Karamin kwalin ya dauko yana kokarin budewa tare da fadin wanan naki ne sadiya zai taimaka maki wurin karatu sosai.
Da sauri na dago ido ina kallon shi da mamaki halimatun ce za a bawa laptop haka karami mai kyau da tsada.
Halima ta dan rike mai hannu tare da fadin yaya na gode Allah ya saka da alheri ya kara yawan arziki mai albarka yayi murmushi kawai.
Wanan abin yaban mamaki gaskiya shiru nayi da bakina har ya fita a dakin ya dago kai yana kallona tare da miko min sauran kwalayen dake gefen shi.
Nima ba wani magana ko nuna murna kan kyautan haka na karasa na amsa a can kasan makoshi nace dashi angode.
Na nufi gefen shi na aje tare da juya na duka ina tattara takardun dana bari a kasa ya bini da kallo yana dan girgiza kai ya mike tsaye zai bar dakin.
Sai kuma ya juyo yana fadin idan idan fa abincin da kuke tafiya dashi bai maku ba zaku iya magana su canza maku akwai komai idan babu zasu sayo ma.
Yayi kawai na basa amsa don ni haka kawai yanzu nake jin wani irin haushin shi a raina wanda na rasa dalilin hakan ni dai kawai haushinsa nakeji kawai.
Shima ya fita yana tunane a zuciyar shi don ya zaci zanyi murna sosai da wanan kyautar saidai kuma yaga sabanin hakan.
A fili yake fasin kai mata dai suna da kama da hawainiya yau ka gansu fari gobe baki ji wanan yarinyar har tasan wani abu can fushi da mutum yanzu .
Toma wai me akai mata take shan wanan kamashi da mutane haka ta nisanta kanta da shiga mutane ta kuma hana yar uwanta sakewa yanzu.
Ban yarda halimatu tayi amfani da su ba don yana fita dakin da murnan ta ta shiga budewa ina kallon ta saida ta gama budewa ta koma ga nawa ta fara budewa.
Laptop ne samfarin Apple da abin cajin shi sai wasu tarkace nasa a cikin kwalin ta koma ga dayan kwalin ashe wayace kiran iphone ya sayo min nina dauka duk takarcen laptop din ce duka ashe wayace a ciki.
Mamakine ya kamani kwarai da ganin haka bayan wanda ke hannuna baiyi komai ba a lokacin.
Haka na dauka ina kallo cike da mamaki sai naji banji dadin rashin godiyan da bai ma da muhinmamci koma dai me yakeyi kanshi ruwansa ai tunda har yai min alheri haka ya kamata in gode mashi sosai ai.
Muryan halimatu ne ya dawo dani ga tunanen tana fadin yayan mu sai ki ban wanan tshon naki ke nan ko ?.
Haba halimatu ya kamata ki tsaya a matsayin ki ko kin manta da cewa mu din diyan tallakawane wai ?
Koni kina gani da taka tsantsan nake takona a gidan nan don ban yarda na zurewa komai ba tunda auren nawa kila wa kala ne kindai san komai.
Ko yau ko gobe mami na iya cewa danta ya sakeni kinga sai mu koma gun iyayyen mu da zama ki fada min idan mun saba mun shagala a cikin daula haka ?
Idan mun koma gida halimatu waye zai bamu wanan dadin wani hali kikeson mu shiga a lokacin idan mun saba da wanan gatan haka ?
Kai ta dukar kasa tana wasa da hannayen ta nace niko wanan laotop din daya sayo maki ba zan yarda kiyi amfani dashi ba a yanzu balle wata waya can.
Saidai idan nawa zaki dauka ki dinga amfani dashi ba zan hanaki ba halimatu amma ki rike wanan abin sam wallahi ba yanzu ba gaskiya.
Ta dago kai da sauri don jin abinda na fada nace eh haka nace ko baki yarda da hakan bane yanzu in kira Inna in fada mata tunda ga waya na samu yanzu ?
Tace na yarda mana yayan mu baga shi zamu dinga amfani da naki ba nace haka nake son ji halimatu shiyasa nake jin dadin ki wallahi yar kanwata.
Haka na kwana da wanan abin har washegari banji dadin yadda ban nuna mai jin dadin abinda yasayo min ba.
Karshe dai na yanke shawaran inje in sameshi tunda ranan ba aiki nayi masa godiya don yasan na yaba da kyatan nasa gareni.
Na shirya tsab dani waini a dale zan shiga wurin maigida yasa na danyi kwaliya daga cikin ire iren kayan da yake sayo min a yanzu.
Halimatu na barcin ta hankali kwance saman gado har na gama shirina na fita dakin bata sani ba na jawo kofa na rufo.
Tunda na tun kari kofan haka kawai naji gabana yana faduwa bansan dalilin hakan ba gareni cikin daurewa har na karasa na tura kofan falon yana bude na sa kai na shiga da sallamana.
Duk da nasan ba lalai bane in sameshi a falon lokacin don yau ranan hutu ne ga kowa saidai ina shiga idona yai arba dashi a zaune saman kujera daga shi sai tawul a jikin shi daure.
Wanan Nabil din dan kasan Egypt yana kwance shima kamar yadda ya jafar din yake sai dan karamin tawul a jikin shi ya dora kan shi saman cinyar yaya danin suna dariya.
Innalillahi na fada da karfi tare da saurin juyawa na bar falon gurin sauri ma ban ko rufo kofan ba a yadda na sameshi haka na bar masu shi a bude don gigita.
Daki na koma na mayar da sauri na isa bakin gado na zauna gabana sai faduwa yakeyi fa fa fa fa kamar zasu iya biyoni nake gani nakai kallona ga kofan naga ai na saka sakata dana shigo.
Gudun kada ya biyoni a baya shi kanshi karo na biyu ke nan da nake ganin sa ba tufafi a jikin shi ko wani lokaci kuma tare da wanan shedanin mai abin mata.
Don ni yagin yan daudon garin mu dake suyan kaji da masa nake gani a gareshi ko yaushe idan na gansa a gidan.
Haka kawai nake jin tsanarshi a raina balle yanzu da nake yawan ganin sa a gidan tun da su hjy suka bar garin .
Yake yawan zama a gidan ko yaushe ko zamu hadu bangaidashi shima bai gaidani saidai ya wuce in wuce na kumayi warning din halimatu sosai kan kowa itama bata kula sha,anin sa sam.
Don ya koma kamar dan gidan don wani lokaci zaka ganshi a dining zaune yana cin abinci ko yana falo mu yana kallo ko wani abindai a gidan.
Tambayan kaina nagi wai ashe maza suna haka dama to aini banga mata suna wanan rashin kunya ba koda yan uwane .
Da zarab sun fara girma zasu fara boyewa junan su tsiraicin su su kuma nisanta jikin su ga kowa koda kuwa daki daya suke.
Wanan din hakan shine wayewan ko turancin koko zama da jajjayen fata yasa yaya yake kokarin barin addinin shi ne wai haka ?
Gaskiya shi kan yaya ya fita daban nake gani da yan uwan sa wai dama haka yake baida kunya ashe kana ganin sa da farko zaka dauka mutumin kwarai ne yasan addinin shi.
Ka ganshi kamar kamili a idanu wallahi na dauka shidin wani uztazune farkon ganina dashi da sanin danayi masa.
Gashi da tausayi ga idanu da kawar da kai ga kowa da yake tare dashi bai shiga harkan kowa kona yan uwansa kuwa.
Amma zuwan mu nan duk na raina wa yan nan halaiyan nasa ga baki daya sam baida riko ga addinin shi nake gani.
Ni banyi barci ba kuma ban fita ba ban yi wani abu a dakin ba har lokacin da halimatu ta tashi ta sameni a hakana.
Ta shiga wanka ta fito ta shirya cikin wani dan riga a jikin ta take fadin yayan mu muje mu karya a kasa ina zaune kamar an dasani a wurin .
Ban motsa ba kuma ban bata amsa ba har ta kara maimaita abinda ta fada ki je kici na fada ba tare dana kalleta ba .
Itama wani irin kallkn zargi take min lokaci guda har lokacin idona sai hasko mi yanayin dana samesu a ciki yake min.
Ko naje na hado muna ne ta fada na girgiza mara kai tare da mikewa don ban yarda in barta ta fita da wanan dan iskan dake gidan ba a yanzu tunda na gane nan ya kwana tunda a tube na gansa ai.
Irin tarbiyan da innan mu tabani na nisantamu da maza dama kowa nake kokarin ba halimatu a yanzu don sam ni ban yarda da tarbiyan su ba a kasan.
Tare muka fito muka zauna har saida taci ta koshi take fadin yayan mu ba zakici bane nayi dan murmushi na fara tsiyaya ruwan tea a cup sugar kadan na zuba na kafa kai ina kurba a hankali.
Shine ya fara fitowa nayi saurin kawar da kai daga kalon su saiga dayan ya fito wanan karon sunyi wanka sun saka tufafi a jikin su saidai ina ganin bai kula damu a wajen ba don ya fito yana waya tare da sauri ya fita.
Saiga shi Nabil din ya biyo bayan shi shima suka fice a tare na aje cup din ina jin wani iri a raina godiya na ga Allah halimatu bata kula dashi ba kartace zata gaidashi.
Tun wanan lokacin nikan ban fito ba ina daki haka nayi weekend din kumshe a dakin sai ko idan na dan fito da halimatu ba zan dadeba zamu koma ciki.
Bansan kome ya gani ba da daren lahadi muna shirin kwanciya sai gashi ya shigo dakin namu kallon halimatu da hankalinta ke gun waya yayi yana fadin halimaru .
Ya kamata dai a saka maku kayan kallo a part din nan tunda baku fita falo yanzu ku zauna ka barshi muma ba jimawa zamuyi a kasan nan ba gida zamu koma.
Yaushe ke nan ya tambaya ko gobe ne idan ka shirya sallaman mu na basa amsa ina kawar da idona garshi .
Baki shirya tafiya ba ke nan idan dai nine zan sallameku ashe na gane bakya son a zauna lafiya dai ?
Idan dai wanan dan isk, , , sai kuma nayi shiru kafin in sake fadin gaskiya ba zan iya zama gidan nan da wanan katon daka aje muna ba a gidan nan .
Wani kallo yai min da sauri yake fadin wani katon ko bakon nawa kike son kira da kato yanzu kina da hankali kuwa ?
Shiru nayi ban kara magana ba na dukar da kaina kasa shiru yayi shima ya ya tsura min ido na dan lokaci kafin ya juya ya fice a dakin.
Muryan halimatune ya dawo dani daga tunane yayan mu zamu koma gidane ko ?.
Wallahi nima ina son inje gida sa,adatu taga yadda na koma a yanzu duk sun san nafisu wayewa yanzu ?
Halimatu ki barni don Allah kin cikanu da surutu wallahi na fada a dan hasale yarinyar fa bini da idanu don tasan batayi min komai ba na hauta da fada haka.
Munyi haka dashi kwana biyu sai na bar ganin Nabil din a gidan nasa din maganan da mukayine dashi ya sallameshi .
Tun dana kula da hakan na danji sanyi a raina ranan har muka fito falo muka zauna a cikin sakewa don yan aikin sukan ba ruwan su damu basu kuma shigowa inda muke kasafai sai idan sun shigo yin wani abu a gurin mu din.
Tunda na samu waya yanzu akai akai nake kiran innan mu saidai ban fada mata matsalan danake fuskanta a gurin shi ba.
Idan ta tambaye mu muna lafiya nakance lafiyan mu kalau nakan bawa halimatu suyi ta hira da yan uwan mu tana basu labarin abubuwan da muke gani a nan.
Suma sukan labarta mata abindake gida har sukan zolayeta da ta dawo gida tace dasu sai tare da yayan mu idan zata zo mu koma tare.
Hakan nawa innan mu dadi a ranta takan nasa muna zaune cikin salama da jin dadin rayuwa nida mijina ke nan wanda take alfahari da hakan ko yaushe.
Idan mutane sun tambaya takan ce muna lafiya ita kan gaskiya sai sam barka don yanzu ta huta gaskiya don haihuwan diya mace yai mata rana a rayuwan ta.
Da ace innan mu ta sanda zaman hakkurin da nakeyi da bata furta hakan a kaina da zata kwanmace in dawo gida gabata zaifi.
Irin wanan tunanen nakanyi idan na tuna da alfaharin innan mu din a kan auren nawa da zata san halin da mijin nawa ke ciki dayi tir da Allah waidai da halin sa.
A nan falon ya shigo ya samemu nayi mamakin ganin sa gida a wanan lokacin don rabona ma da ganin sa tun ranan da mukayi wanan zancen dashi.
Ya shigo muna gaidashi ya amsa muna da kyat ya shige part dinshi binshi mukayi da kallo halimatu ke fadin kamar dai yayan mu baida lafiya fa ?
Nikan ban kara bi ta kansa ba tunda banga ya fito ba har muka shige dakin mu bai fito ba dare yayi ina shirin kwanciya naji waya na ana kira na dauka bakon layi ne na kasanbake kiran dashi.
Da tsoro na dauka na kara a kunnena muryan shine naji murya a ciki ciki yana fadin.
Zainab ki shigo banda lafiya sosai ki taimaka min don Allah ?
A dan razane na mike tare da jan hijjab dina na fita a firgice na bar dakin wanan karon ma a tsorace na shiga part din.
Baya falon nasa don haka nasa kai zuwa dakin da nake zaton shine na kwanan sa don nan din nake tsanmani dakin sa.
Da sallama a bakina na shiga na hangoshi saman gado sai faman juyi yakeyi yana wani irin nishi da kugi mai sauti tun daga kofan nake iya jiwo shi.
Da sauri na karasa kusa ina fadin yaya meya sameka a rude nake magana don bansan irin taimakon da zan bashi ba a lokacin.
Da kyar ya iya dago kai ya dan kalleni tare da min nuni da hannu yana fadin da kyar duba cikin fridge ki dauko min magani nan a wani kwalba fari.
Na juya da sauri zuwa inda fridge din yake na bude idona ne ya fara tozali da kwalaben giya dako ba a fada ba nasan na giyane duka.


ZAINAB IDRIS MAKAWA




Hannuna na rawa nake daga kwalban a hankali ina kallo daga wanda yai rabi sai wanda ya kusa karewa saiko wanda ba,a ma bude ba.
Wani iri nake ji a zuciyana naga kwalban da yai min kwatance in dauko mashi na dauka na koma da sauri har lokacin yana a yadda na barshi yana nishin .
Mika mai nayi zan juya naji yana fadi cikin wani yanayi ki taimaka ki bude min don Allah ki bani ba zan iya komai ba yanzu.
Dan hararan shi nayi babu wanan tausayin nasa a fuskana irin na dazunna balle marfin roban na zuba mai a marfin na mika mai ina kawar da kaina gefe daya.
Don na gane shi din ba abin tausayi bane gama wani labari dana karanta na wani mashayin giya da yadda giya take wahal dashi kuma bai daina sha ba.
Ki taimaka ki kaini bandaki na watsa ruwa ko zanji dan karfin jikina bayan ya miko min marfin ina kokarin rufewa.
Dago kai nayi da sauri na dan kalleshi kamar zanyi magana sai dai na dake don alama ya nuna yana jin jikin nasa sosai a lokacin.
Cikin daurewa na juya ba tare da yin magan ba na nufi bandakin na hada mai ruwan mai dan zafi
Na dawo na sameshi a kwance wanan karon saman kafet yake kwance a tsakiyan dakin shi.
Ban san lokacin dana kai durkushe ba gaban shi take idona ya fara fitar da hawaye lokaci guda.
Sai wani nishi yakeyi mai ban tsoro wanda hakan ya kara firgitani a fili baima san ina gaban shi ba don idon shi a rufe yake yana faman juyi.
Ko yaji kanshim jikina ko kuma zuciyar shi ta bashi ina gurin ne ya bude ido a hankali ya sauke a kaina.
Cikin wani irin murya yake fadin ki daure ki taimakeni zainab zan mutu yana mika hannun shi zuwa inda nake gurfane muryan shi tankar ba nasa ba.
A cikin rudu nace yaya mai zan ma yanzu wa zan kirama ya kaika asibiti shi zaifi ba zama gida da wanan ciwon ba tun kan dare yayi.
Ji yayi tankar ya rungumeni don wani irin sha,awan dake taso mai lokaci guda kamar ransa zai fita.
Ya lumshe ido ya mika hannunn shi ya riko hannuna yana fadin kirjina da marana kamar zai fashe wani irin ciwo yake min.
Ya danke hannuna sosai ji nayi jikin shi na wani irin kadawa tausayin shi ya kamani lokaci guda har na manta da haushin sa da nake ji a raina ina jin tankar na yaye masa ciwon ya huta da wahala.
A hankali na runtse idona don tausayin shi da nake ji ga kuma hannun shi daya rike nawa ina jin wani yanayi a tare dani.
Ga jikin
Showing 225001 words to 228000 words out of 390011 words