yai matukar bata mashi rai sosai har yakai ya tara mu a gaban shi ni dai ina falona don ina up a wurin aiki ban fita ko ina sai gashi tunda safe daddy ya kirani a waya na samay shi a falon shi.
Ban kawo komai ba a raina na shirya dama a shirye nake dan gyarawa kawai nayi.
Duk kan su suna falon kowacen su ta hakkince a zaune cikin nata kalar shigan sai shi may gidan da alama ya nuna ko wankan shirin fita baiyi ba a lokacin.
Da mamaki na karasa cikin falon tare da sallama da fargaban may kuma ya faru haka son ruwa baya tsami banza a hakan.
Ina shigowa ya dago kai tare da sauke idanuwan shi a kaina yana mai amsa sallamana.
Na samu wuri na zauna can daga karshe nace gani daddy lafiya dai ko ?
Da hannu ya nuna min na zauna na karasa kaiwa zaune din ina mai kura mai idanuwa na don ban bi ta kan kowa ba dake falon a lokacin.
Shiru falon yayi can ya dan nisa tare da shafo fuskan shi yace na kiraku ne don wani magana da naji daga bakin wanan yarinyar ya nuna inda Niima take zaune da fuskan shi.
Sai kowan mu ya gyara zaman shi don jin may ya faru kuma haka yaci gaba da fadin daren jiyane ta fuskance ni da wani zancen da ya kona min rai a gidan nan akan yaran nan marayu da Saade ta bar min ko nace ta bar mu dasu.
Daga inda nake zaune nace tau fa ?
Yace eh tazo min da zancen wai ita bazata yarda ba sai itama na bata kudi kamar yadda nake bawa kowa a gidan nan don har su Amira da Nasir na ware ma makuddan kudi daka jikina na basu a matsayin kyauta don tallafawa rayiwan su.
Kuma ba kowa yasani yin haka ba sai Rahama don tana bakin ciki na mutu a raba gado kowa ya samu yasa ta bani wanan shawaran
Take naji raina ya yi mugun baci nace a hasale wai wanan matar may kike so danine a gidan nan wai ?
Yace dani dakata hakana magana nake yi sai nai shiru tare da komawa na zauna da kyau.
Yace maganan ya bani matukar mamaki don ban san ina ta samo wanan zancen nata ba haka ?
Ya juya gunta yace Niima jiya da kike min wannan magana kikaga na yi shiru akwai abinda nake tunane ne bawai na kyale ki bane hakana sai kuma kyale kin da nayi ya bani daman karasa sauraren abinda ni ban sani ba a gidan nan.
Kafan ta take kadawa a hankali yayin da tai tagumi da hannun ta daya tana mashi wani irin kallo mai kama da tsanane ko haushi ?
Yanzu ina son ji daga bakinki a ina wanan maganan yafito maki haka na ki fada muna ke muke saurare.
Sai tai shiru tunda naji Zulfa tace da ita ke Niima may yakaiki yin wanan maganan don Allah nasan akwai wata a kasa in baki manta ba mai karatu Anty marigayiya tasha fada min cewa nai hankali sosai da Zulfa don munafukace ta gaske amma a zatona ta daina halin nata ne yanzu girma yazo mata .
Muryan daddy yadawo dani daga tunanen da nakeyi naji yace ke muke saurare fa kada ki shanya mu anan ?
Shiru tayi sai ya dan gyara zaman shi da kyau yace saurara kiji wallahi kinji na rantse maki ko ki fada min ko yanzu ki raina kanki ga hukuncin da zan yanke a kan ki.
Don duk wanda har yake jiran ka mutu yaci gadon ka to kuwa zai iya kashe ka ya kaiga manufan shi a tare da kai.
Tace nima ai fada min akayi gadon ka kuma ai ba ni kadai ke jiran ci ba don duk wacce ke tare dakai shi suke jira suma.
Ko don an fini wayon iya gilibibi yasa nawa kawai za a gani don nai magana kawai.
Hindatu tace ke ki iya bakin ki don mu ba mayunwata bane irin ki sai ta watsa ma hindatun harara tace shi kan shi ya sani ai .
Badon cin gadon akace Rahama na haihuwa akai akai don tafi kowa kaso ba a gidan dariya maganan ta ya bani ban iya magana ba don ya kwabe ni da farko nasan ko yanzu ba zai bari na sake wani maganan ba ma.
Yace ai saiki fada muna wanda ya fada maki tace akan may zan fada don an raina min za ace don nai magana da kai za a zo a tsureni gaban kowa nai magana.
Da suke siri dakai tsuresu kakeyi ko may dani za ai min hakan don raini.
Wani uban tsawa ya daka mata sai data dan razana yace zaki fada ko yanzu na zartan da hukuncin da nai niyya a kan ki don ba zan iya zama da macen da ta iya fitar min da zuciyar ta damanufanta ba haka a fili.
Jin abinda ya fada yasa tace a dai muna hukunci da wacce ta fada min don nima daga bakin uwar gidan ka na samu labari.
Da sauri zulfa tace ke kada ki fara ki min sheri wallahi ko don yanzu za a jimu dake a gidan nan.
Tace sherin may zan maki bake kika fada min ba kikace duk yadda zanyi na kawar da Rahama a gidan nan nayi ko bata fita ba ta koma ita da babu duk daya.
Daddy yace kinji Zulfa kinji yanzu abinda ta sake fada ko Niiman tace ai ba kazafi nai mata ba.
Kince kudin shi Rahama ke komai dashi tana labewa ga aiki take samu sai abinda tace ake kuna kallo a gidan daku da yaran ku kamar babu ku a wurin shi.
Daga inda nake zaune nace Allah na gode ma da baiwar da kai min ka rabani da hassada a rayuwa na.
Nace Zulfa ai kun riga da kunyi sake diyar zakanyya ta girma sai hakkuri yanzu don haka munafuncin ki da hassada zai sa ki tabbata a boran ki har abada don babu mai iya sauya ma wani hali shi sai Allah.
Don da zaki daina munafunci a bayan ido zama dani dayasa kin daina ko tuntuni may yafi nan kunya ki zauna da yarinya karama kina gulma irin haka don hassada kawai da bakin ciki.
May na rage ki dashi na mutuntawa a rayuwan zaman mu dake ba yau ba na sani akwai wanan ranan yana tafe gun munafuki ai.
Kada ki kara kirana da munafuka Rahama karya ne may Saade din ta bari da za, ace wai gadon yaran tane wanan kudin da ake fada.
Tace dakata gaskiya dai ya baiyyana yanzu kundai yi maganan da Niima ke nan a gidan nan ko ?
Tace munyi sai dai ba yadda ta fada ba aiko hindatu ta sani da sauri hindatu tace da kukazo min da maganan may na fada maku ni ?
Ba cewa nayi yanzu na gaji da wanan halin ba abinda ke gabana ya isheni kuma ke Zulfa na fada maki Rahama bada tsiya take nufar mu ba kibi a hankali koba haka mukayi dake ba.
Tace yanzu ko da maganan ya zama haka amma aiko ke da cewa kike don tafi kowa kaso take haihuwa akai akai haka a gidan nan bake kika fara fada ba.
Tun fara cacan baki a wurin ya dafe kan shi baiyi magana sai da yaga abin bana karewa bane yake cewa damu.
Kai ya isheni haka na yanzu na gane inda maganan nan ya fito don haka dake da kika fada min da ita data fada maki duk hukuncin da zan yanke ya hau ka ku.
Zulfa ba zanyi duban irin zumuncin dake tsakanina dake ga don na fahinci duk wani tsegumi na gidan nan daga gareki yake fitowa don haka dake da Niima ku saurara da kyau kuji.
Kudi dai banawa bane bana Rahama bane dukiyan yara ne da nake juyawa na uwar su tun tana a raye kamar yadda ta dauki amana tabani haka na rike wanan amanan har shekara goma sha tara ina rike dasu a hannuna.
Sune yanzu ganin yaran sun kawo hankali na fara gabatar masu da dukiyar su don su san dashi a gare ni.
Rahama ga tanan a matsayin ta na mata na dake rike mun yaran ita na fara gabatawa dukiyan yaran.
Sai Allah ya taimake ni ta bani shawaran da ya dace akan na kafa hujja da yan uwana da kuma yan uwan mahaifiyan su.
Nasan kuma zaman da mukayi da su a kano har yasa kuka samu wanan labarin yazo gare ku.
Amma da yake baku da tsoron Allah a tare daku ita da ta taimaka min ta bani mafita kuka dauki sheri da zargi kuka saka mata dashi.
Mai son abinka har rayuwan ka yana so idan ya samu don haka bazan taba iya zama da irin mutanem nan ba a rayuwa na .
Ya fadin haka ya mike daga inda yake zaune yace ku bani wuri don Allah zan shirya ni.
Nice ta farkon mikewa a nan zabbar kunya na barsu su uku suna cacan baki a tsakanin su ina shiga wurina wani kuka mai sosa zuciya yazo min a lokaci daya.
Ban fito ba sai da lokacin zuwa dauko yarana makaranta yayi naiwa mama Sallama na fita daga gidan gidan yai shiru ba motsin kowa ko irin kidan da kakeji yana tashi a part din Niima yau babu shi a gidan ko kadan.
Haka na fita daga gidan naje na dauko yaran muka juyo zuwa gida muna shiga ne na hadu da wata kawar Niima zata fita tabini da kallo ban kula taba na shige abina.
Naiwa yaran wanka muna zaune ina basu abinci sai ga daddy ya shigo wirin mu nai mashi sannu da dawowa yake cewa da shi.
Yaran har sun dawo ashe nace eh yanzu na dauko su yake cewa zan tafi lagos yanzun nan tafiyan ya kamani sai dai kafin na dawo na fadawa Zulfa da Niima su bar min gida don haka ina fada maki ne babu ruwanki da zancen su kuma.
May hakan ke nufi da subar maka gidan ka dakace dasu yace maganin kiyayya nace rabuwa.
Yace dani to na rabu dasu duk su biyun ba zan iya zama da masu son rayuwana ba, don ni dukiyana na nemawa iyalina rufin asiri ne banga abinda na rage wata daga cikin ku dashi ba da har suke jiran mutuwa don na bar masu dukiyata suci.
Ita Zulfa yanzu zataci na diyan ta idan na mutu din ita ko Niima ta tafi da abinda ta samu a wurina a yanzu.
Daddy don Allah kayi hakkuri da wanan zancen haka na kowa da halin sa ake zama dashi ai.
Yace naki ra, ayin ke nan nikan ba zan iya zama da masu son rayuwana ba.
Yana fadan haka ya fice daga part din nawa da kyat na bude bakina daga kalkon mamakin da nake mai nai mashi Allah ya tsare hanya.
********* ********* *********
Zulfa kan bai dawo ya samay ta a gidan ba don ta tafi kano tun washegari sai Niima ce taki tafiya kamar yadda yaba da umurni.
Ya dawo ya samayta a gidan yai mata cin mutunci badon taso ba dole ta bar gidan kamar yadda yace din.
Da dare ina gurin shi yana cin abinci sai ga wayan hajitan shi ya ahigo mai suka gaisa suna gama gaisuwa da ita take tambayan shi dalilin turo Zulfa gida dayayi don gata sun samay ta da uwarta.
Yace eh hajiya nina sallamay ta don ba zan iya zama da ita ba haka laifi sukai min kuma na riga da na yanke hukuncin duk wanda ke da hannu a wanan maganan zan dauki mataki gare shi ko wanene tunda ba son Allah da Annabi suke min ba.
Kai Alhaji ka saurareni da kyau babu abinda zaka boye min yanzu kai bakiji kunya ba akan wata bare can zaka sallami yar uwarka ta jini.
Yace hajiya wacece baren da na sallamay ta akan ta tace maku ?
Waye banda Rahama da ta gama da kai baka ganin kowa da gashi in ba ita ba da diyan ta a gidan ka.
Wayan na a handfree don haka na mike tsam don na bar falon yai min nuni da hannu don na dawo na zauna.
Banki ba duk da ban so ba kada naji abinda raina zai baci gareshi naji yace amma hajiya yanzu in ga halarci ai Rahama ta wuce bare a wurin mu tunda na haihu da ita har diya biyar.
Dama shine gurin ta ta mallake ka da gida ka shiyasa taita haihuwa kamar bera nida naga sugar mai iyali ana nuna min zazagan hanji.
Yai murmushi yace hajiya sai dai ayi hakkuri na riga da na yanke hukuncina a kan su ba abinda ya saura yanzu.
Tace baka isa ba aiba kai ka kawo kanka duniya ba zan dawo da Zulfa idan ka isa ka dawo min da ita nan mu gani.
Yace hajiya gidana ai gidan ta ne tazo ta zauna idan zata iya ga gidan nan gata.
Daga haka sukai sallama ta kashe wayan tana ta fada dashi sai lokacin na nisa nace dama nasan duk laifin a kaina zai dawo ai.
Yace hado min passport din ki dana yara yanzu ki fadawa hindatu kuma ina neman ta shiru nayi sai naji yace dani badake nake bane.
Na mike na tafi hado mai passport din dayace daga can na tura akira mashi hindatun daya yace don mu biyu muka saura a gidan.
Kamar yadda ya fada min haka ya fada mata nakawo yasani daukan permision a wurin aikina ba kakautawa suka bani.
Kwana uku yazo ya ce mu shirya zamu tafi London da yara ita kuma hindatu zasu tafi italy da yaran ta.
Hakan akayi muka tafi hutun dole ga Zulfan ta dawo da yan uwanta da da suka rakota nan muka barsu a gidan muka tafi.
Wanan abin yai matukar bata masu rai sun kwana biyu suna zaton zamu dawo maigadi ke fada masu cewa ai bamu ma kasan gaba dayan mu gidan mun fita waje.
Haushine ya kama hajiyan ta tace su dawo kano har mu dawo maigadi ya rufe gidan bayan tafiya su.
Wasa wasa sai gashi mun kwashe wata uku a can hakan ya bani dama yin couses di da nake son yi.
Allah ya taimake ni a wanan tafitan kuma gurin Nasir ya cika ya samu gurbin zuwa yin ilimin na sojoji a can don dama shine burin mu a kullun da mun dawo zai shirya ya koma tunda sun kammala karatun su.
Airen Amira da ya taso ne ya dawo damu gida duk da ba a kasa daya muke ba kusan a lokaci daya muka shigo su hindatu sun dawo da kwana uku muma muka iso kasan shine bai samu dawowa ba a tare da mu.
Mun dawo da Sati biyu muka kwasa sai kano don a can zamuyi bukin Amirah saboda yan uwa gana mahaifinta dana mahaifiyan ta kowa nason ganin auren ta.
Kwanan biyu muka shiga gidan su daddy gaida hajiyan shi fuska a daure take amsa muna gaisuwan mu.
Hakan bai damay ni ba don ba bakon alamari bane yin haka a gareta sai bayan mun gaisa ne ta mayar da hankalinta ga jikokin ta ta share ni nima ban dade ba namike ina gyara gyalen dake jikina ina fadin zamu tafi tace dani yaran ma bazaki barsu mu gaisa ba dasu zaki kwashe su ki tafi.
Ki sani dai yara jinane ko kinki ko kin so dole dai a kira su da jikokina idan kuma rabasu dani zakiyi don kin iya raba anta da jin shi ke sai mu gani.
Nace hajiya ayi hakkuri idan zasu zauna sai na barsu don ni akwai inda zan tafi dama nai mata sallama natafi tana bina da bakaken magana.
Gidan Zarah na nufa mun dade muna hira da ita wayan gajiye ne ya isheni na dauka take ce min ga yara an dawo dasu daga gidan hajiya tun dazu suna kuka.
Nai murmushi don dama nasan bazasu zauna ba ai son fitina ne irin na hajiya kawai dani yasa tace nabar mata su.
Nadawo ne jinior ke fada min irin zagin dataita masu wai sn biyo mugun hali irin na uwarsu shiyasa basu san kowa ba a dangin su ko sunki ko sun so ita dai ce kakar su don ita ta haifi uban su.
Nai dariya nace ai tana da gaskiyan ta watarana ma acan zai kaiku ku kwana wurin ta jinior yace wallahi basu zuwa nace yaro dole ku tafi ai.
Niji dadin zama kano da mukayi kwana biyu don muna ta ziyaran yan uwa da abokan arziki wurin raba kayin buki.
Daddy bai shigo kano ba sai ana gobe kamun Amira ya shigo garin da dare don haka da safe ya shiga gaida mahaifan shi.
Har gidan su Zulfa ya tafi wurin mahaifiyar ta kamar yadda ya saba nan ta tutsiye shi tana fada wai yana wa yar uwarshi wulakanci saboda bare.
Murmushi kawai yai mata ya mike tare da aje mata abindaya saba aje masu ida yazo gaidasu.
Yaran shi yaja
Showing 432001 words to 435000 words out of 456145 words
Ban kawo komai ba a raina na shirya dama a shirye nake dan gyarawa kawai nayi.
Duk kan su suna falon kowacen su ta hakkince a zaune cikin nata kalar shigan sai shi may gidan da alama ya nuna ko wankan shirin fita baiyi ba a lokacin.
Da mamaki na karasa cikin falon tare da sallama da fargaban may kuma ya faru haka son ruwa baya tsami banza a hakan.
Ina shigowa ya dago kai tare da sauke idanuwan shi a kaina yana mai amsa sallamana.
Na samu wuri na zauna can daga karshe nace gani daddy lafiya dai ko ?
Da hannu ya nuna min na zauna na karasa kaiwa zaune din ina mai kura mai idanuwa na don ban bi ta kan kowa ba dake falon a lokacin.
Shiru falon yayi can ya dan nisa tare da shafo fuskan shi yace na kiraku ne don wani magana da naji daga bakin wanan yarinyar ya nuna inda Niima take zaune da fuskan shi.
Sai kowan mu ya gyara zaman shi don jin may ya faru kuma haka yaci gaba da fadin daren jiyane ta fuskance ni da wani zancen da ya kona min rai a gidan nan akan yaran nan marayu da Saade ta bar min ko nace ta bar mu dasu.
Daga inda nake zaune nace tau fa ?
Yace eh tazo min da zancen wai ita bazata yarda ba sai itama na bata kudi kamar yadda nake bawa kowa a gidan nan don har su Amira da Nasir na ware ma makuddan kudi daka jikina na basu a matsayin kyauta don tallafawa rayiwan su.
Kuma ba kowa yasani yin haka ba sai Rahama don tana bakin ciki na mutu a raba gado kowa ya samu yasa ta bani wanan shawaran
Take naji raina ya yi mugun baci nace a hasale wai wanan matar may kike so danine a gidan nan wai ?
Yace dani dakata hakana magana nake yi sai nai shiru tare da komawa na zauna da kyau.
Yace maganan ya bani matukar mamaki don ban san ina ta samo wanan zancen nata ba haka ?
Ya juya gunta yace Niima jiya da kike min wannan magana kikaga na yi shiru akwai abinda nake tunane ne bawai na kyale ki bane hakana sai kuma kyale kin da nayi ya bani daman karasa sauraren abinda ni ban sani ba a gidan nan.
Kafan ta take kadawa a hankali yayin da tai tagumi da hannun ta daya tana mashi wani irin kallo mai kama da tsanane ko haushi ?
Yanzu ina son ji daga bakinki a ina wanan maganan yafito maki haka na ki fada muna ke muke saurare.
Sai tai shiru tunda naji Zulfa tace da ita ke Niima may yakaiki yin wanan maganan don Allah nasan akwai wata a kasa in baki manta ba mai karatu Anty marigayiya tasha fada min cewa nai hankali sosai da Zulfa don munafukace ta gaske amma a zatona ta daina halin nata ne yanzu girma yazo mata .
Muryan daddy yadawo dani daga tunanen da nakeyi naji yace ke muke saurare fa kada ki shanya mu anan ?
Shiru tayi sai ya dan gyara zaman shi da kyau yace saurara kiji wallahi kinji na rantse maki ko ki fada min ko yanzu ki raina kanki ga hukuncin da zan yanke a kan ki.
Don duk wanda har yake jiran ka mutu yaci gadon ka to kuwa zai iya kashe ka ya kaiga manufan shi a tare da kai.
Tace nima ai fada min akayi gadon ka kuma ai ba ni kadai ke jiran ci ba don duk wacce ke tare dakai shi suke jira suma.
Ko don an fini wayon iya gilibibi yasa nawa kawai za a gani don nai magana kawai.
Hindatu tace ke ki iya bakin ki don mu ba mayunwata bane irin ki sai ta watsa ma hindatun harara tace shi kan shi ya sani ai .
Badon cin gadon akace Rahama na haihuwa akai akai don tafi kowa kaso ba a gidan dariya maganan ta ya bani ban iya magana ba don ya kwabe ni da farko nasan ko yanzu ba zai bari na sake wani maganan ba ma.
Yace ai saiki fada muna wanda ya fada maki tace akan may zan fada don an raina min za ace don nai magana da kai za a zo a tsureni gaban kowa nai magana.
Da suke siri dakai tsuresu kakeyi ko may dani za ai min hakan don raini.
Wani uban tsawa ya daka mata sai data dan razana yace zaki fada ko yanzu na zartan da hukuncin da nai niyya a kan ki don ba zan iya zama da macen da ta iya fitar min da zuciyar ta damanufanta ba haka a fili.
Jin abinda ya fada yasa tace a dai muna hukunci da wacce ta fada min don nima daga bakin uwar gidan ka na samu labari.
Da sauri zulfa tace ke kada ki fara ki min sheri wallahi ko don yanzu za a jimu dake a gidan nan.
Tace sherin may zan maki bake kika fada min ba kikace duk yadda zanyi na kawar da Rahama a gidan nan nayi ko bata fita ba ta koma ita da babu duk daya.
Daddy yace kinji Zulfa kinji yanzu abinda ta sake fada ko Niiman tace ai ba kazafi nai mata ba.
Kince kudin shi Rahama ke komai dashi tana labewa ga aiki take samu sai abinda tace ake kuna kallo a gidan daku da yaran ku kamar babu ku a wurin shi.
Daga inda nake zaune nace Allah na gode ma da baiwar da kai min ka rabani da hassada a rayuwa na.
Nace Zulfa ai kun riga da kunyi sake diyar zakanyya ta girma sai hakkuri yanzu don haka munafuncin ki da hassada zai sa ki tabbata a boran ki har abada don babu mai iya sauya ma wani hali shi sai Allah.
Don da zaki daina munafunci a bayan ido zama dani dayasa kin daina ko tuntuni may yafi nan kunya ki zauna da yarinya karama kina gulma irin haka don hassada kawai da bakin ciki.
May na rage ki dashi na mutuntawa a rayuwan zaman mu dake ba yau ba na sani akwai wanan ranan yana tafe gun munafuki ai.
Kada ki kara kirana da munafuka Rahama karya ne may Saade din ta bari da za, ace wai gadon yaran tane wanan kudin da ake fada.
Tace dakata gaskiya dai ya baiyyana yanzu kundai yi maganan da Niima ke nan a gidan nan ko ?
Tace munyi sai dai ba yadda ta fada ba aiko hindatu ta sani da sauri hindatu tace da kukazo min da maganan may na fada maku ni ?
Ba cewa nayi yanzu na gaji da wanan halin ba abinda ke gabana ya isheni kuma ke Zulfa na fada maki Rahama bada tsiya take nufar mu ba kibi a hankali koba haka mukayi dake ba.
Tace yanzu ko da maganan ya zama haka amma aiko ke da cewa kike don tafi kowa kaso take haihuwa akai akai haka a gidan nan bake kika fara fada ba.
Tun fara cacan baki a wurin ya dafe kan shi baiyi magana sai da yaga abin bana karewa bane yake cewa damu.
Kai ya isheni haka na yanzu na gane inda maganan nan ya fito don haka dake da kika fada min da ita data fada maki duk hukuncin da zan yanke ya hau ka ku.
Zulfa ba zanyi duban irin zumuncin dake tsakanina dake ga don na fahinci duk wani tsegumi na gidan nan daga gareki yake fitowa don haka dake da Niima ku saurara da kyau kuji.
Kudi dai banawa bane bana Rahama bane dukiyan yara ne da nake juyawa na uwar su tun tana a raye kamar yadda ta dauki amana tabani haka na rike wanan amanan har shekara goma sha tara ina rike dasu a hannuna.
Sune yanzu ganin yaran sun kawo hankali na fara gabatar masu da dukiyar su don su san dashi a gare ni.
Rahama ga tanan a matsayin ta na mata na dake rike mun yaran ita na fara gabatawa dukiyan yaran.
Sai Allah ya taimake ni ta bani shawaran da ya dace akan na kafa hujja da yan uwana da kuma yan uwan mahaifiyan su.
Nasan kuma zaman da mukayi da su a kano har yasa kuka samu wanan labarin yazo gare ku.
Amma da yake baku da tsoron Allah a tare daku ita da ta taimaka min ta bani mafita kuka dauki sheri da zargi kuka saka mata dashi.
Mai son abinka har rayuwan ka yana so idan ya samu don haka bazan taba iya zama da irin mutanem nan ba a rayuwa na .
Ya fadin haka ya mike daga inda yake zaune yace ku bani wuri don Allah zan shirya ni.
Nice ta farkon mikewa a nan zabbar kunya na barsu su uku suna cacan baki a tsakanin su ina shiga wurina wani kuka mai sosa zuciya yazo min a lokaci daya.
Ban fito ba sai da lokacin zuwa dauko yarana makaranta yayi naiwa mama Sallama na fita daga gidan gidan yai shiru ba motsin kowa ko irin kidan da kakeji yana tashi a part din Niima yau babu shi a gidan ko kadan.
Haka na fita daga gidan naje na dauko yaran muka juyo zuwa gida muna shiga ne na hadu da wata kawar Niima zata fita tabini da kallo ban kula taba na shige abina.
Naiwa yaran wanka muna zaune ina basu abinci sai ga daddy ya shigo wirin mu nai mashi sannu da dawowa yake cewa da shi.
Yaran har sun dawo ashe nace eh yanzu na dauko su yake cewa zan tafi lagos yanzun nan tafiyan ya kamani sai dai kafin na dawo na fadawa Zulfa da Niima su bar min gida don haka ina fada maki ne babu ruwanki da zancen su kuma.
May hakan ke nufi da subar maka gidan ka dakace dasu yace maganin kiyayya nace rabuwa.
Yace dani to na rabu dasu duk su biyun ba zan iya zama da masu son rayuwana ba, don ni dukiyana na nemawa iyalina rufin asiri ne banga abinda na rage wata daga cikin ku dashi ba da har suke jiran mutuwa don na bar masu dukiyata suci.
Ita Zulfa yanzu zataci na diyan ta idan na mutu din ita ko Niima ta tafi da abinda ta samu a wurina a yanzu.
Daddy don Allah kayi hakkuri da wanan zancen haka na kowa da halin sa ake zama dashi ai.
Yace naki ra, ayin ke nan nikan ba zan iya zama da masu son rayuwana ba.
Yana fadan haka ya fice daga part din nawa da kyat na bude bakina daga kalkon mamakin da nake mai nai mashi Allah ya tsare hanya.
********* ********* *********
Zulfa kan bai dawo ya samay ta a gidan ba don ta tafi kano tun washegari sai Niima ce taki tafiya kamar yadda yaba da umurni.
Ya dawo ya samayta a gidan yai mata cin mutunci badon taso ba dole ta bar gidan kamar yadda yace din.
Da dare ina gurin shi yana cin abinci sai ga wayan hajitan shi ya ahigo mai suka gaisa suna gama gaisuwa da ita take tambayan shi dalilin turo Zulfa gida dayayi don gata sun samay ta da uwarta.
Yace eh hajiya nina sallamay ta don ba zan iya zama da ita ba haka laifi sukai min kuma na riga da na yanke hukuncin duk wanda ke da hannu a wanan maganan zan dauki mataki gare shi ko wanene tunda ba son Allah da Annabi suke min ba.
Kai Alhaji ka saurareni da kyau babu abinda zaka boye min yanzu kai bakiji kunya ba akan wata bare can zaka sallami yar uwarka ta jini.
Yace hajiya wacece baren da na sallamay ta akan ta tace maku ?
Waye banda Rahama da ta gama da kai baka ganin kowa da gashi in ba ita ba da diyan ta a gidan ka.
Wayan na a handfree don haka na mike tsam don na bar falon yai min nuni da hannu don na dawo na zauna.
Banki ba duk da ban so ba kada naji abinda raina zai baci gareshi naji yace amma hajiya yanzu in ga halarci ai Rahama ta wuce bare a wurin mu tunda na haihu da ita har diya biyar.
Dama shine gurin ta ta mallake ka da gida ka shiyasa taita haihuwa kamar bera nida naga sugar mai iyali ana nuna min zazagan hanji.
Yai murmushi yace hajiya sai dai ayi hakkuri na riga da na yanke hukuncina a kan su ba abinda ya saura yanzu.
Tace baka isa ba aiba kai ka kawo kanka duniya ba zan dawo da Zulfa idan ka isa ka dawo min da ita nan mu gani.
Yace hajiya gidana ai gidan ta ne tazo ta zauna idan zata iya ga gidan nan gata.
Daga haka sukai sallama ta kashe wayan tana ta fada dashi sai lokacin na nisa nace dama nasan duk laifin a kaina zai dawo ai.
Yace hado min passport din ki dana yara yanzu ki fadawa hindatu kuma ina neman ta shiru nayi sai naji yace dani badake nake bane.
Na mike na tafi hado mai passport din dayace daga can na tura akira mashi hindatun daya yace don mu biyu muka saura a gidan.
Kamar yadda ya fada min haka ya fada mata nakawo yasani daukan permision a wurin aikina ba kakautawa suka bani.
Kwana uku yazo ya ce mu shirya zamu tafi London da yara ita kuma hindatu zasu tafi italy da yaran ta.
Hakan akayi muka tafi hutun dole ga Zulfan ta dawo da yan uwanta da da suka rakota nan muka barsu a gidan muka tafi.
Wanan abin yai matukar bata masu rai sun kwana biyu suna zaton zamu dawo maigadi ke fada masu cewa ai bamu ma kasan gaba dayan mu gidan mun fita waje.
Haushine ya kama hajiyan ta tace su dawo kano har mu dawo maigadi ya rufe gidan bayan tafiya su.
Wasa wasa sai gashi mun kwashe wata uku a can hakan ya bani dama yin couses di da nake son yi.
Allah ya taimake ni a wanan tafitan kuma gurin Nasir ya cika ya samu gurbin zuwa yin ilimin na sojoji a can don dama shine burin mu a kullun da mun dawo zai shirya ya koma tunda sun kammala karatun su.
Airen Amira da ya taso ne ya dawo damu gida duk da ba a kasa daya muke ba kusan a lokaci daya muka shigo su hindatu sun dawo da kwana uku muma muka iso kasan shine bai samu dawowa ba a tare da mu.
Mun dawo da Sati biyu muka kwasa sai kano don a can zamuyi bukin Amirah saboda yan uwa gana mahaifinta dana mahaifiyan ta kowa nason ganin auren ta.
Kwanan biyu muka shiga gidan su daddy gaida hajiyan shi fuska a daure take amsa muna gaisuwan mu.
Hakan bai damay ni ba don ba bakon alamari bane yin haka a gareta sai bayan mun gaisa ne ta mayar da hankalinta ga jikokin ta ta share ni nima ban dade ba namike ina gyara gyalen dake jikina ina fadin zamu tafi tace dani yaran ma bazaki barsu mu gaisa ba dasu zaki kwashe su ki tafi.
Ki sani dai yara jinane ko kinki ko kin so dole dai a kira su da jikokina idan kuma rabasu dani zakiyi don kin iya raba anta da jin shi ke sai mu gani.
Nace hajiya ayi hakkuri idan zasu zauna sai na barsu don ni akwai inda zan tafi dama nai mata sallama natafi tana bina da bakaken magana.
Gidan Zarah na nufa mun dade muna hira da ita wayan gajiye ne ya isheni na dauka take ce min ga yara an dawo dasu daga gidan hajiya tun dazu suna kuka.
Nai murmushi don dama nasan bazasu zauna ba ai son fitina ne irin na hajiya kawai dani yasa tace nabar mata su.
Nadawo ne jinior ke fada min irin zagin dataita masu wai sn biyo mugun hali irin na uwarsu shiyasa basu san kowa ba a dangin su ko sunki ko sun so ita dai ce kakar su don ita ta haifi uban su.
Nai dariya nace ai tana da gaskiyan ta watarana ma acan zai kaiku ku kwana wurin ta jinior yace wallahi basu zuwa nace yaro dole ku tafi ai.
Niji dadin zama kano da mukayi kwana biyu don muna ta ziyaran yan uwa da abokan arziki wurin raba kayin buki.
Daddy bai shigo kano ba sai ana gobe kamun Amira ya shigo garin da dare don haka da safe ya shiga gaida mahaifan shi.
Har gidan su Zulfa ya tafi wurin mahaifiyar ta kamar yadda ya saba nan ta tutsiye shi tana fada wai yana wa yar uwarshi wulakanci saboda bare.
Murmushi kawai yai mata ya mike tare da aje mata abindaya saba aje masu ida yazo gaidasu.
Yaran shi yaja
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22Chapter 23Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32Chapter 33Chapter 34Chapter 35Chapter 36Chapter 37Chapter 38Chapter 39Chapter 40Chapter 41Chapter 42Chapter 43Chapter 44Chapter 45Chapter 46Chapter 47Chapter 48Chapter 49Chapter 50Chapter 51Chapter 52Chapter 53Chapter 54Chapter 55Chapter 56Chapter 57Chapter 58Chapter 59Chapter 60Chapter 61Chapter 62Chapter 63Chapter 64Chapter 65Chapter 66Chapter 67Chapter 68Chapter 69Chapter 70Chapter 71Chapter 72Chapter 73Chapter 74Chapter 75Chapter 76Chapter 77Chapter 78Chapter 79Chapter 80Chapter 81Chapter 82Chapter 83Chapter 84Chapter 85Chapter 86Chapter 87Chapter 88Chapter 89Chapter 90Chapter 91Chapter 92Chapter 93Chapter 94Chapter 95Chapter 96Chapter 97Chapter 98Chapter 99Chapter 100Chapter 101Chapter 102Chapter 103Chapter 104Chapter 105Chapter 106Chapter 107Chapter 108Chapter 109Chapter 110Chapter 111Chapter 112Chapter 113Chapter 114Chapter 115Chapter 116Chapter 117Chapter 118Chapter 119Chapter 120Chapter 121Chapter 122Chapter 123Chapter 124Chapter 125Chapter 126Chapter 127Chapter 128Chapter 129Chapter 130Chapter 131Chapter 132Chapter 133Chapter 134Chapter 135Chapter 136Chapter 137Chapter 138Chapter 139Chapter 140Chapter 141Chapter 142Chapter 143Chapter 144Chapter 145 Chapter 146Chapter 147Chapter 148Chapter 149Chapter 150Chapter 151Chapter 152Chapter 153