fadilan tace mahaifan uwar dakin mu zainab ga kanwata nan da tazo jiya tazo dashi.
Ta dago ido ta dan kalli sa,adatu da mamaki ya fara kasheta a zaune tana fadin owo tazone ashe ?
Babu ko ya mutanen gida sai cewa tayi lafiya dai tazo ko wani abu tazo yi nan din da tazo tare da tsure mu da idanuwan ta tana karewa sa,adatun da mukai matukar kama da ita sai dai hanci da dan dogon fuska da haske kadan dana darata dashi wanda hakan yasa na fita kyau a gani da kuma wayewa shine kawai bambamcin mu.
Kai tsaye wanan karon na bata amsa da fadin duba mu tazo tayi taga saukan mu ta duba lafiyan mu.
Sai ta kawar da kai gefe can Aisha tace meye a cikin roban tana kallona ki duba ki gani mana da idanun ki na fada cikin dakewa.
Mami tayi saurin dago kai tana kallona don jin abinda na fadawa yar nata kai tsaye ta kasa danne zuciyar ta tace koma meye ai ba abinda baki taba gani bane da zai dameki har kina tambaya.
Wayana yai kara daga cikin jakka na sa hannu na dauko sunan ya j na gani a screem din wayan na dauka yake fadin kuna ina nace gidan mami.
Badai matsalan komai ya fada da sauri na ce a wayence babu don kada a gane tambayan da yai min din a lokacin sauran yan matan suka fito dakunan su.
Da yanzu dai ina ganin zaman su ya dawo Abuja ne suma bayan gama karatun su saidai ba wace tayi aure har yanzu a cikin su.
Rufaida ke fadin ba tare data kulamu ba ko tayi muna sannu da shigowa take cewa mami naji kina fada da wanan matar mai shegen baki.
Bari Rufaida macutan mutane ne yan aikin nan dukkan su ka basu amana sai sun yaudare ka maha,inta sai mutum.ya kwaso talaucin shi daga kawai yazo ya sameka da abinka yace zai cuceka har gida.
Af mami ai kin saba da halin su dama wahala ke koro su ai suzo birni aiki kome suka gani sai su dauka a banza ka sameshi kai wasu har su so hada kansu da yan gida su nuna sun fi mutane a karshe.
Dan murmushi na sake kadan ina fadin wanan kuma in kinga haka dama can mutum ba wullakntace bane da baiwan sa yazo .
Wasu ba sunan aikin suke zuwa ba cin arzikine sai kiga sun fi masu gidan iya shege don kawai haye daga sama ba a san kan arzikin ba.
Ai abin ke dai daga Allah ne da yake tsarawa kowa rayuwan shi yadda yaso mu zamu koma mami dama na kawo sa,adatune ta gaida ke.
Ban jira me mami zata fada ba na mike tare da kallon inda su Aisha suke ina fadin mun barku lafiya mun tafi.
Idan mijim ki na gida zan shigo don ina son ganin sa ki fada mai ban ko tsaya ta kanta ba na karasa gaban mami tare dan dukawa ina sallaman ta muka fita.
Shiru motan ba wanda yai magana a cikin mu kowa da irin tunanen da yakeyi a lokaci a zuciyar shi.
Mami kamar bata son ganin mu gidan ta kullun mukazo sai ta dinga daure fuska tana nuna bata son ganin mu.
Babu yadda zatayi ai dole ta ganku tunda danta ya dauko ku gidan shi bai kuma gaza da ku ba a rayuwan shi .
Don haka tayi a banza tunda bata sadai ya sake ki sai dai tace zata kara mashi aure don ki don kawai ta bata maki rai don kiyayya.
Aure kuma aishi yaya din ba zai yarda ba sai dai idan yana ra,ayin hakan dama zai yarda da shawaran nata sa,adatu ta fada .
Nidai ina jinsu ban tanka masu ba ina tunanen wanan maganan da fadila ta fada yanzu don tabbas hakan zai iya faruwa ba wai bs.
Gashi a bakin fadila nake jin zancen don nasanta nasan halin ta idan ta fadi magana kamar ta auna ne kafin ta fada.
Mun tsaya wani shago don sayen yan abubuwan motsa baki da zamu gida dashi har lokacin banda walwala a tare dani har muka koma gida.
Zaune muke a falona muna hira ya shigo da waya a hannun shi yana yi shiru mukayi don shigowan nasa ga waya da yakeyi.
Yana fadin yanzu dai me ya kawo wanan zancen nasan zainab nasan abinda zata iya mami don haka ban yarda da wanan zancen ba.
Na fada maku ban son irin wanan zancen akan yarinyar nan matatace fa zainab don haka yan uwanta nada daman zuwa dubata duk lokacin da sukaga dama.
A hasale yake magana don ranshi daya baci kan abinda mami din ta fada mashi ya karasa zancen da fadin bana son irin hakan .
Wanan dalilin yasa bana son zuwan su nan din tun farko don bana son irin abinda naga anayi din nan gaskiya.
Shiru yayi yana sauraren su kafin muga ya kashe wayan ya tura a aljihun rigan shi ta gaba ya juyo yana fadin meya faru ne da kuka je gaida mami dazun.
Nima da mamaki nace wani abin kuma akace munyi da mukaje ya ja tsuki tare da fadin yanzu mami ta kirani tana fadin wai naja maki kunne kan abinda taga kina son yi mata yanzu.
Ni din bana fatan ranan da zanwa wani babba rashin kunya ko wani abinda bai dace ba don nasan darajan iyayyena da manya na tun kan nakai haka.
Nasan neman bakine kawai sukeyi kan hakan yasa na dauki matakin da ya dace a yanzu kan hakan.
Indai nice su bar bata lokacin su ai na fada ina kawar da kaina gefe don raina da yake a bace.
Ya juya ya fita sai lokacin Sa,adatu ke fadin amma matar nan bata da hali ashe har me akayi bayan sune suke gasa muna magana ba a kula su ba.
Ni yau da nice da sun san suna sake min magana don wallahi ba zan kyale suba su dinga daukana kaskantata koda yaushe bayan Allah ya daukakani a cikin su su nuna min bakin ciki.
Haka kawai zasu azawa mutum tsana da kiyayya don kawai hassada da bakin ciki irin na dan adam me suka rasa a rayuwan su da zasu kyashe da baiwan da Allah yai maki yanzu.
Da nace daku kada mu tafi ai zaku ga kamar banson zuwan kune gidan amma yanzu da kuka gane wa idon ku komai ko na fada nan gaba zaku yarda dani.
Ai itama tana da yara mata a gaban ta bata san inda Allah zai jefa rayuwan su ba nan gaba shi tallaka ba abin rainawa bane sam a duniya.
Ranan sa,adatu tayi fada har ta gaji ta kyale don kanta nidai ba wanan ne a gabana ba don inda sabo na saba da halin mami da yaranta tun kan na auri danta a baya.
Fadila ko cewa tayi idan bata so ai sai ta dawo da tsaraban karshen kiyayya ke nan ai da zata nuna min sa,adatu tace shine ai.
Sai na dauka zasu dawo da tsaraban da muka kai na sa,adatu din sai gashi naji shiru banga an dawo dashi ba har tsawon kwanaki shima bai kara zancen ba.
Sai dai bai kara zancen mami din ko wani na gidan su ba a gaban mu sai mazan ne kan shigo su dubamu jefi jefi zamu gaisa a cikin mutunci dasu.
Nakan yi mamaki sosai yadda mami wai ta manta da komai na halin yaya take kokarin daukan laifi ta dora min koda yaushe sam bata kokarin maganan kan zancen halaiyar nasa balle a san mafita a kan dan nata.
A kan wanan tunanen na tsaya a zuciyana cewa duk ranan da wani zance ya kara hada mu zan fito fili in fada mata hakan don tasan dan da take min kyashin zama dashi fa ba cikakken namiji yake kamar kowa ba.
Sai dai me kuma a bangaren shi yaya Jafar din gaskiya yanzu yana jefa min wasi wasin akan shi ko da yaushe.
Don a gaskiya yana tsayuwan sosai akaina kan yadda mami din take kokarin nuna min zai tsaya ko a gaban kowa ya nuna shi bai yarda da hakan ba sam wanan ya kawo saukin wasu halaiyan da mami din ta dauko nuna min.
Wasa wasa saida sa,adatu ta shafe sati da kwanaki a wurin mu kafin ya shirya zancen zuwa gidan mu a lokacin.
Nayi mamakin irin tsaraban daya shiryawa tafiyan mu din da zan kaiwa iyayyena da yan uwa a gida.
Ga kuma kudi daya ban don kawai wanan tafiyan da har na rasa me zanyi dasu idan naje gida din don yawan su.
Lalai ka bar wanda yafika da wayaushi da hikima a kanka don sai Allah zai iya kwato ka gareshi gaskiya .
Don nikan yaya Jafar ya nuna min ya fini hikima da wayau tare da sanin duniya a yadda yake nuna min kamar babu gobe a kan mu wurin kulawa.
Saidai hakan bai hanani matawa da irin zaman da mukeyi dashi ba duk da yana rudina da abin duniyan da yake gani zai iya matar dani ga komai dake tsakanin din dashi na basajan da yakeyi wa mutane dani.
Wanda ya samu hakan ne ta dalilin hakkurina da zurfi ciki da Allah yai min wanda sam ban nunawa mutane sai idan kana da kula sosai zaka iya gane hakan.
Don ko zuwan sa,adatu wuri mu ban yarda ta fahinci irin rayuwan da mukeyi dashi din ba don yawan shakuwan dake tsakanin mu dashi zaka dauka wani zamane najin dadi akeyi tunda ba a daki daya nake kwana dasu ba.
Muka dauki hanyan garin mu a safiyan tafiyan cike da dauki da ka,idan zamuyi sati daya a gida mu dawo Abuja lokacin.
Na dauki duk wani abinda nake bukata har takarduna da bazan iya bari su a yanzu ba a matsayin riban da naci a zama gidan yaya jafar din danayi dashi.
Tafiyan mota masu lafiya karfe biyu da yan kai muna cikin gidan mu da mukai masu zuwan bazata a ranan do ba wanda yasan da zuwan mu a ranan sak ganin mu sukayi kawai ana muna sannu da zuwa.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
HASBUNALLAHU WANI IMAL WAKEEL YA HAIYYU YA KAIYUMU BINRAHAMATIKA YA ASTAGIS, , , ,
BARKAN MU DA SHAN RUWA UBANGIJI ALLAH YA KARBA MUNA IBADUN MU YASA MUNA CIKIN YANTTANTUN BAYIN SA YA SADA MU DA RAHAMOMIN SA YA GAFARATAWA MAGABATAN MU YASA MU GAMA DA DUNIYA YA TSARE MUNA ZURI,AN MU DAGA FITUNTUNUN DUNIYA ALLAHUMA AMIN, , , ,
Yan uwa nayi rashin kanwar mahaifiyata hjy hazeena Ahmed dake aure a garin zuru matar Ahmed jolly provose na yauri.
Allah ya karbi ranta bayan gajeren jinya datayi anshan ruwa lafiya da ita ranan asabar ciwon kai da ulcer yayi sanadiyan barin ta duniya a ranan ta rasu tabar yara biyu a duniya da fatan zakuyi mata addu,a irin na addinin musulcin nagode.
Ba wanda yasan da zuwan mu ranan sai gani mu akayi mota ta tsaya da baki a kofan gidan mu idon mutane dake shawagi a lokacin ya dawo gare mu.
Sai ganin Sa,adatu data fito farko daga motan ya dawo da hankalin su sanin cewa bakin gidan mune wanan.
Saida na dan dade ban fito a motar ba ina daukan jakkata da sauram kayan dana rike a hannuna kafin na zuru kafata farare da suka canza dan samun daula a yanzu waje.
Kafin gaba daya na fito daga cikin motan nida sadiya kusan lokaci guda muka fito daga motan kallo ya koma garemu nan kowa ke fadin albarkacin bakin shi a kan mu.
Don wasu na tambayan ina sa,adatu ta samo turawa wasu na fadin yartane da yar uwanta da akace suna turai zaune an sayar dasu ga wani mai kudi sai kudi yake turowa iyayyen su ba a san ko suna raye ba daga cikin irin maganganun da Lantana ke yadawa a garin game damu.
Na juya ina magana da driver kafin na juyo na fuskanci shagon tsoho baba iro wanda na bari ds kaya cike a ciki a baya inda mafi yawan mazan unguwan mu ke zama da can amma yanzu banga kayan ba .
Ba kuma jama,a da yawa a wurin basu fi su biyar zaune wurin ba a ranan na dan daga masu hannu tare da fadin baba iro mun sameku lafiya ?
Da sauri suke amsa min tare da fadin cewan wani a cikin su kungaji aina fada maku itace don bata da girman kai kaf a cikin su.
Nidai na shige ina jin su ban tsaya kula su ba don maganan da suke fadi a lokacin game damu din.
Sa,adatu ce a gaba muna bayan ta muka shiga da sallama Lantana na wanki a part din ta ta dago kai don ganin wanda ya shigo don sai ka shiga ta cikin tsohon part din mu zaka shiga kofan da zai sadaka dana innan mu a yanzu tunda basu bude kofan su na baya da aikai masi Abban mu ya hana hakan duk cikin dokan lantana a lokacin.
Wanda ba don komai tayi hakan ba sai don duk wanda zai shigo wurin inna mu tana gani da kuma abinda za a shigo gidan dashi din.
Sa,adatu bata tsaya bin ta nata ba duk da ta dago tana muna kalon mamakin data kasa boyeshi a lokacin a fuskanta don zaka gane a rude take da gani mu din.
Wurinta na nufa da yar fara,a a fuskana ina fadin anty Lantana mun sameku lafiya tunda ita ta kasa magana sai idon data waro a bude a lokacin.
Can kamar a firgice take fadin ai Abu kune tafe ashe sannun ku da zuwa a yadda ta tareni wanan karon naji mamaki matuka tankar ba Lantana bace.
Na duka ina daukan yarta dake zaune tana kuka ga yarinyar ko wanka safe ba ai mata ba sai tsamin dauda da ke fita a jikin ta .
Uwar ke fadin kada ta bata maki kaya Abu fitina take ji dashi halinta ke nan kukan banza ko yaushe.
Bayan na dauki yarinyar na juyo ina fadin mun sameku lafiya ya bayan rabo cikin kame kame har lokacin take fadin ahe zaku zo yau bankoji ana fada ba.
Nace ba wanda yasan da zuwan mu a yau din shiyasa ina Asabe da cewa kakan mu tana wurin ta ta ban amsa sai bina da kallon mamaki da takeyi.
Ihun kanne da suka fito daga part din innan mune ya dauke muna hankali duk suka zo suka kankame muna a jiki nida sadiya dake makale dani duk inda na saka kafata.
Lah yaya kika dauki wanan mai dattin haka ta bata maki jiki kanwata ta fada a cikin gatse don lantana taji haushi.
An dauke ta din ai ita ba irin ku bace da kuke raba daya biyu a gidan nan an dai ji din a ajeta kada ta bata mata jiki.
Ban tsaya ta kansu ba don zasu iya rikidiwa a wurin nake gani don haka na nufi part din asabe kakan mu ina tambayan su hanyan part din.
A wurin asabe din sun tsaya suna wagala tsohuwar da tsokana wai mu din bakin turawane mun zo muyi mata alluran riga kafin tsufa ne.
Ita kuma ta yarda da maganan su ta shiga yin bare bare ban taba riga kafi ba tun zamanin shagari da akai muna lamba a hannu ina lafiya sai yanzu za a zo min wani allura can.
Asabe wai baki gani ni bane Abuce fa na fada ina kallon ta ina murmushi tace tana kallo a cikin mamaki.
Abu dai Abun dana sani sai kawai ta fashe da kuka tana fadin hakan ta rungumeni tana fadin.
Abu ashe zan ganki kafin na mutu Allah na godema da ka nuna min yaran nan sun dawo garemu lafiya.
Ana ta fadin mun sayar daku ga mutumin da bamu sani ba don munga kudi ya rude mu sai gashi mutumin arziki da alherin sa yana ta turo muna da abin arziki a gidan nan kai da kai.
Sai da muka dan dade a part din na asabe tana faman bamu dariya kafi mu taso zuwa part din innan mu har lokacin yaran lantana suna biye damu a baya har lokacin.
Asamau kanwata ta juyo cikin hattara tana fadin ku kuma ina zaku haka kuna wani bin mu a baya ?
Da sauri na juyo ina fadin haba asma,u ki daina hattaran su haka mana jin muryan Lantana mukayi daga bayan mu tana dauke da ruwan pure water da ta sayo muna tana fadin.
Haka suke masu ai komai bakin cikin ku kuwa sai kun gansu a cikin gidan nan wa yanda sukai gadon mugun abu a zuciya.
Duk da zancen nata ya dakeni a zuciya don nasan gun innan mu take nufin sun gado bakin halin ta manta da nata halin ita
Showing 312001 words to 315000 words out of 390011 words
Ta dago ido ta dan kalli sa,adatu da mamaki ya fara kasheta a zaune tana fadin owo tazone ashe ?
Babu ko ya mutanen gida sai cewa tayi lafiya dai tazo ko wani abu tazo yi nan din da tazo tare da tsure mu da idanuwan ta tana karewa sa,adatun da mukai matukar kama da ita sai dai hanci da dan dogon fuska da haske kadan dana darata dashi wanda hakan yasa na fita kyau a gani da kuma wayewa shine kawai bambamcin mu.
Kai tsaye wanan karon na bata amsa da fadin duba mu tazo tayi taga saukan mu ta duba lafiyan mu.
Sai ta kawar da kai gefe can Aisha tace meye a cikin roban tana kallona ki duba ki gani mana da idanun ki na fada cikin dakewa.
Mami tayi saurin dago kai tana kallona don jin abinda na fadawa yar nata kai tsaye ta kasa danne zuciyar ta tace koma meye ai ba abinda baki taba gani bane da zai dameki har kina tambaya.
Wayana yai kara daga cikin jakka na sa hannu na dauko sunan ya j na gani a screem din wayan na dauka yake fadin kuna ina nace gidan mami.
Badai matsalan komai ya fada da sauri na ce a wayence babu don kada a gane tambayan da yai min din a lokacin sauran yan matan suka fito dakunan su.
Da yanzu dai ina ganin zaman su ya dawo Abuja ne suma bayan gama karatun su saidai ba wace tayi aure har yanzu a cikin su.
Rufaida ke fadin ba tare data kulamu ba ko tayi muna sannu da shigowa take cewa mami naji kina fada da wanan matar mai shegen baki.
Bari Rufaida macutan mutane ne yan aikin nan dukkan su ka basu amana sai sun yaudare ka maha,inta sai mutum.ya kwaso talaucin shi daga kawai yazo ya sameka da abinka yace zai cuceka har gida.
Af mami ai kin saba da halin su dama wahala ke koro su ai suzo birni aiki kome suka gani sai su dauka a banza ka sameshi kai wasu har su so hada kansu da yan gida su nuna sun fi mutane a karshe.
Dan murmushi na sake kadan ina fadin wanan kuma in kinga haka dama can mutum ba wullakntace bane da baiwan sa yazo .
Wasu ba sunan aikin suke zuwa ba cin arzikine sai kiga sun fi masu gidan iya shege don kawai haye daga sama ba a san kan arzikin ba.
Ai abin ke dai daga Allah ne da yake tsarawa kowa rayuwan shi yadda yaso mu zamu koma mami dama na kawo sa,adatune ta gaida ke.
Ban jira me mami zata fada ba na mike tare da kallon inda su Aisha suke ina fadin mun barku lafiya mun tafi.
Idan mijim ki na gida zan shigo don ina son ganin sa ki fada mai ban ko tsaya ta kanta ba na karasa gaban mami tare dan dukawa ina sallaman ta muka fita.
Shiru motan ba wanda yai magana a cikin mu kowa da irin tunanen da yakeyi a lokaci a zuciyar shi.
Mami kamar bata son ganin mu gidan ta kullun mukazo sai ta dinga daure fuska tana nuna bata son ganin mu.
Babu yadda zatayi ai dole ta ganku tunda danta ya dauko ku gidan shi bai kuma gaza da ku ba a rayuwan shi .
Don haka tayi a banza tunda bata sadai ya sake ki sai dai tace zata kara mashi aure don ki don kawai ta bata maki rai don kiyayya.
Aure kuma aishi yaya din ba zai yarda ba sai dai idan yana ra,ayin hakan dama zai yarda da shawaran nata sa,adatu ta fada .
Nidai ina jinsu ban tanka masu ba ina tunanen wanan maganan da fadila ta fada yanzu don tabbas hakan zai iya faruwa ba wai bs.
Gashi a bakin fadila nake jin zancen don nasanta nasan halin ta idan ta fadi magana kamar ta auna ne kafin ta fada.
Mun tsaya wani shago don sayen yan abubuwan motsa baki da zamu gida dashi har lokacin banda walwala a tare dani har muka koma gida.
Zaune muke a falona muna hira ya shigo da waya a hannun shi yana yi shiru mukayi don shigowan nasa ga waya da yakeyi.
Yana fadin yanzu dai me ya kawo wanan zancen nasan zainab nasan abinda zata iya mami don haka ban yarda da wanan zancen ba.
Na fada maku ban son irin wanan zancen akan yarinyar nan matatace fa zainab don haka yan uwanta nada daman zuwa dubata duk lokacin da sukaga dama.
A hasale yake magana don ranshi daya baci kan abinda mami din ta fada mashi ya karasa zancen da fadin bana son irin hakan .
Wanan dalilin yasa bana son zuwan su nan din tun farko don bana son irin abinda naga anayi din nan gaskiya.
Shiru yayi yana sauraren su kafin muga ya kashe wayan ya tura a aljihun rigan shi ta gaba ya juyo yana fadin meya faru ne da kuka je gaida mami dazun.
Nima da mamaki nace wani abin kuma akace munyi da mukaje ya ja tsuki tare da fadin yanzu mami ta kirani tana fadin wai naja maki kunne kan abinda taga kina son yi mata yanzu.
Ni din bana fatan ranan da zanwa wani babba rashin kunya ko wani abinda bai dace ba don nasan darajan iyayyena da manya na tun kan nakai haka.
Nasan neman bakine kawai sukeyi kan hakan yasa na dauki matakin da ya dace a yanzu kan hakan.
Indai nice su bar bata lokacin su ai na fada ina kawar da kaina gefe don raina da yake a bace.
Ya juya ya fita sai lokacin Sa,adatu ke fadin amma matar nan bata da hali ashe har me akayi bayan sune suke gasa muna magana ba a kula su ba.
Ni yau da nice da sun san suna sake min magana don wallahi ba zan kyale suba su dinga daukana kaskantata koda yaushe bayan Allah ya daukakani a cikin su su nuna min bakin ciki.
Haka kawai zasu azawa mutum tsana da kiyayya don kawai hassada da bakin ciki irin na dan adam me suka rasa a rayuwan su da zasu kyashe da baiwan da Allah yai maki yanzu.
Da nace daku kada mu tafi ai zaku ga kamar banson zuwan kune gidan amma yanzu da kuka gane wa idon ku komai ko na fada nan gaba zaku yarda dani.
Ai itama tana da yara mata a gaban ta bata san inda Allah zai jefa rayuwan su ba nan gaba shi tallaka ba abin rainawa bane sam a duniya.
Ranan sa,adatu tayi fada har ta gaji ta kyale don kanta nidai ba wanan ne a gabana ba don inda sabo na saba da halin mami da yaranta tun kan na auri danta a baya.
Fadila ko cewa tayi idan bata so ai sai ta dawo da tsaraban karshen kiyayya ke nan ai da zata nuna min sa,adatu tace shine ai.
Sai na dauka zasu dawo da tsaraban da muka kai na sa,adatu din sai gashi naji shiru banga an dawo dashi ba har tsawon kwanaki shima bai kara zancen ba.
Sai dai bai kara zancen mami din ko wani na gidan su ba a gaban mu sai mazan ne kan shigo su dubamu jefi jefi zamu gaisa a cikin mutunci dasu.
Nakan yi mamaki sosai yadda mami wai ta manta da komai na halin yaya take kokarin daukan laifi ta dora min koda yaushe sam bata kokarin maganan kan zancen halaiyar nasa balle a san mafita a kan dan nata.
A kan wanan tunanen na tsaya a zuciyana cewa duk ranan da wani zance ya kara hada mu zan fito fili in fada mata hakan don tasan dan da take min kyashin zama dashi fa ba cikakken namiji yake kamar kowa ba.
Sai dai me kuma a bangaren shi yaya Jafar din gaskiya yanzu yana jefa min wasi wasin akan shi ko da yaushe.
Don a gaskiya yana tsayuwan sosai akaina kan yadda mami din take kokarin nuna min zai tsaya ko a gaban kowa ya nuna shi bai yarda da hakan ba sam wanan ya kawo saukin wasu halaiyan da mami din ta dauko nuna min.
Wasa wasa saida sa,adatu ta shafe sati da kwanaki a wurin mu kafin ya shirya zancen zuwa gidan mu a lokacin.
Nayi mamakin irin tsaraban daya shiryawa tafiyan mu din da zan kaiwa iyayyena da yan uwa a gida.
Ga kuma kudi daya ban don kawai wanan tafiyan da har na rasa me zanyi dasu idan naje gida din don yawan su.
Lalai ka bar wanda yafika da wayaushi da hikima a kanka don sai Allah zai iya kwato ka gareshi gaskiya .
Don nikan yaya Jafar ya nuna min ya fini hikima da wayau tare da sanin duniya a yadda yake nuna min kamar babu gobe a kan mu wurin kulawa.
Saidai hakan bai hanani matawa da irin zaman da mukeyi dashi ba duk da yana rudina da abin duniyan da yake gani zai iya matar dani ga komai dake tsakanin din dashi na basajan da yakeyi wa mutane dani.
Wanda ya samu hakan ne ta dalilin hakkurina da zurfi ciki da Allah yai min wanda sam ban nunawa mutane sai idan kana da kula sosai zaka iya gane hakan.
Don ko zuwan sa,adatu wuri mu ban yarda ta fahinci irin rayuwan da mukeyi dashi din ba don yawan shakuwan dake tsakanin mu dashi zaka dauka wani zamane najin dadi akeyi tunda ba a daki daya nake kwana dasu ba.
Muka dauki hanyan garin mu a safiyan tafiyan cike da dauki da ka,idan zamuyi sati daya a gida mu dawo Abuja lokacin.
Na dauki duk wani abinda nake bukata har takarduna da bazan iya bari su a yanzu ba a matsayin riban da naci a zama gidan yaya jafar din danayi dashi.
Tafiyan mota masu lafiya karfe biyu da yan kai muna cikin gidan mu da mukai masu zuwan bazata a ranan do ba wanda yasan da zuwan mu a ranan sak ganin mu sukayi kawai ana muna sannu da zuwa.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
HASBUNALLAHU WANI IMAL WAKEEL YA HAIYYU YA KAIYUMU BINRAHAMATIKA YA ASTAGIS, , , ,
BARKAN MU DA SHAN RUWA UBANGIJI ALLAH YA KARBA MUNA IBADUN MU YASA MUNA CIKIN YANTTANTUN BAYIN SA YA SADA MU DA RAHAMOMIN SA YA GAFARATAWA MAGABATAN MU YASA MU GAMA DA DUNIYA YA TSARE MUNA ZURI,AN MU DAGA FITUNTUNUN DUNIYA ALLAHUMA AMIN, , , ,
Yan uwa nayi rashin kanwar mahaifiyata hjy hazeena Ahmed dake aure a garin zuru matar Ahmed jolly provose na yauri.
Allah ya karbi ranta bayan gajeren jinya datayi anshan ruwa lafiya da ita ranan asabar ciwon kai da ulcer yayi sanadiyan barin ta duniya a ranan ta rasu tabar yara biyu a duniya da fatan zakuyi mata addu,a irin na addinin musulcin nagode.
Ba wanda yasan da zuwan mu ranan sai gani mu akayi mota ta tsaya da baki a kofan gidan mu idon mutane dake shawagi a lokacin ya dawo gare mu.
Sai ganin Sa,adatu data fito farko daga motan ya dawo da hankalin su sanin cewa bakin gidan mune wanan.
Saida na dan dade ban fito a motar ba ina daukan jakkata da sauram kayan dana rike a hannuna kafin na zuru kafata farare da suka canza dan samun daula a yanzu waje.
Kafin gaba daya na fito daga cikin motan nida sadiya kusan lokaci guda muka fito daga motan kallo ya koma garemu nan kowa ke fadin albarkacin bakin shi a kan mu.
Don wasu na tambayan ina sa,adatu ta samo turawa wasu na fadin yartane da yar uwanta da akace suna turai zaune an sayar dasu ga wani mai kudi sai kudi yake turowa iyayyen su ba a san ko suna raye ba daga cikin irin maganganun da Lantana ke yadawa a garin game damu.
Na juya ina magana da driver kafin na juyo na fuskanci shagon tsoho baba iro wanda na bari ds kaya cike a ciki a baya inda mafi yawan mazan unguwan mu ke zama da can amma yanzu banga kayan ba .
Ba kuma jama,a da yawa a wurin basu fi su biyar zaune wurin ba a ranan na dan daga masu hannu tare da fadin baba iro mun sameku lafiya ?
Da sauri suke amsa min tare da fadin cewan wani a cikin su kungaji aina fada maku itace don bata da girman kai kaf a cikin su.
Nidai na shige ina jin su ban tsaya kula su ba don maganan da suke fadi a lokacin game damu din.
Sa,adatu ce a gaba muna bayan ta muka shiga da sallama Lantana na wanki a part din ta ta dago kai don ganin wanda ya shigo don sai ka shiga ta cikin tsohon part din mu zaka shiga kofan da zai sadaka dana innan mu a yanzu tunda basu bude kofan su na baya da aikai masi Abban mu ya hana hakan duk cikin dokan lantana a lokacin.
Wanda ba don komai tayi hakan ba sai don duk wanda zai shigo wurin inna mu tana gani da kuma abinda za a shigo gidan dashi din.
Sa,adatu bata tsaya bin ta nata ba duk da ta dago tana muna kalon mamakin data kasa boyeshi a lokacin a fuskanta don zaka gane a rude take da gani mu din.
Wurinta na nufa da yar fara,a a fuskana ina fadin anty Lantana mun sameku lafiya tunda ita ta kasa magana sai idon data waro a bude a lokacin.
Can kamar a firgice take fadin ai Abu kune tafe ashe sannun ku da zuwa a yadda ta tareni wanan karon naji mamaki matuka tankar ba Lantana bace.
Na duka ina daukan yarta dake zaune tana kuka ga yarinyar ko wanka safe ba ai mata ba sai tsamin dauda da ke fita a jikin ta .
Uwar ke fadin kada ta bata maki kaya Abu fitina take ji dashi halinta ke nan kukan banza ko yaushe.
Bayan na dauki yarinyar na juyo ina fadin mun sameku lafiya ya bayan rabo cikin kame kame har lokacin take fadin ahe zaku zo yau bankoji ana fada ba.
Nace ba wanda yasan da zuwan mu a yau din shiyasa ina Asabe da cewa kakan mu tana wurin ta ta ban amsa sai bina da kallon mamaki da takeyi.
Ihun kanne da suka fito daga part din innan mune ya dauke muna hankali duk suka zo suka kankame muna a jiki nida sadiya dake makale dani duk inda na saka kafata.
Lah yaya kika dauki wanan mai dattin haka ta bata maki jiki kanwata ta fada a cikin gatse don lantana taji haushi.
An dauke ta din ai ita ba irin ku bace da kuke raba daya biyu a gidan nan an dai ji din a ajeta kada ta bata mata jiki.
Ban tsaya ta kansu ba don zasu iya rikidiwa a wurin nake gani don haka na nufi part din asabe kakan mu ina tambayan su hanyan part din.
A wurin asabe din sun tsaya suna wagala tsohuwar da tsokana wai mu din bakin turawane mun zo muyi mata alluran riga kafin tsufa ne.
Ita kuma ta yarda da maganan su ta shiga yin bare bare ban taba riga kafi ba tun zamanin shagari da akai muna lamba a hannu ina lafiya sai yanzu za a zo min wani allura can.
Asabe wai baki gani ni bane Abuce fa na fada ina kallon ta ina murmushi tace tana kallo a cikin mamaki.
Abu dai Abun dana sani sai kawai ta fashe da kuka tana fadin hakan ta rungumeni tana fadin.
Abu ashe zan ganki kafin na mutu Allah na godema da ka nuna min yaran nan sun dawo garemu lafiya.
Ana ta fadin mun sayar daku ga mutumin da bamu sani ba don munga kudi ya rude mu sai gashi mutumin arziki da alherin sa yana ta turo muna da abin arziki a gidan nan kai da kai.
Sai da muka dan dade a part din na asabe tana faman bamu dariya kafi mu taso zuwa part din innan mu har lokacin yaran lantana suna biye damu a baya har lokacin.
Asamau kanwata ta juyo cikin hattara tana fadin ku kuma ina zaku haka kuna wani bin mu a baya ?
Da sauri na juyo ina fadin haba asma,u ki daina hattaran su haka mana jin muryan Lantana mukayi daga bayan mu tana dauke da ruwan pure water da ta sayo muna tana fadin.
Haka suke masu ai komai bakin cikin ku kuwa sai kun gansu a cikin gidan nan wa yanda sukai gadon mugun abu a zuciya.
Duk da zancen nata ya dakeni a zuciya don nasan gun innan mu take nufin sun gado bakin halin ta manta da nata halin ita
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22Chapter 23Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32Chapter 33Chapter 34Chapter 35Chapter 36Chapter 37Chapter 38Chapter 39Chapter 40Chapter 41Chapter 42Chapter 43Chapter 44Chapter 45Chapter 46Chapter 47Chapter 48Chapter 49Chapter 50Chapter 51Chapter 52Chapter 53Chapter 54Chapter 55Chapter 56Chapter 57Chapter 58Chapter 59Chapter 60Chapter 61Chapter 62Chapter 63Chapter 64Chapter 65Chapter 66Chapter 67Chapter 68Chapter 69Chapter 70Chapter 71Chapter 72Chapter 73Chapter 74Chapter 75Chapter 76Chapter 77Chapter 78Chapter 79Chapter 80Chapter 81Chapter 82Chapter 83Chapter 84Chapter 85Chapter 86Chapter 87Chapter 88Chapter 89Chapter 90Chapter 91Chapter 92Chapter 93Chapter 94Chapter 95Chapter 96Chapter 97Chapter 98Chapter 99Chapter 100Chapter 101Chapter 102Chapter 103Chapter 104Chapter 105 Chapter 106Chapter 107Chapter 108Chapter 109Chapter 110Chapter 111Chapter 112Chapter 113Chapter 114Chapter 115Chapter 116Chapter 117Chapter 118Chapter 119Chapter 120Chapter 121Chapter 122Chapter 123Chapter 124Chapter 125Chapter 126Chapter 127Chapter 128Chapter 129Chapter 130Chapter 131