Najuyo nace dashi abinda kai niyar yi a can kasan da kaje har kake ikirari a akaina nake jiran ka dashi har yanzu.
Yace ni banje don yin wani abuba da ina da niyar yin wani abu aida a lokacin nayi ko tunda ba wanda zai hanayi idan natashi yi.
Nace ko yanzu ai sai ka tashi don shi nake jira a gare ka kasani kuma ba zan zauna da mutumin da bai son cigabana ba har abada.
Yai murmushi tare da cewa nine yau kuma bani kaunan cin gaban ki kike iya fadin haka da bakin ki Rahama ?
Kada fa idon ki ya rufe don kinga kin kaiga bukatan ki yau kice ni zaki watsa ma kasa a idona.
Nai murmushi nace aika dade da goranta min ko kan hakan koka manta ne na tuna maka yau ne ?
Na manta sai kin tuna min kila zan tuna don ni ban iya kawo komai a yanzu.
Malam ka ba kan ka lafiya gidan kane dai bazan koma cikin shi ba nagaji da zama da mutanen dake son ganin baya na akoda yaushe.
Suwaye ke son ganin bayan naki nace wanda suka zugoka daddy kazo idon ka a rufe kana son ci min mutunci don an zuga ka.
Ni ban damu da kowacen su ba duk su uku din amma su duk abinda zasuci min dun duniya ta shine gurin su a kullun.
Gida dai ne na bar maku abinku sai a barni na zauna lafiya please ba kare bin damo kuma.
Yau nine karan kuma, Rahama ko wa ?
Ni ba zan taba muzantaka ba don nasan darajan ka a gare ni kuma ko banza uban diya na kake yanzu don haka kada Allah ya kawo ranan da zan aibanta ka a gaban wani hausace ta kumshi haka nai maka.
Yai shiru yana kallo na amma sai nai kamar ban ma san yana tsaye a wurin ba yaja kafan shi ya fita daga dakin ba tare da yai magana ba ko may yasa oho ?
Acan falo naji muryan shi suna magana da mama ya dan dauki lokaci a wurinta kafin ya tafi

********* ********* *********
Nasan zai iya dawowa washe gari don haka tunda safe na shirya muka bar garin zuwa kauyen mu ni da yaran.
Mama na fadin tun yau zaku tafi nazaci ai sai anyi uku zaku wuce can din nace bari na tafi yau mama don wurin aiki sun fara nema na.
Tace to Rahama duk dai abinda zakiyi ki sa tsoron Allah a gaba ki sani auren ki yafi maki komai mutunci a duniya.
Ni dai ban ga wani abin assha a agareki ba ko wanan karramawan dz kikayi na zuwa gurina ki sauka da yaran duk yawan fadin garin nan yai min dadi sosai wallahi .
Yanzu ni abinda nake so dake shine ki janye wanan fushin da kikeyi ki koma dakin ki ki zauna yafi daraja da kima.
Murmushi nayi kawai nace mama da adaiyi hakkuri don hakan shine sauki a gare mu ni dashi mama yaya zan zauna da mutumin da kullun baida ra, ayin kasa sai wanda aka sashi yaiwa mutum may nai wa daddy wanda zai dinga juyani haka akan matan shi.
Tace ya fada min komai amma din Allah kiyi hakkuri ki koma dakin ki nace mama ko zan koma da daddy ba zan zauna a gidan nan ba idan har inda muke bai mai ba yana iya canza muna wuri amma ba nan din ba kan na gama zama da Hindatu kuma.
Tace umm, umm Rahama hakkuri baibar komai ba a duniya kiyi hakkuri dai a sasanta a tsakanin ku nai dariya na gyara gyalen jikina mukai mata sallama na tafi.
Ana sallah muka shiga gida don bamu fito da wuri ba banzo da niyar komawa ba a ranan dama shiyasa Nasir bai biyo mu ba.
Bayan tafiyan mu daddy yazo gidan da Bashir sai samu yayi mun tafi yai mamaki duk da ranshi ya baci amma sai mama ke fada mai yadda mukayi da ita kafin na tafi.
Bashir ne ya iya magana yace wanan kuma sabon zance ne ita kanta ta sani kamar itace idon gidan nan yanzu kuma tace bazata dawo ciki ba ke nan sun zama masu gida daban daban ke nan.
Gaskiya barin Rahama a main house matsala ne don yanzu haka dan barin da tayi din nan mutum bai zuwa ya sha ruwa a gidan nan.
Shi dai daddy bai iya magana ba don shiru yayi kawai abin shi abin ya daure may kai ya rasa may nake nufi ne dashi.
Sun dauki lokaci da ita suna magana sai fada yake kwasa akan ba zai amince da hakan dana zo dashi ba din.
A can gida ma bayan na huta ne maigari ya shigo muka kebe dashi da Inna ta yake min gaisuwan Abba din da kuma tambayana halin da muke ciki ya kuma roke ni da karna baye masu komai don a san mafita ga zancen.
Ban boye masu ba duk yadda mukayi na fada masu komai har abubuwan da ake min a baya ina shanyewa duk na labarta masu komai.
Yace yanzu shu hakkuri zai kara bani amma za, a dakanci zuwan daddy din aji may ya yanke akan bukata na din.
Matan daddy sun samu labarin dawowa na kasan nan itama hindatu ta shiga nata kalar haukan ba hinduba har da Raliya tayi irin nata take cewa dashi.
Ashe yar gwal ta shigo kasan shiyasa naga ka wani birkicewa mutane dan kwana biyun nan haka yai mata wani kallon shekeke yace wace yar gwal kuma ?
Tace matarka mana Rahama tunda ita gani take tafi kowa a wurin ka yace ashe ke baki sani ba tafi kowa din gani kike kamar ita ke ganin hakan ni nasan tafi kowa din ai shiyasa kikaga na birkice ai din.
Nan ta shiga surfa bala,i inda take shiga ba nan take fita ba yai shiru ya kyale ta yagama shirin sa ya fita baiko tsaya karyawa ba shine suka fita zuwa gidan mama da bashir din.
Kwanana biyu a gida ina shirin wucewa ne daddy ya yazo garin nan suka samu wuri da maigari aka kira mahaifina yazo kan zancen namu.
Duk abindana fadi maigari bai rage mashi komai ba sai ya dukar dakai yace a yi hakkuri amma kowa yasan matsalan mata indan sun fi daya a gida sai hakkuri.
Ita Rahama ne bata ganewa nifa nasan abinda nakeyi ba wai ban sani bane komai da nakeyi ina yi ne don zaman lafiyan ta hakan ma da nake duk gani suke ai bayan ta nake ko yaushe.
Sannan maganan canza gida ba zan sake mata gida ba anan dai zata zauna inda muke illa iyaka dan gyaran da za, ai mata kawai shine .
Yanzu ai tunda tana gari bari a kirata taji da kunnuwan ta sai ayita a kare anan ta koma dakin ta idan kun shirya din tsakanin ku.
Ina saye da dogon hijjab dina na shigo da sallama a zauren na samu wuri na zauna tare da gaida mahaifina da kwana.
Yace Rahama ai ina gida ina jiran zuwan ki sai ga sako kuma maigari ya turo nazo mijin ki yazo mun zauna dashi babanki maigari ya mashi bayanin komai kamar yadda kukai magana dashi.
Sai dai gaskiya akan canza wurin zama yace bai amince da hakan ba yanzu dole inda kike din zaki koma sai dan gyaran da za ai maki.
Nai murmushi nace baba nifa dama don ku ne zan koma gidan daddy amma ba don wani abu ba can don nasan in na koma ma halin ba dainawa za, ayi ba mai laifi daban wanda akewa fada daban.
Rahama yace yana gyara zaman shi ban so kimun wanan kaken ba haka don kina da wani manufa a ranki dani.
Nace ni banda manufar komai a kan ka zama dai ne idan ba za a canza min wuri ba sai a hakkura kawai.
Yace wanan kuma dama shine gurin ki kadai ki yunanen don na rabu dake ko bazan iya rayuwa ba ko wani abu
Nace ni awa da zan hanaka rayuwa dama ai ba tare dani kake ba da kake rayuwan ka don haka ko yanzu kuma da bamu tare ba wanda ya hana wani jin dadin duniya sai ma ni da aka tauye kawai.
Kai haba ya isa haka mana sulhu fa muka zo ba batawa ba bashir yace Rahama don Allah kiyi hakkuri abi wanan maganan a tsanake.
Yanzu dai kinji yace bai aminta da zancen raba gida ba don haka ina son kiyi hakkuri da wanan maganan.
Nace Bashir ita wacce ya raba damu din ai bata fimu ba ban damay shi bane da da nima ya yarda danawa bukatan
Ita da ta damay shi ai ya fifita mata gida ta zauna ita kadai babu tsangwaman yara ko namu gare ta.
Yai dan murmyshin yake don jin abinda nace nace aidole kai min dariya tunda na zama abin dariya gareka yanzu don banda wani sauran moriya a gun ka.
To bazan iya ba ni ma don babu wacce ta fini balle a dai rabu kowq ya huta shi ke nan ba mai matsawa wani kuma a zauna lafiya yara dai ne zaka iya wucewa da abinka idan ka so hakan.
Rahama wai kanki daya kuwa kike wanan magana haka a gaban mu inji mahaifina.
Nace Abba ni wallahi mudin ba hada mu za, ayi ba guri daya ba zan ta ba komawa ba gidan nan na kwanmace na zauna ni kadai har bayan raina.
Subbahallahi may yasa kikai saurin rantsuwa ne wai inji Bashir nace wallahi iyakar gaskiya na na fada maku in har yace ba zai canza min gida ba to sai dai ya hade mu guri daya duk mu hudun a zauna tare ko kuma ya sauwaka min kawai .
Kai ban si ki rantse ba dai adai bi zancen a sannu ko nace ni banda wani magana bayan wanan shike da igiyar aure a kan shi zabi ya rage nashi yanzu.
Duk shiru sukayi yadda na zare ban jin kunya kamar ba Rahaman da suka sani ba a baya can shiru shiru dani yanzu girma yazo min na kuma kara wayewa idona ya bude.
Shiko daddy haushin iyayyena yake ji a ran shi don yaso ne su fatatake ni na koma kai tsaye bai san na wuce wanan bz agun su ina da daraja da kima sosai sa kwarjini ga idanuwan su kuma dole su duba min abinda zai fitar dani.
Nace ni tunda bai yarda ba abari na wuce don gobe zan koma Abuja zan fara shiga aiki ranan monday sai dai zan so na san matsayi a gun shi don ban son ina yawo da hakiin aure a kaina.
Haba Rahama ki daina wanan kalamin bai dace dake ba gaskiya iji bashir sai baba na yace Rahama indai har ni na haife ki to ina son kibi mijin ki ki koma dakin ki ki zauna daga yau.
Aiko sai na saka masu kuka nace baba dama baku so na shiyasa baku damu da damuwa na ba ni wallahi da in koma haka ba wani kwakwaran magana daga gare shi gara na mutu kowa ma ya huta.
Salati suka saka namike na shige ciki na barsu nan nan dai suka taran mashi akan ya barni na zauna inda nake amma yace shi bai amince da hakan ba sam.
Yafi son ya hada kan iyalin shi a wuri daya yafi mai suna ciki na barsu na wuce abina ban tsaya ba kowa yai mamakin wanan canzawan nawa niko inayi ne da gangan don samun sauki a kaina.
Nayi hakane don mu zauna wuri daya da ita Raliyan dake suraitai a kaina don ta raina kan ta don nasan zaman su wuri daya da hindatu ba karamin kwasa za, ayi ba tunda bata rike girman ta ba gareni.
Abune mawuyaci na sani ya yarda na koma wani wuri da zama dama don yafi son ya zauna hade da kowa ban san yaya tayi taci kan shi har ya raba muna gida ba da ita tun farko.
Suna hanya ne bashir yace dashi ya kamata kai nazarin maganan yarinyar nan don idan bakayi da gaske ba naga alaman Rahama sai ta kubce maka.
Yace na sani Bashir nasan may wanan yarinyar take nufi dani yanzu tana ganin ta zama abinda burin ta ke son zama shine yanzu zata guje ni.
Bashir yace sam bakai tunane ba kuwa don har gobe matarka na son ka kawai da abinda kukai mata ne kaida matan ka har taji kimar ka ya zube a gareta.
Ya juyo yace kimata ya zube fa kace a wurinta yace kwarai kuwa ba wurinta ba har a wurin iyayyen ta dani ma kaina da muke magana dakai a yanzu din.
Haba haba mutumi da girman ka da kimar ka harka bari mace ta baka shawara kuma ka yarda ka hau ba a karatu da aiki ita takeyi ?
Tana son ka ta kasa sa zaman lafiya a gidan ka kamar yadda ita Rahaman tai ta hakkuri da komai tana shanyewa yanzu dubi fa yaran ka bazakace ba itace ta haife su ba fa.
Amma kana ganin kaf din su akwai wacce zata iya rike maka yaro ko daya ne idan ba ita din ba.
Iska ta furzo daga bakin shi tare da numfasawa yace abinda nake duba ke nan yanzu idan har rabuwan zamuyi yaya zanyi da yaran nan nata da na marigayi din dake wurin ta ?
Don dai kasan bazan bar mata su ba a wurin ta yace kagani sai yace ina mamaki na gane tauein ran mahaifiyar ra ta kwaso ke nan data barsu a gun mahaifin su taje tai wani aure daban shine itama yanzu zatai koyi dashi ke nan.
A, a a fa kada ka kawo wanan tunanen kaidai kaiwa kan ka shawaran abinda zai fisheka kawai don samun mafita idan ita Raliyan son ka take tsakani da Allah may zai sa bazata dawo cikin iyalin naka ta zauna ba ?
Kai bashir kaima kasan zamu kwasa da ita kan hakan sai bashir din yace to kuwa a nan zaka gane gaskiyan Rahama din .
Yace zan gwada in gani amma dole sai anyi gyara ko kuma na samu wani wajen maigirma da zai wadace mu yace da yafi ma don haka ni zan shigo Abuja naga Rahama muyi magana na tsanaki da ita da yardan ubangiji.


ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE DON BA A YAFE BA ONLINE NOVEL NE, , ,
90
Tunda nai sallama dasu mama na shiga gidan su daddy don n yi sallama dasu nan hajiyan shi ta tsure ni tana min fada sai da ta gama ta tashi ta shiga sai ga Amira ta dan matso kusa dani ta make muryan ta tana fadin.
Mummy zan biki mu koma Abuja don Allah na gaji da zama nan hajiya fada gare ta don Allah mummy kice zaki tafi dani Abuja don Allah sai ga hajiyan ta fito da leda a hannun ta.
Nace hajiya dama nazo da magana ne don Allah Amira nake son a ra min zan je su zana wani jerabawa ne a can bazata dade ba zata dawo.
Hajiyan tace dani anya Rahama zaki iya da wanan miskilan yarinyar Amira da kike gani bata da mutunci wallahi nace hajiya ba damuwa bama wani dadewa zatayi ba ai zata dawo nan.
Tace shi uban ya sani ne nace eh munyi magana dashi dama yasan da zancen tace to ai shike nan ni dama ai ba wani abu take min ba anan din banda sani magana.
Nan dai ta ce ta hado kayan ta mu tafi da saurin ta ta mike ta shiga hada kayan ta sai gata da katon akwatin ta tafito dashi.
Hajiyan tace a, a Amira keda ba dadewa zakiyi ba shine zaki kwashi kaya haka da yawa nace ina ruwan Amira ai ra dawo dasu in bata saka duka ba.
Mun bar gidan ke nan mun dauki hanya daddy ya shigo gidan su yace ina Amira bayan sun gaisa sai hajiyan nashi tace , a, a ita Rahama ba tace kasan da tafiyan su ba ta dauki abinta ta wuce da ita ai, wai akwai jerabawa da zasu zana a can ita da yan uwan ta.
Yace kai kai wai may Rahama ta dauke ni ne yanzu please yanzu zan buga mata waya ta dawo min da ya ta ban son iskanci da rainin wayo.
Kai ban son shashanci inji Alhajin shi ita Rahaman bakuwar kane ko kuwa cutawa yarinyar zatayi a can dama a gun wa take ba wurin ta shakiyanci irin nata yasa ta bar gunta.
Yanzu kuma tun ganin su da tayi sun dawo hankalinta yai mugun dagawa kuma ya koma akan su ganin yadda suka sauya gaba dayan su.
Kabar mata yarinyar nan a wurinta tun da kai ka kasa cika alkawari ita ta daure ta dauki amanan da aka bar mata a hannun ta kai da baka iya sai kaje can kaji da gaiyyan matan ka suna juya ka yadda suke so.
Duk ka sake ka rabu da yarinyar nan Rahama ko bayan raina ne wallahi ban yafe maka ba kaji na fada maka.
Take yaji gaban shi yai mugun faduwa
Showing 366001 words to 369000 words out of 456145 words
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22Chapter 23Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32Chapter 33Chapter 34Chapter 35Chapter 36Chapter 37Chapter 38Chapter 39Chapter 40Chapter 41Chapter 42Chapter 43Chapter 44Chapter 45Chapter 46Chapter 47Chapter 48Chapter 49Chapter 50Chapter 51Chapter 52Chapter 53Chapter 54Chapter 55Chapter 56Chapter 57Chapter 58Chapter 59Chapter 60Chapter 61Chapter 62Chapter 63Chapter 64Chapter 65Chapter 66Chapter 67Chapter 68Chapter 69Chapter 70Chapter 71Chapter 72Chapter 73Chapter 74Chapter 75Chapter 76Chapter 77Chapter 78Chapter 79Chapter 80Chapter 81Chapter 82Chapter 83Chapter 84Chapter 85Chapter 86Chapter 87Chapter 88Chapter 89Chapter 90Chapter 91Chapter 92Chapter 93Chapter 94Chapter 95Chapter 96Chapter 97Chapter 98Chapter 99Chapter 100Chapter 101Chapter 102Chapter 103Chapter 104Chapter 105Chapter 106Chapter 107Chapter 108Chapter 109Chapter 110Chapter 111Chapter 112Chapter 113Chapter 114Chapter 115Chapter 116Chapter 117Chapter 118Chapter 119Chapter 120Chapter 121Chapter 122Chapter 123 Chapter 124Chapter 125Chapter 126Chapter 127Chapter 128Chapter 129Chapter 130Chapter 131Chapter 132Chapter 133Chapter 134Chapter 135Chapter 136Chapter 137Chapter 138Chapter 139Chapter 140Chapter 141Chapter 142Chapter 143Chapter 144Chapter 145Chapter 146Chapter 147Chapter 148Chapter 149Chapter 150Chapter 151Chapter 152Chapter 153