jafar ka aikata sabo mai girma a rayuwa.
Ya aikata kan sai dai addua a yanzu tunda Allah ya taimakeshi ya daina a yanzu ga baki daya.
Yanzun malam saika fada muna matsayin da auren su yake ciki a yanzu don kowa yasan zaman shi a yanzu din mami ce duk take wanan maganan tana kallon malam din.
Taci gaba da fadin don a nawa fahintar ya tsaya yana gyaran wani zance haka mai tsawo da bashi ya taramu a nan ba tun dazun.
Why mami why zakice kada na fada ya zama dole in fada a gaban kowa don in kara samun addua da taimakon da Allah zai gafarta min zunubai na jafar yace.
Kafada din ba,a hana ba kana kawo muna wani zancen zainab can tun dazun mami ta fada a hasale.
Malam dake kallon su yace Na,am watau ainihi danki yana da gaskiya haka ake son mai tuba da gaske ya kasance kada yaji kunyar fadan girman zunubin sa komai girman sa don tuba.
Haka zalika ita wanan yarinyar ya nuna inda nake yace tayi matukar kokarin azo a yabe ta kuma a sota ko dan halinta.
Don a wanan zamanin ba ko wace mace bace zaki samu da aikata hakan ta iya boye sirin mijinta a cikin ta daga ita sai shi sai Allah kadai su san da sabon da yake aikatawa haka.
Jafar ya tare malam da fadin wallahi malam abinda zai baka mamaki shine ita din zainab ta shiga ta fita a kasan chaina ta samo min maganin da a yau zan iya komawa kamar kowa.
Na,am malam yace tare da kara masha Allah yarinya kinyi kokari da kika samu wanan yabon a bakin mijin ki haka.
Wallahi malam ba gyarata nakeyi ba ko don wani ya sota a yau ina fadin gaskiyan abinda tayimin ne a rayuwa nan dai ya kora masu labarin komai har da na kakana malam da yake bashi.
Humm,umm ita zainab din duk ta iya hakan ashe ba karya ake fada ba da ake fadin yan kauye komai karantan su ka barsu inda ka gansu.
Shige shige da biye biyen malam ya kare a gidin su yau na kara gaskanta wanan maganan .
Kwarai mami in dai wanan din shine shige shige zainab ta shiga inda yafi nan din data shiga ya mamud ya fada.
Don kuwa mu zainab ta gama muna komai na rayuwa tunda ta kwato muna dan uwan mu cikin bala,i.
Rufa min baki kada in saba maka a wurin nan yanzu mami ta fada dama nasan shirin ku akan hakan yasa na biyo bayan ku inji me kuke kullawa.
To bari kuji koda malam yace akwai zama a tsakanin su aure sai na karawa jafar shi tunda nayi niyar hakan kuma zan nuna masa ni na haifeshi ba wani ba.
Enough mami enough don Allah in anyi magana kice aure zaki kara min aure zaki kara min ga abinda ya dace kimin bakiyi ba lokacin da nike bukatan taimako.
Yanzu da zainab din tayi shine kuma abin laifi ai Allah yace tashin in taimakeka baki tashi din tsaye ba a kaina ita ta tashi har yanzu tana a mai laifi a wurin ki mami ?
Me wanan yarinyar tayi maki haka mami kika tsaneta ne lokaci daya haka halarcin zainab a gareki ba kadan bane har idan ke kika haifenin da kike fadi.
Yarinyar da zan yi amai ta kwashe in fitar da kazanta da namiji dan uwana ta zauna tana gani iyaka taci kuka ta gaji ta share hawayen ta bata taba fadawa wani wanan maganan ba har yau itace kike kokarin ganin kin bakantawa mami ?
Wallahi dani kadaine danki mami da sai ince bake kika haifeni ba kila don son baki kawai na kina nuna min don yadda zainab zata zaunar dani tana min wa,azi mami kin taba min hakan ?
A matsayina na mai,aikata babban laifi irin wanan don haka mami ki gafarceni akan zainab a yanzu zan iya batawa da kowa a duniyan nan.
Zainab tayi min komai a rayuwa ta yadda ba zan iya kimanta darajan ta a zuciyana bayan naki daga ke sai zainab ne mata mafi daraja a idona har abada.
Yau zainab ta tunar dani nauyi da kunyar ubangijina da ke kaina wanda na manta dasu saboda rudin duniya da nake bi a baya.
Aiko mami zainab tayi min komai a rayuwana, kukan da nasake ne ina kaiwa kasa ya dakatar da dan rigiman daya kaure a tsakanin su lokaci daya a wurin.
Malam ka taimakeni kai mun rai ka ceci rayuwana ka rabani da ahalin mami ga baki daya a yanzu nima na gane mami ba zata taba kauna ta ba a duniyan nan.
Duk abinda yaya ya fada anyi shi har ga Allah dama wanda bai sani bai fada din ba duk anyi su a baya.
Kuma bayi don kowa ba sai don Allah da halarcin mami a gareni da kuma shi kanshi ya jafar din ya taimakeni da abinda ba zai taba barina a rayuwa na bashine illimi.
Mami ta sanadiyar ta nabar kauye rayuwa na ya inganta a sanadiyar ta haka tayi min riko na tsakani da Allah da ba zan taba mantawa da hakan ba don ita uwace hakkun har gobe a gareni.
Aurena da ya jafar shine kadai kiyayar mu da mami a fahintana don haka malam ka yake duk wani alaka na aure dake tsakanina da ya jafar a yau don Allah.
Na karasa cikin wani irin kuka ma idaga hankalin mai saurarena a lokacin duk sukai shiru suna saurarena tare da zuba min ido gaba dayan su.
For god sake mami dame wanan abin yai kama haka yarinyar nan dai kema kin sani ta dalili ki ta san bros ta kuma fadi don ki take masa komai.
Koma bata fada ba kowa ya sani don zainab yarinyace mai hankali da natsuwa ke kanki kinsha fadin haka ko a bayan ta yan aiki nawa kika canza zuwa yanzu jamal ne mai wanan maganan rai bace.
A ranan nasan tarbiyan yahudawa mami tayiwa diyan ta ashe tunda kowa na iya fadin magana kai tsaye a gareta ba tare da ta damu da hakan ba.
Don da ace hakan yai mata zafi da wata uwarce a take zata yankewa kowan su kauna a wurin yau naga amsan abinda ya dade yana min yawo a zuciyana .
Kan yadda mami bata damu tabi umurnin hjy ba idan ta tsawta mata kan wani abu da takeyi wanda bai dace ba din.
Salamu Alaikum malam ya fada cikin muryan uztazai wanan ya saka masu natsuwa a wurin malam din yaci gaba da fadin .
Wa,izu billah wanan abin bai kawo kallo ba a tsakanin ku watau anihin dai wanan zancen naku yasani nazarin abubuwa da dama a cikin yanayin zancen nan a yanzu.
Da farko na fahinci akwai wani abu da ke a kasa tsakanin ku a gidan nan tun farko sai abu na biyu shine.
Watau ainihi kan zancen wanan boyar Allah watau hjy zainab gata a zaune watau anihi hajiya iyami ina son ki san wani abu.
Shi lamarin ubangiji mai sauki ne idan bawa ya daukeshi da sauki watau wanan boyar Allah ita din haskene a gareku baki daya a gidan nan.
Haske irin wanda ake kira da Nurul dar sai ya kasance a cikin wanan zancen gaba daya kunyi amfani da baiwan yarinyar nan kun kuma amfana da ita ko.
Yanzu duk ba wanan ba don lokacin sallah ya gabato sai mu gagauta yin bayani kan abinda ya kawo mu nan a yanzu.
Na farko dai bayan nasiha da zan ma kai malam jafar akan tsoron Allah a yanzu dai Alhamdullahi sai ka ya waita istgifar wanan yafiya yana tsakanin Allah da bawan shi.
Ba wani dan Adam da ya isa ya furta wani kalami akan hakan face mu godewa Allah ga baki daya muka yawaita istigir akan mu da dukkan musulmi baki daya .
Ke kuma hjy zainab ki godewa Allah da har kika samu yabo haka gun abokan zaman ki ga baki daya ko wanan ya ishe ki alfahari a duniya.
Zancen akwai aure ko babu aure a tsakanin auren nan yanzu zabi ya rage gareka kai mai auren a hannun ka.
Idan kaga zaka bar matan ka auren ku na nan daram har abada sai dai idan kaika janye igiyan auren ta a kanka yanzu.
Aure dai an riga da an daura a tsakanin a bisa tsarin musulunci ba tare da wani manufa ba ga madaura auren ku din a lokacin kaga ke nan aure ya dauro a tsakanin ku ke nan.
Wanan zancen da ake hasashe ba addini ya fadi hakan ba tsarine na wasu mutane da suke fadab hakan.
Amma dai da ace har yanzu baka tuba ka koma ga Allah, ka daina wanan abubuwan bane to sharia ta yarda da a raba auren naku don taje gaba itama ta samu daidai da ita kada ka cuta mata a nan
Sai dai ina kira a gareku gaba dayan ku kiyayye kyautatawa iyayyen ko da a wajen tausasa harshe ga mahaifa musanman uwa .
Duk wanda yaji hakan yasan dalilin fadan hakan da malam din yayi garesu ya kara da fadin sai na karshe mu kyautatawa wanda ya kyautata muna koda na rana daya ne shima zai bukaci kyautatawan ka watarana a kan shi.
Don haka kada mu zamo masu manta alheri komai kankantanshi don kada Allah ya jarbce mu ta hanyar da bamuyi tsammani ba a rayuwa.
Da wanan nake son inyi sallama dakuba taikace Allah ya gafarta muna kurakuran mu da wanda muka sani da wanda bamu sani ba Allahuma amin.
Yayi muna sallama bayan anyi addua an shafa ya mike zai tafi ya jafar ya saka hannu a cikin aljihun shi ya ciro kudi masu yawa yace a bashi.
Da sauri malam din yace sam ba don kudi ko wani abin sadakan ku nazo ba son kunfi karfin hakan a gareni.
Zanso na gana daku ku ukun nan kafin ka bar kasan nan idan kun samu lokacin haka yayi masu sallama ya tafi.
To ai shike nan bukatan kowan ku yanzu ya biya shiyasa kuka dauko min malam khalid don shi din ya inma bakin sa yazo yai muna wa,azi.
Wa,azi kuma mami akan me zaizo yayi maki wa,azi mu mun kirashi ne yazo ya warware wanan zancen kowa yasan matsayin shi.
Please is enough a bar zancen komai a yanzu ke zainab tashi muje gida daga nan ya fada yana mikewa.
Kamar banji me yake fada ba a lokacin kaina na kasa sade ban dago daga yadda nake ba tun dazun din.


ZAINAB IDRIS MAKAWA.




ASSALAMU ALAIKUM YA YAN UWA MUSULMAI BARKAN DA GANIN WANAN RANAN NA ALHAMIS UBANGIJI ALLAH YA SADAMU DA ALHERUN SA AMIN.
KADA KI MANTA TASHIN DARE A WANAN RANAN MAI ALBARKA KI YAWAITA ISTIGIFAR GA ALLAH KI NEMAWA KANKI GAFARA ALLAH YA BAMU IKON TASHI YA KUMA KARBA MUNA IBADUN MU AMIN.


TUNI LITTAFIN DAI NA KUDINE BA A YARDA WATA TA KANTASHI BA IDAN BATA BIYA BA.


Yana tsaye a kaina yana kallona ba tare daya sake magana ba duk sun zuba min ido suna kallo na don ganin ban motsa daga yadda nake ba sai hawayen da nakeyi.
Sai ya mamud ne ya mike ya tako har inda nake tsugune ina sake hawayen bakin cikin dake cina abu goma da goma sun taru min a kaina lokaci guda.
Zainab kiyi hakkuri ki tashi ku tafi ya fada a gefena cikin nuna damuwa a gareni jin haka na dago kai da idona daya yayi ja don kukan da nasha ina fadi da kyar.
Tare da girgiza kaina gareshi yaya ba zan koma gidan ya jafar ba kai masa magana yayiwa mahaifiyar shi biyayya kan abinda take so dashi.
Allah ya gani da zuciya daya nake zaune dashi tankar yar uwa ta jini don duk abinda mami take nuna min banta jin kinta a raina ba haka diyan data haifa ina jinku tankar yayyuna ne na jini don yadda kuka rikeni tun farko.
Bada case din ya jafar daya hadani da mami ba wani sabani daya taba shiga tsakanina da mami duk zamana da ita.
Ban yarda na auri ya jafar dan son raina ba sai bisa tursasawan hjy gwaggo dashi kanshi ya jafar din da sukai min barazana a lokacin.
A daidai nan na dago kaina na dan kalleshi ido da ido tare da fadin yaya a wanan maganan meye laifina a cikin hakan ina duk saboda darajan mami na aikata hakan.
Yanzun kuma kaji a gaban kowa shima ya fadi bai aureni don yana sona ko wani abu nawa ba sai dan bukatan kanshi da yake ganin zai fiddashi ga idon jama, a.
Alhamdullahi kuma dukkan su bukatan su ya biya a kaina don Allah kusa ya sake don wanan abin ya kare daga yau din nan yaya ?
Na fada ina kara sake wani itin kuka mai tsuma zuciya lokaci guda daga inda mami take zaune ta zuba min ido take fadin kenan da sanin hjy dama duk hakan ya faru ashe ?
Shiko ya jamal sai cewa yakeyi ai gashi idan za ai magana a fadi gaskiya mami ki hana duk wanan abin da yarinyar nan takeyi ni nasan taimakon ki takeyi wallahi.
Kune dai da baku yarda ba da farko kuke ganin don bukatan kanta take hakan yanzu sai ku sama mata maslaha itama taje ta huta.
Jafar daya juya ya bamu baya yana cika yana batsewa ya juyo a hasale yana fadin wallahi baku isa ba babu mai rabani da matana wallahi .
Sai ko idan bana raye wanan kan na yarda da hakan naji mun yaudare ki din da farko daga ke har hjy data shawo min kanki a lokacin baku san komai ba .
Yanzu da nayi comfessing ina neman gafaran Allah da naku duk wanan din bai maki ba zai ba ya fada yana tsureni da idanun shi da sukai wani ja dasu.
Fine naji ya fada cikin wani irin zabura yana fadin sai ki fadi yanzu me kike son nayi maki don ki hakkura mu tafi ?
Na duka na baki hakkuri ko kudi kike sin na zuba maki fadi iya yawan kudin da kike koda duka dukiyanane zan iya ko mami kike son ta baki hakkuri gata zaune.
Ki fada duk a yanzu ko wanine daga ciki za ai maki a yanzun nan ba sai an jima ba.
Kai kai kai Allah ya rabamu da rashin tarbiya wallahi da tashi a cikin daulan da ba kwabo wadattace ga mutum.
Duk wanan abinda ya fada a yanzu shi a nasa zaton sune abinda zai kwantar min da hankali ko wani abu can.
A hankali na girgiza kai tare da fadin ko daya yaya jafar bana rayun ko daya daga cikin abinda ka lissafo min din a yanzu.
Na farko kana ganin dukawan ka a gareni ka ban hakkuri zai iya dawo min da farin cikin bakin cikin da nasha a wurin ka da mami da yan uwanka dake kina.
Ko kuma kana ganin kana da kudin da zai iya sayen mutucin na da imani na a hakan.
Sai mami gata a zaune mami uwace mafi soyuwa a gareni mafi girma da daukaka a idona ita da innata data kawoni duniya don bayan inna sai mami tayi imin komai a rayuwana ba zan taba manta harcin su ba a gareni.
You see mami kinji, kinji yarinya karama tasan halarci irin wanan, ta yaya ku manya zaku kasa gane hakan ?
Har ma wani dadi zainab ta samu a lokacin da take ta fadan kin mata halarci bayan tauyen ta da akeyi ana mai da ita kamar wata boya a ciki gidan nan kowa ya tashi ko ruwane zainab dai zainab dai ku din nan yau kunji inda akewa mutum alheri ya rama ta wani hanya.
Don ku din nan ba irin wullakancin da bakuyiwa zainab a gidan nan ba yau gashi tafi ku da komai a duniya.
Don ko kafanta ba wanda ya taka a cikin ku kaf din ku ba wanda yayi lilmin zainab a yanzu ya fada yana nuna su da yatsan hannun shi.
Ku rage wullakanta dan Adam don Allah don watarana baku san me Allah zai mai dashi ba jamal ya fada a hasale yana mikewa tsaye.
Ya girgiza kai ya saka hanayen shi cikin aljihun shi yana kokarin barin wurin.
Sautin muryan mami ne dake kuka yaji ya hanashi tafiya a lokacin ya juyo da mamaki yana kallon mami din da kuka takeyi wiwi a lokacin.
Ya mamud da sauri ya karasa wurinta yana fadin haba mami me yai zafi haka wanan ai saiki tada hankalin mutanen gida da wanan kukan naki.
Zuwa lokacin ko har sun karaso don Rufaida datake labe saman bene tana sauraron abinda ke
Showing 369001 words to 372000 words out of 390011 words