cin zarafi ku rasa wanda zaku danganta da wanan abin sai dan uwana na jini.
To bari kuji shi wanan harkan da kuke ganin munayi kowan ku nan yasan da addinin shi bai yarda da hakan ba.
Idan baku sani ba yau ku sani a kullun ina mai nadaman shiga wanan harkan naku da kuka koya min wanda addinina da al,adana duka ya haramta wanan abin ga wanin mu.
Yau gaskiya nayi nadaman sanin ku a rayuwana tunda har zaku iya kallon kanina ku nuna mashi sha,awan ku a fili babu dayan ku nan da ban ganin girma da daran dan uwanshi koda yan aikin gidan ku ne.
Daga haka ya juya rai bace ya bude motarshi ya shiga yana kokarin barin su wurin ranshi a bace.
Ganin hakan yasa suka san ranshi ya gama baci sosai alokacin da maganan su don sanin halin shi da sukayine zai iya sharesu har abada ga baki daya daga wanan lokacin.
Ganin ya shiga mota yana kokarin tayarwa ya wuce suna bashi hakkuri ta hanyar daya dace yasa ya jamal din sauke numfashi yana barin wurin da yake tsaye yana sauraren su a cikin takaici ya shige gidan.
Babu kowa a falon kai tsaye ya wuce zuwa part din shi yana mai jin zafin hakan daya faru a zuciyar shi.
Yana jin da zai iya a ranan zai bar gidan dan uwan nasa ya koma Nigeria saidai hakan ba zai yiyu ba don dole ya tsaya kodon hjy dake asibiti da kuma mu da muke zaune a gidan cikin rashin sani.
Don haka yaba kanshi hakkuri yana mai fadi a ranshi cewa fushi yanzu ba nasa bane idan shi yai fushi da dan uwan nasa mu yaya zamu kasance kuma ?
Bamu hadu dashi ba bama wada yasan da dawowan shi gidan a lokacin sai bayan sallah magariba da muka fito falo muka ganshi ya fito falon ya samemu muka gaisa dashi a wurin.
Mamane ke tambayan shi kona biyun nan wai meke damun shi ita fa batagane yadda ya canza ba akwana biyun nan idan anyi magana yace ba komai alhalin ba haka tasan shi ba a baya.
Mama banu komai wallahi ni dai kawai yanayin garin nan ne bai mun ba mun saba a gida muna ganin yan uwa da abokai ko ina.
Ta katse shi da fadin kai banda abinka baka ganin yaran nan matane basa fita ko ina amma a haka sun sake jikin su suna sha,anin su a gidan nan cikin rashin damuwa.
Balle kai na miji kamarka kana nuna haka a yanzu mu mata muce me ta fada a cikin raha.
Daga inda nake na saci kallon shi na fahinci akwai wani abinda ya bata masa rai a lokacin saidai banyi magana ba fun zaman shi a wurin suna ta hiran su da mama kan ciwon hjy da ake samun saukia yanzu kan jikin nata .
Don ko yanzu za a iya sallaman ta ta dawo gida saidai dan binciken da suka tsaya yi a kanta ya hana a sallamota daga asibitin yanzu.
Mikewa nayi don tunanen daya addabi zuciyana a lokacin na dan kallesu ina fadin mama ni zan shiga daga ciki .
Ke ko tun yanzu muna nan muna rage dare don ni wanan shiga kwanan da wuri haka ya fara isata wallahi aiba jamal shi kadai zaman garin nan ya isa ba a yanzu harni nan zama wuri dayan nan ya isheni wallahi.
Gashi mijin ki dawowan shi ba maza ba a gidan nan niko yanayin aikin nasane yake haka har dare ko wani lokaci dan gara yau ma ya dawo gidan nan yau da wuri.
Dan murmushi nayi ina gyara zamana ba tare da yin magana ba a lokacin sai naji ya jamal na fadin kila ta gajine da zama ai.
Ina fa gajiya ai bata dade da fitowa ba kazo kila dai don ta ganka zaune wurin nan ne take son ta tashi.
A,a mama ya jamal ai tun ina gidan mami mun saba dashi yana daga cikin masu tausaya mi a lokacin dashi dasu ya mamud .
Mu din ne bama tausaya maku ashe ta fada tana kallona a cikin zolaye nace da sauri a,a mama ba haka nake nufi ba wallahi kowama yana sona sosai wallahi.
Ai baki sani ba zainab wallahi ban gama danin halinki ba sai a dan zaman nan namu nan yanzu na kara tantace koke waye.
Gaskiya jafar yayi dacen mata idan kun dore a haka don ba ko wace sarakuwane tasan darajan iyayyen mijinta kamar yadda kike nunawa din.
Dadin wanan yabon da mama tayi min a yanzu naji na dukar da kaina ina dan murmushi kasa kasa naji tace kai gaka ba wani sakin fuska kakewa dan uwanka ba kwanan nan aida gobe sai mu rokeshi mu dan fita yawon mike kafa .
Tunda hjy dai taji sauki ba kamar yadda mukszo kasan nan da ita ba a cikin tashin hankali lokacin.
Taji sauki yanzu kan sai dai kuma yanzu data dawo zata fara fitina da mutane kamar yadda ta saba yi a kullun .
Dakuwa mama ta mika mai daga inda take zaune tana fadin ja,iri ai kuma naga hankalin ku ya tashi ai data kwanta ciwo.
Yana dariya ya mike tsaye yana fadin mama ni zan shige akwai dan wani aiki da zanyi matar yaya saida safe ke nan ya fada yana kallona.
Har muka tashi a gurin ya jamal dake dakin shigewan mu yana jin mu nikan ina shiga dakin ban daki na shiga na dauro alwala na fito.
Nafilan da na saba yi duk dare kafin in shiga wanka nayi kafin in dora da shafa,i da wutiri na mike na gyara jikina tsab yau da yake mun dan dauki lokaci muna fira a falon sai yasa ban samu zuwa na kwanta a makwancina da wuri ba.
Na gama tsab na jawo kofana lokacin wata zuciya tana fada min inyi kwanciyana kawai a dakina tunda dare yayi a yanzu.
Saidai na wuce kada hakan ya jawo min laifi a wurin shi kuma tunda mun aje hakan dashi tun zuwan mu garin.
Na fito na jawo kofana na rufe na nufi hanyar part din shi kai tsaye sai dai nayi mamakin ganin kofan a rufe a ranan.
Murdawa nayi don ina jin dan kida yana tashi a ciki yasa nasan baiyi barci ba a lokacin idon shi biyu wata kila yana falke yana sana,arshi ta latsan waya ko computer.
Kofan na dan duka kusan sau uku a lokaci daya naji na a bude ba don haka nayi niyar juyawa in koma dakina.
Naji ana bude kofan haka yasa ni waigo don na koma in shiga tunda ya bude part din a yanzu.
Saidai ana budewa ne idona yayi tozali da wani farin matashi a tsaye daga shi sai tawul daure a kungun shi yana rike da kofi a hannun shi da wani abu a cikin sa.
Da mamaki nake kare mai kallo a cikin wani yanayi dana kasa gane koshi waye da har ya shigo part din yaya din kuma gashi daga shi sai dan tawul a jikin shi.
Muryan yaya naji daga bayan shi dake fitowa daga cikin daki yana fadin who is there ?
Cikin tambayawa sai saurayin ya jaye daga kofan don yaya din ya hangoni shima dai yana daure da towel kamar daurayin na farko.
Wani irin faduwa gabana yayi lokaci guda nake kallon shi da mamakin ganin haka karara a fuskana.
Yanayin fuskan shine ya canza lokaci guda munayin arba da shi a wurin yake fadin ke mekikeyi har yanzu baki kwanta ba.
Saida nayi mai wani kallo na raini na sauke akan cup din dake hannun shi na juya ba tare da na bashi amsa ba na koma dakina na rufo da makulli.
Saman gado na fada lokaci guda wanan karon ban iya yin kuka ba sai tambayan kaina nake me nagani me sukeyi haka a ciki ?
Ta yaya shi yaya zai yarda ya kawo wani bako a part din da muke kwana a tare har zai yarda wani bako yazo haka ya kwana a ciki harda tubewa haka dashi.
Anya waiko yaya yasan addini kuwa yasan abinda shari,a ya tanada kuwa yau aiko matsayin kanwarsa nake bazai kawo wani kato a part din shi ba yasan ina cikin part din kuma.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
Ban fito daga dakin ba sai dana kwatanci fitan shi a gidan don wanan abin na daren jiyan daya tsaya min a raina.
Ina mamaki duk dakunan dake wanan gidan ya jafar ya rasa inda zai sauke bakon shi sai part din shi alhalin yasan bashi kadai bane a part din nima a nan nake kwana.
Anya kuwa ya jafar yasan addini kuwa sosai ai ko ba matar shi nake ba zaman kanwarshi nakeyi a gurin shi balle wanan kasan mutane da nazo ta dalilin shi.
Ya kamata ace ya tsare min mutumcina da kimana na ya mace a gurin kowa balle kuma ina zaman matarshi ta sunna a yanzu.
Idona kodai kodai sai dan fuskana daya kara yin fau ya wani zuke saboda kwana a kusan rayen da naye a daren jiyan .
Nayi mamakin ganin ya jamal a gida shi da yake fita tun safe zuwa duban hjy a asibiti sai gashi yau na ganshi a gida tare dasu mama a falo zaune.
Gaba dayan su ido suka zuba min har na karaso inda suke zaune ban zauna ba saida naje gaban mama na tsugunna na gaida ita da kwana.
Kafi in juyo wurin ya jamal shima na gaida shi ta amsa tana fadin yanzun ko maman ku ta bugo waya tana tambayan ki nace baki tashi ba tukun.
Ashema kina falke ban sani ba na tashi tun dazun mama bandai fito bane kawai ina ciki ina fitar da kayan wankina.
Wurin halimatu na juya ina fadin halimatu lafiya kuwa don yanayin ta danaga ya canza lokaci guda.
Ta dan nisa tare da fasin yayan mu ina kwana ashe ba barci kikeyi ba ma ?
Lafiya kalau take don yanzu take muna zuba a nan tana bamu labarin karatun ta ana dariya kece ma dai yanayin ki ya nuna kamar dai baki da lafiya yau.
Lafiya ta kalau mama na bata amsa ina mikewa tsaye sai naji halimatu na fadin yayan mu ina wanan rigan da nazo dashi sabo shi nake son in saka yau jumma,a.
Yana daki mana ki duba na bata amsa ina zama sai take fadin ban ganshi bane tunda mukazo kuma naga kin dauko min shi.
Na dauko mana yana daki ki duba kafin in gama magana mamata mike tana fadin barin kdan kewaya na fito yanzu da wanan rigiman na sadiya don ni kadai ke kiranta da halimatu kamar yadda muka saba tun a gida.
Barin mama wurin yayi daidai da barin halimatu don haka aka barni dagani sai ya jamal zaune a wurin.
Sai dan shiru ya biyo bayan hakan can na dago kai na dan kalleshi nace ya jiya ya jafar ya ban mamaki a gidan nan.
Banso na fada ma wanan maganan ba amma ya zama dole in fada mashi a yanzu don shi kanshi yaya yasan haramun ne sauke bako haka balagage a part din shi kuma yasan ina a cikkn part din.
Wani kallon mamaki ya jamal ke min hakan ya hanani ci gaba da maganan da nake son fada a lokacin.
Kai naga ya girgiza yana fadin nasan ba zaki so hakan ba idan kin gani don ke ba jahilan addini bace zainab don nasan kinsan kanki duk da kina yarinya karama.
Da sannu zaki fahinci abinda ni na kasa fada maki daga cikin halayai shi saidai ke wani mataki kika dauka da kikaga hakan ?
Na bude baki da zuman magana naji halimatu na fadin nifa ban gani ba yayan mu sai kuma muryan mama tana fadin kijeki duba mata tunda yau fitina take ji kan riga kamar karamar yarinya dake tana hararan ta.
Mikewa bayi don bin umurnin mama din muka jera zuwa ciki da halimatu din muna shiga dakin take fadin nafa ga rigan yayan mu.
Dama ina sin ki tasone in fada maki abinda mami ta fada a kanki da ta kira wayan wai cewa tayi dake wai kece yar mulki dan tallaka bai iya samun wuri ba za a ce har yanzu kina kwance kina barci.
Inji mami din ta fadi hakan don Allah daga yau kome mami ta fada a kaina kada ya kara damun ki kuma ki bar fada min don in banji ba banji bane kin gane ko ?
Ta gyada min kai alaman eh nace ai sai ki dauki rigan ki saka a jiki kada su fahinci abunda kikazo fada min ke nan yanzu a daki.
Tace ai ya jamal ya ce mata mulkin me kikeyi bayan ke ake cuta a kullun don dantane ai mai mulki sai tayi dariya tana fadin yai min daidai ai ba dai taji dadi a gidan nan ba wallahi tunda tace ita yar naci ce da kwadai zataga wullakanci saita raina kanta wallahi.
Niko basu san ina jin komai ba don ina tsaye daga kofan shiga part din mu nake jin komai.
Ido na tsura mata ina mata wani irin kallo kafin ince watau halimatu bakya ji ko saidai da kika fada min komai yanzu.
Ai na bari tunda kince in bar fada maki wanan din ne kadai na fada tana wani turo baki a gaba tare da daukan kayan dake gabata data fitar ta saka ta fice a dakin.
Zaune ta barni ina faman tunane sai yaushe mami zata daina hattarana kan dan ta ne dan da ba wani dadin zama dashi nake ji ba a tare dashi.
A hankali na mayar ds idona na runtse wuri daya don yanzu na daina wanan ruwan hawayen da nakeyi saidai yawan tunane kawai da shiga halin damuwa.
Duk aikin da yakeyi a ranan rashi bace yake idan ya tuna abinda ya faru a daren jiyan tsakanin mu ya rasa laifin waye a cikin mu har hakan ya faru.
Shin laifina zai gani ko laifin Nabil daya bude kofan ko kuma laifin shi da sakacin shi yasa har hakan ya faru.
Da bai bada daman in shigo shiyan in dinga kwana saboda dan maganan da mama tayi ba da duk haka bai faru ba a daren jiyan.
Inda Allah ya gyara banga komai daya faru ba a tsakanin su da tashin hankalin da zai shiga a yau yasan yafi wanan girma.
Da yanzu asirin shi ya gama zubewa a idon kowa don yasan ba zan iya rike kaina ba a lokacib mutane zan tara masa a gida don wauta.
Gashi har raini yana son shiga tsakanin mu don dan abinda idona ya ganar min ranan yakai yanzu ban tsoron shi kamar da can baya.
Ji itin kallon dana watsa mai a daren jiyan da sauri ya tambayi kanshi ko dai yarinyar nan tasan abinda nake yine tayi min irin wanan kallon ya tambayi kansa.
Da sauri ya girgiza kanshi tare da fadi a cikin hausa kai ina bata gane komai ba kawai dai nike tunanen hakan.
To wanan kallon tsanar fa na meye take min shi haka a daren jiyan don kawai ganin wanan gay din a karo na farko a part dina ?
Koma dai meye ya zama dole in canza komai yadda wani bazai taba fahintar komai ba saidai jamal fa ya tambayi kansa yana dan murza goshin shi.
Idon shi ya lumshe yana dan juya kujeran da yake zaune a kai ya zurfafa a cikin tunane.
Karshe ya furta a fili wama zai yarda da wanan idan har sun fada tunda ba ganina akayi dumu dumu ina aikatawa ba ai.
Zan fara da zainab don dole in tsawata mata kan ta fara zargina da wani abu na tabbatar da haka zata ja bakinta ta rufe gum.
Har yamma ranan bai samu tsinana komai ba a office ya dai kula zuwan su a garin nan yana son ya jawo mashi koma baya aikin shi a yanzu don haka sai ya jajircewa abin.
Dama hakan yake gudu ya faru dashi gashi kuma yarinyar da yake dauka ba wayau komai a tare da ita tana shirin jawo mashi matsala babba.
Ya mike yana mamakin kansa wai yau shine da jin kunya da nauyin arinyar daya raina ma wayau ya fito daga office din driver shi yazo ya jashi saida suka hau hanya yake tambayan shi inda zasu tafi asibiti ya bashi amsa ba tare da dago kai ba.
Ya samu hjy a zaune tana shan fruit salad da jamal ya sayo mata don tana yawan shan yayan icce sosai tun a gida yasa tun ranan data fara sha take sa ya sawo matashi tasha don yafi mata wanan abincin nasu na kasan dadi a bakinta.
Turo kofan yayi da sallama sukai arba da jamal dake zaune a gefen gadon yana duban yadda take shan fruit din
Showing 210001 words to 213000 words out of 390011 words
To bari kuji shi wanan harkan da kuke ganin munayi kowan ku nan yasan da addinin shi bai yarda da hakan ba.
Idan baku sani ba yau ku sani a kullun ina mai nadaman shiga wanan harkan naku da kuka koya min wanda addinina da al,adana duka ya haramta wanan abin ga wanin mu.
Yau gaskiya nayi nadaman sanin ku a rayuwana tunda har zaku iya kallon kanina ku nuna mashi sha,awan ku a fili babu dayan ku nan da ban ganin girma da daran dan uwanshi koda yan aikin gidan ku ne.
Daga haka ya juya rai bace ya bude motarshi ya shiga yana kokarin barin su wurin ranshi a bace.
Ganin hakan yasa suka san ranshi ya gama baci sosai alokacin da maganan su don sanin halin shi da sukayine zai iya sharesu har abada ga baki daya daga wanan lokacin.
Ganin ya shiga mota yana kokarin tayarwa ya wuce suna bashi hakkuri ta hanyar daya dace yasa ya jamal din sauke numfashi yana barin wurin da yake tsaye yana sauraren su a cikin takaici ya shige gidan.
Babu kowa a falon kai tsaye ya wuce zuwa part din shi yana mai jin zafin hakan daya faru a zuciyar shi.
Yana jin da zai iya a ranan zai bar gidan dan uwan nasa ya koma Nigeria saidai hakan ba zai yiyu ba don dole ya tsaya kodon hjy dake asibiti da kuma mu da muke zaune a gidan cikin rashin sani.
Don haka yaba kanshi hakkuri yana mai fadi a ranshi cewa fushi yanzu ba nasa bane idan shi yai fushi da dan uwan nasa mu yaya zamu kasance kuma ?
Bamu hadu dashi ba bama wada yasan da dawowan shi gidan a lokacin sai bayan sallah magariba da muka fito falo muka ganshi ya fito falon ya samemu muka gaisa dashi a wurin.
Mamane ke tambayan shi kona biyun nan wai meke damun shi ita fa batagane yadda ya canza ba akwana biyun nan idan anyi magana yace ba komai alhalin ba haka tasan shi ba a baya.
Mama banu komai wallahi ni dai kawai yanayin garin nan ne bai mun ba mun saba a gida muna ganin yan uwa da abokai ko ina.
Ta katse shi da fadin kai banda abinka baka ganin yaran nan matane basa fita ko ina amma a haka sun sake jikin su suna sha,anin su a gidan nan cikin rashin damuwa.
Balle kai na miji kamarka kana nuna haka a yanzu mu mata muce me ta fada a cikin raha.
Daga inda nake na saci kallon shi na fahinci akwai wani abinda ya bata masa rai a lokacin saidai banyi magana ba fun zaman shi a wurin suna ta hiran su da mama kan ciwon hjy da ake samun saukia yanzu kan jikin nata .
Don ko yanzu za a iya sallaman ta ta dawo gida saidai dan binciken da suka tsaya yi a kanta ya hana a sallamota daga asibitin yanzu.
Mikewa nayi don tunanen daya addabi zuciyana a lokacin na dan kallesu ina fadin mama ni zan shiga daga ciki .
Ke ko tun yanzu muna nan muna rage dare don ni wanan shiga kwanan da wuri haka ya fara isata wallahi aiba jamal shi kadai zaman garin nan ya isa ba a yanzu harni nan zama wuri dayan nan ya isheni wallahi.
Gashi mijin ki dawowan shi ba maza ba a gidan nan niko yanayin aikin nasane yake haka har dare ko wani lokaci dan gara yau ma ya dawo gidan nan yau da wuri.
Dan murmushi nayi ina gyara zamana ba tare da yin magana ba a lokacin sai naji ya jamal na fadin kila ta gajine da zama ai.
Ina fa gajiya ai bata dade da fitowa ba kazo kila dai don ta ganka zaune wurin nan ne take son ta tashi.
A,a mama ya jamal ai tun ina gidan mami mun saba dashi yana daga cikin masu tausaya mi a lokacin dashi dasu ya mamud .
Mu din ne bama tausaya maku ashe ta fada tana kallona a cikin zolaye nace da sauri a,a mama ba haka nake nufi ba wallahi kowama yana sona sosai wallahi.
Ai baki sani ba zainab wallahi ban gama danin halinki ba sai a dan zaman nan namu nan yanzu na kara tantace koke waye.
Gaskiya jafar yayi dacen mata idan kun dore a haka don ba ko wace sarakuwane tasan darajan iyayyen mijinta kamar yadda kike nunawa din.
Dadin wanan yabon da mama tayi min a yanzu naji na dukar da kaina ina dan murmushi kasa kasa naji tace kai gaka ba wani sakin fuska kakewa dan uwanka ba kwanan nan aida gobe sai mu rokeshi mu dan fita yawon mike kafa .
Tunda hjy dai taji sauki ba kamar yadda mukszo kasan nan da ita ba a cikin tashin hankali lokacin.
Taji sauki yanzu kan sai dai kuma yanzu data dawo zata fara fitina da mutane kamar yadda ta saba yi a kullun .
Dakuwa mama ta mika mai daga inda take zaune tana fadin ja,iri ai kuma naga hankalin ku ya tashi ai data kwanta ciwo.
Yana dariya ya mike tsaye yana fadin mama ni zan shige akwai dan wani aiki da zanyi matar yaya saida safe ke nan ya fada yana kallona.
Har muka tashi a gurin ya jamal dake dakin shigewan mu yana jin mu nikan ina shiga dakin ban daki na shiga na dauro alwala na fito.
Nafilan da na saba yi duk dare kafin in shiga wanka nayi kafin in dora da shafa,i da wutiri na mike na gyara jikina tsab yau da yake mun dan dauki lokaci muna fira a falon sai yasa ban samu zuwa na kwanta a makwancina da wuri ba.
Na gama tsab na jawo kofana lokacin wata zuciya tana fada min inyi kwanciyana kawai a dakina tunda dare yayi a yanzu.
Saidai na wuce kada hakan ya jawo min laifi a wurin shi kuma tunda mun aje hakan dashi tun zuwan mu garin.
Na fito na jawo kofana na rufe na nufi hanyar part din shi kai tsaye sai dai nayi mamakin ganin kofan a rufe a ranan.
Murdawa nayi don ina jin dan kida yana tashi a ciki yasa nasan baiyi barci ba a lokacin idon shi biyu wata kila yana falke yana sana,arshi ta latsan waya ko computer.
Kofan na dan duka kusan sau uku a lokaci daya naji na a bude ba don haka nayi niyar juyawa in koma dakina.
Naji ana bude kofan haka yasa ni waigo don na koma in shiga tunda ya bude part din a yanzu.
Saidai ana budewa ne idona yayi tozali da wani farin matashi a tsaye daga shi sai tawul daure a kungun shi yana rike da kofi a hannun shi da wani abu a cikin sa.
Da mamaki nake kare mai kallo a cikin wani yanayi dana kasa gane koshi waye da har ya shigo part din yaya din kuma gashi daga shi sai dan tawul a jikin shi.
Muryan yaya naji daga bayan shi dake fitowa daga cikin daki yana fadin who is there ?
Cikin tambayawa sai saurayin ya jaye daga kofan don yaya din ya hangoni shima dai yana daure da towel kamar daurayin na farko.
Wani irin faduwa gabana yayi lokaci guda nake kallon shi da mamakin ganin haka karara a fuskana.
Yanayin fuskan shine ya canza lokaci guda munayin arba da shi a wurin yake fadin ke mekikeyi har yanzu baki kwanta ba.
Saida nayi mai wani kallo na raini na sauke akan cup din dake hannun shi na juya ba tare da na bashi amsa ba na koma dakina na rufo da makulli.
Saman gado na fada lokaci guda wanan karon ban iya yin kuka ba sai tambayan kaina nake me nagani me sukeyi haka a ciki ?
Ta yaya shi yaya zai yarda ya kawo wani bako a part din da muke kwana a tare har zai yarda wani bako yazo haka ya kwana a ciki harda tubewa haka dashi.
Anya waiko yaya yasan addini kuwa yasan abinda shari,a ya tanada kuwa yau aiko matsayin kanwarsa nake bazai kawo wani kato a part din shi ba yasan ina cikin part din kuma.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
Ban fito daga dakin ba sai dana kwatanci fitan shi a gidan don wanan abin na daren jiyan daya tsaya min a raina.
Ina mamaki duk dakunan dake wanan gidan ya jafar ya rasa inda zai sauke bakon shi sai part din shi alhalin yasan bashi kadai bane a part din nima a nan nake kwana.
Anya kuwa ya jafar yasan addini kuwa sosai ai ko ba matar shi nake ba zaman kanwarshi nakeyi a gurin shi balle wanan kasan mutane da nazo ta dalilin shi.
Ya kamata ace ya tsare min mutumcina da kimana na ya mace a gurin kowa balle kuma ina zaman matarshi ta sunna a yanzu.
Idona kodai kodai sai dan fuskana daya kara yin fau ya wani zuke saboda kwana a kusan rayen da naye a daren jiyan .
Nayi mamakin ganin ya jamal a gida shi da yake fita tun safe zuwa duban hjy a asibiti sai gashi yau na ganshi a gida tare dasu mama a falo zaune.
Gaba dayan su ido suka zuba min har na karaso inda suke zaune ban zauna ba saida naje gaban mama na tsugunna na gaida ita da kwana.
Kafi in juyo wurin ya jamal shima na gaida shi ta amsa tana fadin yanzun ko maman ku ta bugo waya tana tambayan ki nace baki tashi ba tukun.
Ashema kina falke ban sani ba na tashi tun dazun mama bandai fito bane kawai ina ciki ina fitar da kayan wankina.
Wurin halimatu na juya ina fadin halimatu lafiya kuwa don yanayin ta danaga ya canza lokaci guda.
Ta dan nisa tare da fasin yayan mu ina kwana ashe ba barci kikeyi ba ma ?
Lafiya kalau take don yanzu take muna zuba a nan tana bamu labarin karatun ta ana dariya kece ma dai yanayin ki ya nuna kamar dai baki da lafiya yau.
Lafiya ta kalau mama na bata amsa ina mikewa tsaye sai naji halimatu na fadin yayan mu ina wanan rigan da nazo dashi sabo shi nake son in saka yau jumma,a.
Yana daki mana ki duba na bata amsa ina zama sai take fadin ban ganshi bane tunda mukazo kuma naga kin dauko min shi.
Na dauko mana yana daki ki duba kafin in gama magana mamata mike tana fadin barin kdan kewaya na fito yanzu da wanan rigiman na sadiya don ni kadai ke kiranta da halimatu kamar yadda muka saba tun a gida.
Barin mama wurin yayi daidai da barin halimatu don haka aka barni dagani sai ya jamal zaune a wurin.
Sai dan shiru ya biyo bayan hakan can na dago kai na dan kalleshi nace ya jiya ya jafar ya ban mamaki a gidan nan.
Banso na fada ma wanan maganan ba amma ya zama dole in fada mashi a yanzu don shi kanshi yaya yasan haramun ne sauke bako haka balagage a part din shi kuma yasan ina a cikkn part din.
Wani kallon mamaki ya jamal ke min hakan ya hanani ci gaba da maganan da nake son fada a lokacin.
Kai naga ya girgiza yana fadin nasan ba zaki so hakan ba idan kin gani don ke ba jahilan addini bace zainab don nasan kinsan kanki duk da kina yarinya karama.
Da sannu zaki fahinci abinda ni na kasa fada maki daga cikin halayai shi saidai ke wani mataki kika dauka da kikaga hakan ?
Na bude baki da zuman magana naji halimatu na fadin nifa ban gani ba yayan mu sai kuma muryan mama tana fadin kijeki duba mata tunda yau fitina take ji kan riga kamar karamar yarinya dake tana hararan ta.
Mikewa bayi don bin umurnin mama din muka jera zuwa ciki da halimatu din muna shiga dakin take fadin nafa ga rigan yayan mu.
Dama ina sin ki tasone in fada maki abinda mami ta fada a kanki da ta kira wayan wai cewa tayi dake wai kece yar mulki dan tallaka bai iya samun wuri ba za a ce har yanzu kina kwance kina barci.
Inji mami din ta fadi hakan don Allah daga yau kome mami ta fada a kaina kada ya kara damun ki kuma ki bar fada min don in banji ba banji bane kin gane ko ?
Ta gyada min kai alaman eh nace ai sai ki dauki rigan ki saka a jiki kada su fahinci abunda kikazo fada min ke nan yanzu a daki.
Tace ai ya jamal ya ce mata mulkin me kikeyi bayan ke ake cuta a kullun don dantane ai mai mulki sai tayi dariya tana fadin yai min daidai ai ba dai taji dadi a gidan nan ba wallahi tunda tace ita yar naci ce da kwadai zataga wullakanci saita raina kanta wallahi.
Niko basu san ina jin komai ba don ina tsaye daga kofan shiga part din mu nake jin komai.
Ido na tsura mata ina mata wani irin kallo kafin ince watau halimatu bakya ji ko saidai da kika fada min komai yanzu.
Ai na bari tunda kince in bar fada maki wanan din ne kadai na fada tana wani turo baki a gaba tare da daukan kayan dake gabata data fitar ta saka ta fice a dakin.
Zaune ta barni ina faman tunane sai yaushe mami zata daina hattarana kan dan ta ne dan da ba wani dadin zama dashi nake ji ba a tare dashi.
A hankali na mayar ds idona na runtse wuri daya don yanzu na daina wanan ruwan hawayen da nakeyi saidai yawan tunane kawai da shiga halin damuwa.
Duk aikin da yakeyi a ranan rashi bace yake idan ya tuna abinda ya faru a daren jiyan tsakanin mu ya rasa laifin waye a cikin mu har hakan ya faru.
Shin laifina zai gani ko laifin Nabil daya bude kofan ko kuma laifin shi da sakacin shi yasa har hakan ya faru.
Da bai bada daman in shigo shiyan in dinga kwana saboda dan maganan da mama tayi ba da duk haka bai faru ba a daren jiyan.
Inda Allah ya gyara banga komai daya faru ba a tsakanin su da tashin hankalin da zai shiga a yau yasan yafi wanan girma.
Da yanzu asirin shi ya gama zubewa a idon kowa don yasan ba zan iya rike kaina ba a lokacib mutane zan tara masa a gida don wauta.
Gashi har raini yana son shiga tsakanin mu don dan abinda idona ya ganar min ranan yakai yanzu ban tsoron shi kamar da can baya.
Ji itin kallon dana watsa mai a daren jiyan da sauri ya tambayi kanshi ko dai yarinyar nan tasan abinda nake yine tayi min irin wanan kallon ya tambayi kansa.
Da sauri ya girgiza kanshi tare da fadi a cikin hausa kai ina bata gane komai ba kawai dai nike tunanen hakan.
To wanan kallon tsanar fa na meye take min shi haka a daren jiyan don kawai ganin wanan gay din a karo na farko a part dina ?
Koma dai meye ya zama dole in canza komai yadda wani bazai taba fahintar komai ba saidai jamal fa ya tambayi kansa yana dan murza goshin shi.
Idon shi ya lumshe yana dan juya kujeran da yake zaune a kai ya zurfafa a cikin tunane.
Karshe ya furta a fili wama zai yarda da wanan idan har sun fada tunda ba ganina akayi dumu dumu ina aikatawa ba ai.
Zan fara da zainab don dole in tsawata mata kan ta fara zargina da wani abu na tabbatar da haka zata ja bakinta ta rufe gum.
Har yamma ranan bai samu tsinana komai ba a office ya dai kula zuwan su a garin nan yana son ya jawo mashi koma baya aikin shi a yanzu don haka sai ya jajircewa abin.
Dama hakan yake gudu ya faru dashi gashi kuma yarinyar da yake dauka ba wayau komai a tare da ita tana shirin jawo mashi matsala babba.
Ya mike yana mamakin kansa wai yau shine da jin kunya da nauyin arinyar daya raina ma wayau ya fito daga office din driver shi yazo ya jashi saida suka hau hanya yake tambayan shi inda zasu tafi asibiti ya bashi amsa ba tare da dago kai ba.
Ya samu hjy a zaune tana shan fruit salad da jamal ya sayo mata don tana yawan shan yayan icce sosai tun a gida yasa tun ranan data fara sha take sa ya sawo matashi tasha don yafi mata wanan abincin nasu na kasan dadi a bakinta.
Turo kofan yayi da sallama sukai arba da jamal dake zaune a gefen gadon yana duban yadda take shan fruit din
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22Chapter 23Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32Chapter 33Chapter 34Chapter 35Chapter 36Chapter 37Chapter 38Chapter 39Chapter 40Chapter 41Chapter 42Chapter 43Chapter 44Chapter 45Chapter 46Chapter 47Chapter 48Chapter 49Chapter 50Chapter 51Chapter 52Chapter 53Chapter 54Chapter 55Chapter 56Chapter 57Chapter 58Chapter 59Chapter 60Chapter 61Chapter 62Chapter 63Chapter 64Chapter 65Chapter 66Chapter 67Chapter 68Chapter 69Chapter 70Chapter 71 Chapter 72Chapter 73Chapter 74Chapter 75Chapter 76Chapter 77Chapter 78Chapter 79Chapter 80Chapter 81Chapter 82Chapter 83Chapter 84Chapter 85Chapter 86Chapter 87Chapter 88Chapter 89Chapter 90Chapter 91Chapter 92Chapter 93Chapter 94Chapter 95Chapter 96Chapter 97Chapter 98Chapter 99Chapter 100Chapter 101Chapter 102Chapter 103Chapter 104Chapter 105Chapter 106Chapter 107Chapter 108Chapter 109Chapter 110Chapter 111Chapter 112Chapter 113Chapter 114Chapter 115Chapter 116Chapter 117Chapter 118Chapter 119Chapter 120Chapter 121Chapter 122Chapter 123Chapter 124Chapter 125Chapter 126Chapter 127Chapter 128Chapter 129Chapter 130Chapter 131