ina kwana a kusa dashi da nakeyi ashe yana cikin dokan su yin hakan garesu su kusanci mace ko numfashin mace a makwanci daya su da mace dokane a gare su
Wa, iyazu billahi asirin ma kanshi wahalane kawai a cikin sa ga dan mami na cikin fitina da masifa daya jefa kanshi.
Amma ita mami din mulki da giyan duniya ya hana mami ta kwantar da hankalinta ta fahinci komai a lokacin.
Bayan mun gaisane nake fadin umma yace in fada maki mota na nan da zakuyi tafiya dashi ga makulin motar yace abawa yaya uzaifa ita nasa ne yabashi.
Yar nan me kike fada kuma bayan wanan alherin da kuka cika mu dashi a baya sai kawai ta fashe da kuka lokaci guda.
Dakin yai shiru haka ya sakamu muma dake dakin a lokacin sake hawayen daga idanuwan mu sai umma ta bude baki kamar zatayi magana sai kuma ta kara fashewa da kuka mai ban tausayi.
Fadilace da a yanzu take wani ja da baya damu bata sakewa tun dawowan mu na kula da hakan a gareta ta shigo dakin don ta fada muna yaya Uzaifa yaja falon yana jiran fitowa su umma.
Ta samemu a cikin wanan halin na kuka ba maiwa wani magana taja ta tsaya tana kallon mu a cikin mamaki.
Kafin ta bude baki tace haba hjy koma mene ai bai kamata ke ki sare masu gwiwa ba don kukan ki dole ya sakasu a wani hali haka.
Yar nan dole in kuka wanan alheri haka kamar kaika haifi mutum banda baki godiya kukan nan kawai zan iyayi a yanzu.
Mama kiyi hakkuri don Allah haihuwane mai akbarka kukayi shi ya jawo maku wanan yanzu.
Da ace kun haifi wata ba zainab dake da sanin ya kamata ba da duk wanan alheri baku sameshi ba hakkurin ta da dauriya ne ya jawo mata hakan.
Hakane yar nan dadin haihuwa mai albarka ke nan gun iyayye duk wata uwa tsakanin ta da danta tun yana ciki shine adduan samun mai albarka dama.
Haka dai ta samu ta lalashi umma har suka fara shirin tafiya a falo suka tsaya jira shi ya fito suyi ban kwana dashi.
Sai gashi ya fito a cikin shirin shi na bakaken suith a jikin shi yana cikin ujula yana sauri ganin su yasa yaja ya tsaya suka gaisa.
Nan umma ta shiga mashi godiya bai tsaya ba yace haba ba komai umma na fadawa uzaifa ya dawo wani sati ya sameni nan kafin mu koma.
Kai Alhaji dawainiyar yayi yawa ba mu kadai bane wanan irin alherin haka ubangiji Allah ya saka da alheri kuma ya baku masu rama maku nan gaba ya hadaku da zuri,a masu albarka aka amsa da amin nikan a cikin zuciya na amasa hakan.
Yan uwa ina mika sakon ta,aziyana a gun yan uwan da sukai rashi a cikin satin nan ubangiji Allah ya gafartawa musulmi yakai hasken rahama a kabarin su amin ya gafartawa duk wani musulmi daya kwanta daman shi Allahuma amin.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
ASSALAMU ALAIKUM WARAHAMUTULLAH YAN UWA FATAN ALHERI A GAREMU BAKI DAYA ALLAH YA SADAMU DA ALHERUN SA AMIN, , ,
LITTAFIN KUFINE KI BIYA KI KARANTA A CIKIN SALAMA YAR UWA DON GUJEWA SHIGA HAKKIN WANI, , , , ,
Naga maki da al,ajabu a cikin yan kwanakin nan don ranan dasu umma suka tafi ranan munyi barci a tsaye a dakin don ni kaina tsoro aka fara bani ina tsaye da kiran Allah.
Saidai abinda ke ban mamaki a yanzu shine a lokaci yaya zai koma kamar bashi ba amma in gari ya waye sai ya dawo min mutum daidai kamar bashi bane muka kwana a raye yana min saddabarun a cikin dare.
Sai gashi gari ya waye ya koma kamar bashi ba da zarah biyar tayi daidai lokacin da za,a fara kiran sallah ya fara samun sauki lokacin gari ya fara wayewa ke nan.
Ina kula da hakan tun fara kwanana a dakin shi a daidai wanan lokacin ne yake samun natsuwa ya koma normal kamar kowa.
Kamar kullun dakina na nufa ina idar da sallah ban tsaya jiran wani abu ba na haye gado sai barci a ranan nayi barci sosai.
Don ban tashi ba sai after one na rana koshi nasan don sabo da lokacin sallah ne duk inda musulmi yake da zaran wanan lokacin yayi zai fara ji a jikin shi.
Wanka na fada kodana fito time din yayi har ya gwauta a gurguje na tayar da sallah din don makaran da nayi.
Ina zaune ina shafa mao a gaban mirrow dakina ya shigo dakin a cikin madubi muka hada ido dashi nayi saurin dukar da kaina a kasa.
Kin tashi ke nan ai na zata har yanzu din barci kikeyi baki tashi ba da zance dake kada ki kwana a dakin sai ki dauki hakab da wani manifa a zuciyar ki.
Ko yanzu din da idona ya gane min gaskiya bashi zaisa in fasa kwana a dakin ba komai shedancin mutum dai ai Allah ya fishi.
Gaskiyane amma kuma Allah baice ki kusanci abinda zai iya ja maki illa ba ai zuwana biyu dakin nan kina ta barci baki tashi ba.
Idan har zan samu barcin da rana inyi na daren ba damuwa bane matukar addua akan hakan zai muna tasiri ai.
OK ina maki fatan alheri ga hakan na ce amin kamar a fusace ya sake dan murmushi ya juya zai fita daga dakin sai kuma yaja ya dakata yana fadin.
Zan so tunda kin fara fahintar hakan kiyi nisa dani kamar yadda na umurce ki dayi tun farko kada ki jefa kanki ga halaka.
Ban fahinta ba nace a cikin mamaki na juyo da sauri ina kallon shi kafin in ce dashi.
Ke nan hakan na nufi in barka har abada ko me don magana kayi min a dunkule wanda na kasa fassara ma,anan shi yanzu ?
Da zaki dauki shawaran da zan baki zaifi maki sauki a rayuwan ki ki zauna kamar yadda na umurce ki da nisantana tun farko.
Saida na sake wani irin laulausan murmushi a fuskana na mike tsaye na fuskan ce shi a lokacin saboda tsaban rudewa na manta da daura gaba nake tsaye a gaban shi don yadda nake ji nace.
A yanzu idan har zanyi hakan dayan biyune zai biyo baya kodai na nisance ka har abada ko kuma kai din da kanka ka rubuta min takarda shedan ka sakeni in koma wurin iyayyena da zama.
Shima murmushin ya mayar min kamar yadda nayi masa da farko yace kina ban mamaki a yanzu da wanan taurin kan naki zainab.
Idan wani ya fada min ke din zaki iya hakan a baya zan iya mussanta masa hakan akan bai fahince ki bane ya fadi hakan.
Zaka iya fadan komai saidai amsan bukatana nake saurare a yanzu don hakan nima ya isheni don ban san a matsayin da nake a zuciyar ka ba har yanzu.
Zaki iya fadan komai a yanzu zainab mutukar ba zaki daukeni a matsayin makiyin ki ba dai yana fadin haka ya juya ya fice rai bace.
Na bishi da kallo ban san lokacin da wani irin kuka yanzo min ba lokaci guda don takaici bakin gado na koma na zauna ina hawaye ni kaidai.
Sai faman tunane da nakeyi na yadda mutane su a wajen su suke min kallon wace ta dace da mijin aure .
Basu san cewa ABU A CIKIN DUHU SIRINE BA da ace zan zauna in fada wa wata irin rayuwan tashin hankalin da nake ciki tun shigana gidan sa da mata da yawa sun gane ba daula ne arzkin da mace ke cikin shine zamana jin dadin aure ba a yanzu.
Eh nasan da yawa kan sun dace amma akwai irin mu da ke cikin jarabtan aure ta hanyoyi daban daban a duniyan nan.
Sai dai muce ubangji Allah ya kawo muna dauki ya fitar damu da ma wa yanda basu shiga ba amma yana zane a kundin kaddaran rayuwan su sauki.
Na gaji da kukana ni kadai na kuma ba kaina hakkuri na mike na saka dogon riga haka kawai naji zuciyana yana son kiran maya a ranan.
Duk da zuwana Nigeria na kirata sau biyu mun gaisa take fada min cewa ta samu aiki a wani karamin company yanzu ta fara aiki a nan.
Saida kiran ya kusa katsewa ta daga tana fadin inyi hakkuri bata kusan da wayan ne a lokacin.
Mun gaisa nake tambayan ta aikin ta da iyayyen ta ta amsa da kowa lafiya aiki kuma tana nan tanayi saidai wurin bai mata ba idan ta samu wani zata canza.
Nake dan bata hakkuri akan tayi hakkuri dashi for now don ta rage zaman banza hakana tace hakane.
Ya kuke ina mijin ki da sady nace suna lafiya ta kara jefo min tambayan dake cina a raina tace muryan ki ya nuna min cewa kinyi kuka yau zeey ?
Dan murmushi na sauke har tana iya jina a lokacin naji tace why zeey why da zaki zauna kina kuka akan abu daya kullun.
Nasan dai a kan halin sane kike kukan naki ko zee nace a cikin muryan kuka maya kasheni yake son yi kawai nan dai na fara kora mata labarin komai da ya faru zuwan mu gida.
A karshe ta ban hakkuri tana fadin in bari idan taje gida zata kirani muyi magana yanzu tana wurin aikintane.
Mukai sallama da ita na kashe wayan ina ajiyan zuciya na mike na nufi hanyar fita daga dakin dakin sadiya na fara lekawa bata cikin dakin .
Na nufi falo kai tsaye don nasan tunda ban ganta a dakin ba tana falo ke nan a nan na sameta zaune tana kallon wani film.
Kallon ta nayi watau sadiya dai sai gyara Allah ranan da wanan daulan ya subce muna muka koma gida da zama.
Don duk dabi,un ta na diyan masu kudine ita ba zakace gidan mu ta taso ba a lokacin saboda irin rayuwan da na hango a gareta.
Har na karaso kusa da ita bata sani ba jin takon mutum ta juyo da sauri tana fadin lah anty ashe kin tashi na shiga daki kinata barci.
Remote na duka na dauka saman table na kashe tv ina fadin tashi kije kiyi sallah kada in saba maki yanzu na fada rai bace.
Ganin ba wasa a fuskana don wani lokaci mukanyi wasa har da kokawa a tsakanin mu idan mun bushi iska a tsakanin mu.
Wanan karon kan babu wanan sakin fuskan a gareni don haka ta mike tsam tana turo baki ta bar falon.
A hankali na juyo bayan na gama binta da harara ina sake ajiyan zuciya na kai zaune dan table din dake kofan na jawo na dora kafana .
Ko zanji dadin zama a hakan ta hanyar mike kafafuwana saman dan stole din na dora hannuna saman fuskana .
Ina zaune shiru ban motsa ba ban kuma kunna tv ba don komai bana jin dadin shi a lokacin sai wani tunane yazo min.
Tambayan kaina nayi wani makusamcin shi zan fadawa damuwana ne da zai duba min wanan zancen
Amsa naba kaina da fadin ya mamud shi ya cancanci in fadawa don yasan halin da dan uwan shi yake ciki a yanzu.
Na dawo naba kaina amsa da kaina da fadin in kuma na fada mai ai kamar na tonawa kaina asirine kuma.
Hujja dai iyayyena suke so a gareni ko yanzun kuma ina da babban hujan da zan basu ai akanshi.
Zancen mu da innan mu ya fado min a rai da take fadin nayi hakkuri na zauna dashi ko dan mahaifiyar shi da basu sona dashi ya nace min.
Da wanan bakin nacin ai gara shima ya kini din zaifi min dadi na bawa kaina amsa ni kadai muryan fadilace ya katseni tana fadin .
Ashe kin tashi lafiya dai kike ko nayi mayawa da mayanni don mu gaisa kina kwance.
Hannuna na sauke ina fadin lafiya kalau nake take fadin an wuni lafiya abinci har yayi sanyi baki karya ba.
Barci ne ban samu sosai ba a dareb jiya yasakani wanan barcin dan ruwan zafi zan kurba ya isheni koshi hanjina nake son ya bude.
Ta juya da sauri bata jima ba sai gata da kayan shayi ta hado min ita da kanta ta hada min komai nace nagode har ta juya zata wuce nake fadin.
Ya yaran ki kin samu lekasu kuwa jin haka yasa ta juyo tana fadin ko gafarceni don Allah nasan kinsan komai a kaina don oga ya fada min maganan daya girgizani a ranan.
Na dago da sauri ina tambayan ta akan mefa don bansan abinda kike magana a kaiba yanzu ?
Kai ta dukar kasa sai naji wani iri naci gaba da fadin indai akan matsalan mune ki barshi kawai dani don yanzu ba da bane nasan ciwon kaina a yanzu.
A hankali ta dawo inda nake tana zama take fadin zan fada maki magana daya zainab ko ki yarda ko kada ki yarda Allah ya sheda har cikin raina gaskiya daya nake fada maki.
Sai tayi shiru kafin tace dani duk yadda kike ganin munin halim mijin ki zainab ki hakkuri ki zauna dashi hakana da halinsa.
Duk da nasan a yanzu ba lalai bane ki yarda da zancen da zan fada maki din don kin san koni waye a wuri ku yanzu tynda mijin ki ya sani ya kuma fada min yasan zamanan aikin da nakeyi gidan nan tare daku.
Jin hakan na dago kai na dan kalleta da mamaki don jin abinda ta fada din a lokacin a raina nace ke nan ya jafar ya sanar da ita mun san zaman da takeyi a tare damu ke nan.
Tace haka ba zai hana ni zama daku tsakani da Allah ba zainab don ni musulmace kamar ku ba zan taba bada shedan karya akan abinda banga makamancin shi a wurin ku ba gaskiya.
Nazo nan aikine bisa zargin da akewa mijin naki da yin fasa kwari da sauran abubuwa na rayuwa don gani shi da da mahaukacin kudin da kasa suke zargin shi dashi.
Sai dai zamana din don bincike a cikin ku zainab na gano mijin ki tsayayyen mutum ne wanda ya tsaya da kafan shi wurin nema ya kuma dage da aikin shi kuma da kafafun shi yana neman na kasa ba kamar yadda ake tuhumar shi din ba.
Yawan kyautatawan ku gareni yasa ni kaina na fara zargin hakan kafin in binciko komai na gane gaskiya .
Yanzu nazo maki nan ne a matsayin yar uwa kuma aminiya kamar yadda kika rikeni a baya a matsayin yar uwa kuma aminiya saidai yanzun da kika san koni din wacece ba ki dauke hakan ba ayanzu sai dai duk da hakan.
Zanso kiyi hakkuri ki kuma kara hakkuri ki zauna da Jafar har abada a rayuwan ki don shine kawai yanzu mafita a gareki da rufin asirin ki.
Zainab abinda baki sani ba shine kina fita gidan jafar kema kanki mutane zasu kyamace ki idan kowa yasan irin rayuwan da kika guda a gareshi har ki barshi.
Sai zargi ya fara yawo a zukatan mutane a kanki cewa ta yaya kika zauna dashi na tsawon wanan shekurun a cikin wanan halin nasa ?
Kaina dago da sauri na kalle ta tare da zuba mata ido don jin abinda ta fada zai iya faru game dani nan gaba idan nace zan bar gidan shi tace eh haka zancen yake gaskiya a wurin mutane.
Shi mutum dan tara ne bai cika goma ba kowa da kike gani yana da nasa kalar jerabawan rayuwa da Allah ke dora mashi sai idan Allah na son kane .
Karshe sai ya yaye maka wanan jerabawan ta hanyar sauki da lumana Allah ya jefoki a rayuwan mijin kine do ki taimaka masa kuma kina taimakawan ba laifi.
Don ba ko wace mace bace zata zauna tayi hakkurin shekaru kamar yadda kikayi zainab don koni din da nake magana ba lalai bane na iya hakan.
Nasan jafar yana da rauni duk da baki fada min ba nasan komai don kin san aikin mu bawai kawai saka ido bane ga binciken da mukeyi akan mutum ba kawai mu leki asirin aikin daya kawo mu wurin mutum mu barshi.
A, a komai daya shafeka sai mun gane a lokaci guda a irin hakane na gano mijin ki ba mai sha,awan mata bane shi a rayuwan shi.
Zaman turai da kuma miyagun abokai ya bata rayuwan mijin naki da kuma asiri irin namu na bakaken mutane ya bata rayuwan shi duk da hali irin na kyautatawa nasa.
Sai da ya samu akasi a rayuwa yana wanan aikin da ko wani addini da al,ada bai yarda da irin wanan fasadin ba a doron kasa.
Ki godewa
Showing 339001 words to 342000 words out of 390011 words
Wa, iyazu billahi asirin ma kanshi wahalane kawai a cikin sa ga dan mami na cikin fitina da masifa daya jefa kanshi.
Amma ita mami din mulki da giyan duniya ya hana mami ta kwantar da hankalinta ta fahinci komai a lokacin.
Bayan mun gaisane nake fadin umma yace in fada maki mota na nan da zakuyi tafiya dashi ga makulin motar yace abawa yaya uzaifa ita nasa ne yabashi.
Yar nan me kike fada kuma bayan wanan alherin da kuka cika mu dashi a baya sai kawai ta fashe da kuka lokaci guda.
Dakin yai shiru haka ya sakamu muma dake dakin a lokacin sake hawayen daga idanuwan mu sai umma ta bude baki kamar zatayi magana sai kuma ta kara fashewa da kuka mai ban tausayi.
Fadilace da a yanzu take wani ja da baya damu bata sakewa tun dawowan mu na kula da hakan a gareta ta shigo dakin don ta fada muna yaya Uzaifa yaja falon yana jiran fitowa su umma.
Ta samemu a cikin wanan halin na kuka ba maiwa wani magana taja ta tsaya tana kallon mu a cikin mamaki.
Kafin ta bude baki tace haba hjy koma mene ai bai kamata ke ki sare masu gwiwa ba don kukan ki dole ya sakasu a wani hali haka.
Yar nan dole in kuka wanan alheri haka kamar kaika haifi mutum banda baki godiya kukan nan kawai zan iyayi a yanzu.
Mama kiyi hakkuri don Allah haihuwane mai akbarka kukayi shi ya jawo maku wanan yanzu.
Da ace kun haifi wata ba zainab dake da sanin ya kamata ba da duk wanan alheri baku sameshi ba hakkurin ta da dauriya ne ya jawo mata hakan.
Hakane yar nan dadin haihuwa mai albarka ke nan gun iyayye duk wata uwa tsakanin ta da danta tun yana ciki shine adduan samun mai albarka dama.
Haka dai ta samu ta lalashi umma har suka fara shirin tafiya a falo suka tsaya jira shi ya fito suyi ban kwana dashi.
Sai gashi ya fito a cikin shirin shi na bakaken suith a jikin shi yana cikin ujula yana sauri ganin su yasa yaja ya tsaya suka gaisa.
Nan umma ta shiga mashi godiya bai tsaya ba yace haba ba komai umma na fadawa uzaifa ya dawo wani sati ya sameni nan kafin mu koma.
Kai Alhaji dawainiyar yayi yawa ba mu kadai bane wanan irin alherin haka ubangiji Allah ya saka da alheri kuma ya baku masu rama maku nan gaba ya hadaku da zuri,a masu albarka aka amsa da amin nikan a cikin zuciya na amasa hakan.
Yan uwa ina mika sakon ta,aziyana a gun yan uwan da sukai rashi a cikin satin nan ubangiji Allah ya gafartawa musulmi yakai hasken rahama a kabarin su amin ya gafartawa duk wani musulmi daya kwanta daman shi Allahuma amin.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
ASSALAMU ALAIKUM WARAHAMUTULLAH YAN UWA FATAN ALHERI A GAREMU BAKI DAYA ALLAH YA SADAMU DA ALHERUN SA AMIN, , ,
LITTAFIN KUFINE KI BIYA KI KARANTA A CIKIN SALAMA YAR UWA DON GUJEWA SHIGA HAKKIN WANI, , , , ,
Naga maki da al,ajabu a cikin yan kwanakin nan don ranan dasu umma suka tafi ranan munyi barci a tsaye a dakin don ni kaina tsoro aka fara bani ina tsaye da kiran Allah.
Saidai abinda ke ban mamaki a yanzu shine a lokaci yaya zai koma kamar bashi ba amma in gari ya waye sai ya dawo min mutum daidai kamar bashi bane muka kwana a raye yana min saddabarun a cikin dare.
Sai gashi gari ya waye ya koma kamar bashi ba da zarah biyar tayi daidai lokacin da za,a fara kiran sallah ya fara samun sauki lokacin gari ya fara wayewa ke nan.
Ina kula da hakan tun fara kwanana a dakin shi a daidai wanan lokacin ne yake samun natsuwa ya koma normal kamar kowa.
Kamar kullun dakina na nufa ina idar da sallah ban tsaya jiran wani abu ba na haye gado sai barci a ranan nayi barci sosai.
Don ban tashi ba sai after one na rana koshi nasan don sabo da lokacin sallah ne duk inda musulmi yake da zaran wanan lokacin yayi zai fara ji a jikin shi.
Wanka na fada kodana fito time din yayi har ya gwauta a gurguje na tayar da sallah din don makaran da nayi.
Ina zaune ina shafa mao a gaban mirrow dakina ya shigo dakin a cikin madubi muka hada ido dashi nayi saurin dukar da kaina a kasa.
Kin tashi ke nan ai na zata har yanzu din barci kikeyi baki tashi ba da zance dake kada ki kwana a dakin sai ki dauki hakab da wani manifa a zuciyar ki.
Ko yanzu din da idona ya gane min gaskiya bashi zaisa in fasa kwana a dakin ba komai shedancin mutum dai ai Allah ya fishi.
Gaskiyane amma kuma Allah baice ki kusanci abinda zai iya ja maki illa ba ai zuwana biyu dakin nan kina ta barci baki tashi ba.
Idan har zan samu barcin da rana inyi na daren ba damuwa bane matukar addua akan hakan zai muna tasiri ai.
OK ina maki fatan alheri ga hakan na ce amin kamar a fusace ya sake dan murmushi ya juya zai fita daga dakin sai kuma yaja ya dakata yana fadin.
Zan so tunda kin fara fahintar hakan kiyi nisa dani kamar yadda na umurce ki dayi tun farko kada ki jefa kanki ga halaka.
Ban fahinta ba nace a cikin mamaki na juyo da sauri ina kallon shi kafin in ce dashi.
Ke nan hakan na nufi in barka har abada ko me don magana kayi min a dunkule wanda na kasa fassara ma,anan shi yanzu ?
Da zaki dauki shawaran da zan baki zaifi maki sauki a rayuwan ki ki zauna kamar yadda na umurce ki da nisantana tun farko.
Saida na sake wani irin laulausan murmushi a fuskana na mike tsaye na fuskan ce shi a lokacin saboda tsaban rudewa na manta da daura gaba nake tsaye a gaban shi don yadda nake ji nace.
A yanzu idan har zanyi hakan dayan biyune zai biyo baya kodai na nisance ka har abada ko kuma kai din da kanka ka rubuta min takarda shedan ka sakeni in koma wurin iyayyena da zama.
Shima murmushin ya mayar min kamar yadda nayi masa da farko yace kina ban mamaki a yanzu da wanan taurin kan naki zainab.
Idan wani ya fada min ke din zaki iya hakan a baya zan iya mussanta masa hakan akan bai fahince ki bane ya fadi hakan.
Zaka iya fadan komai saidai amsan bukatana nake saurare a yanzu don hakan nima ya isheni don ban san a matsayin da nake a zuciyar ka ba har yanzu.
Zaki iya fadan komai a yanzu zainab mutukar ba zaki daukeni a matsayin makiyin ki ba dai yana fadin haka ya juya ya fice rai bace.
Na bishi da kallo ban san lokacin da wani irin kuka yanzo min ba lokaci guda don takaici bakin gado na koma na zauna ina hawaye ni kaidai.
Sai faman tunane da nakeyi na yadda mutane su a wajen su suke min kallon wace ta dace da mijin aure .
Basu san cewa ABU A CIKIN DUHU SIRINE BA da ace zan zauna in fada wa wata irin rayuwan tashin hankalin da nake ciki tun shigana gidan sa da mata da yawa sun gane ba daula ne arzkin da mace ke cikin shine zamana jin dadin aure ba a yanzu.
Eh nasan da yawa kan sun dace amma akwai irin mu da ke cikin jarabtan aure ta hanyoyi daban daban a duniyan nan.
Sai dai muce ubangji Allah ya kawo muna dauki ya fitar damu da ma wa yanda basu shiga ba amma yana zane a kundin kaddaran rayuwan su sauki.
Na gaji da kukana ni kadai na kuma ba kaina hakkuri na mike na saka dogon riga haka kawai naji zuciyana yana son kiran maya a ranan.
Duk da zuwana Nigeria na kirata sau biyu mun gaisa take fada min cewa ta samu aiki a wani karamin company yanzu ta fara aiki a nan.
Saida kiran ya kusa katsewa ta daga tana fadin inyi hakkuri bata kusan da wayan ne a lokacin.
Mun gaisa nake tambayan ta aikin ta da iyayyen ta ta amsa da kowa lafiya aiki kuma tana nan tanayi saidai wurin bai mata ba idan ta samu wani zata canza.
Nake dan bata hakkuri akan tayi hakkuri dashi for now don ta rage zaman banza hakana tace hakane.
Ya kuke ina mijin ki da sady nace suna lafiya ta kara jefo min tambayan dake cina a raina tace muryan ki ya nuna min cewa kinyi kuka yau zeey ?
Dan murmushi na sauke har tana iya jina a lokacin naji tace why zeey why da zaki zauna kina kuka akan abu daya kullun.
Nasan dai a kan halin sane kike kukan naki ko zee nace a cikin muryan kuka maya kasheni yake son yi kawai nan dai na fara kora mata labarin komai da ya faru zuwan mu gida.
A karshe ta ban hakkuri tana fadin in bari idan taje gida zata kirani muyi magana yanzu tana wurin aikintane.
Mukai sallama da ita na kashe wayan ina ajiyan zuciya na mike na nufi hanyar fita daga dakin dakin sadiya na fara lekawa bata cikin dakin .
Na nufi falo kai tsaye don nasan tunda ban ganta a dakin ba tana falo ke nan a nan na sameta zaune tana kallon wani film.
Kallon ta nayi watau sadiya dai sai gyara Allah ranan da wanan daulan ya subce muna muka koma gida da zama.
Don duk dabi,un ta na diyan masu kudine ita ba zakace gidan mu ta taso ba a lokacin saboda irin rayuwan da na hango a gareta.
Har na karaso kusa da ita bata sani ba jin takon mutum ta juyo da sauri tana fadin lah anty ashe kin tashi na shiga daki kinata barci.
Remote na duka na dauka saman table na kashe tv ina fadin tashi kije kiyi sallah kada in saba maki yanzu na fada rai bace.
Ganin ba wasa a fuskana don wani lokaci mukanyi wasa har da kokawa a tsakanin mu idan mun bushi iska a tsakanin mu.
Wanan karon kan babu wanan sakin fuskan a gareni don haka ta mike tsam tana turo baki ta bar falon.
A hankali na juyo bayan na gama binta da harara ina sake ajiyan zuciya na kai zaune dan table din dake kofan na jawo na dora kafana .
Ko zanji dadin zama a hakan ta hanyar mike kafafuwana saman dan stole din na dora hannuna saman fuskana .
Ina zaune shiru ban motsa ba ban kuma kunna tv ba don komai bana jin dadin shi a lokacin sai wani tunane yazo min.
Tambayan kaina nayi wani makusamcin shi zan fadawa damuwana ne da zai duba min wanan zancen
Amsa naba kaina da fadin ya mamud shi ya cancanci in fadawa don yasan halin da dan uwan shi yake ciki a yanzu.
Na dawo naba kaina amsa da kaina da fadin in kuma na fada mai ai kamar na tonawa kaina asirine kuma.
Hujja dai iyayyena suke so a gareni ko yanzun kuma ina da babban hujan da zan basu ai akanshi.
Zancen mu da innan mu ya fado min a rai da take fadin nayi hakkuri na zauna dashi ko dan mahaifiyar shi da basu sona dashi ya nace min.
Da wanan bakin nacin ai gara shima ya kini din zaifi min dadi na bawa kaina amsa ni kadai muryan fadilace ya katseni tana fadin .
Ashe kin tashi lafiya dai kike ko nayi mayawa da mayanni don mu gaisa kina kwance.
Hannuna na sauke ina fadin lafiya kalau nake take fadin an wuni lafiya abinci har yayi sanyi baki karya ba.
Barci ne ban samu sosai ba a dareb jiya yasakani wanan barcin dan ruwan zafi zan kurba ya isheni koshi hanjina nake son ya bude.
Ta juya da sauri bata jima ba sai gata da kayan shayi ta hado min ita da kanta ta hada min komai nace nagode har ta juya zata wuce nake fadin.
Ya yaran ki kin samu lekasu kuwa jin haka yasa ta juyo tana fadin ko gafarceni don Allah nasan kinsan komai a kaina don oga ya fada min maganan daya girgizani a ranan.
Na dago da sauri ina tambayan ta akan mefa don bansan abinda kike magana a kaiba yanzu ?
Kai ta dukar kasa sai naji wani iri naci gaba da fadin indai akan matsalan mune ki barshi kawai dani don yanzu ba da bane nasan ciwon kaina a yanzu.
A hankali ta dawo inda nake tana zama take fadin zan fada maki magana daya zainab ko ki yarda ko kada ki yarda Allah ya sheda har cikin raina gaskiya daya nake fada maki.
Sai tayi shiru kafin tace dani duk yadda kike ganin munin halim mijin ki zainab ki hakkuri ki zauna dashi hakana da halinsa.
Duk da nasan a yanzu ba lalai bane ki yarda da zancen da zan fada maki din don kin san koni waye a wuri ku yanzu tynda mijin ki ya sani ya kuma fada min yasan zamanan aikin da nakeyi gidan nan tare daku.
Jin hakan na dago kai na dan kalleta da mamaki don jin abinda ta fada din a lokacin a raina nace ke nan ya jafar ya sanar da ita mun san zaman da takeyi a tare damu ke nan.
Tace haka ba zai hana ni zama daku tsakani da Allah ba zainab don ni musulmace kamar ku ba zan taba bada shedan karya akan abinda banga makamancin shi a wurin ku ba gaskiya.
Nazo nan aikine bisa zargin da akewa mijin naki da yin fasa kwari da sauran abubuwa na rayuwa don gani shi da da mahaukacin kudin da kasa suke zargin shi dashi.
Sai dai zamana din don bincike a cikin ku zainab na gano mijin ki tsayayyen mutum ne wanda ya tsaya da kafan shi wurin nema ya kuma dage da aikin shi kuma da kafafun shi yana neman na kasa ba kamar yadda ake tuhumar shi din ba.
Yawan kyautatawan ku gareni yasa ni kaina na fara zargin hakan kafin in binciko komai na gane gaskiya .
Yanzu nazo maki nan ne a matsayin yar uwa kuma aminiya kamar yadda kika rikeni a baya a matsayin yar uwa kuma aminiya saidai yanzun da kika san koni din wacece ba ki dauke hakan ba ayanzu sai dai duk da hakan.
Zanso kiyi hakkuri ki kuma kara hakkuri ki zauna da Jafar har abada a rayuwan ki don shine kawai yanzu mafita a gareki da rufin asirin ki.
Zainab abinda baki sani ba shine kina fita gidan jafar kema kanki mutane zasu kyamace ki idan kowa yasan irin rayuwan da kika guda a gareshi har ki barshi.
Sai zargi ya fara yawo a zukatan mutane a kanki cewa ta yaya kika zauna dashi na tsawon wanan shekurun a cikin wanan halin nasa ?
Kaina dago da sauri na kalle ta tare da zuba mata ido don jin abinda ta fada zai iya faru game dani nan gaba idan nace zan bar gidan shi tace eh haka zancen yake gaskiya a wurin mutane.
Shi mutum dan tara ne bai cika goma ba kowa da kike gani yana da nasa kalar jerabawan rayuwa da Allah ke dora mashi sai idan Allah na son kane .
Karshe sai ya yaye maka wanan jerabawan ta hanyar sauki da lumana Allah ya jefoki a rayuwan mijin kine do ki taimaka masa kuma kina taimakawan ba laifi.
Don ba ko wace mace bace zata zauna tayi hakkurin shekaru kamar yadda kikayi zainab don koni din da nake magana ba lalai bane na iya hakan.
Nasan jafar yana da rauni duk da baki fada min ba nasan komai don kin san aikin mu bawai kawai saka ido bane ga binciken da mukeyi akan mutum ba kawai mu leki asirin aikin daya kawo mu wurin mutum mu barshi.
A, a komai daya shafeka sai mun gane a lokaci guda a irin hakane na gano mijin ki ba mai sha,awan mata bane shi a rayuwan shi.
Zaman turai da kuma miyagun abokai ya bata rayuwan mijin naki da kuma asiri irin namu na bakaken mutane ya bata rayuwan shi duk da hali irin na kyautatawa nasa.
Sai da ya samu akasi a rayuwa yana wanan aikin da ko wani addini da al,ada bai yarda da irin wanan fasadin ba a doron kasa.
Ki godewa
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22Chapter 23Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32Chapter 33Chapter 34Chapter 35Chapter 36Chapter 37Chapter 38Chapter 39Chapter 40Chapter 41Chapter 42Chapter 43Chapter 44Chapter 45Chapter 46Chapter 47Chapter 48Chapter 49Chapter 50Chapter 51Chapter 52Chapter 53Chapter 54Chapter 55Chapter 56Chapter 57Chapter 58Chapter 59Chapter 60Chapter 61Chapter 62Chapter 63Chapter 64Chapter 65Chapter 66Chapter 67Chapter 68Chapter 69Chapter 70Chapter 71Chapter 72Chapter 73Chapter 74Chapter 75Chapter 76Chapter 77Chapter 78Chapter 79Chapter 80Chapter 81Chapter 82Chapter 83Chapter 84Chapter 85Chapter 86Chapter 87Chapter 88Chapter 89Chapter 90Chapter 91Chapter 92Chapter 93Chapter 94Chapter 95Chapter 96Chapter 97Chapter 98Chapter 99Chapter 100Chapter 101Chapter 102Chapter 103Chapter 104Chapter 105Chapter 106Chapter 107Chapter 108Chapter 109Chapter 110Chapter 111Chapter 112Chapter 113Chapter 114 Chapter 115Chapter 116Chapter 117Chapter 118Chapter 119Chapter 120Chapter 121Chapter 122Chapter 123Chapter 124Chapter 125Chapter 126Chapter 127Chapter 128Chapter 129Chapter 130Chapter 131