Allah yasa su gane gaskiya su daina a koma daidai a gidan don ni banga abinda akewa wanan fitinan ba haka.
Jan jikin shi yayi ya jingina da kujera tare da zaman dirsha a kasa zo nan Rama yace na dago kai na kalleshi.
Yadda yace hakan nayi na dan yunkuro zuwa inda yake din yace naji kince baki san may yasa suke haka ba ko ?
Ina a durkushe na gyada mashi kai alaman eh yake cewa dani har yanzu Rahama baki fara so na bane a ranki balle ki faran kishin nawa ke ma ?
Kunya maganan shi ya bani sai na koma na zauna zama irin na mai shin cin abinci tare da dafe dayan hannuna a kasa daga gefena.
Yace tell me har yanzu da alaman ban samu gurbi ko kadan ba daga zuciyar ki wanda ke ma zai sa kiji abinda suke jin din don ance kishi a jinin ku mata take ?
Da zan iya fada danace dashi nafi kowa jin zafin kinshin shi a dan zaman kwana kadan da nayi dashi ya lasa min zuman da ban san akwai shi ba aduniya haka ?
Amma na daure na cije bani fatan ko rana daya na nuna wanan irin haukan kishin haka.
Bazaki bani amsa ba ina tambayan ki shiru nayi sai can nace dashi na hada ma ruwan wanka ko .
Yace kin matsu mu kwanta ke nan ko kunya da mamakin yadda in muna tare mu biyu yake sake jiki yana min magana irin haka.
Yace dauko min cajin da kika saka tunda baki bari na kalli news sai mu shige ko ?
Nace bari dai na kwashe kayan nan na shiga dasu ciki na dawo ban wa yara adduan kwanciya ba kuma ban sallami anty ba.
Yace you can go amma kada ki shanyani anan please kan yaran nan naki masu shagwaba.
Na danyi murmushi kawai na mike na fara tattara kayan na fice zuwa cikin gida ban dawo ba sai da nakai ga yin wanka na gyara jikina tsab naiwa anty sallama na koma part din shi.
Sai dai ina shiga naji muryan shi sama sama kamar yana fada yana cewa ban son rashin hankali may zai kawo ki nan wanan lokacin.
Ki fice min daga falo bani son fitina.
Dana fita da ita ina ranan girkin tane na fita da ita din ko kece da girki da zaki zo min da maganan banza ai da kika isa sai kije ki tambaye ta may nasayo mata a ledan da kikaga na shiga dashi.
Daidai lokacin na shigo falon don a zatona ma da waya yake magana amma sai naga Hindatu a zaune tana cika tana batsewa.
Kamshin turarena yasa ta dago kai tana kallon na ban yi magana ba na kama hanyan bedroom kawai na shige na barsu nan.
Bai jima ba naga ya shigo dakin wanka ta shiga ya fito ya tsaya ya gyara ko ina najikin shi ya hawo gado ya kwanta.
Rugumoni yayi zuwa jikin shi yana sauke numfashi tausayin shi naji ya kamani na lumshe idanuwa na ina tunane.
Nasan cewa tunda har ya iya bude baki ya furta min damuwan shi yau abin yakai mai inda yakai don na fahinci hakkuri yakeyi kawai.
Barci mu kayi ranan ba wani abinda ya wakana a tsakanin mu sai dai ina rungumay a jikin shi har safe .
Da safe zan shiga school don haka ban bata lokaci ba na abinda zanyi a gagauce na shirya nafito cikin shirina na bayan nayi sallama da duk wanda ya dace na sallama na bargidan.
Sai daya tashi ya shirya yazo part din anty nan ya dab zauna tare suke hira da ita tace dashi jita sai hajita ta ganka da amaryan ka ko ?
Kamar yadda na bata fuska haka ya bata nashi yace da ita eh sai dai ai kin san halin hajiya.
Ban taba tsanmanin zata iyawa wanan yarinyar cin fuska haka ba sai gashi tai mata abinda bai dace ba har tana kiranta diyan matsiyata mai farar kafa for god sake.
Subbahanallahi Rama ce kuma mai farar ka mai tayi kuma na farar kafa har yaushe ta shigo gidan ma ?
Yace halin hajiya ne baki sani ba kuma haushin ki akan ta ya koma tunda tace kece kikai hadin.
Amma kuma kaga Rama bata fada min komai ba wallahi.
Asalima dana tambaye ta suna lafiya tace lafiya suke suna gaishe mu ai.
Yace bazata fada ba aiko can ta bani mamaki don bata nuna komai ba har muka dawo dama nai mata magana sai cewa tayi dani ai hajiya uwace a gareta.
Ji yayi anty tace Alhamdullahi Allah mun gode ma ka fara ganin hasashen da nai maka ke nan akan son auren yarinyar nan.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABUIDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE, IDAN KUMA KIN KARANTA DAKE DA ALLAH, , , , , ,
IDAN KIN BIYA KIKA TURAWA WANDA BAI BIYA BA MUN BARKI GA ALLAH SHI ZAI BI MUNA HAKKIN MU A KANKI , , ,
45
Ruwan sama aka tashi dashi agarin tun da asuba ake tsula ruwa ba kakautawa.
Hakan ne ya jawo rashin yawan firan wasu daga gidajen su har da mutanen gidan mu don ranan ko yara basu samu hanyan fita zuwa school ba don ruwan yai yawa ga sanyi.
Sai zuwa goma da rabi na safe aka dan rage yawan ruwan sai dai still ana dan yayafi mai karfi.
Na shirya don dole sai na fita zuwa school din part din anty na shiga wacce yanayin yasa ta dunkulewa a cikin abin rufa.
Na gaida da ita muka amsa take cewa dani fita zakiyi ne haka cikin ruwan nan Rama , ?
Nace anty dole na fita don kin san rashin fitana ba zai hana aiyi muna karatu ba sai dai wanda bai fita ba yai hasara kawai.
Nace ba zan dade ba zan dawo ai har nakai kofa tace kada ki fita baki sallami besty ba fa ko kun gaisa ne dashi da safen nan.
Naja na tsaya tare da ce mata a, a bamu gaisa ba da shi yau.
Jeki ku gaisa dashi, ai yanzu killa yana falo shi ya fito har ga raina ban so haka ba don idan ban da girki bani zuwa part din nashi hakana.
Da sallama na shiga falon suna zaune da Hindatu ta wani dan kwanta da gefen jikin ta a saman jikin shi kamar suna wani maganan arziki ne idan ka gansu.
Jin sallama na yasa shi dago kai daga bin computer din shi dake a hannun shi da yakeyi.
Wani harara Hindatu ta watso min sai da naji yan hajin cikina sun kada min lokaci guda.
Cikin dakewa da gyara natsuwa na nake ce wa ina kwana daddy anty ina kwana ?
Tace malama lafiya kika shigo mina muna hutawa ko jarabar taki kuma ya kai ki kasa hakkuri kijirashi yazo gareki.
Ke kan tir da halin jaraba wallahi irin naki bazan daukar maki wanan rainin ba don ni ba saar ki bace.
Allah ya baki hakkuri anty dama nazo gaida daddy ne na sallamay shi zan tafi school ne yanzu.
Ke dan Allah rufe wa mutane baki jarababban banza kawai mara tunane.
Hindatu zan saba maki yanzu akan wanan haukan naki keda kike shigowa idan tana da girki ashe kin fita jaraba ke nan.
Jaraba kuma ai isa ne a gun miji tayi jaraban sai may tunda har kin fahinci jarababba ce ita.
Ya juya inda nake yake cewa ina ga ai ba a tsayar da ruwan saman ba har yanzu ki bari na sauke ki.
Ka sauke ta ina ranan girkin nawa zakace zaka fita da waban kwailar mai kama da mage.
Ke fice ki bani guri ana mazuru ana shaho ace wai ana fita karatu kullun.
Maganan yai min zafi don haka na kasa danne zuciya na na juya na dan kalleta nai murmushi nace ai ko gara dani.
Don ni har ina da inda na fake ga fita na kowa yasan inda nake zuwa ashe fitan ma da ake fiye da sau goma a wuni mazuru da sha akeyi sai yau na gane hakan.
Dama abinda kakeyi shi kake tsamanin kowa ma haka yake ni banda lokacin haukan ki don ban dauke ki cikin masu hankali ba tun farko.
Daga haka na juta na fara tako takalmina yana ba da sauti kwas kwas kwas na fice daga falon ko ba komai dai yau na bata amsa ai.
Ina jinta tana hargowa wai fada ban tsaya sauraren ta ba nabar falon na mike hanyan fita zuwa inda kowa ke aje motan shi a gidan.
Ina kokarin bude mota naji muryan shi a bayana yana cewa ba nace ki bari na sauke ki ba.
Tsayawa nayi har ya karso ya jawo motar da zai fita dashi muka shiga tana tsaye daga coridor tana ta zabga masifa wai ita anci mata girkin ta.
Tana kallo ya ja mota muka bar gidan muna fita daga haraban gidan mun dan yi nisa naji wani hawayen bakin ciki ya silalo min a fuskana.
Jin sheshekar kuka na yasa yadan juyo ya kalleni baiyi magana ba sai mika min hankicin da yayi.
Ban karba ba naji yayi murmushi kawai yaci gaba da tukin shi har muka kai school din nai godiya zan fita yace karfe nawa zan dawo daukan ki ?
Nace hudu a takaice na fice daga motar banji ya tayar da motar ba ni ma ban juya ba na shige ciki don ruwan da ya dawo da dan karfi.
Ranan haka na wuni a cikin bacin rai har four yayi sai hamza driver ne yazo daukana yace maigida ne ya turo shi ya dauke ni.
Na dawo na fara shiga gurin anty na gaida ita ban tsaya ba na wuce part dina ina cire kaya gajiye ta shigo take cewa dani ashe kin dawo ?
Na dan kakaro murmushi a fuskana nace nadawo na duba kitchen baki ciki.
Tace abinci fa bari na kawo maki nan nace a, a dakin barshi idan nai sallah zan fito sai naci.
Har ta juya kamar zata fita sai kuma taja ta tsaya tace Rahama kiyi hakkuri akan sherin matan gidan nan dama hakan shine kishi ai.
Dazu bayan fitan ki anyi fada sosai kaca kaca da maigidan da hindatu har sai da mahaifanta suka zo gidan nan.
Murmushin takaici na kakaro nace da ita na gode kawai a raina kuma nace ashe shiyasa daddy bai zo daukana ba da kan shi ke nan ?
Bayan na fito na shiga gurin anty tana zaune falo na gaishe ta na samu kujera na zauna na dan daga kaina sama ina tunane.
Muryan gajiye naji tana cewa ga abincin ki Rahama na karba tare saukowa kasa na zauna saman carpet din tsakiyan falon.
Cibi biyu naci sai naji abincin ya fita min a rai ina ta dan juya spoon din na kasa cin abincin alaman ina a cikin damuwa.
Rama naji muryan anty na kirana tace kada halin matan nan ya tayar maki da hankali a gidan nan haka halinsu yake ko yaushe.
Hawaye ne masu zafi suka fara zubo min shar a idanuwana tace nasan zakici gaba da cin karo da abubuwan bacin rai masu zafi ko yaushe a cikin wanan gidan.
Amma idan kin fahinci halin kowa zaki iya zama da su da halinsu don su a kullun burin su ne su ga rayuka ya baci kawai.
Basu kaunar suga besty yana hurda da wata mace ko da a tsakanin su ne bayan su.
Naji abinda ya faru dake da kuka je gaida su hajiya wanda sam banji dadin jin hakan ba.
Sai dai na yaba da kaifin hankalin ki yadda kika nuna a gaban ita hajiyan da kuma shi kan shi maigidan.
Hakan da kikayi ya nuna cewa nan gaba ma zaki iya hadiyan duk wani fitinan da zai bullo a gidan nan ko a gare mu.
Rama sanin kanki ne ban da wani buri a duniya da ya wuce naga yaran nan, sun samu ingantattacen rayuwa da kulawa yadda ya dace wanda Alhamdullahi zan iya cewa mun samu ko yanzu.
Don ni dai banda ta inda zan raina maki akan irin kulawan da kike bawa yaran nan wanda tun yanzun ma sun dsuke ki tankar ni a gare su.
Aikin dake gaban ki shine na besty wanda ya kamata ki kara kaimai gurin kara fahintar halin da yake ciki a gida da waje wanda yana da matukar bukatar taimako da surport din mace a bangaren shi.
Rama zaki iya komai idan har kin saka hakan a ranki nasan cewa a yanzu nice ke maki shamaki akan komai da kikeyi don kina kawaici a kan hakan nasani.
Ina mai rokon ki da ki sake jikin ki kada kiyi amfani dani ki cutawa kan ki ki kwato hakkin ki ga kowa dake son nakasa ki a gidan nan acikin hikima da basira basai kinyi fada a fili ba.
Akwai hikimomi na mata kala daban daban wanda zaki iya don kinga bazan tsaya akan ko yaushe nace sai na tsaya a bayan ki ina fada kinga sai a dauka nice nake saka ki yin wani abin.
Yau ayi va dadi a gidan nan tsakanin besty da hindatu har sai da mahaifan ta suka zo wai akan may zai fita dake bayan ita ce da girki.
Don haka ina son ki natsu ki kiyaye duk abinda zai kawo shiga hakkin wani don ki samu bakin magana idan hakan ya taso a kan ki.
Sai lokacin na daure nai magana ina cewa anty ban san may na tsarewa wanan matar ba nan dai na fada mata irin abubuwan da take yawan yi min tun shigowa na cikin su.
Rama nasan komai bani dai magana ne kawai don naga kina da fahinta irin wanda ake son mace na gari ta dinga yi.
Ba ko yaushe zaka tsaya kana maida martani ba akan abinda ake maka sai idan ka tara rana guda ka tsiyaye shi yafi zafi ga kishi.
Yadda kika rufe ido kika bata amsa daya dayace da maganar data fada maki magana daya yasa ta haukacewa bayan itace ta fara fada maki shi.
Idan ma tayi ne don neman fitina da son musgunawa yanzu tayiwa kanta ai don taja wa kanta saboda ansaka doka a gidan babu mai fita nan da can bada izinin miji ba kuma.
Kamar yadda suka saba a baya sai dai mace ta kada kai tafita duk inda taga dama babu mai magana bayan sun saba da hakan .
Gashi yanzu an saka dokan tabaci a gidan kinga sun jawa kan su ba wani ba don sune masu fita ba wani ba.
Kiyi hakkuri don Allah kinji Rama kada ki sawa kanki damuwa akan komai a gidan nan.
Ki sake jikin ki kamar kowa a gidan kiyi yadda ko wace mace keyi a matsayinta na mata a gurin mai gida bawai ina zuga ki bane kiyi rashin mutunci ga mutane a,a ki dai nuna kema fa mace ce shine zai kwato ki ga wa yan nan don ba fasawa zasu yi ba don halinsu ne.
Amma idan kin faso kema zaki samu saukin cin fuska irin nasu zasu rage maki shakiyancin su sosai zasu san kin iya kema.
Nai ajiyan zuciya don na gamsu da bayanin ta kuma na gane may take nufi da maganan ta.
Nan dai naita tunane ina dan juya spoon din dake hannuna a cikin plate din a hankali naji abincin ya fita raina.
Hiran mama Altine ta dauko min shi ya dan kawar min da damuwan da nake ciki.
Nake fada mata naso Fatima yar wurin maigari ta danzo min zama na kwana biyu sai dai ban fada mata bane kawai.
Tace ai hakan yana da kyau Rama don zama da naka akwai dadi sosai wallahi gashi yanzu naga wata yar kunya da shakku ya shiga tsakani na dake sosai.
Na dago nace kai anty ni kuma tace ke mana Rama in ba haka may zai sa ki boye min abinda hajiya tai maki da wanda matan gidan nan ke maki yanzu.
Nace ba hakana bane anty bana son kina fama da lalurar ki na kuma kara maki wani akai.
Nidai da Allah ya nufa da fanin hakan sai naji dashi tace haba Rama, ya kamata fa ki gode min gaki ga daddy ki lafiya lau bako yadda na tsanmanin kiyi ba ?
Kunya ya kamani sosai na dukar da kaina a jikina nace hai anty idan kuma banyi bakice ban maki mutunci ba fa ?
Tace cikin dariya to aini dai bance komai ba da kina gida kikaga yadda yau dadi ya haukace da fada gidan nan da kin sha mamaki wallahi.
Nace anty ba dai a kaina ba kan sai dai in wani abin can dama ya hada su.
Wanan matar tashi da yake ji da ita ko fa tana abu a gaban shi daddy baya daukan mataki sai dai yai kamar baiji ba ko bai gani ba.
Tace lalai da sauran ki Rama Allah ya taimakeki, baki da rawan kai dakin gane kuren ki ai.
Baki san yadda take taka masu
Showing 192001 words to 195000 words out of 456145 words
Jan jikin shi yayi ya jingina da kujera tare da zaman dirsha a kasa zo nan Rama yace na dago kai na kalleshi.
Yadda yace hakan nayi na dan yunkuro zuwa inda yake din yace naji kince baki san may yasa suke haka ba ko ?
Ina a durkushe na gyada mashi kai alaman eh yake cewa dani har yanzu Rahama baki fara so na bane a ranki balle ki faran kishin nawa ke ma ?
Kunya maganan shi ya bani sai na koma na zauna zama irin na mai shin cin abinci tare da dafe dayan hannuna a kasa daga gefena.
Yace tell me har yanzu da alaman ban samu gurbi ko kadan ba daga zuciyar ki wanda ke ma zai sa kiji abinda suke jin din don ance kishi a jinin ku mata take ?
Da zan iya fada danace dashi nafi kowa jin zafin kinshin shi a dan zaman kwana kadan da nayi dashi ya lasa min zuman da ban san akwai shi ba aduniya haka ?
Amma na daure na cije bani fatan ko rana daya na nuna wanan irin haukan kishin haka.
Bazaki bani amsa ba ina tambayan ki shiru nayi sai can nace dashi na hada ma ruwan wanka ko .
Yace kin matsu mu kwanta ke nan ko kunya da mamakin yadda in muna tare mu biyu yake sake jiki yana min magana irin haka.
Yace dauko min cajin da kika saka tunda baki bari na kalli news sai mu shige ko ?
Nace bari dai na kwashe kayan nan na shiga dasu ciki na dawo ban wa yara adduan kwanciya ba kuma ban sallami anty ba.
Yace you can go amma kada ki shanyani anan please kan yaran nan naki masu shagwaba.
Na danyi murmushi kawai na mike na fara tattara kayan na fice zuwa cikin gida ban dawo ba sai da nakai ga yin wanka na gyara jikina tsab naiwa anty sallama na koma part din shi.
Sai dai ina shiga naji muryan shi sama sama kamar yana fada yana cewa ban son rashin hankali may zai kawo ki nan wanan lokacin.
Ki fice min daga falo bani son fitina.
Dana fita da ita ina ranan girkin tane na fita da ita din ko kece da girki da zaki zo min da maganan banza ai da kika isa sai kije ki tambaye ta may nasayo mata a ledan da kikaga na shiga dashi.
Daidai lokacin na shigo falon don a zatona ma da waya yake magana amma sai naga Hindatu a zaune tana cika tana batsewa.
Kamshin turarena yasa ta dago kai tana kallon na ban yi magana ba na kama hanyan bedroom kawai na shige na barsu nan.
Bai jima ba naga ya shigo dakin wanka ta shiga ya fito ya tsaya ya gyara ko ina najikin shi ya hawo gado ya kwanta.
Rugumoni yayi zuwa jikin shi yana sauke numfashi tausayin shi naji ya kamani na lumshe idanuwa na ina tunane.
Nasan cewa tunda har ya iya bude baki ya furta min damuwan shi yau abin yakai mai inda yakai don na fahinci hakkuri yakeyi kawai.
Barci mu kayi ranan ba wani abinda ya wakana a tsakanin mu sai dai ina rungumay a jikin shi har safe .
Da safe zan shiga school don haka ban bata lokaci ba na abinda zanyi a gagauce na shirya nafito cikin shirina na bayan nayi sallama da duk wanda ya dace na sallama na bargidan.
Sai daya tashi ya shirya yazo part din anty nan ya dab zauna tare suke hira da ita tace dashi jita sai hajita ta ganka da amaryan ka ko ?
Kamar yadda na bata fuska haka ya bata nashi yace da ita eh sai dai ai kin san halin hajiya.
Ban taba tsanmanin zata iyawa wanan yarinyar cin fuska haka ba sai gashi tai mata abinda bai dace ba har tana kiranta diyan matsiyata mai farar kafa for god sake.
Subbahanallahi Rama ce kuma mai farar ka mai tayi kuma na farar kafa har yaushe ta shigo gidan ma ?
Yace halin hajiya ne baki sani ba kuma haushin ki akan ta ya koma tunda tace kece kikai hadin.
Amma kuma kaga Rama bata fada min komai ba wallahi.
Asalima dana tambaye ta suna lafiya tace lafiya suke suna gaishe mu ai.
Yace bazata fada ba aiko can ta bani mamaki don bata nuna komai ba har muka dawo dama nai mata magana sai cewa tayi dani ai hajiya uwace a gareta.
Ji yayi anty tace Alhamdullahi Allah mun gode ma ka fara ganin hasashen da nai maka ke nan akan son auren yarinyar nan.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABUIDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE, IDAN KUMA KIN KARANTA DAKE DA ALLAH, , , , , ,
IDAN KIN BIYA KIKA TURAWA WANDA BAI BIYA BA MUN BARKI GA ALLAH SHI ZAI BI MUNA HAKKIN MU A KANKI , , ,
45
Ruwan sama aka tashi dashi agarin tun da asuba ake tsula ruwa ba kakautawa.
Hakan ne ya jawo rashin yawan firan wasu daga gidajen su har da mutanen gidan mu don ranan ko yara basu samu hanyan fita zuwa school ba don ruwan yai yawa ga sanyi.
Sai zuwa goma da rabi na safe aka dan rage yawan ruwan sai dai still ana dan yayafi mai karfi.
Na shirya don dole sai na fita zuwa school din part din anty na shiga wacce yanayin yasa ta dunkulewa a cikin abin rufa.
Na gaida da ita muka amsa take cewa dani fita zakiyi ne haka cikin ruwan nan Rama , ?
Nace anty dole na fita don kin san rashin fitana ba zai hana aiyi muna karatu ba sai dai wanda bai fita ba yai hasara kawai.
Nace ba zan dade ba zan dawo ai har nakai kofa tace kada ki fita baki sallami besty ba fa ko kun gaisa ne dashi da safen nan.
Naja na tsaya tare da ce mata a, a bamu gaisa ba da shi yau.
Jeki ku gaisa dashi, ai yanzu killa yana falo shi ya fito har ga raina ban so haka ba don idan ban da girki bani zuwa part din nashi hakana.
Da sallama na shiga falon suna zaune da Hindatu ta wani dan kwanta da gefen jikin ta a saman jikin shi kamar suna wani maganan arziki ne idan ka gansu.
Jin sallama na yasa shi dago kai daga bin computer din shi dake a hannun shi da yakeyi.
Wani harara Hindatu ta watso min sai da naji yan hajin cikina sun kada min lokaci guda.
Cikin dakewa da gyara natsuwa na nake ce wa ina kwana daddy anty ina kwana ?
Tace malama lafiya kika shigo mina muna hutawa ko jarabar taki kuma ya kai ki kasa hakkuri kijirashi yazo gareki.
Ke kan tir da halin jaraba wallahi irin naki bazan daukar maki wanan rainin ba don ni ba saar ki bace.
Allah ya baki hakkuri anty dama nazo gaida daddy ne na sallamay shi zan tafi school ne yanzu.
Ke dan Allah rufe wa mutane baki jarababban banza kawai mara tunane.
Hindatu zan saba maki yanzu akan wanan haukan naki keda kike shigowa idan tana da girki ashe kin fita jaraba ke nan.
Jaraba kuma ai isa ne a gun miji tayi jaraban sai may tunda har kin fahinci jarababba ce ita.
Ya juya inda nake yake cewa ina ga ai ba a tsayar da ruwan saman ba har yanzu ki bari na sauke ki.
Ka sauke ta ina ranan girkin nawa zakace zaka fita da waban kwailar mai kama da mage.
Ke fice ki bani guri ana mazuru ana shaho ace wai ana fita karatu kullun.
Maganan yai min zafi don haka na kasa danne zuciya na na juya na dan kalleta nai murmushi nace ai ko gara dani.
Don ni har ina da inda na fake ga fita na kowa yasan inda nake zuwa ashe fitan ma da ake fiye da sau goma a wuni mazuru da sha akeyi sai yau na gane hakan.
Dama abinda kakeyi shi kake tsamanin kowa ma haka yake ni banda lokacin haukan ki don ban dauke ki cikin masu hankali ba tun farko.
Daga haka na juta na fara tako takalmina yana ba da sauti kwas kwas kwas na fice daga falon ko ba komai dai yau na bata amsa ai.
Ina jinta tana hargowa wai fada ban tsaya sauraren ta ba nabar falon na mike hanyan fita zuwa inda kowa ke aje motan shi a gidan.
Ina kokarin bude mota naji muryan shi a bayana yana cewa ba nace ki bari na sauke ki ba.
Tsayawa nayi har ya karso ya jawo motar da zai fita dashi muka shiga tana tsaye daga coridor tana ta zabga masifa wai ita anci mata girkin ta.
Tana kallo ya ja mota muka bar gidan muna fita daga haraban gidan mun dan yi nisa naji wani hawayen bakin ciki ya silalo min a fuskana.
Jin sheshekar kuka na yasa yadan juyo ya kalleni baiyi magana ba sai mika min hankicin da yayi.
Ban karba ba naji yayi murmushi kawai yaci gaba da tukin shi har muka kai school din nai godiya zan fita yace karfe nawa zan dawo daukan ki ?
Nace hudu a takaice na fice daga motar banji ya tayar da motar ba ni ma ban juya ba na shige ciki don ruwan da ya dawo da dan karfi.
Ranan haka na wuni a cikin bacin rai har four yayi sai hamza driver ne yazo daukana yace maigida ne ya turo shi ya dauke ni.
Na dawo na fara shiga gurin anty na gaida ita ban tsaya ba na wuce part dina ina cire kaya gajiye ta shigo take cewa dani ashe kin dawo ?
Na dan kakaro murmushi a fuskana nace nadawo na duba kitchen baki ciki.
Tace abinci fa bari na kawo maki nan nace a, a dakin barshi idan nai sallah zan fito sai naci.
Har ta juya kamar zata fita sai kuma taja ta tsaya tace Rahama kiyi hakkuri akan sherin matan gidan nan dama hakan shine kishi ai.
Dazu bayan fitan ki anyi fada sosai kaca kaca da maigidan da hindatu har sai da mahaifanta suka zo gidan nan.
Murmushin takaici na kakaro nace da ita na gode kawai a raina kuma nace ashe shiyasa daddy bai zo daukana ba da kan shi ke nan ?
Bayan na fito na shiga gurin anty tana zaune falo na gaishe ta na samu kujera na zauna na dan daga kaina sama ina tunane.
Muryan gajiye naji tana cewa ga abincin ki Rahama na karba tare saukowa kasa na zauna saman carpet din tsakiyan falon.
Cibi biyu naci sai naji abincin ya fita min a rai ina ta dan juya spoon din na kasa cin abincin alaman ina a cikin damuwa.
Rama naji muryan anty na kirana tace kada halin matan nan ya tayar maki da hankali a gidan nan haka halinsu yake ko yaushe.
Hawaye ne masu zafi suka fara zubo min shar a idanuwana tace nasan zakici gaba da cin karo da abubuwan bacin rai masu zafi ko yaushe a cikin wanan gidan.
Amma idan kin fahinci halin kowa zaki iya zama da su da halinsu don su a kullun burin su ne su ga rayuka ya baci kawai.
Basu kaunar suga besty yana hurda da wata mace ko da a tsakanin su ne bayan su.
Naji abinda ya faru dake da kuka je gaida su hajiya wanda sam banji dadin jin hakan ba.
Sai dai na yaba da kaifin hankalin ki yadda kika nuna a gaban ita hajiyan da kuma shi kan shi maigidan.
Hakan da kikayi ya nuna cewa nan gaba ma zaki iya hadiyan duk wani fitinan da zai bullo a gidan nan ko a gare mu.
Rama sanin kanki ne ban da wani buri a duniya da ya wuce naga yaran nan, sun samu ingantattacen rayuwa da kulawa yadda ya dace wanda Alhamdullahi zan iya cewa mun samu ko yanzu.
Don ni dai banda ta inda zan raina maki akan irin kulawan da kike bawa yaran nan wanda tun yanzun ma sun dsuke ki tankar ni a gare su.
Aikin dake gaban ki shine na besty wanda ya kamata ki kara kaimai gurin kara fahintar halin da yake ciki a gida da waje wanda yana da matukar bukatar taimako da surport din mace a bangaren shi.
Rama zaki iya komai idan har kin saka hakan a ranki nasan cewa a yanzu nice ke maki shamaki akan komai da kikeyi don kina kawaici a kan hakan nasani.
Ina mai rokon ki da ki sake jikin ki kada kiyi amfani dani ki cutawa kan ki ki kwato hakkin ki ga kowa dake son nakasa ki a gidan nan acikin hikima da basira basai kinyi fada a fili ba.
Akwai hikimomi na mata kala daban daban wanda zaki iya don kinga bazan tsaya akan ko yaushe nace sai na tsaya a bayan ki ina fada kinga sai a dauka nice nake saka ki yin wani abin.
Yau ayi va dadi a gidan nan tsakanin besty da hindatu har sai da mahaifan ta suka zo wai akan may zai fita dake bayan ita ce da girki.
Don haka ina son ki natsu ki kiyaye duk abinda zai kawo shiga hakkin wani don ki samu bakin magana idan hakan ya taso a kan ki.
Sai lokacin na daure nai magana ina cewa anty ban san may na tsarewa wanan matar ba nan dai na fada mata irin abubuwan da take yawan yi min tun shigowa na cikin su.
Rama nasan komai bani dai magana ne kawai don naga kina da fahinta irin wanda ake son mace na gari ta dinga yi.
Ba ko yaushe zaka tsaya kana maida martani ba akan abinda ake maka sai idan ka tara rana guda ka tsiyaye shi yafi zafi ga kishi.
Yadda kika rufe ido kika bata amsa daya dayace da maganar data fada maki magana daya yasa ta haukacewa bayan itace ta fara fada maki shi.
Idan ma tayi ne don neman fitina da son musgunawa yanzu tayiwa kanta ai don taja wa kanta saboda ansaka doka a gidan babu mai fita nan da can bada izinin miji ba kuma.
Kamar yadda suka saba a baya sai dai mace ta kada kai tafita duk inda taga dama babu mai magana bayan sun saba da hakan .
Gashi yanzu an saka dokan tabaci a gidan kinga sun jawa kan su ba wani ba don sune masu fita ba wani ba.
Kiyi hakkuri don Allah kinji Rama kada ki sawa kanki damuwa akan komai a gidan nan.
Ki sake jikin ki kamar kowa a gidan kiyi yadda ko wace mace keyi a matsayinta na mata a gurin mai gida bawai ina zuga ki bane kiyi rashin mutunci ga mutane a,a ki dai nuna kema fa mace ce shine zai kwato ki ga wa yan nan don ba fasawa zasu yi ba don halinsu ne.
Amma idan kin faso kema zaki samu saukin cin fuska irin nasu zasu rage maki shakiyancin su sosai zasu san kin iya kema.
Nai ajiyan zuciya don na gamsu da bayanin ta kuma na gane may take nufi da maganan ta.
Nan dai naita tunane ina dan juya spoon din dake hannuna a cikin plate din a hankali naji abincin ya fita raina.
Hiran mama Altine ta dauko min shi ya dan kawar min da damuwan da nake ciki.
Nake fada mata naso Fatima yar wurin maigari ta danzo min zama na kwana biyu sai dai ban fada mata bane kawai.
Tace ai hakan yana da kyau Rama don zama da naka akwai dadi sosai wallahi gashi yanzu naga wata yar kunya da shakku ya shiga tsakani na dake sosai.
Na dago nace kai anty ni kuma tace ke mana Rama in ba haka may zai sa ki boye min abinda hajiya tai maki da wanda matan gidan nan ke maki yanzu.
Nace ba hakana bane anty bana son kina fama da lalurar ki na kuma kara maki wani akai.
Nidai da Allah ya nufa da fanin hakan sai naji dashi tace haba Rama, ya kamata fa ki gode min gaki ga daddy ki lafiya lau bako yadda na tsanmanin kiyi ba ?
Kunya ya kamani sosai na dukar da kaina a jikina nace hai anty idan kuma banyi bakice ban maki mutunci ba fa ?
Tace cikin dariya to aini dai bance komai ba da kina gida kikaga yadda yau dadi ya haukace da fada gidan nan da kin sha mamaki wallahi.
Nace anty ba dai a kaina ba kan sai dai in wani abin can dama ya hada su.
Wanan matar tashi da yake ji da ita ko fa tana abu a gaban shi daddy baya daukan mataki sai dai yai kamar baiji ba ko bai gani ba.
Tace lalai da sauran ki Rama Allah ya taimakeki, baki da rawan kai dakin gane kuren ki ai.
Baki san yadda take taka masu
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22Chapter 23Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32Chapter 33Chapter 34Chapter 35Chapter 36Chapter 37Chapter 38Chapter 39Chapter 40Chapter 41Chapter 42Chapter 43Chapter 44Chapter 45Chapter 46Chapter 47Chapter 48Chapter 49Chapter 50Chapter 51Chapter 52Chapter 53Chapter 54Chapter 55Chapter 56Chapter 57Chapter 58Chapter 59Chapter 60Chapter 61Chapter 62Chapter 63Chapter 64Chapter 65 Chapter 66Chapter 67Chapter 68Chapter 69Chapter 70Chapter 71Chapter 72Chapter 73Chapter 74Chapter 75Chapter 76Chapter 77Chapter 78Chapter 79Chapter 80Chapter 81Chapter 82Chapter 83Chapter 84Chapter 85Chapter 86Chapter 87Chapter 88Chapter 89Chapter 90Chapter 91Chapter 92Chapter 93Chapter 94Chapter 95Chapter 96Chapter 97Chapter 98Chapter 99Chapter 100Chapter 101Chapter 102Chapter 103Chapter 104Chapter 105Chapter 106Chapter 107Chapter 108Chapter 109Chapter 110Chapter 111Chapter 112Chapter 113Chapter 114Chapter 115Chapter 116Chapter 117Chapter 118Chapter 119Chapter 120Chapter 121Chapter 122Chapter 123Chapter 124Chapter 125Chapter 126Chapter 127Chapter 128Chapter 129Chapter 130Chapter 131Chapter 132Chapter 133Chapter 134Chapter 135Chapter 136Chapter 137Chapter 138Chapter 139Chapter 140Chapter 141Chapter 142Chapter 143Chapter 144Chapter 145Chapter 146Chapter 147Chapter 148Chapter 149Chapter 150Chapter 151Chapter 152Chapter 153