contact dina nima bana kiran kowa naci gaba da harkokina na watsar da komai balle namiji irin daddy daya cika mata a gida kowa da nata kalar sallon data iya.
Ya neme ni daya sauko don yaji lafiyan yaran shi amma layin bai shiga sai daga baya ya fahinci kila na canza layi ne hakan yasa ina nan akan bakana dashi ke nan ban sauko ba.
Niko nasan zanji surutun mutane akaina sosai amma hakan bai damay ni ba don ba zan zauna da kurciyana sunnun namiji ya kashe ni ba a raina.
Don ni kadau nasan irin hakkurin da nake a gidan ba a gani saboda hakkuri na sai gani ake nice ke yadda raina yaso ba a san cewa na zamay irin matan da akewa kirari da MARUCIN KAN DUTSE bane.
Kafin ya tofo sai an dauki shekaru bai tsiro ba a gani hakan ke sa ana daukan alhakin wasu mata ake ganin suke shanawa a gidan miji don hakkurin su.
Hakkuri idan yai yawa yakan baci ga dan adam don wani lokaci yana zama cuta haka yasa na dauku matakin don nuna mai nifa mutunce mai jini a zuciya ba wai ruwa kawai nake sha ba na zauna hakana.
Sannu sannu kwana nesa sai gashi na gama karatuna lafiya har Nasir da Atika sun samu kammala nasu karatun.
Sun so rike ni a kasan nai aiki dasu amma hakan ba zai yuyu ba don kaucewa zargi irin na mutanen mu don haka na daure nai aiki dasu na wata shidda kafin na karbi komai na yaran mu tattaro mu dawo gida gaba daya.
Ranan labara ranan saa muka sauka gida Nageria ni da yaran lokaci har Abdul ma yana tafiya da kafan shi ya fara karatu a can don shekaran shi biyu da dan kai.
Sai da muka huta a lagos har kwana uku don nisan tafiyan da muka kwaso muka dan huta anan.
Shigan safe mukayi Abuja a gidan da aka tanadar min na sauka na ma, aikatan mu nan na sauka ni da yarana baki dayan mu.
Na canza na koma wata matar manya ga aji ga class komai na tara a rayuwana bana shayin kowa kuma a halin yanzu ta fannin kishiya.
Sai washe gari na saka layin dana saya na nan gida Nigeria don an min wellcome back.
Na fara kiran yan uwa da abokan arziki muna gaisawa dasu don su san na dawo gida a lokacin.
Ban san dan gulman daya fadawa daddy cewa muna cikin Abuja ba mun sauka ni da yaran .
Yai matukar mamaki sosai don shi dama a hakane ta hake min zaiga yadda zan dawo gidan don yasan dai dole gidan shi zan dawo banda wani wurin zuwa kuma.
Sai gashi yana zaune mama laraba ta sake kiran shi tana cewa ashe Allah ya dawo da yaran nan lafiya jiya da dare Rahama ta kirani take fada min sun sauka lafiya sun dai iso lafiya ko ?
Wani iri yaji a ranshi amma a fili yace lafiya suka iso mama tai min addua ta kashe wayan sai lokacin ne ya ke tunane may wanan yarinyar take nufi ne wai dani ?
Daurewa yayi ya kira bashir din ya fada mai halin da muke ciki na dawo kasan ban nemay shi ba.
Bashir yai matukar mamaki sosai yace dama mai hakkuri bai iya fushi ba don haka kaida iyalinka ke hannunta ba fushi zakayi ba da su.
Daurewa zakayi kaje kanemayta ku sulhunta a tsakanin ku tun maganan baiyi nisa ba sosai don kaga yanzu fa ba da bane.
Rahama na da ilimi tawaye tasan duniya don haka juyata yadda kake nufi tunda ta hau haka kabita ka lalabata kawai a wuce wurin.
Ya dauki shawaran abokin nashi don ya nemay ni amma ban daga wayan ba, hakan bai mashi ba sai gashi ya nemi gidan da muke yayi zuwa yakai ukku amma naki yarda ya ganni.
Don ko yaushe gidan namu a rufe yake bamu fita ko ina mutum ma bai sanin akwai mutane a ciki don muna bakin shiga don da gidan empty yake ba kowa a cikin sa.
Hankalinshi ya tashi gashi ko yaran shi na hanashi ganin su balle yaji dan sanyi a ran shi idan ya gan su din.
Ganin baida wani mafita ga matakin da na dauka yasa shi yanke shawaran da zai fishe shi kawai don haka.
Kano ya nufa ya je kauyen mu ya sanarwa iyayyena halinda muke ciki ni dashi abin yai matukar basu mamaki sosai.
Kin san halin iyayye da rufe ido su ba yarsu laifi nima hakan ne ya kasance da nawa iyayyen don laifina suka gani ga zancen.
Tare suka shirya zuwa Abuja da daddy anyi tafiyan ne da maigari da mahaifina da liman da wani abokin babana.
Gidan da aka bani babbane akwai dakuna uku da katon falo sai haraban gida da sauran abubuwan rayuwa.
Zaune nake da yaran gaba dayan mu a falon mun dawo ke nan daga wurin shan icce cream tare dasu mukaji ana nocking din kofan gidan namu.
Nasir yake amsawa da ana zuwa yayi tsawo ya girma ya zama saurayi yana bude kofan gidan sukai tozali dashi mahaifin nashi ne a gaba.
Yace daddy you are wellcome cikin harshen turanci tare da cewa sauran da hausan shi daya dan sauya dan yawan turanci a can.
Sannun ku da zuwa sai ya dan riko hannun daddy nasu yana fadin daddy we miss you, ya rungumo yaron tare da riko hannun shi yana tambayan shi mummy ku na ciki ko ?
Yaron yace tana nan ciki gata can zaune a falo ma a lokacin ina zaune a kasa namike kafuwa na Abdul ya hau kan kafafuwan nawa yana shan icce cream sai jinior dake zaune saman kujera dana kara jikina gap da kaina yana shan ice cream din shi a roba mai dan fadi duk sun zagaye ni muna hira.
Sai ganin shi nayi yana shigowa rike da hannun Nasir a nashi ga mutane a bayan shi.
Na dago kai naga mutanen da yake tare dasu da sauri na mike ina gyara zamana tare da fadin sannun ku da zuwa baba.
Sai dai daga cikin su babu wanda ya amsa min gaisuwan nawa haka yasa na san anzo dani arai sosai don duk sun dauki zafi sosai dani
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE DON BA A YAFE BA ONLINE NOVEL NE, , ,
89
Duk na daburce na rasa may zanyi don ganin su da nayi a gidan nawa na dauke yaron dake jikina ina masu sannu da zuwa.
Wuri suka samu suka kai zaune take Aisha ta shiga kawo masu abin sha a gaban su suna ta bin mu da kallo.
Nasan ba komai bane sai ganin irin yadda dagani har yaran gaba daya duk mun sauya ma ganin su.
Don munyi fresh mun kara girma da kyau nayi jiki da fari don canjin yanayi dana samu a can din.
Nan na fara gaida su tare da masu sannu da zuwa sai dai basu wani karba min a cikun farin ciki da gani na din.
Sai baba maigari ne ke fadin Rahama a she kun dawo nace eh baba wallahi mun dawo yace yaya karatun ya jama, a can da kuma yaran nace dashi Alhamdullahi.
Yace sai dai kuma yaya na gan ku a nan ba a gidan mijin ki ba kuma don can naga ya kamata ace kun sauka aiko.
Nace eh baba akasi aka samu sai dai kune baku sani ba amma gaskiya a halin yanzu bamu tare da shi don tun ina can muka samu matsala dashi gaskiya baba ba ni da auren daddy a kaina don mun dade da rabuwa dashi akan wasu dalilai.
Magana nai masu ditect ba wani farga ba komai a zuciya na sai sune ma naga sun shiga rudani wanan ya kalin wancan suka fara a tsakanin su.
Sai shi maigari ne yai karfin halin fadin Alhaji Yusuf wai abinda take fadi gaskiya ne ko may don bamu fahinta ba mu ?
Daddy yai dan murmushi tare da girgiza kan shi yace ba gaskiya bane baba asalima ban san inda wanan maganan ya fito mata ba ni.
Na dai san mun dan samu matsala da ita tana can tun wanan lokacin kuma bamu sake haduwa ba da ita har yaran sai yau din nan baba ni ba irin mutanen nan bane masu saurin sakin mace akan da matsala kadan.
Maigari yace dani Rahama ban taba tsanmanin wanan halin daga gare ki ba kada ki kasancce a cikin irin matan nan da abin duniya oan yi saurin badewa idanuwan su.
Nace baba kada kuyi min wanan zaton don bani daga cikin masu wanan irin halaiyan ko kadan.
Haba Rahama koma may ya faru a tsakanin ku ai ya kamata ace mun sani ba wai ki bugun gaban kan ki ba ki tare a wani wurin da bamu da masaniyan shi a rayuwan ki.
Nai murmushi nace baba ku kwantar da hankalin ku kun san wa kuka haifa ai bazan yi wani abin assha wanda zai taba mutuncin ku a duniya ga idon mutane.
Sai lokacin babana yai magana yace na sani Rahama kuma ina shedan ki ga hakan amma ki sani gidan mijin ki yafi maki daraja ga komai.
Nasani baba amma kuyi hakkuri fa wanan hukuncin da har kukaga na dauka a kaina don shi abu mafi sauki ga rayuwa na daya dace inyi.
Baba ni ke zama da daddy yanzun kuma nace bana yi don Allah kada ku tsaurara min matakan da zuciyana baya iya jure daukan shi ga yin hakan danayi.
Baba na roke ku da kuyi hakkuri ku barni na samu natsuwa a rayuwa kan abin da zai fitar dani daga wanan rayuwan da bawan Allah nan yake son jefani a ciki.
Amma Rahama daga ke har shi din kun barmu a cikin duhu kan maganan din mu bamu fahinci may kuke fadi ba gar yanzu bamu san may ye matsalan ba.
Maimakon nai magana sai hawaye suka fara zubo min shar shar sai duk hankalin su ya tashi wanan abokin na mahaifina da suka zo tare ne yai magana.
Yace ni ina ganin da mun bawa wanan yarinyar dan lokaci har ta samu natsuwa sai a san mafita akan zancen don tunda muka ga Rahama har ta bude baki taimuna wanan magana haka yau ya kamata mu bita a sannu.
Sai duk sukayi shiru can baba maigari yace gaskiyane nima tunanen da nake ke nan yanzu a raina don haka kai malam Yusuf kayi hakkuri don Allah harta samu natsuwa.
Da haka aka bar maganan sukai min sallama ko abinci basu tsaya sunci ba acan ma bayan sun fita basu tsaya ba don a ranan zasu koma gida acewan su.
Sun tafi suna cike da mamaki da fargaban abinda ya faru yau din a tsakanin mu don abin ya daure masu kai sosai.
A motane suke magana shi wanan mutumin yace ya kamata abi zancen a hankali kamatayi suji ta bakina tunda har na jajirce masu akan hakan don da alama shi mijin baida gaskiya bayan musaawan da yayi bai kawo wani kwararen hujjaba akan maganan ai.
Nima dai abinda ya daure min kai ke haka iji maigari yace dole akwai wani matsala tunda tun auren su bata taba kawo muna wani kara ba makamancin haka din.
Ni dai tun tafiyan su haka na wuni a hargitse dani don nasha alwashin daukan wa kaina fansa akan abinda daddy ke min din.
Daga baya na ba kaina shawara na fitar da zancen a raina na rugunmi yara na na bar zancen wani daddy can.
Bayan kamar yan kwanaki na gama hutawa na ina batun fara aiki muka samu waya Abban anty ba lafiya sosai.
Ban tsaya ba washe gari na kwashi yaran sai kano muka dira a gidan mama laraba nai muna masauki don bamu je gidan daddy ba.
Wurin mama ne nake samun labarin wai an gyarawa amaryan daddy part din anty da ke kusa da nawa din a nan garin yanzu a ciki take zaune.
Ban damu ba don batun shi ni ya fice min akai ko mun tafi da dare asibiti mun duba jikin tsoho ba lafiya ko kadan yana jin ance mune cikin karfin hali ya bude idanuwan shi yana dan murmushi ya mikawa Nasir hannu yazo inda yake.
Yaje sun gaisa haka yaiwa sauran yaran abin gwanin ban tausayi yace cikin murmushi Rahama naso na zauna dake na taya ki duba yaran nan amma ban tsanmanin hakan ba don ciwon nan da wuya yabarni.
Don Allah kici gaba da kokarin da kikeyi a kan su kece da dadin hakan wata rana kin yi kankanta da daukan wanan nauyin a kanki amma kuma gashi cikin ikon Allah kin rike wanan amanan da aka bar maki da kyau ina maki fatan alheri dake da yaran nan a rayuwan ku nan gaba.
Kuka na fara haka yasa na bar dakin mun dan jima asibitin sai godiya yan uwan su ke tamin ganin yadda yaran suka koma a lokaci guda bakacewa suna da maraicin uwa a tare dasu don na zamay masu uwa ko a garesu yadda ya dace.
Sai dare muka koma gida tun da safe labarin rasuwan Abba ya samay mu ba mu tsaya ba muka garzaya gidan gaba dayan mu.
Damu akai komai aka kai daddy masaukin shi daddy bai san da zuwan mu ba sai da yazo yaga Nasir a waje yai matukar mamaki sosai.
Bayan sun kebe ne yake tambayan yaron da yaushe suka zo yake fada mai ai da aka bugowa mummy waya shine jiya muka taso har yake labarta mai yadda mukayi da tsohon a daren jiya da muka zo ganin shi.
A ran shi yace wanan yarinyar akwaita da bakin wayo sai dai ban san Rahama da riko irin haka ba ai dole ne na sauke girmana nabi yarinyar nan a sannu a zauna lafiya tunda nagane yanzu bani gaban ta .
Sun shiga ciki ina waje zaune da wata sister din anty da muke shiri tun banyi aure ba muna hiran mahaifin su ya shigo ciki gaisuwa.
Damu ya fara cin karo zaune saman farar kujera mun mai gaisuwa shima kamar babu komai a tsakanin mu ya shiga ciki yai ma sauran yan uwa ta, aziya yafito tun wanan lokacin ban san yaya ya karata ba kuma.
Sai dai na nemi yaran ban gansu ba ake ce min sun fita da daddy su ai shiya tafi dasu da zai wuce.
Naso sa damuwa amma na danne don ina tsoron mutane su fahinci abin da ke a tsakanin mu dashi a wurin.
Tsora kada ya rike yaran ya biyo min ta nan yaci galaba na sai dai yadda nake ji a raina koda zai karbe yaran shi ne zan iya hakkuri dasu din in har ya biyo min ta nan.
Mun dawo gidan mama har nai shirin kwanciya bai dawo da yaran ba gida hankalina yana atashe sai mamane ke tambayana wai ko zai dawo dayaran nan kuwa yau.
Nace a sanyaye ban sanu ba mama tace barin kirashi naji ina ya tsaya dasu ga dare yayi tana kiran shi ya dauki wayan.
Tace kana ina da yara ga dare ya soma baka dawo mata dasu ba har yanzu yace da ita suna nan gida tare dani.
Mama tace dawo mata da yaranta hakana su kwanta dare yayi zaiyi magana tace dashi Alhaji karami kada ka soma kace zaka tsoma yara a cikin zancen ku.
Kanemi shiri yadda ta dace a gun matarka yafi wanan hanyan dakake son dauka.
Yai dariya yace mama ba rike su zanyi ba nima ina son ganin su ne tunda hardasu ta hana min ganin yara na.
Tace na fada ma dawo mata dasu yanzu batai magana ba amma nasan abin zai damay ta a rai.
Yace gamu tafe mama aishi Abdul din ma da bai sanni ba sosai tundazun fitina yake min shiko takwarana sau fada yake wai wata ta shiga dakin maman su bazan iya rigimar yaran ba gani tafe dasu mama.
Tace cikin dariya aika dandana kaima kaji abinda take ji yau dasu ku dai maza nakan rasa ina tunanen ku yakan shiga idan kun tashi tsula tsiyan ku.
Tunda mama tace ga shi tafe da yaran na shige ciki abina don bani kaunan ganin shi ma idan na tuna yadda ya rufe ido yazo tsula min tsiya a baya.
Dana bita son miji da yanzu bankai wanan matsayin da Allah yakaini gareshi ba da akaso ai min bakin ciki akan shi.
Ina cikin wanan tunanen ne naji muryan su sun dawo suna nema na nan Nasir ya shigo dakin dauke da kanin shi a kafadan shi yayi barci ko.
Yana shimfideshi sau ga uban a bayan shi dauke da Haidar shima yayi barci a jikin shi sai daya aje shi yace da yaron dake tsaye ya fita.
Yaron na fita nai kamar ban ganshi ba adakin sai wani irin kallo yake bina dashi kamar ranan ya fara gani na, naji yace Rahama wai may kike nufi ne damu haka ?
Da har zaki zo garin nan kiki sauka a dakin ki kizo nan gidan mamana ki sauka ban fahunci har yanzu inda kika dosa ba fa da auren mu.
Showing 363001 words to 366000 words out of 456145 words
Ya neme ni daya sauko don yaji lafiyan yaran shi amma layin bai shiga sai daga baya ya fahinci kila na canza layi ne hakan yasa ina nan akan bakana dashi ke nan ban sauko ba.
Niko nasan zanji surutun mutane akaina sosai amma hakan bai damay ni ba don ba zan zauna da kurciyana sunnun namiji ya kashe ni ba a raina.
Don ni kadau nasan irin hakkurin da nake a gidan ba a gani saboda hakkuri na sai gani ake nice ke yadda raina yaso ba a san cewa na zamay irin matan da akewa kirari da MARUCIN KAN DUTSE bane.
Kafin ya tofo sai an dauki shekaru bai tsiro ba a gani hakan ke sa ana daukan alhakin wasu mata ake ganin suke shanawa a gidan miji don hakkurin su.
Hakkuri idan yai yawa yakan baci ga dan adam don wani lokaci yana zama cuta haka yasa na dauku matakin don nuna mai nifa mutunce mai jini a zuciya ba wai ruwa kawai nake sha ba na zauna hakana.
Sannu sannu kwana nesa sai gashi na gama karatuna lafiya har Nasir da Atika sun samu kammala nasu karatun.
Sun so rike ni a kasan nai aiki dasu amma hakan ba zai yuyu ba don kaucewa zargi irin na mutanen mu don haka na daure nai aiki dasu na wata shidda kafin na karbi komai na yaran mu tattaro mu dawo gida gaba daya.
Ranan labara ranan saa muka sauka gida Nageria ni da yaran lokaci har Abdul ma yana tafiya da kafan shi ya fara karatu a can don shekaran shi biyu da dan kai.
Sai da muka huta a lagos har kwana uku don nisan tafiyan da muka kwaso muka dan huta anan.
Shigan safe mukayi Abuja a gidan da aka tanadar min na sauka na ma, aikatan mu nan na sauka ni da yarana baki dayan mu.
Na canza na koma wata matar manya ga aji ga class komai na tara a rayuwana bana shayin kowa kuma a halin yanzu ta fannin kishiya.
Sai washe gari na saka layin dana saya na nan gida Nigeria don an min wellcome back.
Na fara kiran yan uwa da abokan arziki muna gaisawa dasu don su san na dawo gida a lokacin.
Ban san dan gulman daya fadawa daddy cewa muna cikin Abuja ba mun sauka ni da yaran .
Yai matukar mamaki sosai don shi dama a hakane ta hake min zaiga yadda zan dawo gidan don yasan dai dole gidan shi zan dawo banda wani wurin zuwa kuma.
Sai gashi yana zaune mama laraba ta sake kiran shi tana cewa ashe Allah ya dawo da yaran nan lafiya jiya da dare Rahama ta kirani take fada min sun sauka lafiya sun dai iso lafiya ko ?
Wani iri yaji a ranshi amma a fili yace lafiya suka iso mama tai min addua ta kashe wayan sai lokacin ne ya ke tunane may wanan yarinyar take nufi ne wai dani ?
Daurewa yayi ya kira bashir din ya fada mai halin da muke ciki na dawo kasan ban nemay shi ba.
Bashir yai matukar mamaki sosai yace dama mai hakkuri bai iya fushi ba don haka kaida iyalinka ke hannunta ba fushi zakayi ba da su.
Daurewa zakayi kaje kanemayta ku sulhunta a tsakanin ku tun maganan baiyi nisa ba sosai don kaga yanzu fa ba da bane.
Rahama na da ilimi tawaye tasan duniya don haka juyata yadda kake nufi tunda ta hau haka kabita ka lalabata kawai a wuce wurin.
Ya dauki shawaran abokin nashi don ya nemay ni amma ban daga wayan ba, hakan bai mashi ba sai gashi ya nemi gidan da muke yayi zuwa yakai ukku amma naki yarda ya ganni.
Don ko yaushe gidan namu a rufe yake bamu fita ko ina mutum ma bai sanin akwai mutane a ciki don muna bakin shiga don da gidan empty yake ba kowa a cikin sa.
Hankalinshi ya tashi gashi ko yaran shi na hanashi ganin su balle yaji dan sanyi a ran shi idan ya gan su din.
Ganin baida wani mafita ga matakin da na dauka yasa shi yanke shawaran da zai fishe shi kawai don haka.
Kano ya nufa ya je kauyen mu ya sanarwa iyayyena halinda muke ciki ni dashi abin yai matukar basu mamaki sosai.
Kin san halin iyayye da rufe ido su ba yarsu laifi nima hakan ne ya kasance da nawa iyayyen don laifina suka gani ga zancen.
Tare suka shirya zuwa Abuja da daddy anyi tafiyan ne da maigari da mahaifina da liman da wani abokin babana.
Gidan da aka bani babbane akwai dakuna uku da katon falo sai haraban gida da sauran abubuwan rayuwa.
Zaune nake da yaran gaba dayan mu a falon mun dawo ke nan daga wurin shan icce cream tare dasu mukaji ana nocking din kofan gidan namu.
Nasir yake amsawa da ana zuwa yayi tsawo ya girma ya zama saurayi yana bude kofan gidan sukai tozali dashi mahaifin nashi ne a gaba.
Yace daddy you are wellcome cikin harshen turanci tare da cewa sauran da hausan shi daya dan sauya dan yawan turanci a can.
Sannun ku da zuwa sai ya dan riko hannun daddy nasu yana fadin daddy we miss you, ya rungumo yaron tare da riko hannun shi yana tambayan shi mummy ku na ciki ko ?
Yaron yace tana nan ciki gata can zaune a falo ma a lokacin ina zaune a kasa namike kafuwa na Abdul ya hau kan kafafuwan nawa yana shan icce cream sai jinior dake zaune saman kujera dana kara jikina gap da kaina yana shan ice cream din shi a roba mai dan fadi duk sun zagaye ni muna hira.
Sai ganin shi nayi yana shigowa rike da hannun Nasir a nashi ga mutane a bayan shi.
Na dago kai naga mutanen da yake tare dasu da sauri na mike ina gyara zamana tare da fadin sannun ku da zuwa baba.
Sai dai daga cikin su babu wanda ya amsa min gaisuwan nawa haka yasa na san anzo dani arai sosai don duk sun dauki zafi sosai dani
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE DON BA A YAFE BA ONLINE NOVEL NE, , ,
89
Duk na daburce na rasa may zanyi don ganin su da nayi a gidan nawa na dauke yaron dake jikina ina masu sannu da zuwa.
Wuri suka samu suka kai zaune take Aisha ta shiga kawo masu abin sha a gaban su suna ta bin mu da kallo.
Nasan ba komai bane sai ganin irin yadda dagani har yaran gaba daya duk mun sauya ma ganin su.
Don munyi fresh mun kara girma da kyau nayi jiki da fari don canjin yanayi dana samu a can din.
Nan na fara gaida su tare da masu sannu da zuwa sai dai basu wani karba min a cikun farin ciki da gani na din.
Sai baba maigari ne ke fadin Rahama a she kun dawo nace eh baba wallahi mun dawo yace yaya karatun ya jama, a can da kuma yaran nace dashi Alhamdullahi.
Yace sai dai kuma yaya na gan ku a nan ba a gidan mijin ki ba kuma don can naga ya kamata ace kun sauka aiko.
Nace eh baba akasi aka samu sai dai kune baku sani ba amma gaskiya a halin yanzu bamu tare da shi don tun ina can muka samu matsala dashi gaskiya baba ba ni da auren daddy a kaina don mun dade da rabuwa dashi akan wasu dalilai.
Magana nai masu ditect ba wani farga ba komai a zuciya na sai sune ma naga sun shiga rudani wanan ya kalin wancan suka fara a tsakanin su.
Sai shi maigari ne yai karfin halin fadin Alhaji Yusuf wai abinda take fadi gaskiya ne ko may don bamu fahinta ba mu ?
Daddy yai dan murmushi tare da girgiza kan shi yace ba gaskiya bane baba asalima ban san inda wanan maganan ya fito mata ba ni.
Na dai san mun dan samu matsala da ita tana can tun wanan lokacin kuma bamu sake haduwa ba da ita har yaran sai yau din nan baba ni ba irin mutanen nan bane masu saurin sakin mace akan da matsala kadan.
Maigari yace dani Rahama ban taba tsanmanin wanan halin daga gare ki ba kada ki kasancce a cikin irin matan nan da abin duniya oan yi saurin badewa idanuwan su.
Nace baba kada kuyi min wanan zaton don bani daga cikin masu wanan irin halaiyan ko kadan.
Haba Rahama koma may ya faru a tsakanin ku ai ya kamata ace mun sani ba wai ki bugun gaban kan ki ba ki tare a wani wurin da bamu da masaniyan shi a rayuwan ki.
Nai murmushi nace baba ku kwantar da hankalin ku kun san wa kuka haifa ai bazan yi wani abin assha wanda zai taba mutuncin ku a duniya ga idon mutane.
Sai lokacin babana yai magana yace na sani Rahama kuma ina shedan ki ga hakan amma ki sani gidan mijin ki yafi maki daraja ga komai.
Nasani baba amma kuyi hakkuri fa wanan hukuncin da har kukaga na dauka a kaina don shi abu mafi sauki ga rayuwa na daya dace inyi.
Baba ni ke zama da daddy yanzun kuma nace bana yi don Allah kada ku tsaurara min matakan da zuciyana baya iya jure daukan shi ga yin hakan danayi.
Baba na roke ku da kuyi hakkuri ku barni na samu natsuwa a rayuwa kan abin da zai fitar dani daga wanan rayuwan da bawan Allah nan yake son jefani a ciki.
Amma Rahama daga ke har shi din kun barmu a cikin duhu kan maganan din mu bamu fahinci may kuke fadi ba gar yanzu bamu san may ye matsalan ba.
Maimakon nai magana sai hawaye suka fara zubo min shar shar sai duk hankalin su ya tashi wanan abokin na mahaifina da suka zo tare ne yai magana.
Yace ni ina ganin da mun bawa wanan yarinyar dan lokaci har ta samu natsuwa sai a san mafita akan zancen don tunda muka ga Rahama har ta bude baki taimuna wanan magana haka yau ya kamata mu bita a sannu.
Sai duk sukayi shiru can baba maigari yace gaskiyane nima tunanen da nake ke nan yanzu a raina don haka kai malam Yusuf kayi hakkuri don Allah harta samu natsuwa.
Da haka aka bar maganan sukai min sallama ko abinci basu tsaya sunci ba acan ma bayan sun fita basu tsaya ba don a ranan zasu koma gida acewan su.
Sun tafi suna cike da mamaki da fargaban abinda ya faru yau din a tsakanin mu don abin ya daure masu kai sosai.
A motane suke magana shi wanan mutumin yace ya kamata abi zancen a hankali kamatayi suji ta bakina tunda har na jajirce masu akan hakan don da alama shi mijin baida gaskiya bayan musaawan da yayi bai kawo wani kwararen hujjaba akan maganan ai.
Nima dai abinda ya daure min kai ke haka iji maigari yace dole akwai wani matsala tunda tun auren su bata taba kawo muna wani kara ba makamancin haka din.
Ni dai tun tafiyan su haka na wuni a hargitse dani don nasha alwashin daukan wa kaina fansa akan abinda daddy ke min din.
Daga baya na ba kaina shawara na fitar da zancen a raina na rugunmi yara na na bar zancen wani daddy can.
Bayan kamar yan kwanaki na gama hutawa na ina batun fara aiki muka samu waya Abban anty ba lafiya sosai.
Ban tsaya ba washe gari na kwashi yaran sai kano muka dira a gidan mama laraba nai muna masauki don bamu je gidan daddy ba.
Wurin mama ne nake samun labarin wai an gyarawa amaryan daddy part din anty da ke kusa da nawa din a nan garin yanzu a ciki take zaune.
Ban damu ba don batun shi ni ya fice min akai ko mun tafi da dare asibiti mun duba jikin tsoho ba lafiya ko kadan yana jin ance mune cikin karfin hali ya bude idanuwan shi yana dan murmushi ya mikawa Nasir hannu yazo inda yake.
Yaje sun gaisa haka yaiwa sauran yaran abin gwanin ban tausayi yace cikin murmushi Rahama naso na zauna dake na taya ki duba yaran nan amma ban tsanmanin hakan ba don ciwon nan da wuya yabarni.
Don Allah kici gaba da kokarin da kikeyi a kan su kece da dadin hakan wata rana kin yi kankanta da daukan wanan nauyin a kanki amma kuma gashi cikin ikon Allah kin rike wanan amanan da aka bar maki da kyau ina maki fatan alheri dake da yaran nan a rayuwan ku nan gaba.
Kuka na fara haka yasa na bar dakin mun dan jima asibitin sai godiya yan uwan su ke tamin ganin yadda yaran suka koma a lokaci guda bakacewa suna da maraicin uwa a tare dasu don na zamay masu uwa ko a garesu yadda ya dace.
Sai dare muka koma gida tun da safe labarin rasuwan Abba ya samay mu ba mu tsaya ba muka garzaya gidan gaba dayan mu.
Damu akai komai aka kai daddy masaukin shi daddy bai san da zuwan mu ba sai da yazo yaga Nasir a waje yai matukar mamaki sosai.
Bayan sun kebe ne yake tambayan yaron da yaushe suka zo yake fada mai ai da aka bugowa mummy waya shine jiya muka taso har yake labarta mai yadda mukayi da tsohon a daren jiya da muka zo ganin shi.
A ran shi yace wanan yarinyar akwaita da bakin wayo sai dai ban san Rahama da riko irin haka ba ai dole ne na sauke girmana nabi yarinyar nan a sannu a zauna lafiya tunda nagane yanzu bani gaban ta .
Sun shiga ciki ina waje zaune da wata sister din anty da muke shiri tun banyi aure ba muna hiran mahaifin su ya shigo ciki gaisuwa.
Damu ya fara cin karo zaune saman farar kujera mun mai gaisuwa shima kamar babu komai a tsakanin mu ya shiga ciki yai ma sauran yan uwa ta, aziya yafito tun wanan lokacin ban san yaya ya karata ba kuma.
Sai dai na nemi yaran ban gansu ba ake ce min sun fita da daddy su ai shiya tafi dasu da zai wuce.
Naso sa damuwa amma na danne don ina tsoron mutane su fahinci abin da ke a tsakanin mu dashi a wurin.
Tsora kada ya rike yaran ya biyo min ta nan yaci galaba na sai dai yadda nake ji a raina koda zai karbe yaran shi ne zan iya hakkuri dasu din in har ya biyo min ta nan.
Mun dawo gidan mama har nai shirin kwanciya bai dawo da yaran ba gida hankalina yana atashe sai mamane ke tambayana wai ko zai dawo dayaran nan kuwa yau.
Nace a sanyaye ban sanu ba mama tace barin kirashi naji ina ya tsaya dasu ga dare yayi tana kiran shi ya dauki wayan.
Tace kana ina da yara ga dare ya soma baka dawo mata dasu ba har yanzu yace da ita suna nan gida tare dani.
Mama tace dawo mata da yaranta hakana su kwanta dare yayi zaiyi magana tace dashi Alhaji karami kada ka soma kace zaka tsoma yara a cikin zancen ku.
Kanemi shiri yadda ta dace a gun matarka yafi wanan hanyan dakake son dauka.
Yai dariya yace mama ba rike su zanyi ba nima ina son ganin su ne tunda hardasu ta hana min ganin yara na.
Tace na fada ma dawo mata dasu yanzu batai magana ba amma nasan abin zai damay ta a rai.
Yace gamu tafe mama aishi Abdul din ma da bai sanni ba sosai tundazun fitina yake min shiko takwarana sau fada yake wai wata ta shiga dakin maman su bazan iya rigimar yaran ba gani tafe dasu mama.
Tace cikin dariya aika dandana kaima kaji abinda take ji yau dasu ku dai maza nakan rasa ina tunanen ku yakan shiga idan kun tashi tsula tsiyan ku.
Tunda mama tace ga shi tafe da yaran na shige ciki abina don bani kaunan ganin shi ma idan na tuna yadda ya rufe ido yazo tsula min tsiya a baya.
Dana bita son miji da yanzu bankai wanan matsayin da Allah yakaini gareshi ba da akaso ai min bakin ciki akan shi.
Ina cikin wanan tunanen ne naji muryan su sun dawo suna nema na nan Nasir ya shigo dakin dauke da kanin shi a kafadan shi yayi barci ko.
Yana shimfideshi sau ga uban a bayan shi dauke da Haidar shima yayi barci a jikin shi sai daya aje shi yace da yaron dake tsaye ya fita.
Yaron na fita nai kamar ban ganshi ba adakin sai wani irin kallo yake bina dashi kamar ranan ya fara gani na, naji yace Rahama wai may kike nufi ne damu haka ?
Da har zaki zo garin nan kiki sauka a dakin ki kizo nan gidan mamana ki sauka ban fahunci har yanzu inda kika dosa ba fa da auren mu.
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22Chapter 23Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32Chapter 33Chapter 34Chapter 35Chapter 36Chapter 37Chapter 38Chapter 39Chapter 40Chapter 41Chapter 42Chapter 43Chapter 44Chapter 45Chapter 46Chapter 47Chapter 48Chapter 49Chapter 50Chapter 51Chapter 52Chapter 53Chapter 54Chapter 55Chapter 56Chapter 57Chapter 58Chapter 59Chapter 60Chapter 61Chapter 62Chapter 63Chapter 64Chapter 65Chapter 66Chapter 67Chapter 68Chapter 69Chapter 70Chapter 71Chapter 72Chapter 73Chapter 74Chapter 75Chapter 76Chapter 77Chapter 78Chapter 79Chapter 80Chapter 81Chapter 82Chapter 83Chapter 84Chapter 85Chapter 86Chapter 87Chapter 88Chapter 89Chapter 90Chapter 91Chapter 92Chapter 93Chapter 94Chapter 95Chapter 96Chapter 97Chapter 98Chapter 99Chapter 100Chapter 101Chapter 102Chapter 103Chapter 104Chapter 105Chapter 106Chapter 107Chapter 108Chapter 109Chapter 110Chapter 111Chapter 112Chapter 113Chapter 114Chapter 115Chapter 116Chapter 117Chapter 118Chapter 119Chapter 120Chapter 121Chapter 122 Chapter 123Chapter 124Chapter 125Chapter 126Chapter 127Chapter 128Chapter 129Chapter 130Chapter 131Chapter 132Chapter 133Chapter 134Chapter 135Chapter 136Chapter 137Chapter 138Chapter 139Chapter 140Chapter 141Chapter 142Chapter 143Chapter 144Chapter 145Chapter 146Chapter 147Chapter 148Chapter 149Chapter 150Chapter 151Chapter 152Chapter 153