Allah daya nufi mijin ki da samun rayun shi a yanzu ga daina wasu halaiya nasa masu muni da yakeyi a baya can .
Duk da mahaifiyar shi ce ya dace tayi hakan amma ta kasa tsayawa ta duba rayuwan dan nata sai shirme da zugan mutane da ke rudin hankalin ta.
Hakkuri gareki zainab shine mafita a yanzu don ki girbi wahalan ki da hannun ki idan kinyi sake kinaji kina gani sai watace zata zo daga baya taci gajiyan wanan hakkurin naki a gaba.
Nasani zainab mahaifiyar mijin ki na kokarin shirya yi mai aure don a ganin ta ke din baki cancanci zama da danta ba haka matsayin ki dana iyayyen ki baikai na yadda take son matan diyan ta su kasance ba.
Na dago kai da sauri na dan kalleta again tace yes zainab wlh bawai hjy mami bata son ki bane a, a wanan ne kawai ya kawo maku rashin jittuwa a tsakanin ku da ita .
A gabana gidan nan kwanaki dan uwan mijin ki yazo da wanan zancen gidan nan yana fadawa mijiki abinda mahaifiyar tasu take kulla mai wai zata aura mai wata a dole don kare martaban shi.
Sai dai amsan da ya bayar a lokacin shi ya wadatar dani a lokacin na kara sanin kina da tasiri matuka a zuciyar shi.
Sai gashi daga baya kuma kina neman ki bada wanan kafan a garesu suyi yadda suke so a kanki.
Don duk da sanin halin danta da tayi kin san ance uwa bata taba ganin laifin danta kome akace ya aikata zataga sheri ake masa don tarbiyan data bashi ita kadai tasan halin shi.
Wanan matsalan ke damun wasu uwaye a yanzu da basu tsayawa su natsu su san yanzu da zamani komai ke tafiya a yanzu.
Duk da nasan sheri shedan ne da har ya rudeki kike ganin bari gidan nan shine mafita a gare ki da har zaki iya gudu ki bar dakin ki wata tazo ta gaje daga baya.
Kada kiyi mamakin yadda nasan hakan duba da irin shakuwan dake tsakanina dake a baya yakai har mijin ki yake zargin nasan wani abu a game da tafiyan naki .
Shine ranan ya titsiyeni a nan falon yake min warning kan na fada mai inda kika shiga a kasan nan kika boye ?
A lokacin gaskiya hankalina ya tashi sosai da jin haka da nasan zaki aikata hakan da na baki shawaran karki soma yin hakan a yanzu.
Inda na kara tsorata da zancen sai nake ganin suna yawan shigowa gidan nan akai akai na gane hakan da takeyi na son cusa mashi wani manufane na daban a lokacin.
Sai gashi Allah ya gyara kin dawo kwatsam a lokacin da kowa bai tsamaci hakan ba da zaki dawo a kan lokaci ba tare dana waje sun fahinci komai ba.
Ko suma na gidan kansu ya daure da ganin kin dawo salin alin duk da akarshe hjy mami cewa tayi kwadayine ya dawo dake gidan nan ai.
Ido na lumshe dama nasan zata fadi hakan a kaina koda banji haka a bakin fadila ba din nasan abinda mami zata fada ke nan kan dawowa na din a lokacin.
Ta dan motso kadan daga inda take zaune takai kai hannun ta saman gwiwana ta dafa haka yasani bude idanuna dana runtse a lokaci guda don takaicin kalami mami a gareni da nake ji a lokacin har kasan raina.
Hakkuri zakiyi zainab kowa da irin tasa kaddaran a rayuwa wata kila Allah ya jefoki a cikin sune don ki zamo masu haske a nan gaba ita bata sani ba ta tsaya tana hauka a yanzu.
Ki nuna komai bai dameki ba zainab kibar nuna bacin ranki haka a fili don ko zaman da kikayi nan na fahinci abinda ke damun ki ke nan yasa kikaji ina maki wanan bayanin haka a yanzu.
Nasha fada maki ke di mace ce zainab kin kuma nunawa duniya ke mace ce don kinyi amfani da iliminki na mata gashi yau har kin kai ga taka nasara akan shi kin rabashi da wasu halaiya masu muni a rayuwan shi.
Koya sani a yanzu ko bai sani ba shi da duk wani nasa dole a karshe zasu san hakan da cewa ke din ce haske a garesu kinyi namiji kokari sosai kiris ya rage ki kai ga in ma nasara ki akan komai da yardan ubangiji.
Tana fadin haka ta mike tare da fadin ni zan tafi don yan kwanaki ya rage min a gidan nan zamana ya kusa karewa daku tynda na gama hada abinda nazo samu a wurin ku din.
Sai dai ina fatan zaki bi shawaran dana baki din kiyi amfani dashi don Allah kada ki bari kowa yasan zaman da kikeyi a gidan nan yanzu a bar ABU A CIKIN DUHU YA ZAMA SIRIN KA KAI KADAI.
Tana fadin haka ta juya zata tafi da kyar na iya budan bakina nace mata nagode anty bayan hakan ban kara furta komai ba akanshi.
Hanyar kitchen ta nufa na bita da kallo a inda nake zaune ina mamakin wasu zantuka da tai min yanzu din a karshe.
Tabbas ABU A CIKIN DUHU din ne kuwa zama a gidan yaya jafar din don mutane na min kallon jin dadi da samun duniya a gidan shi yanzu.
Ni kuma ina zaman hakkuri da danne zuciya akan tayuwan wani don duk wanan hangen da mutane suke min bashine a gabana ba yanzu.
Zakaji duk wani na tare dani zai ga kamar don abinda mami din take min ne nake son barin gidan a lokacin har iyayyena da suke ganin wanan ne ya tayar min da hankali har nake son yiwa jafar din sheri akan wai baya kwana dani.
Kwana dani ba shine a gabana ba mutane sun ki su gane hakan a gareni maganan fadila din ne don ya zama dole inyi hakkuri in bar zancen a raina koda hakan shine ajalina a gidan nasa.


ZAINAB IDRIS MAKAWA



JUMMA,AT MUBARAK YAN UWA MUSULMI UBANGIJI ALLAH YA SADA MU DA ALHERIN DAKE CIKIN WANAN RANAN ALLAHUMA AMIN.
YAR UWA LITTAFIN KUDINE KI BIYA KI KARANTA VIKIN SALAMA DON KARUWAN KANKI DA KANKI YAR UWA, , ,

Kamar yadda maya tayi min alkawarin kirana karfe takwas na dare ina daki zaune saman sallaya ta kira layina din.
Na dauka muka gaisa take fadin yanzu haka tana gidan kakarta don yadda tajini a dazun bata ji dadin haka ba.
Da yake video call mukeyi da ita ta nuna min fuskan kakar nata a screen din wayan ta tsohuwar take murmushi ba yaren su nake ji ba don haka na daga mata hannu alaman gaisuwa a gareta .
Bayan mun gaisa din takewa maya yare mayan ta kalloni tana fadin wai me ye damuwana a yanzu ido na dan lumshe kafin na sauke ajiyan zuciya na fara ba maya din bayani ita kuma tanawa tsohuwar kamar yadda nake fada mata.
Daga ta bata fuska sai ta dan kada kai tsohuwar keyi don jin bayanin da nakewa maya din.
Saida na gama ta fara magana tana dan tafiya a duduke zuwa wurin da take aje maganin ta ta dauko ta juya tanawa maya magana.
Maganin naga maya ta amsa a hannun ta tana nuno min tare da fadin wai ki duba irin wanan maganin ta baki irin sa kwanaki.
Shi zaki dauko kiyi amfani dashi a yanzu ta bude maganin tare da nuna min shi sosai a screen din wayan ta nace nagane.
Ta sake fadin zaki jika mai a ruwa har sau uku daga nan ki bar bashi sai tsohuwar ta katse ta da bayanin da takeyi din ta fara magana tana nuna mata wani farin garin magani dake hannunta.
Nan dai sukayi min bayanin komai na yadda zanyi amfani da magugunan data bani a kwanaki da na tafi masu sallama zamu dawo Nigeria.
Don ni na barsu kenan a nufina bazan sake komawa kasan chaina din ba kuma a yadda na yanke a zuciyana.
Bayan mun gama wayan ne dasu ba nufi wardrobe dina ina binciken inda na aje maganin da tsohuwar ta bani din.
Suna ajiye kamar yadda na ajesu daya bayan daya na duba ko wani na dauko na dawo bakin gado na zauna ina kallon maganin.
Can kasan zuciyana nace Allah kaga nufi a kan hakan banyi don na raina ma yin ka ba ya Allah ka gafarceni akan hakan idan na saba maka .
Kasa wanan karon iyakar wahalance ga hakan kasa mu dace da nasarorin ka ya Allah na fada ina shafa hannuna a fuskana.
Tashi nayi daga inda nake zaune din na nufi inda wasu cup suke ajiye na dauko tare da goran ruwa na zauna a inda na tashi din.
Ruwan na fara zubawa a kofin na daga tare da karanta fatiha kafa bakwai a cikin sa don ance kome ke damun ka fatiha na maganin sa da yardan ubangiji.
Na kawo garin farin maganin na dan zuba a cikin sa kadan na fara karkadawa kafin in daga in kai bakina da bissimillah.
Na gama duk yadda ta fada min din inyi bayan na kamallah na koma na kwanta saman gadona ina mayar da numfashina a hankali.
Ina nan kwance ido a rufe naji an turo kofan dakin an shigo na bude idona a hankali sadiyace ta shigo tana fadin anty kin kwantane da wuri haka yau.
Zan tashi yanzu na bata amsa ina mikewa tare da fadin kin ci abincine tace min bata ciba muje yanzu muci na fada a daidai lokacin dana sauko saman gadon.
Mun zauna falon ke nan ya shigo fuska a daure nice na fara mashi sannu da zuwa wanda hakan ya bashi mamaki don ya dauka a yadda muka rabu da rana ina cike dashi a ranan.
Haka yasa yaje gidan mami ya zauna abinsa ya yini a can bai dawo ba sai wanan lokacin daya shigo gidan.
Duk da hakan bai tsaya a falon ba ya nufi part din shi kai tsaye bayan ya dan tsaya yana amsawa sadiya gaisuwa tare da tambayan ta tana lafiya ?
Baifi yan mintuna a tsakani ba na mike tsam ina fadin sadiya ina zuwa na nufi part din nasa nima.
Na sameshi tsaye a tsakar dakin yana cire rigan jikin shi na karaso inda yake ina fadin yau ina ka shiga har wanan lokacin ?
Ina gidan mami ya bani amsa kai tsaye a yadda yake amsa min din naji ba dadi gaskiya saidai na hade hakan a raina na kara takowa har inda yake ina fadin .
Suna lafiya ya yaran ya mamud basu zo badai gidan nan har na tambaye shi don rasa na fadi a lokacin .
Kema kinsan uwarsu ba zata bari suzo gidan nan ba din har yanzu fushi takeyi dani bata zuwa ko naje gidan.
Ikon Allah me yai zafi haka a tsakanin ku ta dauki fushi dakai haka hummm kawai yace yana kokarin wuceni ya shiga bayi.
Ya kai kofan bayin duk a cikin daurewa nake fadin mu jirakane ka fito muci abinci na tambayeshi don karfin hali don kawai in nuna mai yanzu ba haka zancen yake ba a guna.
Naci abinci gidan mami a koshe nake ya fada yana shigewa bayin kai tsaye nabi bayan shi da kallo.
Kafin ajiyan zuciya ina mai jin zafi a raina tare da tunane nabar dakin nasa watau mu mata a zalunce mu kuma mu koma bi da biyayya garesu Allah sarki diya mace ubangiji Allah kaiwa mata rahama albarkacin Annabi Mohammadu sallalahu alaihin wasallam.
Falo na dawo na zauna a dinning muka fara cin abincin da aka shirya na dare don mu a gida.
Mun gama hira muka danyi kafin kowan mu ya mike zuwa part di shi har lokacin banga ya leko mu ba .
Haka yasa na gane cewa bazai fito di ba ke nan yake nufi ina shiga daki na fada bandaki nayi wanka na fito na shirya tsam kafin in saka rigan barci na dauki abinda kakan maya tace min in shafa bukata kawai ko bai shafa bashi yaji kakshin shi dab a hancin shi dai kawai ko hakan ya wadatar.
Sosai na mulke jikina da maganin nabi da dan turare a sama saboda kar kamshin maganin ya tashi sosai.
Na dan dade a zaune ina tunanen hanyar da zabibsakon ya isa a hancin shi duk da nasan abune mawuyaci yin hakan garemu a yanzu.
Can dai na daure na mike na dauki hijab din sallah na na dora saman jikina kamar yadda na saba yi idan zan shiga part din.
Bakina tab da addua kamar kullun na nufi part din nasa kofan yana bude har lokacin na shiga jna rufo kofan a hankali nasaka key narufo kofan.
Kwance na hango shi rigingine ya na saye da jallabiya a jikin shi ya dora hannu a fuskan shi kafaduwab shi suna a harde yana dan kada su a hankali.
Duk da nasan ba barci yakeyi ba a lokacin hakan bai hanani tafiya a hankali ba motsi ba na karaso har baki gadon da yake kwance din sama.
hankali nakai zaune saman gadon har lokacin ina kan adduan da nakeyi a lokacin na gama na tofa tare da shafawa a jikina nayi bissimillah na hau gadon da kyau tare da dan jawo jikina zuw inda yake kwance duk da ban taba masa hakan ba sai wanan ranan.
Kaina nakai saman kirjin na dora lokaci guda yayi wani irin zabura yana fadin kanki daya kuwa zainab ?
Sau nawa nake fada maki idan har bukatan hakan ya taso min da kaina zan nemeki da hakan.
Ikon Allah na fada a raina kafin a fili ince dashi ban kwanta a nan don wani feeling ko wani abuba na kwantane kawai don in dan samu sauki a zuciyana a wurin dan uwana don kawai naji dumin wani ajikina.
Ba tare da yai magana ba ya kai hannun shi da zuman bambareni a jikin shi na kara lafewa kamar da gaske a jikin nasa.
Da karfi ya fincikoni zuwa gefeb shi ya juya yana wani irin mayar da numfashin sa da dan sauri kafin can inga ya mike zuwa ban dakin.
Shiru shiru bai fito ba sai zuwa can ya fito da alaman ruwa a jikin shi yayi wanka ke nan a lokacin don kawai na dan taba shi din ya watsa ma jikin shi ruwa a lokacin.
A hankali na mayar da idona na lumshi jin bai hawo gadon ba a lokacin yasa na bude idona yana tsaye gaban mirrow yana faman goge jikin shi.
Tabdi jam ashe abin bana wasa bane na fada a raina ina kara gyara kwanciya har barci ya daukeni ban sani ba lokacin.
Kodana falko a cikin dare na hangoshi can saman kujera kwance kuma har lokacin baiyi barci ba idanun shi biyu da waya a hannu shi.
Tashi nayi zuwa bandaki na dauro alwala kamar yadda na saba yi a kullun don Nafilan dare.
Sai zuwa can ya shiga ban dakin nan ma dai irin abinda yake ji yaji a ban dakin ga kanshi yayi wani irin daure mashi lokaci guda haka dai yaja kafan har ya fito.
Yau ba mafalkin asalima tsorone kawai daya ziyarci zuciyar shi haka kawai yake jin kamar tsoro yake ji saidai baisan na meye ba a lokacin.
Saida yai sallah raka,a hudu ya dan samu saukin abinda yake ji a zuciyar shi muna wurin har akai kiran sallah asuba .
Nayi sallah kamar kullun nabar dakin zuwa dakina sai dai abin mamaki ba kamar yadda ya saba tashi a cikin kuzarin shi ya tashi ba a yau.
Gashi nan so wick dashi bai son magana da kowa a ranan karshe ma ya kwanta yana barcin rana abinda bai taba yi ba ke nan a sanina dashi .
Koda kuwa baida lafiya baya barci da rana saidai ya rufe idon shi kawai na dan lokaci ya bude .
Allah ka tsare muna rayuwan mu daga fadawa a cikin halaka saboda duniya ko neman wani abu makamancin hakan.
Duk da irin halin da nakw ganin shi baisa na fasa shafa wanab magani ba insha kuma a nasa bangaren kuma sam ya rasa gane lafiyan jikin shi sam.
Shidai yasan cewa lafiyan shi kalau baya jin ciwon jikin shi tako ina amma kuma yawan kasala da damuwa ya hanashi sukuni ko kadan.
Ban dada ba ban kara ba a yadda aka ban lokaci da zanyi amfani da magani in bari daga nan kuma aka sake dorani kan wani da zan fara.
Nikan garin ceton wani naga ta kaina yar uwa sai dai abinda zance yanzu gaskiya kamar yadda malam ya fada min ne naga sauki sosai ga harkokin ya jafar a yanzu.
Ranan ya shigo da rana yake fadin in shirya zamu Samunaka mu duba hjy bata jin dadin jikin ta su mami sun tafi mu zuwa yamma jirgin mu
Showing 342001 words to 345000 words out of 390011 words