duniyan nan da abin cikin sa nake bata alherin shi a kullun.
Sai a asirina ya tono ga jamma,an duniya zuwa yanzu din kowa ya gama sanin koni waye a hakan nayi nadama ina fada maki ko yaushe kan shigana wanan harkan duk da ba zance ga lokacin dana tsinci kaina a hakan ba duk da nasan ko nayi rantsuwa ba mai taba yarda da zancena a yanzu.
Tsam naji a duk kan ilahirin jikina don jin saukan hannun ya jafar da nayi ya sauka a jikina wanda hakan ya sani dan razana da yin hakan da yai min din a daidai lokacin da ban taba tsamanin hakan ba a gareshi.
Dan tsoratan da nayi din yayi daidai da runtse idanuwan shi a daidai lokacin yana jin wani bakon yanayi yana sauka mai wanda hakan yake ganin sa kamar zai aikata wani sabone gayin rikon da yai min din a lokacin.
Sai dai kuma duk da hakan ya kasa cire hannun shi daya riko ni dashi a jikina din a lokacin maimakon ya cire din kamar yadda zuciyar shi take gargadin shi da yi saima kara rikoni da yayi a lokacin ya matseni sosai a jikin shi .
A daidai saitin kunne yake magana yana fadin kamar mai rada kin san me zainab ban samu ko fadin a, a ba gareshi a yadda nake razane dashi a lokacin.
Tsorona daya shine kada ya matseni yace zai min dole ta baya wanda hakan tun lokacin da umma ta umurceni da zuwa dakin shi koda bana son hakan idan nazo na saba zanji duk abinda nake ji a kanshi ya gushe min a zuciyana.
Wanda ni ba komai nakewa tsoron haka ba sai gujewa bacin rana irin wanan yaga kamar ni din irin mazan da suka saba mu,amula da sune yazo ya halakani a banza banji ba ban gani ba.
Kaduwa sosai jikina keyi naji yana fadin ko kowa bai yarda da rantsuwana ba aduniyan nan ke zainab nasan zaki yarda da abindana fadi a kaina a ko inane kuwa zaki shedeni a kan wasu halaiyana da kika sani a baya da yanzun da nake fadin na daina din a yanzu.
Duk da tsoron da nake ji a lokacin nasa hakan baisa hankalina ya gushe har na kasa fadin yardan Allah da amincewan shi a yanzu gareka yafi na kowa da zaima ka.
Don Allah subbahanahu kaiwa sabo kuma yafiyan shi zaka nema a yanzu don ya yafe maka kurakuran ka yaya.
Komawa ga Allah gareka a yanzu shine babban abinda ke gaban ka duk na mutane mai saukine .
Allah zai iya sa mantuwa ga zukatan wasu su manta da ka taba aikata hakan a baya, tuban ka zai iya sa Allah ya shafar dasu komai a kanka ga baki daya.
Banyi aune ba a wanan lokacin da nake maganan sai ji alaman kukan nadama da naji yana yi a lokacin.
Nima kukan ne yazo min don ko banza naga wani na kuka haka nake nima sai hawaye yazo min balle wanan da yake shakikina a yanzu mafi kusa dani da kowa a duniyan nan yana cikin wani hali na rayuwa.
Da kyat yayi shiru koshi wayan shi dake ta ringing ne a lokacin ya sa ya mika hannu ya dauka ba tare da yayi magana ba sai sauraren mai magana a lokacin da yayi.
Yana gama wayan ya kashe ya aje a gefe daya ya rufo hannayen shi gaba daya a saman jikina lokaci guda ya matseni ta yadda muke iya jin numfashin juna a lokacin a haka kowa da nasa kalan tunanen barci ya daukeni a jikin shi .
Misalin ukun dare ina barcin kamar a wahalce acan cikin barcin nake jin wani irin nisi a kusa dani wanda tun kan na bude idanu nasan inda nishin yake fitowa .
Shine duk da yana cikin wani irin yanayi hakan baisa ya raba jikina da nasa ba yana rike dani da hannun shi daya a jikin shi.
Yayin daya dafe maran shi da hannun na hagu yana yanka wani irin gumi tun daga kafan shi har zuwa kanshi .
Na tashi a rude ina kokarin kwacewa don na samu na taimaka mai a halin da yake ciki yake fadin kada ki daga nan zainab .
A wahalce yake magana a lokacin duk da na saba da ganin hakan wani lokaci wanan yanayin yafi na duk wanda yayi a baya muni sosai.
Can yakai ga wani irin zabura kafin ya kai ban daki ya fara wani irin kakarin amai kamar zai zubo mai kafin yakai bayin a lokacin.
Ganin hakan yasa dole na mike zaune ina binshi da kallo a cikin yanayin da yake din na ban tausayi da al,ajabi.
Don nasan wanan halin da yake ciki a yanzu yana da nasaba da rikon da yai min muka kwanta a tare ya jawo mai wanan wahalan haka.
Raina naji yayi wani irin baci lokaci daya na gyara zama ina hada kaida gwiwa na takure a wuri daya na dinga kuka a hankali.
Yafito bayin dafe da maran shi yana tafiya dakyat yazo bakin gadon ya dan zauna a gefe ya dukar da kanshi kasa kamar mai tunane.
Sauka nayi zuwa ban daki na dan dauki lokaci na gyara ko ina koda na fito na samu yana sallah a zaune na bishi da kallo.
Muna zaune ba wanda yai magana a cikin mu kowa na lazumin shi motsin da naji daga bayan mu yasa na dan firgita kamar anyi tsoki an fita daga dakin nashi lokacin naji da kunnuwana sai dai Allah ya gyara ban yarda na juya ba .
Wani irin iskane aka fara yi a wajan gidan kamar hadari ya yaso a garin ko guguwa mai karfi cikin dan lokaci kuma muka daina jin hakan.
A daidai lokacin ne na kula da yanayin da yaya da ke zaune a kusa dani yake ciki yana wani irin kaduwa kamar mai jin sanyi ko zazzabi mai karfi a lokacin.
Ni kan naga ta kaina a wanan rayuwan yau nice auren dan giya dan luwadi dan mafia kuma ashe shiga kungiyan ma bala,ine kala kala a rayuwan mutum irin haka.
A dadafe mukaga safiya dashi saidai wanan karon akwai bambamci ga yadda na saba ganin shi a baya idan yayi ciwon shi gari yawaye sai ya mike tamgararan.
Wanan karo kan yasha bamabam da wacan din don zuwa safe kamar ciwon karuwa yakeyi a lokaci.
Sai amai da gudawa yakeyi sosai wanda hakan ya tayar min da hankalina ya mamud na kira a boye don yayi min kashedin fadawa kowa halin da yake ciki din a ranan.
Ba bata lokaci ya iso gidan layina ya kira na fada mai ina sama wurin shi ya sameni a nan saman dakin shi do ban fito ba har lokacin.
Yana ganin yanayjn da dan uwan nasa yake cikine ya rude tare da tambayana zainab yaushe ya fara hakan nace dashi.
Lafiya lau muka kwanta dashi zuwa rabin darene hakan ya faru dashi har wanan lokacin wanan kan ba abin kyalewa bane dole mu sanarwa mami taji ya mamud din ya fada .
Layin mami ya fara nema ya fada mata nan ta hau fada don me ba a wuto dashi asibiti ba tun dazun ko so muke ya halaka a gida.
Mami kizo fa wanan kan ba abin kaiwa asibiti bane gaskiya sai jikinta yayi sanyi ta koma magana a hankali tana fadin .
Wani irin yanayi ne mamud kuyi wani abu don Allah kafin na karaso ta fada hankali tashe me zamu iyayi ga hakan mami sai kawai ta fashe da kuka ya kashe wayan.
Ina jin haka nace yaya ina zuwa na fita zuwa dakina bincike na fara yi kafin ingane maganin da tsohuwa kakan maya tayi min bayani ranan idan naga irin yanayin nan tare dashi.
Na fito da sauri zuwa kitchen na jona heater dan kankanin lokaci ruwan ya tafasa na hada komai na nufi dakin yan aikin gidan sai faman gaidani sukeyi da kwana ban tsaya binta kansu ba yadda na saba sama sama nake amsawa idan sun gaida ni din.
Dakin na nufa na samu yaya ya kamashi zuwa bandaki sun fito na shigo dauke da cup din maganin ina mashi sannu.
Saidana aje cup din nake fadin ya ko zaisha wanan maganin kafin mami tazo mu gani yace zaisha mana zainab kin hadane ya fara sha agani.
Na dan zauna ina fifitawa har yayi sanyi don ta fada min sai yayi sanyi sosai zaisha kamar yadda tace din haka nayi komai daki daki.
Yana kurbawa na farko ya saki wani irin gyatsa mai karfi lokaci guda sai kuma ya fara hamma ba kakautawa muna tsaye muna kallon shi nida ya mamud din .
Ya kara sake wani irin gyatsa har mai warin tsiya saida muka kawar da kanun mu ga kallon shi da sauri anan kasan ya leme sai barci .
Dan uwan na fadin ka hau gado idan barci zakayi zaifi ma dadi jafar ina har barcin ya kwashe shi ko a lokacin.
Daga inda nake na sauke ajiyan zuciyar da har ya fito fili ban sanda hakan ba sai ji nayi ya mamud na fadin .
Zainab kiyi hakkuri da wanan jerabawan da Allah ya aiko maki dashi haka tun ran gini ran zane Allah ya rubuto kece zaki shiga a cikin wanan wahalan haka.
Godiyan mu ga Allah da hakan ya kasance kece a gidan shi a matsyin matar shi a yanzu da wata ce ko wace mami ke gani a lokacin itace ta dace da jafar din ai da tuni zancen ya wuce nan ko.
Amma yanzu kinga tun mami naganin kwadayine har yanzu ita da bakinta ta gane gaskiya tana godiya da haka ya kasance kece a matsayin mata a gareshi.
Nasani zainab watarana mami zata rokeki gafara da bakin ta kan hakan tunda yanzu tasan abunda Allah ya shirya a zaman ki dashi haka.
Hakuri yana da dadi zainab don hakkurin ki yayi muna amfani kowa yanzu ya sani Aisha kanta jiyan nan nake jin tana fadin bata san da wani ido zata kalleki ba a yanzu.
Ko yanzu na sani maganin da kika bashine Allah ya taimakeshi ya samu barcin nan da yayi a yanzu don wallahi da badon Allah ya gyara ba yasha wanan abin da bansan me zai faru ba zuwa yanzu gareshi.
Hawaye ke fito min a idona na kurawa inda yaya din yake kwance ido kawai ina kallon shi ga mutum har mutum idan ka ganshi amma ya samu akasin rayuwa a tare dashi.
Muryan ya mamud din ne yake fadin ni nasan babu yarinyar da zata zauna da jafar ko na tsawon wata daya a wanan hakin haka da yake ciki.
Yanzu ne kowa zai gane shi mutum yana da ranan shi ta hanyar da baka taba zato ba don ance ke yar tallakane baki cancanci auren shi ba a lokacin.
Sai Allah ya nuna muna tallaka yana da ranan sa sosai don zaiyi abinda kudi baya iyayiwa mutum shi a rayuwa don na tabvatar da zabin mami din ya aura a lokacin da yanzu wallahi duniya ta gama sanin komai a yanzu.
Sallaman mami da su jamal ne da suka shigo hankali tashe dakin ya katse shi ga maganan da yakeyi a lokacin.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
ASSALAMU ALAIKUM WARAHAMATULLAH JUMMA,AT MU BARAK YAN UWA MUSULMAI ALLAH YA SADAMU DA ALHERUN DAKE CIKIN WANAN RANAN AMIN, , , , ,
Bin yadda yake kwance a cikin wahala kowan su keyi jamal ke fadin yana numfashi kuwa ?
Yanayi ya mamud ya bashi amsa ai don zainan ma ta taimaka ta bashi wani magani dazun ya sha shine har yake hakan.
Da sauri mami ta juyo ta sauke kallon ta gareni tana fadin me kika bashi ya koma haka zainanb me kika shirya kike son ganin bayan shi a yanzu.
Wallahi idan wani abu ya samu dana bazan taba yafe maki ba kema sai naga bayan ki har iyayyen ki.
Kai haba mami wanan maganan bai dace ba haka dan Allah ba don yarinyar nan data take tsaye a kanshi ba ai bamu san halin da yake ciki ba.
Wa yasan hanlin da suka tsunci kan su zuwa wanan lokacin da badon ita data bashi wanan maganin ba dazun da wallahi kila da yanzu mun rashi ga baki daya har abada.
Itace tafi kusan dashi take zaune dashi tasan irin laluran shi a yanzu don haka ba zamu zargeta ba mami, kan halin da yake bayan duk munsan da abinda yake damun shi a nan.
Jamal ne ya fara fadin gashi kuma mami kai brother asibiti haka kamar tonon asirine a wurin ki a garin nan sai nake ganin kamar a samo yarddaden likita a dauko shi gida yazo ya dubashi a nan.
Nima haka nagani ya mamud ya fada daga gefe mami kan ta koma ta zauna saman kujera ta kurawa dan nata dake kwance a kasa cikin wani hali sai hawaye take sakewa a lokacin.
Bata iya furta komai a wanan lokacin don bakin ciki da takaici da yai mata yawa a zuciyar ta ina zata kai wanan abin kunyar da jafar ya dauko mata a cikin iyalin ta yanzu .
Kai kome zasu fada a kaishi asibiti kawai wallahi a dubashi a san halin da yake ciki zaifi jalal ya fada.
Nima dai abinda naga yafi ke nan Aisha ta sake fada daga inda take zaune a takure a lokacin na dago kai da sauri tare da fadin .
Don Allah kada ku kai shi asibiti a cikin wanan halin da yake ciki haka ku taimaka ku rufa mai asiri da akaishi asibiti gara dai likitan yazo gida ya duba shi don Allah.
Ya mutu kike so Aisha ta fada a hasale tana kallona kamar zata cinyeni danya a lokacin da take wanan maganan cikin kunan rai take tambaya na hakan .
Mami ta dagp kai tana fadin gaskiya zainab ta fada fitar dashi haka zuwa asibiti tonan asirine kamar yadda kuka fada da farko.
Don haka kai mamud wani likita kake ganin zamu nemo a wanan case din nasa yanzu har lokacin idon ta na kansa inda yake kwance tana kallon shi.
Ina gefe ina sauraren shawaran nasu kai mutum dai ba abakin komai yake ba lafiya itace jarin ga mutum da ya kumce ma ka rasa komai, komai arzikin ka kuwa.
Wani likita ya mamud din ya kira yace a bashi dan lokaci yana tafe duk zaman da nakeyi wurin bakina na dauke da addua a lokacin.
Tun ina yi a boye har na fara fitar da sauti ina karatun a fili duk suka bini da kallo kamar kullun amanal rasulu nake karanta mashi sai yasin haka ma wanan lokacin shinakeyi a hankali suna saurarona.
Dakin yayi tsit sai muryana dake tashi a lokacin can ya dan motsa hannun shi kadan alaman yana son ya falka a lokacin.
Gaba dayan mu ido muka zuba mai kafin can ya bude idanun shi da kyat yana fadin zainab bani ruwa in sha don Allah ba wanda zai gane me yake fadi a lokacin don muryan shi daya dakushe bai fita sosai.
Na dago kai na dan kalli ya mamud dake kusa damu ina fadin wai ruwa yake son sha.
Bashi wanan can da kika rufe dazun ya sha tunda a kwai sauki sosai daya sha shi dazun na tashi a daidai lokacin da mami ke fadin ruwan meye wanan din sauran kuma duk suka bini da idanu har na dauko ruwan dake rufe a gefen gado cikin cup din glass.
Na kawo mai tare da dan kiran sunan shi ina fadin yaya ga ruwan ya bude idanun shi da kyat ya sauke a kaina.
Dan yun kurawa yayi don ya sha ruwan dake hannuna ya kafa kai yaja sosai kafin kuma ya dakata na dan lokaci ya dago kai ya kalleni.
Muryan ya mamud din ne yake fadin shanye mana jafar don Allah yana da amfani a gareka sosai.
Ya dan daga kai ya kalli inda ya mamud din yake kafin ya mayar da kanshi ga kallon dakin ga baki daya sai a lokacin yasan a kasa saman ties yake kwance don neman wa jikin sanyi a lokacin.
Muryan mami da yaji tana fadin kasha maganin mana jafar ka tsaya kana kallo kuma da sauri ya juya inda take tana zaune tana magana saman kujeran dakin nasa.
Sannun da yan uwan ke masa ne ya kara juyawa wurin su yana kallon su kamar bai ganesu ba a lokacin.
Karbi ruwan kasha yaya na fada daga inda nake tsungune ina bashi ruwan da zai sha ya juyo a hankali ya karbi ruwan daga hannuna.
Tunda ya kafa kai bai cire a cup din ba sai daya shanye ruwan ga baki daya ya miko min cup din na karba
Showing 357001 words to 360000 words out of 390011 words
Sai a asirina ya tono ga jamma,an duniya zuwa yanzu din kowa ya gama sanin koni waye a hakan nayi nadama ina fada maki ko yaushe kan shigana wanan harkan duk da ba zance ga lokacin dana tsinci kaina a hakan ba duk da nasan ko nayi rantsuwa ba mai taba yarda da zancena a yanzu.
Tsam naji a duk kan ilahirin jikina don jin saukan hannun ya jafar da nayi ya sauka a jikina wanda hakan ya sani dan razana da yin hakan da yai min din a daidai lokacin da ban taba tsamanin hakan ba a gareshi.
Dan tsoratan da nayi din yayi daidai da runtse idanuwan shi a daidai lokacin yana jin wani bakon yanayi yana sauka mai wanda hakan yake ganin sa kamar zai aikata wani sabone gayin rikon da yai min din a lokacin.
Sai dai kuma duk da hakan ya kasa cire hannun shi daya riko ni dashi a jikina din a lokacin maimakon ya cire din kamar yadda zuciyar shi take gargadin shi da yi saima kara rikoni da yayi a lokacin ya matseni sosai a jikin shi .
A daidai saitin kunne yake magana yana fadin kamar mai rada kin san me zainab ban samu ko fadin a, a ba gareshi a yadda nake razane dashi a lokacin.
Tsorona daya shine kada ya matseni yace zai min dole ta baya wanda hakan tun lokacin da umma ta umurceni da zuwa dakin shi koda bana son hakan idan nazo na saba zanji duk abinda nake ji a kanshi ya gushe min a zuciyana.
Wanda ni ba komai nakewa tsoron haka ba sai gujewa bacin rana irin wanan yaga kamar ni din irin mazan da suka saba mu,amula da sune yazo ya halakani a banza banji ba ban gani ba.
Kaduwa sosai jikina keyi naji yana fadin ko kowa bai yarda da rantsuwana ba aduniyan nan ke zainab nasan zaki yarda da abindana fadi a kaina a ko inane kuwa zaki shedeni a kan wasu halaiyana da kika sani a baya da yanzun da nake fadin na daina din a yanzu.
Duk da tsoron da nake ji a lokacin nasa hakan baisa hankalina ya gushe har na kasa fadin yardan Allah da amincewan shi a yanzu gareka yafi na kowa da zaima ka.
Don Allah subbahanahu kaiwa sabo kuma yafiyan shi zaka nema a yanzu don ya yafe maka kurakuran ka yaya.
Komawa ga Allah gareka a yanzu shine babban abinda ke gaban ka duk na mutane mai saukine .
Allah zai iya sa mantuwa ga zukatan wasu su manta da ka taba aikata hakan a baya, tuban ka zai iya sa Allah ya shafar dasu komai a kanka ga baki daya.
Banyi aune ba a wanan lokacin da nake maganan sai ji alaman kukan nadama da naji yana yi a lokacin.
Nima kukan ne yazo min don ko banza naga wani na kuka haka nake nima sai hawaye yazo min balle wanan da yake shakikina a yanzu mafi kusa dani da kowa a duniyan nan yana cikin wani hali na rayuwa.
Da kyat yayi shiru koshi wayan shi dake ta ringing ne a lokacin ya sa ya mika hannu ya dauka ba tare da yayi magana ba sai sauraren mai magana a lokacin da yayi.
Yana gama wayan ya kashe ya aje a gefe daya ya rufo hannayen shi gaba daya a saman jikina lokaci guda ya matseni ta yadda muke iya jin numfashin juna a lokacin a haka kowa da nasa kalan tunanen barci ya daukeni a jikin shi .
Misalin ukun dare ina barcin kamar a wahalce acan cikin barcin nake jin wani irin nisi a kusa dani wanda tun kan na bude idanu nasan inda nishin yake fitowa .
Shine duk da yana cikin wani irin yanayi hakan baisa ya raba jikina da nasa ba yana rike dani da hannun shi daya a jikin shi.
Yayin daya dafe maran shi da hannun na hagu yana yanka wani irin gumi tun daga kafan shi har zuwa kanshi .
Na tashi a rude ina kokarin kwacewa don na samu na taimaka mai a halin da yake ciki yake fadin kada ki daga nan zainab .
A wahalce yake magana a lokacin duk da na saba da ganin hakan wani lokaci wanan yanayin yafi na duk wanda yayi a baya muni sosai.
Can yakai ga wani irin zabura kafin ya kai ban daki ya fara wani irin kakarin amai kamar zai zubo mai kafin yakai bayin a lokacin.
Ganin hakan yasa dole na mike zaune ina binshi da kallo a cikin yanayin da yake din na ban tausayi da al,ajabi.
Don nasan wanan halin da yake ciki a yanzu yana da nasaba da rikon da yai min muka kwanta a tare ya jawo mai wanan wahalan haka.
Raina naji yayi wani irin baci lokaci daya na gyara zama ina hada kaida gwiwa na takure a wuri daya na dinga kuka a hankali.
Yafito bayin dafe da maran shi yana tafiya dakyat yazo bakin gadon ya dan zauna a gefe ya dukar da kanshi kasa kamar mai tunane.
Sauka nayi zuwa ban daki na dan dauki lokaci na gyara ko ina koda na fito na samu yana sallah a zaune na bishi da kallo.
Muna zaune ba wanda yai magana a cikin mu kowa na lazumin shi motsin da naji daga bayan mu yasa na dan firgita kamar anyi tsoki an fita daga dakin nashi lokacin naji da kunnuwana sai dai Allah ya gyara ban yarda na juya ba .
Wani irin iskane aka fara yi a wajan gidan kamar hadari ya yaso a garin ko guguwa mai karfi cikin dan lokaci kuma muka daina jin hakan.
A daidai lokacin ne na kula da yanayin da yaya da ke zaune a kusa dani yake ciki yana wani irin kaduwa kamar mai jin sanyi ko zazzabi mai karfi a lokacin.
Ni kan naga ta kaina a wanan rayuwan yau nice auren dan giya dan luwadi dan mafia kuma ashe shiga kungiyan ma bala,ine kala kala a rayuwan mutum irin haka.
A dadafe mukaga safiya dashi saidai wanan karon akwai bambamci ga yadda na saba ganin shi a baya idan yayi ciwon shi gari yawaye sai ya mike tamgararan.
Wanan karo kan yasha bamabam da wacan din don zuwa safe kamar ciwon karuwa yakeyi a lokaci.
Sai amai da gudawa yakeyi sosai wanda hakan ya tayar min da hankalina ya mamud na kira a boye don yayi min kashedin fadawa kowa halin da yake ciki din a ranan.
Ba bata lokaci ya iso gidan layina ya kira na fada mai ina sama wurin shi ya sameni a nan saman dakin shi do ban fito ba har lokacin.
Yana ganin yanayjn da dan uwan nasa yake cikine ya rude tare da tambayana zainab yaushe ya fara hakan nace dashi.
Lafiya lau muka kwanta dashi zuwa rabin darene hakan ya faru dashi har wanan lokacin wanan kan ba abin kyalewa bane dole mu sanarwa mami taji ya mamud din ya fada .
Layin mami ya fara nema ya fada mata nan ta hau fada don me ba a wuto dashi asibiti ba tun dazun ko so muke ya halaka a gida.
Mami kizo fa wanan kan ba abin kaiwa asibiti bane gaskiya sai jikinta yayi sanyi ta koma magana a hankali tana fadin .
Wani irin yanayi ne mamud kuyi wani abu don Allah kafin na karaso ta fada hankali tashe me zamu iyayi ga hakan mami sai kawai ta fashe da kuka ya kashe wayan.
Ina jin haka nace yaya ina zuwa na fita zuwa dakina bincike na fara yi kafin ingane maganin da tsohuwa kakan maya tayi min bayani ranan idan naga irin yanayin nan tare dashi.
Na fito da sauri zuwa kitchen na jona heater dan kankanin lokaci ruwan ya tafasa na hada komai na nufi dakin yan aikin gidan sai faman gaidani sukeyi da kwana ban tsaya binta kansu ba yadda na saba sama sama nake amsawa idan sun gaida ni din.
Dakin na nufa na samu yaya ya kamashi zuwa bandaki sun fito na shigo dauke da cup din maganin ina mashi sannu.
Saidana aje cup din nake fadin ya ko zaisha wanan maganin kafin mami tazo mu gani yace zaisha mana zainab kin hadane ya fara sha agani.
Na dan zauna ina fifitawa har yayi sanyi don ta fada min sai yayi sanyi sosai zaisha kamar yadda tace din haka nayi komai daki daki.
Yana kurbawa na farko ya saki wani irin gyatsa mai karfi lokaci guda sai kuma ya fara hamma ba kakautawa muna tsaye muna kallon shi nida ya mamud din .
Ya kara sake wani irin gyatsa har mai warin tsiya saida muka kawar da kanun mu ga kallon shi da sauri anan kasan ya leme sai barci .
Dan uwan na fadin ka hau gado idan barci zakayi zaifi ma dadi jafar ina har barcin ya kwashe shi ko a lokacin.
Daga inda nake na sauke ajiyan zuciyar da har ya fito fili ban sanda hakan ba sai ji nayi ya mamud na fadin .
Zainab kiyi hakkuri da wanan jerabawan da Allah ya aiko maki dashi haka tun ran gini ran zane Allah ya rubuto kece zaki shiga a cikin wanan wahalan haka.
Godiyan mu ga Allah da hakan ya kasance kece a gidan shi a matsyin matar shi a yanzu da wata ce ko wace mami ke gani a lokacin itace ta dace da jafar din ai da tuni zancen ya wuce nan ko.
Amma yanzu kinga tun mami naganin kwadayine har yanzu ita da bakinta ta gane gaskiya tana godiya da haka ya kasance kece a matsayin mata a gareshi.
Nasani zainab watarana mami zata rokeki gafara da bakin ta kan hakan tunda yanzu tasan abunda Allah ya shirya a zaman ki dashi haka.
Hakuri yana da dadi zainab don hakkurin ki yayi muna amfani kowa yanzu ya sani Aisha kanta jiyan nan nake jin tana fadin bata san da wani ido zata kalleki ba a yanzu.
Ko yanzu na sani maganin da kika bashine Allah ya taimakeshi ya samu barcin nan da yayi a yanzu don wallahi da badon Allah ya gyara ba yasha wanan abin da bansan me zai faru ba zuwa yanzu gareshi.
Hawaye ke fito min a idona na kurawa inda yaya din yake kwance ido kawai ina kallon shi ga mutum har mutum idan ka ganshi amma ya samu akasin rayuwa a tare dashi.
Muryan ya mamud din ne yake fadin ni nasan babu yarinyar da zata zauna da jafar ko na tsawon wata daya a wanan hakin haka da yake ciki.
Yanzu ne kowa zai gane shi mutum yana da ranan shi ta hanyar da baka taba zato ba don ance ke yar tallakane baki cancanci auren shi ba a lokacin.
Sai Allah ya nuna muna tallaka yana da ranan sa sosai don zaiyi abinda kudi baya iyayiwa mutum shi a rayuwa don na tabvatar da zabin mami din ya aura a lokacin da yanzu wallahi duniya ta gama sanin komai a yanzu.
Sallaman mami da su jamal ne da suka shigo hankali tashe dakin ya katse shi ga maganan da yakeyi a lokacin.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
ASSALAMU ALAIKUM WARAHAMATULLAH JUMMA,AT MU BARAK YAN UWA MUSULMAI ALLAH YA SADAMU DA ALHERUN DAKE CIKIN WANAN RANAN AMIN, , , , ,
Bin yadda yake kwance a cikin wahala kowan su keyi jamal ke fadin yana numfashi kuwa ?
Yanayi ya mamud ya bashi amsa ai don zainan ma ta taimaka ta bashi wani magani dazun ya sha shine har yake hakan.
Da sauri mami ta juyo ta sauke kallon ta gareni tana fadin me kika bashi ya koma haka zainanb me kika shirya kike son ganin bayan shi a yanzu.
Wallahi idan wani abu ya samu dana bazan taba yafe maki ba kema sai naga bayan ki har iyayyen ki.
Kai haba mami wanan maganan bai dace ba haka dan Allah ba don yarinyar nan data take tsaye a kanshi ba ai bamu san halin da yake ciki ba.
Wa yasan hanlin da suka tsunci kan su zuwa wanan lokacin da badon ita data bashi wanan maganin ba dazun da wallahi kila da yanzu mun rashi ga baki daya har abada.
Itace tafi kusan dashi take zaune dashi tasan irin laluran shi a yanzu don haka ba zamu zargeta ba mami, kan halin da yake bayan duk munsan da abinda yake damun shi a nan.
Jamal ne ya fara fadin gashi kuma mami kai brother asibiti haka kamar tonon asirine a wurin ki a garin nan sai nake ganin kamar a samo yarddaden likita a dauko shi gida yazo ya dubashi a nan.
Nima haka nagani ya mamud ya fada daga gefe mami kan ta koma ta zauna saman kujera ta kurawa dan nata dake kwance a kasa cikin wani hali sai hawaye take sakewa a lokacin.
Bata iya furta komai a wanan lokacin don bakin ciki da takaici da yai mata yawa a zuciyar ta ina zata kai wanan abin kunyar da jafar ya dauko mata a cikin iyalin ta yanzu .
Kai kome zasu fada a kaishi asibiti kawai wallahi a dubashi a san halin da yake ciki zaifi jalal ya fada.
Nima dai abinda naga yafi ke nan Aisha ta sake fada daga inda take zaune a takure a lokacin na dago kai da sauri tare da fadin .
Don Allah kada ku kai shi asibiti a cikin wanan halin da yake ciki haka ku taimaka ku rufa mai asiri da akaishi asibiti gara dai likitan yazo gida ya duba shi don Allah.
Ya mutu kike so Aisha ta fada a hasale tana kallona kamar zata cinyeni danya a lokacin da take wanan maganan cikin kunan rai take tambaya na hakan .
Mami ta dagp kai tana fadin gaskiya zainab ta fada fitar dashi haka zuwa asibiti tonan asirine kamar yadda kuka fada da farko.
Don haka kai mamud wani likita kake ganin zamu nemo a wanan case din nasa yanzu har lokacin idon ta na kansa inda yake kwance tana kallon shi.
Ina gefe ina sauraren shawaran nasu kai mutum dai ba abakin komai yake ba lafiya itace jarin ga mutum da ya kumce ma ka rasa komai, komai arzikin ka kuwa.
Wani likita ya mamud din ya kira yace a bashi dan lokaci yana tafe duk zaman da nakeyi wurin bakina na dauke da addua a lokacin.
Tun ina yi a boye har na fara fitar da sauti ina karatun a fili duk suka bini da kallo kamar kullun amanal rasulu nake karanta mashi sai yasin haka ma wanan lokacin shinakeyi a hankali suna saurarona.
Dakin yayi tsit sai muryana dake tashi a lokacin can ya dan motsa hannun shi kadan alaman yana son ya falka a lokacin.
Gaba dayan mu ido muka zuba mai kafin can ya bude idanun shi da kyat yana fadin zainab bani ruwa in sha don Allah ba wanda zai gane me yake fadi a lokacin don muryan shi daya dakushe bai fita sosai.
Na dago kai na dan kalli ya mamud dake kusa damu ina fadin wai ruwa yake son sha.
Bashi wanan can da kika rufe dazun ya sha tunda a kwai sauki sosai daya sha shi dazun na tashi a daidai lokacin da mami ke fadin ruwan meye wanan din sauran kuma duk suka bini da idanu har na dauko ruwan dake rufe a gefen gado cikin cup din glass.
Na kawo mai tare da dan kiran sunan shi ina fadin yaya ga ruwan ya bude idanun shi da kyat ya sauke a kaina.
Dan yun kurawa yayi don ya sha ruwan dake hannuna ya kafa kai yaja sosai kafin kuma ya dakata na dan lokaci ya dago kai ya kalleni.
Muryan ya mamud din ne yake fadin shanye mana jafar don Allah yana da amfani a gareka sosai.
Ya dan daga kai ya kalli inda ya mamud din yake kafin ya mayar da kanshi ga kallon dakin ga baki daya sai a lokacin yasan a kasa saman ties yake kwance don neman wa jikin sanyi a lokacin.
Muryan mami da yaji tana fadin kasha maganin mana jafar ka tsaya kana kallo kuma da sauri ya juya inda take tana zaune tana magana saman kujeran dakin nasa.
Sannun da yan uwan ke masa ne ya kara juyawa wurin su yana kallon su kamar bai ganesu ba a lokacin.
Karbi ruwan kasha yaya na fada daga inda nake tsungune ina bashi ruwan da zai sha ya juyo a hankali ya karbi ruwan daga hannuna.
Tunda ya kafa kai bai cire a cup din ba sai daya shanye ruwan ga baki daya ya miko min cup din na karba
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22Chapter 23Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32Chapter 33Chapter 34Chapter 35Chapter 36Chapter 37Chapter 38Chapter 39Chapter 40Chapter 41Chapter 42Chapter 43Chapter 44Chapter 45Chapter 46Chapter 47Chapter 48Chapter 49Chapter 50Chapter 51Chapter 52Chapter 53Chapter 54Chapter 55Chapter 56Chapter 57Chapter 58Chapter 59Chapter 60Chapter 61Chapter 62Chapter 63Chapter 64Chapter 65Chapter 66Chapter 67Chapter 68Chapter 69Chapter 70Chapter 71Chapter 72Chapter 73Chapter 74Chapter 75Chapter 76Chapter 77Chapter 78Chapter 79Chapter 80Chapter 81Chapter 82Chapter 83Chapter 84Chapter 85Chapter 86Chapter 87Chapter 88Chapter 89Chapter 90Chapter 91Chapter 92Chapter 93Chapter 94Chapter 95Chapter 96Chapter 97Chapter 98Chapter 99Chapter 100Chapter 101Chapter 102Chapter 103Chapter 104Chapter 105Chapter 106Chapter 107Chapter 108Chapter 109Chapter 110Chapter 111Chapter 112Chapter 113Chapter 114Chapter 115Chapter 116Chapter 117Chapter 118Chapter 119Chapter 120 Chapter 121Chapter 122Chapter 123Chapter 124Chapter 125Chapter 126Chapter 127Chapter 128Chapter 129Chapter 130Chapter 131