a wurin yansandan kasan.
Ban komai a dakin sai ibada da kuka sai kuma tunanen hanyan da zanbi mu tsare a kasan da bamu da kowa illa shi da ya kawo mu garin.
A kwana na ukune hakkurin halima ya kare ta matsa min sai mu fita tare sayen abincin kamar yadda na saba fita in sayo muna duk abinda take so a cikin dabara.
Yau kan ta tubure min akan tare zamu fita haka na daure muka fito har waje da ita muka sai abinda zamu saya muka koma ciki.
Saidai irin kallon da mutanen ke min yasa na dan tsargu don da farko na dauka don launin fatan mu daban da tasune yasa suke kallon mu haka.
Bayan na dawo dakin ina zaune ina kallon yadda halimatu take cin abincin ta hankali kwance kamar ba abinda ya dameta.
Wani tunane yazo min lokaci guda na mike na fara tattara kayan mu da sauri naja hannun halimatu muka fito key din su na mika masu don basu biyo mu kudi ba mune ma muka biyo na kwana biyu a wurin su.

Yana tsaye sai waya yake faman yi daya kashe wanan ya dauki wanan ya rike kunkurun shi da hannu daya.
Yayin da dukkan aninaiyan suit din jikin shi suke bude ta gama daka ganshi kasan hankalin shi a tashe yake sosai lokacin.
Waya ya shigo mai ya dan juya ya kalla rai bace tare da jan guntun tsuki yana kawar da kanshi gefe daya.
Bayan kiran ya katse wani ya sake shigowa ya daga a hasale muryan mace yaji tana fadin yaran da ake nema aka bada wanan layin.
Na gansu yanzu a hotel din green land akusa da child center na wanan birnin yace hold on ki kara fada min yadda bayanin shigan su yake.
Ta shiga mai kwatance tare da siffan mu da yanayin komai namu da sauri ya mike ya figi key din shi sai inda suke parking din mota ya shiga daya daga cikin motocin dake wurin.
Ganin haka security din shi suma suka bi bayan shi da sauri duk inda yabi suna biye dashi har zuwa green land motel dake gefen garin.
Inda muke takai da security din hotel din akan kin barin mu mu fita daga cikin hotel din da sukayi don kawai su tabbatar idan bamu bane ake nema.
Muna tsaye wiki wiki ya iso wurin a har gitse halimatu na ganin shi tun daga nesa take nunashi da hannu tana fadin lah ga yaya a cikin harshen hausa ta sheka da gudu ta fada jikin shi .
Shima rungumeta yayi a jikin shi na dan lokaci kafin ya dago kai ya kalleni ba tsoro ko kadan a fuskana illa kara daure fuska danayi kawai.
Mayar da hankalin shi yayi wurin ma,aikatan hotel din suna mashi bayanin tun zuwan mu da yadda suka gane mune ake nema a tv.
Godiya yai masu tare da basu abinda akai alkawarin ba wanda ya ganmu dayan security din ya duka zai dauki dan jakkan kayan dake gabana don har lokacin ban ko motsa a yadda nake zaune ba.
Wani tsawa na daka mai tare da fadin don't touch my bag ya dan dago daga inda yaya yake shikuma yace da mutumin ya dauka su tafi.
A daidai lokacin da yake takowa inda nake zaune ya tsaya a gabana na dan wani lokaci kafin yace kiyi hakkuri mu koma gida muyi magana a can yanzu idon mutane na a kan mu.
Na dago kai na dan kalli wanda suke wurin idanuwan su ko na akan mu suna dan magana kasa kasa.
Haka yasa na mike badon naso ba na fara takawa a hankali yana rike da hannun halimatu suka biyoni a baya.
Motan shi muka shiga saida mukai nisa da hotel batare da ya juyo ba ya fara magana yana fadin daga yau idan zaki kara irin wanan kada ki soma ki tafi da sadiya.
Don ba zaman ki takeyi a garin nan ba ni da kaina na karbota hannun iyayyen ta don haka baki da ikon aiwatar da wani abu a kanta yanzu.
Amma kada ka manta ita din yar uwatace bana wani ba idan ba don niba bazata zo nan kasan ba tare dakai.
Don haka ba zan barta ta zauna a gidan da fasadi yazama ruwan shan don sabon Allah ya zamo shine alkibilan ka ko yaushe.
Dan murmushi naji yayi bayan hakan bai kara furta komai ba har muka isa gidan mota na tsayawa na fito na barsu da halimatu a baya.
Ban bi takan kowa ba part dina na nufa yana rufe na dawo part din fadila sai ganina tayi kamar daga sama ina shiga gado na fada ina kuka.
Sunana ta kira da karfi zainab kece wai Allah mun godema ina kuka shiga haka a wanan kasan mai yawa kuma gashi ba kasan mu ba ?
Jin yadda nake gumjin kuka yasa ta bar tambayan da take min din don itama hankalin ta ya tashi a yadda ta ganni na shigo dakin.
Saiga halimatu tana jan dan troler din mu da gudu ta fada jikin fadila tace sadiya kun dawo wallahi tun tafiyan ku hankalin kows gidan nan a tashe yake.
Shi kanshi me gidan baya zama gida kullun cikin neman ku yake ko za aji labarin ku mundai godewa Allah tunda kun dawo lafiya ai.
Bari na kawo maku abinci kuci ta fada tana kokarin mikewa halimatu tace anty a koshe nake yanzu bazanci abinci ba.
Muryan shine daga kofa yake fadin ki taso an bude part din ki daga haka ya juya ya fice abinshi bai tsaya jiran komai ba.
Dafani fadila tayi tana fadin zainab kin ki ki saurareni ne ranan da baki tafi ba wallahi duk da tafiyan naku ya dagawa mijin ki hankali sosai .
Saidai kusa lefin tafiyan naku duk a kaina ya dora shi yaga laifina sosai dana bari kuka tafi nasan da a Nigeria muke babu abinda zai hana ya koreni tun ranan.
Zainab koma me yai maki mace da hakkuri aka santa bada saurin fushi ba don kinyi kankanta dayin yaji a shekarun nan naki.
Jin abinda ta fada yasa na dago kai nace amma banyi kankanta a wurin hisabi ba ko anty ?
Kina ganin yanzu idan na mutu Allah ba zai mun hisabi bane kwadayi ko son duniya yasa in zauna a gidan mai sabon Allah irin haka.
Yaya jafar ba irin mutanen da suke shirin tuba bane da sabon Allah da sukeyi a rayuwan su har sai yaushe yaya zai daina wanan halin ya tubawa Allah.
Kuka yaci karfina ta samu ta lalabani da ban baki da magana masu taushi har na tsagaita kukan da nakeyi din.
Ban bar fakin ba sai bayan sallah magariba na koma part dina nayi wanka na kwanta duk da nasan ba barci zanyi ba a lokacin.
Tun ina tunanen matakin da ya kamata in dauka har barci yai awon gaba dani a wurin ashe yazo yana kwankwasa kofan ban budeba a lokacin.
Washegari na kunna wayana da ya kwana yana caji a jone sako ya fara shigo min wanda duk kusan sakon maya ce tana tambayan rashin gani school kwana biyu.
Sai kuma sakon shi yaya da yake tambayan muna ina don Allah mu dawo gida idan sakon shi ya sameni.
Zamuyi magana in fada mashi damuwa na ba sai na bar gidan haka ba yana dai tsoratani ga barin gida da mukayi a wanan kasan haka.
Tsuki nayi bayan na gama karantawa na wurga wayan saman gado na mike zuwa wanka nafito na shirya tsab don fita school .
A falo muka hadu da fadila fuskana babu walwala na gaida ita ta amsa min a cikin fara daganin shirina ba sai an tambayi inda zani ba.
Hakan baisa ta kyaleni ba take tambayana bazan tsaya in karya bane nace banjin cin komai a yanzu ina kokarin fita falon.
Nakai kofa take min a dawo lafiya da farko banga driver dake kaini school ba har na nufi katafaren get din gidan naji ana mun horn a bayana na waiga.
Driver ne a cikin wata yar mota daganin motar taci kudi masu yawa kafin a mallaketa.
Madam ga motar da oga ya canza muna yanzu wancan satin aka kawo ta yace an tsaya service din tane.
Kamar bazan shiga ba son dan guntun tunanen danayi a zuciyana sai dai na bude na shiga muka fice gidan.
A school kan nasha kallo don photo na da yai yawo a garin ko ina ana cigiyan mu nida halimatu na.
Fuskewa nayi na shige class din mu nan ma dai ban tsira ba maya ce ta tareni a cikin fara,a da mutuntawa tazo ta rungumeni.
Dama wuri daya muke zama da ita nan muka zauna muna dan hira amma bata sako min zancen batana dataji ance munyi ba a garin.
Sai biyu muka fito break wurina samu nayi alwala da sallah kamar yadda na saba kebewa in yi sallah idan ina school.
Maya na zaune gefe tana karatu har na gama take cewa mu dan taka wurin cin abinci don ita yunwa takeji.
Mun zauna a wurun an bamu dan abincin su da akeci da tsunke na tasa nawa gaba ina tunane ban taba ba.
Dafani maya tayi na dago firgigit na kalleta abincin ta nuna min da ido alaman inci abincin mana.
Dan murmushi na kakaro a fuskana na fara cakulan abincin da dan tsunken dake hannu na kadan naci na ture plate din abincin daga gabana na dauki ruwa na kurba kadan.
Koda baki fada min ba nasan kina da damuwa a ranki wanda hakan ya shafi matsalan gidane ko ?
Kasa nayi da kaina don idona da suka cika min da hawaye lokaci guda ban sa amsan da zan bata ba a lokacin gashi banda abokin shawara bayan fadila.
Fadilan kuma yanzu na kara wayau ba komaine zan iya sheda mata daya shafi mijina ko banza kasan mu daya koda ba garin mu daya ba.
Don a tunane ban dauka da tasan wanan zancen na yaya ba ashe ita kar take daukana tana dai taka tsantasan ne don kada aikinta ya kubce mata.
How can i help you ?
Ta kara fada tana kallona na dago kai a hankali na kalle ta a lokacin har hawayen da nake tarewa sun fara zuba a idona ko.
Tisui ta miko min daga cikin jakkanta na karba na dan goge fuskana dashi a daidai lokacin ta mike tsaye tare da fadin time yayi na komawan mu last period.
Mikewan nayi muka jera zuwa ciki saidai babu wanda ya iya magana a cikin mu don kowa da irin tunanen da yakeyi a cikin ranshi.
Haka na koma kwana biyu bana son magana da kowa a gidan don gaskiya ina cikin damuwa sosai na tsorace da al,amarin yaya zuwa yanzu.
Wanka nafito ina tsaye a dakin ina tsane ruwan kaina da dan karamin towel da daura gaban zani a jikina .
Ranan babu inda zan tafi don satine kowa na gida yana hutu a ranan kamar daga sama sai ganin yaya nayi a dakin.
Kallo daya yai min ya kawar da kanshi da sauri na nufi wurin gado na daki hijjab dina na saka a jikina ya kai zaune yana dan tabe bakin shi alaman ko a jikina ni.
Dan shirune ya biyo dakin kafin naji muryan shi yana fadin wai ke meke damun ki haka kike rama?
Kinbi kin damu kanki kin sakawa zuciyar ki wani damuwa da bai shafeki ba haka ?
Zaka iya fadin haka idan kaga dama kuma hakan ba zai ban mamaki ba ko kadan duba ga yadda ka tara kai shedan nama fitsari ko wani lokaci.
Yau dan musulmi dakai yaya kake wanan fasadin a rayuwan ka kamar dan wasu arnaku da baisan addini ba da abinda Allah yace.
Wani kallo yai min a harzuke take idanuwan shi suka kade sukai wani irin ja jajir ban fasa fadan abinda zan fadi din ba duk da ganun hakan danayi.
Yaya yau yaya mami zataci danta na kwana da maza yan uwan shi mazan ma ba daya ba yaya har maza biyu a lokaci guda.
Wa,iyazu billahi ko dabbo bi yan a halal kitabi bazasu taba aikata hakan ba don sun san da Allah ya hanesu da hakan suna tsoron azaban da Allah ya tanadarwa mai wanan dabian.
Wani irin kallo yake min lokaci guda kamar ranan ya taba ganina a rayuwan shi ji nayi kawai ya dankeni iya karfi shi.
Sai dana dan sake karan wahala muryan shi naji yana fadin uban wa ya fada baki nazo dake nan ne don ki saka mi ido ga al,amarina.
Kin isheni kin dameni da fitina irin naki kada ki dauka don na saka maki ido kamar wani abu nake bukata a wurin ki.
Mace kike ni kuma mata ba ra,ayina bane na daukoki nan ne don rufi asirina in rufa maki ki rufa min asiri.
Idan kina da ra,yin yadda kikaga dama kofan hakan a bude yake maki zaki iya morewa rayuwan ki don yanzu nagane kin girma.
Irin naki ra,ayin ba zan iya daukan hakan bani don haka zan baki dama kiyi duk abinda zai kawo maki sauki da jin dadin rayuwan ki matakur ba zaki shigo min gida da wani ba.
Wa iyazu billahi na fada da karfi kafin inyi luuuu yaji na sake a jikin shi don tun lokacin daya fara magana idona ya fara rufewa a hankali.
Da karfi ta fara girgizani tare da kiran sunana a rude saidai ba alaman farkawa alokacin a rude ya nufi bandakin ya debo ruwa a wani dan roba yazo inda nake kwance saman gado kamar yadda ya barni ya dinga shafa min a fuska a hankali.
Wani iri ajiyan zuciya na sauke tare da bude idanuna a hankali ganin shi gaba na tsura mai ido kamar ban taba sanin shi ba a duniya.
A hankali na mayar da idona na rufe ya kira sunana a sanyayye da zainab har sau uku na sake bude idon da kyar na sauke a kanshi .
Ruwan ya sake shafa min a fuska har saman wuyana a hankali na sauke wani irin ajiyan zuciya na bude idon ina kallon shi.
Wani irin hawaye masu zafi suka dinga fito a idanuwana saboda zancen shi da suke min yawo a kwakwalwana a lokacin.
Mikewa nayi kokarin yi da sauri don gaba daya na tsorata dashi Allah ya ban sa,a na samu na jaye daga inda yake tsugunne .
Na fara ja da baya a hankali ina girgiza kai tare da fadin yaya dama kai ba musulmi bane ashe ?
Idon shi naga ya runtse don jin abindana fada yaya kai da bakin ka kake fadin hakan alhalin ina matarka na sunna.
Baka tuna ko yanzu ko anjima yau ko gobe Allah na iya karban rayuwan daya baka aro a kyauta ka koma gareshi.
Can kasan makoshin shi naji ya sake kiran suna da fadin ke baki san wasa bane a rayuwa ?
Na fadi hakane don ki saurara min ga abinda kike yawan fada min amma na fadi hakane bawai ina nufin hakan ba har zuciyana.
Dan Allah yaya na rokeka kayi hakkuri ka mayar dani gida wurin iyayyena tun kan rayuwana ya samu illa.
Nayi ma alkawari kamar yadda nasha fada ma ba zanyi wanan zancen da kowa ba a gidan mu.
Enough ya fada da karfi sai dan shiru ya kura min ido a hasale can yace ban aureki ko dauko ki nan dan mu rabu ba.
Na daukokine a bisa wani dalili nawa da ba lalaine ki sanshi ba a yanzu tunda naga kurciya na wahalal dake.
Abinda nake so dake idan zaki iya yanzu shine ki kawar da idanun ki ga al,amarina gaba daya.
Ki maida hankali ga karatun ki da kikeyi idan zaki iya kuma ki mun addu,a idan kin samu lokaci.
Idan kinyi hakan babu wanda zai ji mu dake har zuwa lokacin da komai zaizo ya daidaita zuwa lokacin kema kin idar da karatun ki .
Kinga kina da zabi idan zaki koma gida a lokacin sai ki koma amma yanzu ina rokon ki kwantar da hankalin ki ida nufi a tsanake.
Kaina kada a tsorace tare da hada hanayena wuri daya ina rokon shi da fadin na rokeka ko meye manufan ka yaya kada ka cuta ma rayuwan mu nida yar uwata.
Baiyi magana ba ya mike tsaye ya dan tsura min ido kafin ya sa kai ha fice daga dakin na dora hannuna a kai ina neman kuka a idona na rasa.
Jikina yai wani irin sanyi ga tsoro dake saukar min duk a lokaci guda haka na
Showing 243001 words to 246000 words out of 390011 words