yake fadin Sady ya na ganki a haka kamar an bata maki rai ko ?
Shafawa nayi tare da dago kai ina fadin fushin banza takeyi tunda bata son a fada mata gaskiya don tana kokarin kwasan dabi,an nasara ta dorawa kanta yanzu niko ba yarda zanyi da hakan ba.
Me tayi ya fada yana kallon sadiya din ai gatanan ta fada da bakin ta ina mikewa don dauko mai ruwa don nasan ko ban dauko ba zai tambaya idan zai tsshi.
Ina zaki ya tambayeni ruwa zan dauko ma a fridge na fada naci gaba da tafiya na dan dade a kicin din don adduan dana tsaya yi a cikin ruwan ba wani addu,a bane sai fatiha dana tsiri karanta mai kafa goma sha daya a ruwan wanda kafin nasa nakan karanta na aje mai ya danyi sanyi daya tambaya na dauko mai shi.
Sai ranan na manta ban karanta masa ba har ya shigo part din namu haka yasa na dan tsaya ina karantawa har na bata lokaci a karamin kitchen din namu na part din.
Wai ke zainab tunda yarinyar nan tana son waya don me baki bata wayan can dana ce ki bata ba tun farko.
Tiren Ruwan da cup na aje a gaban shi cikin ladabi ina kokarin budewa yace min barshi sai na tashi zansha a cikin muryan shin nan me kamar na rowa ga mutum idan bashi yaso magana ba.
Wayar tana inane tunda kin hana mata naki ya sake maimaitawa nace tana nan aje wanan ma ai ya ishe mu amfani banda mutanen gida wa muke kira dashi.
Naki ma ai wani za a saya tunda ba zaki gida da wayar data sha hannu ba sai ki bata ta ci gaba da gamen dinta a zauna lafiya ko gimbiyar game ?
Sai lokacin tayi murmushi a fuskanta jin abinda ya fada din yace to koke fa sadiya kin zauna kin hade rai haka kamar wata matar soja can dake ?
Ni da naga sa,adatu hade fuskanta ai baiban tsoro na fada ina zama a inda na tashi muryan shine ya sake fadin akwai wani abinda kuke son sayane zaku tafi dashi gida duk da dai ba dadewa zamuyi ba zamu dawo ?
Don hutun nasu na tambaya baida yawa kwarai akace wanan karon saboda sadiya sai mu dawo da wuri yaya nikan sai na gama koda zan dawo na bashi amsa.
Tunda kece mai shirya tafiyan ya fada a dan hasale amma yaya kasan dai mun dade rabo mu da gida ai na fada ina kallom shi.
To idan hakane sai a fasa tafiyan in hakan bai maki ba wata daya na yanke zamuyi a can zuwa lokacin nasan kin gama dai abinda ya kaiki ai.
Duk da naji dadin zancen a raina amma a fili cewa nayi wata daya kuma yaya ina laifin dai wata biyu zuwa uku haka ?
Karatun nata fa wai zainab bana son wasa da abinda ya shafi karatun ku ga baki daya kema na saya maki form da mun dawo zaki koma karatu ne nan gaba.
Ko hakan bai maki bane zaki tsaya batawa kanki lokaci zanso ace kin hada karatun ki kaf a nan kafin mu tattara mu koma Nigeria gaba daya da zama can don hakan nake planning nan gaba don mami ta fara fadin mu koma gida hakana.
Mami tana da gaskiya yaya zama acan kusa da yan uwa zaifi ma tana ganin ka a kusa da ita hankali zaifi kwanciya ai balle ni wa yanan abokan naka yaya basu min ba sam.
Zainab yaushe kika san abokaina da har kika san basuyi maki ba ya tambaya da mamaki yana kallona .
Nasan su tunda sune mahalakan ka a yanzu na fada a hankali sai naji ya sake dan murmushi kawai yana kada kai .
Can yace zainab da kinfi haka bansan inda wayau ki zai tsaya min ba don kallon da nake maki kin wuce haka a wurina.
Abi ma dariya ya bani na kai bayana saman kujera ina dan murmusawa tare da fadin ni di kuma yaya sadiya karya na fada matar da take zaune a gida take fadin abokaina.
Yanzu da nayi magana yayan mu laifina zata gani yaya ta fada tana nokewa ga maganan ruwan dake gaban sa ya bude ya zuba a cup din tare da dan kurba a hankali yana kada kai kafin yace ina ganin ranan Friday mai zuwa muna Nigeria.
Don haka idan akwai abinda kowan ku keso sai ya fada ko ku fita ku sayo da kanku zaifi min sauki saidai bana son kaya masu nauyi da yawa kin sani ga tafiya.
Duk iya abinda zan rika yaya tufafine ko dan wani abin amfanin mu na bashi amsa ina cikin farin ciki da jin zamu wuce gida dabai fi an kwanaki ba a lokacin ashe .
Tu wanan ranan sosai muke busy yawon fita sayayya duk ban san cewa ya riga da yai muna sayayyan da ban taba zato ba don wanan tafiyan.
Kafin ranan duk mun gama wani shiri na tafiyan mu inda nikan shiri nakeyi sosai na barin kasan gaba daya a raina don haka duk wani abunda zan tuna nayi dana sani bukatan shi a can na tanada don komawa dashi gida duk ya yaya yace baya son muyi tarkacen kaya da yawa ga tafiyan.
Ranan daya bukaci mu fitar a tafi da kayan airport yasha mamakina sosai don bai iya boye bacin ranshi a zuciyar shi ba don ganin yawan kayan da yayi dana fitar.
Haka ya daure akai muna packed din shi zuwa airport inda kayan da alaman zasu rigamu isa ga nawa tunanen.
Shiri sosai mukayi daga gyaran jiki zuwa duk wani abinda ya kamata ace munyi don ban yarda na bar kasan ba saida naje har kauyen su maya mukai sallama da ita da iyayyen ta kan na tafi na tafi ke nan ba zamu sake haduwa da suba idan na tafi.
Kamar yadda duk wani sabo yake udan za a rabu haka muka rabu da maya da yan uwan ta kakarta bata barni haka ba saida ta ban wasu abunuwa datace na zanka amfani dasu har yayana nan gaba muka rabu cikin kewa da juna ina kuka maya ma tanayi.
Washe gari da daren ranan muka bar kasan chaina zuwa Nigeria sai dai naji haushin tsayawan mu a kasan Dubai da muka kanceqa da yayi wani aiki ya taso mashi a can da zai tsaya ya dan yi.
Ba laifi mun tsaya a Dubai mun kuma sha dadi sosai duk da shikan baida lokacin mu kullun sai dare yake dawowa masaukin da muka sauka wani lokacin ma kafin ya dawo zai samu munyi barci ko.
Wasa wasa kwanan mu biyar a dubai din wanda ni dai nayisu ba a cikkn dadin rai bane do na matsu na bufe ido na ganni a kasata Nigeria a lokacin.
Shiko hakan ko a jikin shi don ba abinda ya dameshi a zamanu din sai ranan da yake fadin gobe zamu bar kasan ya danga walwalana kadan.
Alhamdullahi mun sauka Nigeria da dare amma ta kano ba kamar ta Abuja ba kamar yadda ya tsara muna.
Nasan maganan hauka zanyi idan nace ya barmu mu fara zuwa gida don gamu a kano don yafi muna kusa da gida a lokacin.
Amma nasan zuciyana hauka take ban don ba zai taba yarda da hakan ba sai idan mun danganta da wurin mami da yanzu zaman ta ya koma garin Abujane kamcankan duk da an sauke su a lokacin.
Don lokacin har waya tayo min kan wai ban kirata na mata jajen saukan su a mulki ba ta fada don takanas ta kirani a waya ta balbaleni ni dai sai hakkurin dana bata kawai a lokacin.
Duk da an sauke su bata kwaso ta dawo kadana da zama ba sai suka zauna can ga baki daya tunda dama gidan su na kansu suke zaune a cikin sa yanzu ba na gwaunati ba.
Duk wani gyaran gidan da aka kara yi yaya J ne ya kara gyara masu shi suke zaune a cikin sa yanzu.
Karfe goman safe duk muna Abuja ba zance ga unguwar da muke shiga ba don garin gaba daya ya kara sauya min ga dan sanin danayi mai a baya.
Duk da rudewan sauyawan wurin hakan bai hanani gane ba wancan gidan da muka zauna a farkon aurena dashi bane kafin mu wuce zuwa chaina.
Wanan gidan na yanzu yaci uban wancan sosai ga fasali da keruwa komai na gidan sabone ba sai an fadawa mutum haka ba.
Motocine a haraban gidan gasunan birjit a cikin rigunan su rurufe sai shuke shuke da zai tarbe ka.
Tun saukan mu kano ya sauya layin wayan shi naga ya aje wancan wayan da mukai tafiya dashi haka kuma ya miko min nima waya sabuwa a kwalin ta kiran samsung full ita kuma sadiya iphone karama mai kyau da su.
Zakace duk biyun ba zaka gane bambancin su ba don kyau godiya nayi a fili a zuciyana kuma fadi nake kyautan karshe ke nan tsakanina dakai baka sani ba.
Don yanzu sai lalabashi kawai nakeyi in samu naga mun sauka ya mika mu gida lokacin zan tayar da balli na a garesu.
Don duk wani rudi da abin duniya da yake min yanzu ni bashine a gabana ba kaina kawai nake son na kwata a garesu naga na fita hannun shi baki alaikum ba tare da duniya ta zargi komai a hakan ba.
Kinga gidan ki na abuja ke nan da fatan tsarin ginan yayi maki kyau sosai ya fada kamar mai rada a lokacin.
Don naga kina da sha,awan ruwa wancan kuma babu swimming poll a cikin sa yasa na fadada wanan din aka gyara makushi sosai.
Dan murmushi yake na sake tare da fadin gidan yayi kyau sosai wallahi ballw ni yar tallaka ina ni ina wani zabem gida mai kyau gareni.
Bana son kina kiran kanki da hakan don yanzu a matata kike a idon kowa don haka wanan kallaman ya fita a bakin ki.
Donke din matar jafar kankia ce ba yar anchau ne ko meye sunan garin naku ba na manta ya fada yana kawar da kanshi don motar data tsaya gab da kofan shiga gidan.
Innalillahi zakace wasu basu tunanen lahira idan suna hada duniyan su kamar ba zasu barshi ba don tsarin gidan kamar ba gobe.
Haka muka fito muna bin gidan da kallon mamaki zuwa cikin gidan saidai duk hakan bai hanani addua a bakina duk da na rude da ganin wanan gidan haka.
Sai tambayan kaina nake wai ya jafar ne mai mahaukacin kudin nan haka kamar wani mai shekaru a duniyan nan daya tara kudi irin haka.
Oyyoyo da uwar dakina muryan fadilace ya daki kunnena lokaci guda sun fito tare da wasu daga cikin gidan.
You again muryan sadiya ta fada da dan karfi ta nufi wurin ta da gudu don murnan ganin ta a lokacin.
A hankali nake takowa cikin dan murmushi zuwa gareta ta hadamu ta rugume ga baki daya kafin sauran mata su shiga gaida mu suna muna sannu da zuwa cikin nuna kulawa a gare mu.
Na dago ina fadin mun sameku lafiya suka amsa a cikin fara,a da murna kamar sun taba sani mu da farko.
Shine ke waya da bansan wanda yake wayan dashi ba a bayan mu yake fadin mun iso a kawo mai abinda yace azo dashi din.
A raina nace giya ke nan ko wani katon tun da naji ya fadi hakan yayin da matan suka shiga gaidashi da zuwa da sauran yan aikin gidan.
Muna shiga wani katon hoton mu da muka dauka a chaina dashi ranan sallah ne ya tareni don nasha kwaliya a photon zakace ko balarabiyace ta asili yadda na fito a photon.
Da murmushi na sake tare da tambayan kaina yaushe har ya yi wanan aikin haka kai yaya ya iya duk wani abinda zai kawar da zargi a zukatan mutane shikan .
Ai wanan photon sai a dauka ni din matarshice ta gaskiya yadda photon ya karbi falom kamar kai magana damu mu amsa ma a fili.
A falo muka zauna aka shiga gaisawa da masu aiki sai kuma wasu biyu da ban sani ba na dai ga suna zirga zirga a gidan kamar yan uwan shi.
Kafin shi ya fara mikewa a daidai lokacin da Fadila ke fadin ai maza a kara gyara table din abincin don muna da gajiya kafim mu shige ciki mu huta.
No saidai su nikan zan shiga na watsa ruwa ya bada amsa yana kallon agogon hannun shi kafin ya juyo yana fadin mami bata san da zuwan mu na fa nasan zaku kwasa da ita karshe.
Da nayi laifin me tunda tasan bani bace mai tafiyan a raina kuma fadi nayi saidai tayi da wanda ta gani don ni goben nan zan bar gidan nan idan ma ba kasani ba ka sani.
Don a kage nake ko zuwa abujan duk bat da saune kawai nayi mai kada mu raba hali tun a hanya shiko sai wani nuna jiji damu da yakeyi a gaban kowa yadda kasan auren gaskiya muke a tsakani mu dashi.


ZAINAB IDRIS MAKAWA



YA ALLAH KASA MUNA CIKIN YANTTATUN BAYIN KA UBANGIJI KA KARBA MUNA IBADUN MU KA GAFARTAWA DUKKAN MAGABATAN MU KA BAMU CIKAWA DA IMANI A ZUKATAN MU ALLAHUMA AMIN, , , , ,


LITTAFIN NAN NA KUDINE YAR UWA KI BIYA KI KARANTA A CIKIN SALAMA BA TARE DA HAKKIN KOWA AKANKI BA YAR UWA, , , ,

DON SAMUN LITTAFIN NAN ZAKI KIRA 08036959257 KO 09026931792 DARI UKU NE KACAL KUDIN SHI, , ,


Dakin namu nabi da kallo komai ansaka na jin dadin rayuwa dan Adam a dakin kamar ba gobe a wurin bawa.
Wanka na shiga na fito na samu an shigo mun da kayana dana zo dashi ranan na bude wardrobe da niyar aje jakkar kayan gaba daya ba tare dana zazzage kayan ba don idan zan tafi gida dauka kawai zanyi na tafi dashi.
Saidai abinda nagani a cikin wardrobe din shi ya girgizani lokaci guda don kayane ciki shake nau,i nau,i na mata irin namu na kasan Africa.
Wanan ko a wata dayan da yace zamuyi mu koma yaushe zan saka su a jikina duk a cikin wata dayan balle su kare.
Don sun kai kala hamsin ko fiye da hakan a cikin wardrobe din idan ma basufi hakan ba ga lissafin.
Nan na karewa kayan kallo ina sauke ajiyan zuciya kasa daukan ko daya daga cikin kayan wardrobe din na zari guda a cikin jakkana na saka na koma bakin gado na zauna ina tunanen wanan halin na yaya J.
Na kasa fassara wanan halin na yaya J gaskiya don wani sahu zan saka shi a yanzu shin zan iya kiransa da mai yawan alheri ko kuma mai iya yaudara ne ?
Don wanan halin nasa idan ba wani akasi ba sai mace tace ta dace da miji gaskiya don irin halaiyar nan nasa.
Salaman sadiya dakin yasa na dago kai ina kallon ta fuskanta da fara,a take tafe tana fadin wai yayan mu kinga yadda aka cika min wardrone da kaya.
Nuna mata nawa nayi da hannu ina fadin duba can ki gani sadiya wanan ai haukane ko ?
Ta nufi wurin wardrobe din tana fadin a,a yayan mu zamu saka mu ji dadi wallahi gaskiya yaya j mutum ne yasan harkan arziki sosai wallahi.
Tana budewa taci gaba da fadin da har ina kallon ina karawa g wanda muka sayo a can da zamu zo ashe ga wanda yaci uban wanan din a nan.
Wani irin ihu ta sake lokacin data bude wardrobe taga kayan shine ta sake wanan ihun a firgice tana taba kayan da ta gani din a ciki .
Yaushe duk zaki saka wanan kayan haka masu yawa yayan mu, gasu nan dai na bata amsa ina mikewa take fadin zan saka sau uku ko biyu a wuni nikan duk sai na saka su a jikina kafin mu koma.
Ta gama daddaga kayan ta juyo da nufin ganina a inda ta barni zaune bana wurin ina tsaye bakin mirrow dina ina kallon kayan shafen dake wurin.
Wani dan turare ne ya dauki hankalina na mika hannu na dauko ina karanta sunan shi sunan da larabci aka rubata shi aswad.
Jin hannun sadiya nayi a kafadana tana fadin wai amma yana da kyau sosai nace sadiya meye baida kyau a wurin nan.
Mun gama kallo muka koma kan waya zube muke saman gadon tana danne danne a wayan nikan barci ne ya fara daukana a wurin.
Fadila ta shigo dauke da tire da sauran tarkace tana fadin na dauka kunyi barci don gajiya kasan nan akwai nisa sosai da nan duk ka sauka sai ka yi hutun gajiya wallahi.
Bude idona nayi da suke a lumshe
Showing 294001 words to 297000 words out of 390011 words