mukayi waje da gudun mu cikin firgici.
Nan mukaci karo da anty da tafito daga dakin ta sabale da danta suma barcin sukeyi a lokacin sukaji ihun suka fito.
Da gudu muka kwasa muka fita inda ake ihun mutanen gidan kaf suna waje gurin katon rizabuwan ruwan dake a gefen da mai wanki ke wanki da muma mukanyi sauran aiyuka a gurin wani lokaci can ta bayan dakin Hindatu.
Mun isa gurin ganin yadda suke ihu muna tambayan ko may ke faruwa sai nuna muna katon rizabuwan ruwan sukeyi suna kiran Hanifa hanifa ta fada cikin tankin ruwa.
Innalillahi nace shine kuke tsaye kuna kallon ta hindatu dake kusa da uwarta dake ta ihun neman taimako tace yaya kike son muyi mu yanzu ?
Lekawa nayi naga yarinyar tasha ruwa har ta taso sama da sauri na gyara na tsunduma ciki na dago yarinyar tare da dabara na mikota maigadi da shima ihun yakeyi kamar mace yana neman taimako ya cabe ta shida gajiye hakana fito a galabaice don na dade rabona da ruwa haka.
Babu alaman motsi ko kadan ga yarinyar nan uwar ta sai faman yanka kuwa tana fadin ta mutu tamutu ko na shiga uku na lalace shike nan hanifa shike nan na rasa yar guda daya da Allah yabani na shiga uku ku taimaka min kudawo min da farinciki na don Allah.
Sun kewaye ta sai faman kuka sukeyi ina fitowa nace don Allah ku daina kuka nan, ba kyau aiwa wanda ya fada ruwa saurin kuka haka please.
Gurin na nufa da sauri na duka na fara jaye mata ruwan ta hancin ta da ta bakin ta ina zubarwa ba motsi ko kadan gareta, sai cewa hindatu keyi aikubar wahala ta mutu kawai wanan bazata tashi ba ai.
Nan Zulfa ta zube kasa somama a kasa don kalamin hindatu ya kara firgita ta su kayi kan ta da ihu suna kiran sunan ta da karfi tare da firgici suke girgizata da karfi.
Dukawa nayi dakyau na kuma naja ruwan hancin da karfi tai wani irin tarawa ta bude ido sai kuma ta rufe nace Farida dauko min key din motana da sauri please bata dauki lokaci ba sai gata dashi muka kwasa ni da Farida da mai aikin uwarta dake rugumay da ita sai gajiye sai asibiti.
A guje muka shiga asibitin muna zuwa aka karbi yarinyar suka wuce da ita emargyncy da sauri.
Babu mai waya a cikin mu balle a kira mu sai da Zulfa ta farfado ne maigadi ke fada masu aina wuce da yarinyar asibiti.
Nan anty takira uba su lokacin yana gonan shi yana kallon dawa kan shi a can yaga kiran ta nan take fada mai yadawo gida ba lafiya fa take tai mai bayanin abinda ke faruwa agidan nasa.
Cikin razana yake tambayan yarinyar ta mutu ko, take Rahama ta wuce da it's asibiti dai, wani asibiti suka kai yarinyar tace mun dai fice da ita a hannu.
Mun kai awa daya da rabi sai gasu daddy da anty dasu mama laraba sun samay mu.
A gigice yake tambayan mu ta mutu ko na girgiza kai a hankali nace bata mutu ba suna ciki da ita dai tun dazun.
A lokacin likitan ya bude kofa yafito nan ya shiga mai bayani bayani sun gaisa da daddy yake tambayan shi yace ai an auna arziki an rage mata ruwan tun gida shine saukin ta gaskiya an ceci rayuwan ta da kafin Azo nan ruwan zai iya Mata I,lla ya kasheta, amma yanzu da sauki sosai gaskiya sai dai za, a bata gado don ta jirgita da yawa mu gani har wani lokaci.
Bayan an bada gado muka zauna a tare da ita dagani sai rigar barci dake a jikina lokacin nake zaune saboda yadda muka fito gidan a firgice damu.
Daddy ya shigo dakin da ledan magani a hannun shi kallo daya yaima inda nake zaune ya kawar da kan shi gefe yake tambayan tana numfashi kuwa ?
Tanayi daddy naba shi amsa a takaice batare da na dago kana ba hannu na yana rike dana yarinyar ina murzawa a hankali, sai ga gayyan mutanen gidan mu, Zulfa na gaba hankali a tashe ina ganin ta na mike a kujeran da nake zaune akai don in bata guri don nasan tana iya cewa may yakawo ni gurin yarta.
Mama Laraba dake tsaye gefe tun shigowan su sun tsura muna ido suna kallon abinda nakewa yarinyar tace ina zauna Rahama ake jaruma ce kinyi kokari wallahi koke ya kamata kiga likita yadda ake fadin kin yi din gurin ceto yarinyar.
Zulfa ta zauna a bikin gado tana cewa dani sannu Rahama nagode nagode kinji nan kowa ya shiga fadin albarkacin bakin shi akai.
Ni dai na mike nafice daga dakin na samu su Farida nake ce wa dasu muje gida na canza kayan jikinan nawa please.
A haraban asibitin muka hade da daddy naji kunyan yarda nake a yamutse dagani sai yar rigan barcin dake jikina sai rigan da aka cirewa hanifa ne ma na dora akaina madadin dan kwali ko hulla.
Yake cewa cikin son ji yaya akayi kuma Farida ce tai katfin halin bashi amsa tace zamu je gida ne ta cire kayan jikin ta yace yafi.
Muka fice daga haraban asibitin mun fara tafiya na sauke ajiyan zuciya a hankali farida tace ke Rahama ashe kin iya ruwa ne haka.
Murmushi nai mata nace kin manta ni yar kauye ce Farida sai dai na manta yaushe rabona da ruwa wallahi.
Ai kinyi kokari ji yadda anty zulfa ta gigice tana sambatu da mutuwa tayi killa ita ma mutuwan zatayi.
Nace bari maganan Farida insha Allahu zata tashi da yardan ubangiji ban son yarinyar nan ta mutu wallahi.
Sai da nake wankan ne naga inda naji ciwo a jikina duk firgici bai bari na sani ba sai yanzu da hankalina yadan kwanta.
Nafito na shirya cikin wani wando da riga falo na koma na zauna nan yaran suka rufe ni da tambaya dana shiga ruwa yaya nayi tun ina basu amsa inajin kaina yana dan sara min a hankali.
Haka yasa na dan kai kwance daga inda nake zaune har barci ya dauke ni a haka ban sani ba sai muryan anty naji tana tambaya ko lafiya na kwanta lokacin la,asar.
Firgigit na falka ina salati sai dai jikina ya dauki zafi a lokacin haka na mike naje nai sallah da karfin hali nazo gurin hada abin buda baki ranan adadafe na taimakawa Gajiye muka hada komai nakoma daki na dunkule saman gado sanyi nake ji a lokacin sosai.
Nasir ne yaje yake fadawa maman su wai banda lafiya sai gata a rude tana shigowa ta tsugun na gabana tana cewa Rama baki da lafiya inji danki.
Nace kaina ke ciwo anty ta dora hannun ta a kaina jikina radau yake a lokacin .
A hankali na runtse idona don sanyin hannun ta da naji a jikina huci na fitar daga bakina ina mika ta mike da sauri tana fadin baki da lafiya shine koka kumshe a daki haka.
Maza ki tashi muje asibiti cikin karfin hali nake ce mata bari dai nasha magani basai mun tafi asibiti ba anty.
Kin faye gardama wallahi sai ta fice daga dakin zuwa wani lokaci sai muryan daddy naji a dakin yana cewa .
Ke Rahama mike muje asibiti dama tun dazun nai tunanen a dubaki ke ma tun a asibitin.
Karasowa yayi bakin gadon tare da dan kai hannun shi saman wuya na a hankali.
Wani irin yanayi naji a lokacin tundags kaina hae yatsan kafana sai da naji yar ajikina gaba daya.
Na rutse idanuwa na sai ga hawaye na zubo min a hankali a idanuwa yace ku fito da ita mutafi ina waje ina jiran ku.
Da tai makon gajiye na fito dakin jiki sai kaduwa yake kamar ana shocking dina a lokacin.
Tare dashi da anty muka tafi asibitin nan muka karbi kati aka shiga dani ganin likita nan ya rubuta min allurai da maganunuwa da zan sha.
Bayan an gama muka juyo zuwa gida a hanya daddy ya tsaya wani shago ya sayo muna kayan sanyi da nama gassasa mai zafi sosai na mikawa anty yace kila bazata iya cin abinci ba sai ki bata wanan taci.
Tunda muka dawo gida na kwanta ban fito ba koda asuba tea din da gajiye ta hada min ban wani sha sosai ba .
Washegari ba laifi na samu zazzabin ya dan sauka min yanzu na dan samu sauki na dawo falo na zauna da sauran mutane.
Anty ce tafito daga daki ta samay ni zaune a gurin tace kin falka Rama yaya jikin yanzu daddy yazo ai har sau biyu kina barci ya tafi asibiti don ance jikin hanifa ba dadi tun daren jiya basuyi barci da dadi ba da ita.
Farida tace da suwa suka kwana acan anty tace uwar ta da mahaifiyarta sai mama Laraba.
Kai shine bata barsu su kwana da yarinyar ba Anty Zulfau bata da kirki wallahi sai lokacin nai magana nace ba rashin kirki bane tana son yarta ne shiyasa.
Dubi yadda taci wa Rahama mutunci ranan sai gashi jiya ta taimaki yarta ni wallahi naga karfin halinki Rahama da kika fada cikin ruwan nan haka na ni may zai kaini.
Nace nima wallahi ban san lokacin dana fada ba Farida yadda naga yarinyar a ciki kamar matatta hankalina ya daga sosai wallahi.
Har da ciwo naji saida nazo wanka nagani ban ma san naji ba wallahi.
Anty tace ai shine daddy ku ke magana tun a asibiti yake cewa bai masan irin godiyan da zai maki ba wallahi.
Wayan anty ne yai kara ta dauka daddy ne a layi muryan shi bai fita yake cewa da ita yana ganin hanifa ta rasu fa.
Da karfi anty tace hanifa ta rasu besty ?
Lokaci daya duk muka mike tsaye muna fadin innalillahi wa, inna alaihin raji,u.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE , , ,
IDAN KON BIYA KIKA TUWA WANDA BAI BIYA BA HAKKIN AMANA YANA KANKI YAR UWA
28
Hankali a tashe gaba dayan mu muka mike sai muka nufi hanyar waje cikin tashin hankali.
Babu kowa a haraban gidan a lokacin sai mai gadi dake kokarin kunna redion shi na hannu.
Anty ke cewa maigadi ba a shigo da gawan yarinyar bane gida ko kuwa yace hajiya shin wani gawa badai Allah yaiwa yarinya rasuwa ba.
Take cewa yanzu maigida ya bugo waya yake fada min abinda ya faru akan yarinyar.
Cikin karfin hali nace anty bari kawai muje asibitin mu samay su a can asibitin gaba daya .
Asibitin na kudi ne mai tsari daki ne harda kayan kallo da naura sanyi akwai a dakin mun samay su jugun jugun a tsaye daga kofan dakin hankalin su a tashe a lokacin.
Daga inda muke tsaye muna kallon likita na kokarin ceto rayuwan yarinyar a lokacin.
Hawaye ne yake sauka a idanuwana a hankali na dafe bakina da hannu kada sautin kuka na ya fito a lokacin.
Na dafa kaina a bango yadda nake kuka shi ya kara tayar wa mutanen dake gurin da hankali sai cewa suke haba Rahama ku daina kuka haka mana.
Daddy dake fitowa daga dakin tare da likita ya dago kai ya dan kalli gurin da nake manne da bango ina kuka cikin tashin hankali.
Tambayan daddy da likita da suka fito daga dakin su mama ke tambaya da cewa ta tafi ko .
Daddy ne ya juyo inda suke yake cewa sai hakkuri mama , Allah ya karbi abinshi ko.
Nan gaba daya a lokaci guda guri ya rude da ihu shi kanshi daddy gani daya zakai mai ka fahinci karfin hali yakeyi kawai alokacin.
Gaba daya muka kwaso muka nufi gida kowa hankalin shi a tashe gidan mahaifan daddy aka wuce da kayan yarinyar a can akai mata sutura aka kaita makwancin ta Allah ya karbi bakunci musulmi Allah ya gafartawa hanifa.
Gidan ya koma shiru baka jin motsin komai sai dan hayaniya jefi jefi daga sauran bangaren gida ita ko Zulfa abin yaso ya mayar da ita kamar wata zautata don mutuwan ya bugeta sosai a zuciyar ta .
Ba uwarta ba ko mu da muka dan saba da ita rashin ta yai muna zafi balle uwarta mahaifiyar ta ita ke nan mata a duniya ana neman haihuwan ido rufe don sun saka lamarin haihuwa a cikin kishin su.
Bamu shiga gurin ta ba sai da dare lokacin mutane sun rage yawa a part din nata ni da gajiye da farida da Amira da Nasir muka shiga part din mata wani tsami ne ya daki hancin mu kace kamar ba dakin yar kwalisa bace irin Zulfa ashe namane ya rube a fridge yake wanan warin haka.
Da sallama muka shiga dakin tana zaune da mahaifiyarta da mama laraba a dakin ta ga kaya a saman gadon an tara ko ina kwamatse a part din kamar dakin tsohuwa .
Sallama muka fara yi sai muka fara gaida su muna masu yaya hakkuri Allah yasa ta huta.
Mama Laraba tace Amira Amira Allah sarki kaunar ki abokiyar wasan ki yau Allah ya karbi abin shi .
Shiru mukayi kowa da yadda yake jin zafi a ranshi sai Zulfa ne da tun ahigowan mu ta fara kuka sosai nasan ganin yaran da tayi ne na anty ya tayar mata da mikin rashin diyar ta datayi.
Mun dan dauki lokaci zaune a falon munyi shiru nice nafara mikewa tsaye sai sauran suka mike mama ke cewa sannun ku da kokari kunje.
Rahma Allah baiyi hanifa rayayya bace dan ba don ke ba ma ai da bata kara kwana ba kila don zuwan ki ne kika shige ciki aka dauko ta .
Mama Zulai tace da ace tazo da wuri kila da bata sha ruwa hakana ba sosai.
Nace wallahi muma muna cikin barci ne a cikin barci ne muka dinga jin ihu jin mu ke nan muka fito a lokacin ta dade ina gani a ruwan.
Sai Zulfa dake kuka take cewa ai na dauka maigadi zai iya fitar da ita don nace a fada maku Hindatu tace wai a, a a bari mai gadi ya gwada a gani ko zai iya fitar da ita lokacin.
Nan uwar ta ta hau fada tana cewa da ita ai idan baki daina bin wanan hindatun ba sai ta kaiki ta baro sosai.
Farida tace ni haushi ma tabani data kama kirawa yarinya mutuwa tun bata mutu ba nan dai Farida ta basu labarin komai kaf ai kamar an tunzura Zulfa da Uwarta mama Zulai ne a lokacin.
Mu dai muka fice muka barsu nan suna ta maida magana kuwa bayan yaki don mai faruwa ya riga da ya faru ko a lokacin.
Haka na farko azumin yazo gidan ba dadin rai rasuwan yarinyar ya hana uban komawa Abuja gurin aikin shi a lokaci sai dai yakan je ya dawo amma ba ya irin dade bai gida din nan ba.
An sa an kwashe ruwan tank din da Hanifa ta fada ciki an kara mai tsayi sama sosai ko babba sai yayi da gaske zai iya ganin iyakar shi amma akwai kan fanfo daga kasa inda ruwa ke fita.
Mutuwar yarinyan yadan rage yawan fitina a gidan don yanzu ba wani hadin kai na gulma da suka saba hadewa ayi don a kullawa anty sheri da mu ma damuke a karkashin ta a gidan.
Da alama Zulfa ta ja baya da hindatu sun samu matsala a tsakanin su a gida don yanzu ko azumine basu yawan zama guri daya da junan su kowa harkan gaban ta takeyi a lokacin.
Ranan da maigidan ya kirasu kan abin kayan sallah da za, a saya a gidan nan rikci ya kaure a tsakanin su.
Ko wacce na fadin irin abinda za, a sayawa yara a lokacin, Zulfa na daga gefe daya tana sauraren su abinda suke fadi.
Har aka kawo kan zancen kayan sallah yaran gidan nan Hindatu ta zake itace mai bayanin abinda za, a dinkawa yara na sallah.
Idan kaji yadda take bayani kasan da gaiyya take magana adole sune masu yaya a gidan yanzu don haka magana ya zama nasu bada Zulfa ba da bata da ko dunge a gidan.
Sai da ta gama bayanin ta kaf Anty Saade da maigidan suna sauraren ta can anty ta nisa tana cewa ni dai hakan bai min ba ni da Yaran zamu shiga boutiqu mu diba abindaya dace har yan matan dake gurina.
But sukaga Zulfa ta mike ta fice daga falon inda suke zaune tana sharare hawayen a fuskanta.
Tausayin ta ya kama daddy da Anty shine ya mike yabi bayan ta yana bata hakkuri akan tayi tawakkali tabarwa Allah.
Anty ma da yamma ta shiga part din na Zulfa ta samay ta a har lokacin a ya mutse ta zauna taci kuka har tagaji.
Jin shigowan Anty Saade dakin yasa ta dago kanta daga inda take zaune a kasa duk ta kode da ita take cewa wa, alaikis salam.
Ansha ruwa lafiya maman Hanifa sai kawai ta fashe da kuka jin an kirata da maman hanifa don anty ce kawai mai kiranta da wanan sunnan.
Don ita Anty duk kan
Showing 108001 words to 111000 words out of 456145 words
Nan mukaci karo da anty da tafito daga dakin ta sabale da danta suma barcin sukeyi a lokacin sukaji ihun suka fito.
Da gudu muka kwasa muka fita inda ake ihun mutanen gidan kaf suna waje gurin katon rizabuwan ruwan dake a gefen da mai wanki ke wanki da muma mukanyi sauran aiyuka a gurin wani lokaci can ta bayan dakin Hindatu.
Mun isa gurin ganin yadda suke ihu muna tambayan ko may ke faruwa sai nuna muna katon rizabuwan ruwan sukeyi suna kiran Hanifa hanifa ta fada cikin tankin ruwa.
Innalillahi nace shine kuke tsaye kuna kallon ta hindatu dake kusa da uwarta dake ta ihun neman taimako tace yaya kike son muyi mu yanzu ?
Lekawa nayi naga yarinyar tasha ruwa har ta taso sama da sauri na gyara na tsunduma ciki na dago yarinyar tare da dabara na mikota maigadi da shima ihun yakeyi kamar mace yana neman taimako ya cabe ta shida gajiye hakana fito a galabaice don na dade rabona da ruwa haka.
Babu alaman motsi ko kadan ga yarinyar nan uwar ta sai faman yanka kuwa tana fadin ta mutu tamutu ko na shiga uku na lalace shike nan hanifa shike nan na rasa yar guda daya da Allah yabani na shiga uku ku taimaka min kudawo min da farinciki na don Allah.
Sun kewaye ta sai faman kuka sukeyi ina fitowa nace don Allah ku daina kuka nan, ba kyau aiwa wanda ya fada ruwa saurin kuka haka please.
Gurin na nufa da sauri na duka na fara jaye mata ruwan ta hancin ta da ta bakin ta ina zubarwa ba motsi ko kadan gareta, sai cewa hindatu keyi aikubar wahala ta mutu kawai wanan bazata tashi ba ai.
Nan Zulfa ta zube kasa somama a kasa don kalamin hindatu ya kara firgita ta su kayi kan ta da ihu suna kiran sunan ta da karfi tare da firgici suke girgizata da karfi.
Dukawa nayi dakyau na kuma naja ruwan hancin da karfi tai wani irin tarawa ta bude ido sai kuma ta rufe nace Farida dauko min key din motana da sauri please bata dauki lokaci ba sai gata dashi muka kwasa ni da Farida da mai aikin uwarta dake rugumay da ita sai gajiye sai asibiti.
A guje muka shiga asibitin muna zuwa aka karbi yarinyar suka wuce da ita emargyncy da sauri.
Babu mai waya a cikin mu balle a kira mu sai da Zulfa ta farfado ne maigadi ke fada masu aina wuce da yarinyar asibiti.
Nan anty takira uba su lokacin yana gonan shi yana kallon dawa kan shi a can yaga kiran ta nan take fada mai yadawo gida ba lafiya fa take tai mai bayanin abinda ke faruwa agidan nasa.
Cikin razana yake tambayan yarinyar ta mutu ko, take Rahama ta wuce da it's asibiti dai, wani asibiti suka kai yarinyar tace mun dai fice da ita a hannu.
Mun kai awa daya da rabi sai gasu daddy da anty dasu mama laraba sun samay mu.
A gigice yake tambayan mu ta mutu ko na girgiza kai a hankali nace bata mutu ba suna ciki da ita dai tun dazun.
A lokacin likitan ya bude kofa yafito nan ya shiga mai bayani bayani sun gaisa da daddy yake tambayan shi yace ai an auna arziki an rage mata ruwan tun gida shine saukin ta gaskiya an ceci rayuwan ta da kafin Azo nan ruwan zai iya Mata I,lla ya kasheta, amma yanzu da sauki sosai gaskiya sai dai za, a bata gado don ta jirgita da yawa mu gani har wani lokaci.
Bayan an bada gado muka zauna a tare da ita dagani sai rigar barci dake a jikina lokacin nake zaune saboda yadda muka fito gidan a firgice damu.
Daddy ya shigo dakin da ledan magani a hannun shi kallo daya yaima inda nake zaune ya kawar da kan shi gefe yake tambayan tana numfashi kuwa ?
Tanayi daddy naba shi amsa a takaice batare da na dago kana ba hannu na yana rike dana yarinyar ina murzawa a hankali, sai ga gayyan mutanen gidan mu, Zulfa na gaba hankali a tashe ina ganin ta na mike a kujeran da nake zaune akai don in bata guri don nasan tana iya cewa may yakawo ni gurin yarta.
Mama Laraba dake tsaye gefe tun shigowan su sun tsura muna ido suna kallon abinda nakewa yarinyar tace ina zauna Rahama ake jaruma ce kinyi kokari wallahi koke ya kamata kiga likita yadda ake fadin kin yi din gurin ceto yarinyar.
Zulfa ta zauna a bikin gado tana cewa dani sannu Rahama nagode nagode kinji nan kowa ya shiga fadin albarkacin bakin shi akai.
Ni dai na mike nafice daga dakin na samu su Farida nake ce wa dasu muje gida na canza kayan jikinan nawa please.
A haraban asibitin muka hade da daddy naji kunyan yarda nake a yamutse dagani sai yar rigan barcin dake jikina sai rigan da aka cirewa hanifa ne ma na dora akaina madadin dan kwali ko hulla.
Yake cewa cikin son ji yaya akayi kuma Farida ce tai katfin halin bashi amsa tace zamu je gida ne ta cire kayan jikin ta yace yafi.
Muka fice daga haraban asibitin mun fara tafiya na sauke ajiyan zuciya a hankali farida tace ke Rahama ashe kin iya ruwa ne haka.
Murmushi nai mata nace kin manta ni yar kauye ce Farida sai dai na manta yaushe rabona da ruwa wallahi.
Ai kinyi kokari ji yadda anty zulfa ta gigice tana sambatu da mutuwa tayi killa ita ma mutuwan zatayi.
Nace bari maganan Farida insha Allahu zata tashi da yardan ubangiji ban son yarinyar nan ta mutu wallahi.
Sai da nake wankan ne naga inda naji ciwo a jikina duk firgici bai bari na sani ba sai yanzu da hankalina yadan kwanta.
Nafito na shirya cikin wani wando da riga falo na koma na zauna nan yaran suka rufe ni da tambaya dana shiga ruwa yaya nayi tun ina basu amsa inajin kaina yana dan sara min a hankali.
Haka yasa na dan kai kwance daga inda nake zaune har barci ya dauke ni a haka ban sani ba sai muryan anty naji tana tambaya ko lafiya na kwanta lokacin la,asar.
Firgigit na falka ina salati sai dai jikina ya dauki zafi a lokacin haka na mike naje nai sallah da karfin hali nazo gurin hada abin buda baki ranan adadafe na taimakawa Gajiye muka hada komai nakoma daki na dunkule saman gado sanyi nake ji a lokacin sosai.
Nasir ne yaje yake fadawa maman su wai banda lafiya sai gata a rude tana shigowa ta tsugun na gabana tana cewa Rama baki da lafiya inji danki.
Nace kaina ke ciwo anty ta dora hannun ta a kaina jikina radau yake a lokacin .
A hankali na runtse idona don sanyin hannun ta da naji a jikina huci na fitar daga bakina ina mika ta mike da sauri tana fadin baki da lafiya shine koka kumshe a daki haka.
Maza ki tashi muje asibiti cikin karfin hali nake ce mata bari dai nasha magani basai mun tafi asibiti ba anty.
Kin faye gardama wallahi sai ta fice daga dakin zuwa wani lokaci sai muryan daddy naji a dakin yana cewa .
Ke Rahama mike muje asibiti dama tun dazun nai tunanen a dubaki ke ma tun a asibitin.
Karasowa yayi bakin gadon tare da dan kai hannun shi saman wuya na a hankali.
Wani irin yanayi naji a lokacin tundags kaina hae yatsan kafana sai da naji yar ajikina gaba daya.
Na rutse idanuwa na sai ga hawaye na zubo min a hankali a idanuwa yace ku fito da ita mutafi ina waje ina jiran ku.
Da tai makon gajiye na fito dakin jiki sai kaduwa yake kamar ana shocking dina a lokacin.
Tare dashi da anty muka tafi asibitin nan muka karbi kati aka shiga dani ganin likita nan ya rubuta min allurai da maganunuwa da zan sha.
Bayan an gama muka juyo zuwa gida a hanya daddy ya tsaya wani shago ya sayo muna kayan sanyi da nama gassasa mai zafi sosai na mikawa anty yace kila bazata iya cin abinci ba sai ki bata wanan taci.
Tunda muka dawo gida na kwanta ban fito ba koda asuba tea din da gajiye ta hada min ban wani sha sosai ba .
Washegari ba laifi na samu zazzabin ya dan sauka min yanzu na dan samu sauki na dawo falo na zauna da sauran mutane.
Anty ce tafito daga daki ta samay ni zaune a gurin tace kin falka Rama yaya jikin yanzu daddy yazo ai har sau biyu kina barci ya tafi asibiti don ance jikin hanifa ba dadi tun daren jiya basuyi barci da dadi ba da ita.
Farida tace da suwa suka kwana acan anty tace uwar ta da mahaifiyarta sai mama Laraba.
Kai shine bata barsu su kwana da yarinyar ba Anty Zulfau bata da kirki wallahi sai lokacin nai magana nace ba rashin kirki bane tana son yarta ne shiyasa.
Dubi yadda taci wa Rahama mutunci ranan sai gashi jiya ta taimaki yarta ni wallahi naga karfin halinki Rahama da kika fada cikin ruwan nan haka na ni may zai kaini.
Nace nima wallahi ban san lokacin dana fada ba Farida yadda naga yarinyar a ciki kamar matatta hankalina ya daga sosai wallahi.
Har da ciwo naji saida nazo wanka nagani ban ma san naji ba wallahi.
Anty tace ai shine daddy ku ke magana tun a asibiti yake cewa bai masan irin godiyan da zai maki ba wallahi.
Wayan anty ne yai kara ta dauka daddy ne a layi muryan shi bai fita yake cewa da ita yana ganin hanifa ta rasu fa.
Da karfi anty tace hanifa ta rasu besty ?
Lokaci daya duk muka mike tsaye muna fadin innalillahi wa, inna alaihin raji,u.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE , , ,
IDAN KON BIYA KIKA TUWA WANDA BAI BIYA BA HAKKIN AMANA YANA KANKI YAR UWA
28
Hankali a tashe gaba dayan mu muka mike sai muka nufi hanyar waje cikin tashin hankali.
Babu kowa a haraban gidan a lokacin sai mai gadi dake kokarin kunna redion shi na hannu.
Anty ke cewa maigadi ba a shigo da gawan yarinyar bane gida ko kuwa yace hajiya shin wani gawa badai Allah yaiwa yarinya rasuwa ba.
Take cewa yanzu maigida ya bugo waya yake fada min abinda ya faru akan yarinyar.
Cikin karfin hali nace anty bari kawai muje asibitin mu samay su a can asibitin gaba daya .
Asibitin na kudi ne mai tsari daki ne harda kayan kallo da naura sanyi akwai a dakin mun samay su jugun jugun a tsaye daga kofan dakin hankalin su a tashe a lokacin.
Daga inda muke tsaye muna kallon likita na kokarin ceto rayuwan yarinyar a lokacin.
Hawaye ne yake sauka a idanuwana a hankali na dafe bakina da hannu kada sautin kuka na ya fito a lokacin.
Na dafa kaina a bango yadda nake kuka shi ya kara tayar wa mutanen dake gurin da hankali sai cewa suke haba Rahama ku daina kuka haka mana.
Daddy dake fitowa daga dakin tare da likita ya dago kai ya dan kalli gurin da nake manne da bango ina kuka cikin tashin hankali.
Tambayan daddy da likita da suka fito daga dakin su mama ke tambaya da cewa ta tafi ko .
Daddy ne ya juyo inda suke yake cewa sai hakkuri mama , Allah ya karbi abinshi ko.
Nan gaba daya a lokaci guda guri ya rude da ihu shi kanshi daddy gani daya zakai mai ka fahinci karfin hali yakeyi kawai alokacin.
Gaba daya muka kwaso muka nufi gida kowa hankalin shi a tashe gidan mahaifan daddy aka wuce da kayan yarinyar a can akai mata sutura aka kaita makwancin ta Allah ya karbi bakunci musulmi Allah ya gafartawa hanifa.
Gidan ya koma shiru baka jin motsin komai sai dan hayaniya jefi jefi daga sauran bangaren gida ita ko Zulfa abin yaso ya mayar da ita kamar wata zautata don mutuwan ya bugeta sosai a zuciyar ta .
Ba uwarta ba ko mu da muka dan saba da ita rashin ta yai muna zafi balle uwarta mahaifiyar ta ita ke nan mata a duniya ana neman haihuwan ido rufe don sun saka lamarin haihuwa a cikin kishin su.
Bamu shiga gurin ta ba sai da dare lokacin mutane sun rage yawa a part din nata ni da gajiye da farida da Amira da Nasir muka shiga part din mata wani tsami ne ya daki hancin mu kace kamar ba dakin yar kwalisa bace irin Zulfa ashe namane ya rube a fridge yake wanan warin haka.
Da sallama muka shiga dakin tana zaune da mahaifiyarta da mama laraba a dakin ta ga kaya a saman gadon an tara ko ina kwamatse a part din kamar dakin tsohuwa .
Sallama muka fara yi sai muka fara gaida su muna masu yaya hakkuri Allah yasa ta huta.
Mama Laraba tace Amira Amira Allah sarki kaunar ki abokiyar wasan ki yau Allah ya karbi abin shi .
Shiru mukayi kowa da yadda yake jin zafi a ranshi sai Zulfa ne da tun ahigowan mu ta fara kuka sosai nasan ganin yaran da tayi ne na anty ya tayar mata da mikin rashin diyar ta datayi.
Mun dan dauki lokaci zaune a falon munyi shiru nice nafara mikewa tsaye sai sauran suka mike mama ke cewa sannun ku da kokari kunje.
Rahma Allah baiyi hanifa rayayya bace dan ba don ke ba ma ai da bata kara kwana ba kila don zuwan ki ne kika shige ciki aka dauko ta .
Mama Zulai tace da ace tazo da wuri kila da bata sha ruwa hakana ba sosai.
Nace wallahi muma muna cikin barci ne a cikin barci ne muka dinga jin ihu jin mu ke nan muka fito a lokacin ta dade ina gani a ruwan.
Sai Zulfa dake kuka take cewa ai na dauka maigadi zai iya fitar da ita don nace a fada maku Hindatu tace wai a, a a bari mai gadi ya gwada a gani ko zai iya fitar da ita lokacin.
Nan uwar ta ta hau fada tana cewa da ita ai idan baki daina bin wanan hindatun ba sai ta kaiki ta baro sosai.
Farida tace ni haushi ma tabani data kama kirawa yarinya mutuwa tun bata mutu ba nan dai Farida ta basu labarin komai kaf ai kamar an tunzura Zulfa da Uwarta mama Zulai ne a lokacin.
Mu dai muka fice muka barsu nan suna ta maida magana kuwa bayan yaki don mai faruwa ya riga da ya faru ko a lokacin.
Haka na farko azumin yazo gidan ba dadin rai rasuwan yarinyar ya hana uban komawa Abuja gurin aikin shi a lokaci sai dai yakan je ya dawo amma ba ya irin dade bai gida din nan ba.
An sa an kwashe ruwan tank din da Hanifa ta fada ciki an kara mai tsayi sama sosai ko babba sai yayi da gaske zai iya ganin iyakar shi amma akwai kan fanfo daga kasa inda ruwa ke fita.
Mutuwar yarinyan yadan rage yawan fitina a gidan don yanzu ba wani hadin kai na gulma da suka saba hadewa ayi don a kullawa anty sheri da mu ma damuke a karkashin ta a gidan.
Da alama Zulfa ta ja baya da hindatu sun samu matsala a tsakanin su a gida don yanzu ko azumine basu yawan zama guri daya da junan su kowa harkan gaban ta takeyi a lokacin.
Ranan da maigidan ya kirasu kan abin kayan sallah da za, a saya a gidan nan rikci ya kaure a tsakanin su.
Ko wacce na fadin irin abinda za, a sayawa yara a lokacin, Zulfa na daga gefe daya tana sauraren su abinda suke fadi.
Har aka kawo kan zancen kayan sallah yaran gidan nan Hindatu ta zake itace mai bayanin abinda za, a dinkawa yara na sallah.
Idan kaji yadda take bayani kasan da gaiyya take magana adole sune masu yaya a gidan yanzu don haka magana ya zama nasu bada Zulfa ba da bata da ko dunge a gidan.
Sai da ta gama bayanin ta kaf Anty Saade da maigidan suna sauraren ta can anty ta nisa tana cewa ni dai hakan bai min ba ni da Yaran zamu shiga boutiqu mu diba abindaya dace har yan matan dake gurina.
But sukaga Zulfa ta mike ta fice daga falon inda suke zaune tana sharare hawayen a fuskanta.
Tausayin ta ya kama daddy da Anty shine ya mike yabi bayan ta yana bata hakkuri akan tayi tawakkali tabarwa Allah.
Anty ma da yamma ta shiga part din na Zulfa ta samay ta a har lokacin a ya mutse ta zauna taci kuka har tagaji.
Jin shigowan Anty Saade dakin yasa ta dago kanta daga inda take zaune a kasa duk ta kode da ita take cewa wa, alaikis salam.
Ansha ruwa lafiya maman Hanifa sai kawai ta fashe da kuka jin an kirata da maman hanifa don anty ce kawai mai kiranta da wanan sunnan.
Don ita Anty duk kan
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22Chapter 23Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32Chapter 33Chapter 34Chapter 35Chapter 36Chapter 37 Chapter 38Chapter 39Chapter 40Chapter 41Chapter 42Chapter 43Chapter 44Chapter 45Chapter 46Chapter 47Chapter 48Chapter 49Chapter 50Chapter 51Chapter 52Chapter 53Chapter 54Chapter 55Chapter 56Chapter 57Chapter 58Chapter 59Chapter 60Chapter 61Chapter 62Chapter 63Chapter 64Chapter 65Chapter 66Chapter 67Chapter 68Chapter 69Chapter 70Chapter 71Chapter 72Chapter 73Chapter 74Chapter 75Chapter 76Chapter 77Chapter 78Chapter 79Chapter 80Chapter 81Chapter 82Chapter 83Chapter 84Chapter 85Chapter 86Chapter 87Chapter 88Chapter 89Chapter 90Chapter 91Chapter 92Chapter 93Chapter 94Chapter 95Chapter 96Chapter 97Chapter 98Chapter 99Chapter 100Chapter 101Chapter 102Chapter 103Chapter 104Chapter 105Chapter 106Chapter 107Chapter 108Chapter 109Chapter 110Chapter 111Chapter 112Chapter 113Chapter 114Chapter 115Chapter 116Chapter 117Chapter 118Chapter 119Chapter 120Chapter 121Chapter 122Chapter 123Chapter 124Chapter 125Chapter 126Chapter 127Chapter 128Chapter 129Chapter 130Chapter 131Chapter 132Chapter 133Chapter 134Chapter 135Chapter 136Chapter 137Chapter 138Chapter 139Chapter 140Chapter 141Chapter 142Chapter 143Chapter 144Chapter 145Chapter 146Chapter 147Chapter 148Chapter 149Chapter 150Chapter 151Chapter 152Chapter 153