
Nace aini da kai mun san fadi ne kawai amma may akai min wanda su ba ai masu shi ba sai dai suce ina nan garin a tare da kai ni kuma ban hana kowa zuwa ba ai tunda suma gidan mijin su ne nan din.
Murmushi yayi yace keda bakin ki don bacin rai kike fadin wai wata tazo ku zauna da ita anan din ?
Nace in Allah yayi akwai wacce zata zo mu zauna dani dakai ai duk bamu isa mu hana ba daddy .
Daddy Allah ne fa mai tsarawa bawan sa rayuwan da zai yi a duniya ba wai tsarin bawa bane duk mai zama tazo mu zauna mana.
Don ka ne nake ganin wa yan nan abubuwan daddy baka tsaya bincike ba ka rufe idanuwan ka ka sauke min masifa akaina yadda kake so don kawai ka gyarawa matar ka rai.
Dariya magana na ya bashi yace idan na san yadda ake tsayawa gyarawa mace rai ai kin fi kowa sanin hakan gare ni ke dai kice matsalana daukan mataki batare da na tsaya bincike ba kawai.
Nace ni ko may ye yanzu ai ya wuce sai dai ka sani Allah ya na tare da mai gaskiya ko yaushe banga dalilin da da hannun ka ka rufe kofan ka ba da zata zo ita tace na bude mata dakin dan na kowa ne.
Yace yanzu dai komai ya wuce ai Allah ya wanke ki banga abin tsayawa bata rai ba anan tunda zancen ya wuce.
Nace ai kaine duk wani sanadin fitina na dasu ina son in tabbatar ma daddy zan jure ko wani irin hali da zan shiga dasu akan ka nakuma jure hakan na zama jaruma a wurin su, don na tabbatar masu da kai kan ka cewa ni zama nake da kowan ku tsakani da Allah.
Insha Allahu daddy bazaka taba danasanin aure na da kayi ba indai ta wurina matsala zai fito har mu saba maka.
A hankali ya karasa takowa inda nake yakai zaune tare da min kiss a goshina yace nagode da kika kara tabbatar min da hakan da bakin ki Rahama.
Na dade da sanin kina gujewa bacin zuciyan wasu ki hade shi a ran ki ni kaina nazo nayi nadaman yadda nai maki gama yadda Allah yai saurin nuna min kuskuren abinda nayi da wuri.
Wani sanyi naji ya lulubeni a lokaci daya atake kuma hawayen nadama suka soma zubo min don nasan nayi kuskuren daukan zafin da nayi da kowa bayan Allah ya wanke ni ga maganan ko.
Yace ina son daga yau ki saki ranki da kowa ki koma normal batare da su mama sun fahinci akwai matsala a tsakanin mu ba.
Nace in sha Allahu ya wuce zanyi yadda kace tunda haka kake so amma ni kawai dama dan hutawa nake kafin na koma bakin aikina.
Yace ai ban ki hutun ba nima ina son hakan amma a rika dan kula mutane aba kowa hakkin shi don Allah.
Ya fice daga dakin bayan mun samu fahintar junan mu nace a raina dama ance matan yanzu a dakin su suke yaji ba sai wani yaji ba.
Gashi mun samu matsala kuma mun shirya a tsakanin mu batare da tsofin dake gidan sun fahince mu ba.
Tun washe gari na dan fara shiga mutane in dan zauna sai dai ban jin dadi sosai saboda dana zauna zan fara barci a gurin.
Har sai nake tunanen ko dai wani ciwo ne ya shigeni haka na barci na san dai dana haihu duk wani treatment din daya dace aimin a asibiti Faiza tai min shi a gida.
Ashe ba haka bane gajiya ne kawai yake sani barcin bayan kwana biyu sai na murmure har na fara zuwa gun aikina yadda ya dace don saura wata daya da kwanaki mu gama bautar kasan namu ko .
Haka yasa na dage sosai ga aiyukana na gidan mijina dana wurin bauta ma kasa don kada na samu matsala a ko wani ban gare.
Daddy yakan yi kwana goma zuwa sha daya ko sha biyu sai ya leka kano yai kusan kwanakin da yayi muna ya dawo.
Har nai arbain wanda yazo daidai kuma da gama bautan kasa na a asibitin da nakewa aiki din.
Sun karbi takatdun mu mu hudu sunce zasu iya neman mu anty time idan bukatan hakan ya taso garesu.
An bamu kyaututuka na yabo kamar kada a rabu muka barsu suna jin kewar mu sai kuma gida gasu mama na shirin komawa gida don yanzu hankalin su ya koma gida sosai sun gaji da zama wuri daya.
Daddy yaban kudi masu yawa mukaje dasu sukai sayayya saura kwana uku su tafi sai shirin tafiyan su akeyi don shi zai mayar dasu gida da kan shi.
Naso zuwa amma daddy ya hana yace na bari idan sallah yazo sai mu tafi can muyi sallah tunda ya gabato su ma don azumi suke son komawa dakunan su.
Ranan da zasu tafi kusan duk mun nuna damuwan mu don bamu son su tafi saboda suna da dadin zama sosai.
Bayan tafiyan su sai gidan ya koma muna shiru kamar ba kowa dama ance bako Rahama ne ga wuri.
Shirun da gidan yayi yasa muna shirin kwanciya ranan saiga Ihisan cikin kayan barcin ta take cewa wai ita bazata iya kwana dakin ta ba tsoro take ji.
Nace a, a Ihisan in banda abinki ai ba yau kika fara kwana dakin ba kuma kefa kika matsa da abaki wanan dakin ke shi kike so.
Don haka kiyi hakkuri ki koma dakin ki ki kwanta kiyi addua Allah zai tsare ki tace itafa atabau sai dai in Atika zata zo su dinga kwana a tare.
Atika tace wa ni wallahi bazan tafi ba keda kike fada a school din mu cewa ba baban mu daya mu yan aikin gidan ku ne anty mu ta karbewa mamakin miji shine mukewa mutane sallon banza kika sa akai min dariya.
Wani iri naji ba dadi a raina amma na daure nace haba Atika don kawai tace ki tayata kwana shine zaki mata sheri haka ?
Tace wallahi anty ba sheri bane ai mama Laraba ce tai muna sharia da muka dawo gida tace kuma nayi hakkuri kada na fada maki.
To ai yanzu gashi duk da anbaki hakkuri kin fada naji tace ai haushi naji wallahi ni ba zan tafi ba na juya inda Ihisan take da alama dai tsoro take ji din nakoma lalashin Atika din tace muje amma kinci arzikin anty wallahi nace nagode.
Na juya wurin Ihisan nace da ita haba ihisan ai ba sai kin tozarta dan uwan ki ba zakiji dadi kowa ma ai yasan cin arziki mukazo gidan ku shi mutum rana gare shi da kike ganin shi don akwai ranan da zai taimaka maka.
Tace Iam sorry mummy bazan sake ba ai mamanace tace dama idan sun min tsiya na fada masu hakana amma na bari tun ranan da grandma tai min fadan hakan.
Nace good girl haka ake son yaro ya dauki fadan manya dama ki bari kinji a zauna lafiya da mai kudi da tallaka ai duk Allah yayi shi ko.
Suka wuce zuwa dakin nace kada a manta ayi addua dai idan za a kwanta suka insha Allahu.
Bayan tafiyan su mamakine fal a zuciyana yadda mace zata zaunar da karamar yarinya haka tana koya mata kissa da kisisina Allah kadai yasan irin hudubar da taiwa yarinya da zatazo ko idan sunyi waya.
Don haka zan bi yarinyar sannu a hankali na fahinci komai da take kullawa agidan don idan nai sakaci zata iya min wani kulli da ba zan iya fitar da kaina a ciki ba wata rana.
Sai da na samu kebewa da Atika nai mata fada mai kama da jan kunne akan ta sani ba daya suke ba da Ihisan don kada wata rana taga tayi abu tace ita ma zatayi sosai naja mata kunne Alhamdullahi kuma yarinyar ta fahinci maface ni sosai.
********* ********* *********
Bayan daddy ya isa gida ya kai su mama Laraba gidan ta inda anan Attu zata kwana sai
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22Chapter 23Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32Chapter 33Chapter 34Chapter 35Chapter 36Chapter 37Chapter 38Chapter 39Chapter 40Chapter 41Chapter 42Chapter 43Chapter 44Chapter 45Chapter 46Chapter 47Chapter 48Chapter 49Chapter 50Chapter 51Chapter 52Chapter 53Chapter 54Chapter 55Chapter 56Chapter 57Chapter 58Chapter 59Chapter 60Chapter 61Chapter 62Chapter 63Chapter 64Chapter 65Chapter 66Chapter 67Chapter 68Chapter 69Chapter 70Chapter 71Chapter 72Chapter 73Chapter 74Chapter 75Chapter 76Chapter 77Chapter 78Chapter 79Chapter 80Chapter 81Chapter 82Chapter 83Chapter 84Chapter 85Chapter 86Chapter 87Chapter 88Chapter 89Chapter 90Chapter 91Chapter 92Chapter 93Chapter 94Chapter 95Chapter 96Chapter 97Chapter 98Chapter 99Chapter 100Chapter 101Chapter 102Chapter 103 Chapter 104Chapter 105Chapter 106Chapter 107Chapter 108Chapter 109Chapter 110Chapter 111Chapter 112Chapter 113Chapter 114Chapter 115Chapter 116Chapter 117Chapter 118Chapter 119Chapter 120Chapter 121Chapter 122Chapter 123Chapter 124Chapter 125Chapter 126Chapter 127Chapter 128Chapter 129Chapter 130Chapter 131Chapter 132Chapter 133Chapter 134Chapter 135Chapter 136Chapter 137Chapter 138Chapter 139Chapter 140Chapter 141Chapter 142Chapter 143Chapter 144Chapter 145Chapter 146Chapter 147Chapter 148Chapter 149Chapter 150Chapter 151Chapter 152Chapter 153