lokacin kuma nasan dani take maganan sai dai naja na tsaya daga kofa kadan.
Au kardai ince kema din baki son bin mijin naki can ne yanzu mama Ramatu ta fada tana kallona.
A, a kada kuyi mata fassaran daba shi ba babu wanda zaiso yabar gida irin haka shekara da shekaru mutum naizo gida ba fa .
Tazo din kuma bai barta ta gama bin dangi ba ya tayarwa mutane da hankali kamar gareshi farau yin mata .
Yaki nan kinji kyale shi idan ba zaki koma ba yanzu sai ya tafi ya barki nan har ki kara ganin mu ai muma nan bamu gaji dake ba.
Baiyi magana ba sai fita da yayi daga dakin ya barni tare dasu baki hjy ta fara ban kan nayi hakkuri ai dama haka aure ya gada.
A cikin zancen su ne na fahinci tafiyan mu a yanzu bai da wani nisa ke nan duk da ni bai min zancen tafiya ba har lokacin.
Duk dana dan sake jiki munyi hira da hjy a dakin nata haka baisa na sake zuciyana kan zancen tafiyan namu ba a lokacin.
Tambayan da hjy din ta sako min ne ya dawo da hankalina gareta tana fadin ina dai kawata ba kin biyewa mijin ki bane kuna tsarin iyali nan da sukeyi na kafirai.
Lah hjy wallahi bai taba min wanan zancen ba tun zamana dashi kawai dai bama rayuwa irin na sauran ma,aurata dashine har yanzu , na fadi hakan don na kawo hanyar da tafiyan mu zai fasa a lokacin na fadi hakan.
Kamar ya ban gane hakan ba da kika fada yanzu don magana kikai min a dunkule hjy haka maganan yake dana fada.
Na fada ina dukar da kaina kasa lokaci guda ido hjy ta kura min na dan lokaci kafin tace ki min bayani yadda zan fahinta don wanan ba karamin magana bane kike fadi a yanzu zainab.
Shin kina nufin bai taba tabaki a matsayin aurataya ba zainab ko dai kina nufin bai gamsar dake ne yadda ya dace.
Zainab ki kwantar da hanlinki ki fada min gaskiyan komai yadda ya dace jafari ba fin karfina yayi ba dagashi har uwantasa zan iya daukan mataki a kansu kan hakan.
Jin ta ambaci sunana na sake fadin hjy haka maganan yake har yanzu bawai wani zama mukeyi dashi ba yadda ya dace haka.
Wai zancen nan gaskiyane ko al,mara nake ji don na dade da zargin hakan a gareku har in wanan zancen ya zamo gaskiya gaba dayan ku zan dauki mataki a gareku har uwan naku data boye min hakan.
Ba laifin mami a nan hjy don ina ganin bata san da wanan zancen ba har yanzu innalillahi hjy ta fada hankali tashe tana fadin shike nan yaron nan ya cuce mu a rayuwa.
Me yake nufi da hakan daya aikata ya tauye maki hakki yana daukan alhakin ki haka yar nan ko baida lafiyane ba a sani ba haka ?
Lafiyan shi kalau hjy kawai dai bai sha,awan mata ne yace na fada kai tsaye har ina mamakin kaina banda malam kakana ban taba irin wanan maganan da kowa ba a duniyan nan sai ita hjy da nake fadawa ranan.
Yau na shiga uku ni zainabu Abu kuna da wanan matsalan haka akai shiru aka saka maku ido a cikin sa.
A kira min mijin naki ta fada hankali tashe na mike da sauri na tashi zuwa kiran nasa inda nabar tsohuwar a zaune.
A falon shi yake zaune yana shan coffee mai zafi sai turiri yake tashi a cup din daga gefen shi ya bude laptop din shi yana aiki a cikin sa.
Na shigo ya dan dago ya amsa sallaman nake fadin hjyce tace na kiraka yace me kuma zan mata yanzu ya fada yana dan jan tsuki dagani aikine mai muhinmanci yakeyi a lokacin.
Akan zaman mune da kai na fada mata komai yau take kiran ka akanshi wani irin dago kai yayi yana fadin what da karfi tare da fadin me kika fadawa hjyn ?
Kanki daya kuwa zainab ko kin samu matsalane na dan kalleshi ina murguda baki kafin ince kaina daya wallahi.
Nadai fada matane don ba zan yarda in koma wurin wa yan nan muggan abokan naka ba a kashe ni a banza wanan kasan ba .
Ko a nan din sukaso kashe ki kina ganin ba zasu iya bane idan ma wasa kikeyi a hakan kinyi kuskure wallahi zainab ya fada yana ture computer shi a gefe daya ya mike tsaye.
Talkaman shi dake aje gefe daya ya zura a kafan shi ya fita nabi bayan shi ina kallon yadda hankalin shi ya tashi lokaci guda.
Har mun kai kofa yaja ya tsaya ya jiyo a hasale yana fadin ki gagauta gyara duk abinda kika fada a yanzu don kinsan condition din da hjy take a ciki yanzu .
Idan maganan ki ya kara ja mata matsala a yanzu ta kara kwantawa ciwo ki kuka da kanki ga duk abinda zai iya biyowa baya gun yayanta dake.
Baki da hankaki ne ko ina wayau ki ya shiga da zaki zauna kina wanan zancen da hjy at her age baki tunanen komai da zai iya biyowa baya ba.
Ya juya ya fara tafiya ina biye dashi har lokacin a bayan shi ba tare da jin komai ba na warning din da yai min din kan hjyn a raina ni dai kawai mafita nake nema a yanzu.
A tare muka shiga dakin dashi mun samu hjy tabar kasa inda na barta zaune tana jin mun shigo ta dago kai ta kalle mu .
Yanayinta gaba daya ya canza a lokacin kallon shi tayi ba tare data yi magana ba ta nuna muna kujera mu zauna.
Shi yakai zaune saman kujeran yana kallon ta na samu wuri a kasa na zauna sai dan shiru ya biyo a dakin .
Can ta dago kai ta kallemi tana fadin yanzun muna hira da kawata nake bugun cikin ta a haka naji wani maganan daya daure min kai a tare daku jafari.
Me kikaji hjy ya tambaya ta kalleni tace takwara sake maimaita abinda kika fada min yanzu a nan.
Na dukar da kai kafin na sake dagowa ina fadin cewa nayi a matsayin budurwa nake da kike tambayana ko nasha maganin haihuwane ban haihu ba har yanzu.
Hjy ya tare da fadi nasan zainab a yanzu zata iya fadin komai da zai kawo rashin komawan ta can tare dani .
Nagodewa Allah dake ta fadawa wanan maganan haka ba wani ba ai gata a zaune me na rage ta dashi na zaman takewan aure da akeso namiji yaiwa iyalin shi.
Duk mai hankali dai ya dubi zainab a yanzu yasan bata tare da wani damuwa a gidana shi haihuwa ba Allah ke kawo shi ba idan lokacin hakan yayi.
Nasan ina da rauni kwarai wurin mu,amula da taraiya da ita a yanzu na kuma sha bata hakkuri a kan hakan tun da ni din ba mazauni gida bane ko yaushe.
Hjy tace a, a takwara wai haka maganan yake dama kika barni ina tunanen wani abu har hankalina ya daga haka ?
Hjy ni dai ki masa magana gaskiya bana son komawa kasan nan wallahi na fada kamar zanyi kuka a lokacin.
Don ga daman magana ya samu a gareni kuma hakan yanzu ba zai yuyu ba don ya samu wurin fakewa akan ciwon hjy din wanda gaskiya ne ya fada kuma.
Wani abu zai iya samun hjy din a dalilin maganan mu din gaba daya zasu dawo su tsaneni kan hakan danayi tunane.
Sai kawai naja bakina nayi shiru ban fasa kwan gaba daya gun hjy ban da nasan zata dauki mataki a kanshi.
Sai ga hjyn ta koma fadin nasan maza da yawa a zamanin nan suna irin haka ga iyalin su wanda hakan ba daidai bane sam wallahi.
Kuna shiga hakkin iyalan ku da yawa akan aiki da iyakarshi a wanan duniyan zaku barshi yau ina mahaifin ka yake ya rasu ta ba kanta amsa.
Duk ko son aikin ka ina ganin bakai na balarabe ba shi da ko yaushe kaje gidan sa baka masa ganin daya kai uku ko biyu ko yaushe yana kashen duniya yana aiki.
Kuma hakan bai hana shi zama da iyalin shi ba ai har a sameku don haka ina kara tuna maka a yanzu tunda har kaji yarinyar nan ta fadi haka.
A gaskiya tauyewan yayi yawa a gareta ke nan tunda har yana cikin korafin da zata iya fada .
Kada ka manta da yadda auren ku ya kasance da yar nan a baya don haka ka guji duk wani abinda zai kawo matsala a tsakanin ku yanzu.
Hjy indai wanan shine matsalan za a gyara da yardan Allah ya fada har lokacin bai tare da walwala a jikin shi.
Tun daya fita dakin ya barmu hjy tana saman bakin ta dani har akai azahar muka mike don zuwa sallah.
A inda na idar da sallah naji kawai nayi amfani da kayan kakar maya a ranan ya kamata in gwada ko wani kamar yadda tace min inyi dasu.
Nayi din ko wani har sha da shafawa da dai sauran su don su ba hayaki a cikkn maganin su sai dai sha da shafawa kawai zanyi a jikina.
Tun dana shafa ban fito ba duk da baka sanin nayi amfani dashi ma don haka na shige daki abina shima bai leko dakin ba kamar yadda ya saba idan yana gida.
Ban kuma kara ganin shi ba sai da dare da zamu kwanta barci na shiga dakin na sameshi yayi zaune ya daga kai sama yana tunane har nayi sallama bai amsa min ba.
Nima idona ya bushe a yanzu game dashi don haka ban damu da amsawan shi ba a lokacin na gama abinda zanyi na kwamciya na kwanta abina ba tare dana tanka mashi ba.
Ban sani ba ashe maganin yana aiki a kanshi a lokacin ya fara jin wani irin bakon yanayi yana sauka a gareshi a hankali har bai san lokacin da magana yazo mai ba.
Ina hawa gadon naji muryan shi yana fadin ke wani irin abu kika shafa haka mai kamshi ya sawa mutum kasala da hawa kan mutum ya fada yana dan lumshe idanun shi kafin ya sake fadin yayi min karfi a kai.
Ba tare dana kallo shi ba nace ban shafa komai ba sai turaren dana saba amfani dashi kullun na shafa na fada ina jan bargo zuwa jikina.
Banji takowan shi ba sai ganin shi da nayi a kusa dani tsaye gaba daya idanuwan shi sun canza kala kamar ba nasa ba yana fadin ina tambayan ki kina kokarin kwanciya ki kyaleni.


ZAINAB IDRIS MAKAWA




ASSALAMU ALAIKUM WARAHAMATULLAH YAN UWA FATAN ALHERI GARE KU KO YAUSHE UBANGIJI ALLAH YA SA MU GAMA DA DUNIYA LAFIYA DAMU DA IYAYYEN MU DA ZURI,AN BAKI DA TARE DA DUKKAN MUSULMIN DUNIYA AMIN, , , ,

YAR UWA KADA KI MANTA DA NOVEL DIN KUDINE KI SHAGALA BAKI BIYA BA AKWAI NAUYI A HAKAN KIN SANI, , , ,


Allah sarki yar uwa novel dina bana soyayya bane ko wani jin dadin duniya ina novel ne don fadakarwa a yadda rayuwa ke tafiya a yanzu don ki gyara da kanki ko ki gyara wasu ta hanyar novel dina ubangiji Allah yasa mu karu da juna anan duniya ranan lahira ke shedace akan duk abinda na rubuta a ciki.
Bana fata ko in yarda alkalamina ya kaini wuta don kawai in gyara maki rai in saka zuciyoyin ku a cikin wani yanayin dana san za,a tambayeni a kansa gobe kiyama.
Novel dina kan abinda ke faruwane a cikin gidajen mu na hausawa a yanzu da kuma yadda zaki fitar da yar ki ko kanwarki a cikin kangin rayuwa don haka idan zaki karanta ki karanta a hakan don idan kin lura wanan rayuwan na yanzu bawai don kayi aure zuciyar ka ya huta bane da itun kalubalin dake baya.
Allah ya iya muna yasa mufi karfin zukatan mu a rayuwan mu na zaman duniya Allahuma amin Allah.

Zaune yakai bakin gadon tare da dafe kanshi na tsawon wani lokaci yayin da gaba ya shiga faduwa don basan halin da yake jin kasa kusa ba.
Sanin shi din ba cikakken mutum bane kamar kowa a yanzu kallon da nake mai ke nan a zuciyana karfin addu,an iyayyene da ikon Allah dake aiki a kaina na tabbatar ya zaunar dani a yanzu gidan shi.
Don wani lokaci idan ina tunane zanji zuciyana yana raya min na gudu na tafi can duniyan da ba,a sanni ba inyi rayuwana acan da zama a gidan wanan munafukin Allah a yanzu.
Amma koda zan tashi sai naji zuciyana ya canza min shawara akan hakan zanjini wani lokaci wasai ko kuma ina tausayin shi.
Kinsan zama na hana mutum ganin laifin wanda kake zama dashi ko yaushe wani lokacin zaka san ba a daidai mutum yake ba kuma ka kasa rabuwa dashi a hakan.
Idona biyu dai a lokacin ina sauraren shi dan filin dana bari a gefen dana kwanta naji ya kai kwance a wurin hakan ya sani dan bude idanuna ina kallon shi a fakaice.
Kwanciya yayi a rigingine tare da daga kafanshi daya ya tokare na dan kada shi kadan ya jingina bayan shi da kan gadon yana kallon saman dakin.
Zainab a tunane a yanzu ba zaki iya fadawa kowa matsalan ki na zama tare dani ba duba a yadda na rikeki a zuciyana nake gani.
Sai dai kash a she yadda na dauka abin ba haka yake ba ke a wurin ki a zuciyar ki kuma kuma koda yake kinyi kokari a hakan ma don sam banga laifin ki ba ko kadan zainab.
Nasan wanan kwarai ban cancanci wata mace ta zauna dani ba a hakan sam don yadda rayuwana yake da akasin da mu hausawa mukafi tsana a duniya.
Allah yasan nasan kinyi hakkuri kan hakan amma ki kara dora hakkurin ki akan wanan din don ni kaina jikina yana ban zan bar wanan harkan nan gaba kadan insha Allahu.
Sai lokacin na samu magana don hakkurina ya kai karshe a lokacin na fara fadin ka daina ka daina shan giya ko ka daina kwana da maza yan uwan ka ko kuma tsafin zaka daina ?
Naji yace hummm zainab ke nan a yanzu nasan kinsan komai don haka kome zaki kirani dashi ki kirani dashi a yanzu din ya fada yana runtse idanuwan shi a hankali.
Wani iri naji a raina ba dadi don hakan ya zama kamar gori nayi mai a yanzu din ban san lokacin dana bude bakina ina fadin
Nasan jarabtane hakan a gareka don Allah kan jarabci imanin bawan sa tako wani hanya don yaga karfin imanin shi to amma yaya tunda ka gane hakan ka yaki zuciyar ka ka mayar da lamarin ka ga ubangiji ka Allah shine mafita.
Ka dauka ba mai iya yiwa bawa komai a duniyan nan sai Allah shike kashewa ya raya kuma aduk lokacin daya so hakan ga bawan sa.
A jiyan zuciya naji ya sauke daga inda yake kwance din a gefena naci gaba da fadin yau yaya baka zama kayiwa kanka tunane akan wanan rayuwan naka.
Idan akace yau babu kai dukiyan naka da kake nema ya zama ganima da abin wasoso ga duk ahalin ka .
Tunda ba zuria ko wani ka aje a duniya da zai gajeka ba a yanzu a kadara kana da zuria din yaya yaya ka ke son su kasance a cikin al,umma da rayuwan su.
Ni kaina a yanzu a kunyace nake shiga yan uwan ka tunda ina ganin kowa yasan irin rayuwan kyaman da kakeyi a yanzu balle yayan ka na cikin ka da kowa ke maka fatan samu a duniyan nan.
Ina maganan nan ne badon kwadayin abinda kake dashi ba ko dan nagada a,a ina magana ne don tsakanin mu dakai ba a san gawan fari ba a wurin Allah .
Kadara kai namiji ne a kullun mami tana maka fatan samun wata macen wayayya wace ta dace da rayuwa irin naka.
Ya kake tunanen zataji idan ta riskeka a cikin wanan halin baka tuba ka koma ga ubangijin ka Allah ba kana zaton zata kyale duniya bata jiku ba ke nan.
Hannun shi naji ya dora a saman kaina lokaci guda ya dafa min kai yana gyara kwanciyan shi a yadda yake kwancen da farko.
Zai,nab naji ya fada a hankali tare da sauke numfashi a cikin wani irin yanayi ya fara magana a hankali yana fadin .
Nima a kullun akai zancen haihuwa gareki ina mai jin zafin hakan don nasan laifin ba naki bane nine mai laifin ga baki daya kuma ake dorawa a kanki.
Nasan ba ko wace mace bace zata iya daga min kafa a hakan koda kuwa
Showing 354001 words to 357000 words out of 390011 words