furta hakan da nufin tozarci a gareki ba don ba iya ita wanan kalaman zai shafa har mijin ta da kowa a yanzu hakan zai shafa.
Kara matsawa nayi dan nisa dashi a cikin murmushi nace kaiyya idan kai hakan ga yaya mamud baka kyauta ba kuwa .
Don baka da dan uwa mafi soyuwa a gareka bayan shi da jamal duk da ban zauna dasu ba munyi wanan zancen amma naga damuwa karara a tare dasu kan sanin ko kai waye da sukayi.
Shiru yayi gashi yana son bani hakkuri saidai ya rasa kalman da zaiyi amfani dashi wurin bani hakkuri a bakin shi don shi a nasa ganin tsaya a bata lokaci wurin ba mace hakkuri wani abune can na daban .
Gyara kwanciya naga yayi ya mike saman gadon tare da lumshe idanuwan shi sai hakan da yayi min a daki ya zama min wani bakon al,amari kuma tunda ban saba ganin hakan ba ni.
Sai mukai shiru na dan lokaci kowa da abinda yake tunane a ransa sai da na jefo mai tambayan da baiso ne ya bude idanun sa lokaci guda da nace.
Yaushe ne zamu gida muga su inna na tambaya cikin kallon shi inji amsan da zai bani lokacin sai cewa yayi dani sai idan kun kara hutawa zan shiryawa zuwan ku din.
Ba wani hutu don ba aikin komai nakeyi ba ko wani abu a nan yanzu don haka gida muke son zuwa mu ganesu.
Zaku tafi amma ba yanzu ba ya fada yana kara gyara kwanciya vikin dan kara lafewa saman gadon kamar mai shirin yin barci a dakin.
Iya kuluwa na kulu da jin amsan daya bani a lokacin don haka ban ko iya bude baki na ce dashi wani abu ba sai faman tunane da nakeyi a can kasan zuciyana wanda na kasa tsayar da zance guda kan hakan.
A hankali nake ji saukan numfashin sa dake nuna min ya samu barci ne a hakan na sauka saman gado a hankali zuwa bandaki don i kewa ya daga nan na tsaya yin wanka.
Har na fito yana a inda na barshi a kwance yana barci bai tashi ba balle in sa ran fitan shi daga dakin nawa sai abin nasa yake ban mamaki.
Haka na daure na karasa bakin mirrow ina shafa mai a jikkina da sauran al,adun mu na mata idan munyi wanka.
Kamar ance in daga kai yana kwance ya lafe a inda yake din ya kura min ido yana kallona nayi sauri kawar da kai daga hada idon da mukayi dashi da sauri.
Mikewa nayi zuwa wardrobe dina na bude sai lokacin nace dashi an lodawa mutum kaya haka kamar wanda zaiyi wani abu dasu ba sakawa ba.
Idan basuyi maki ba sai ki kyautar ya fada yana juyawa daga barin da yake kwance din nace har yaushe zamuyi amfani da wanan kaya haka wai ?
Har na gama na shirya a boboye duk yana dakin banu abinda nake ji sai haushi da takaici nasa na yadda ya zauna min a dakin da bansan dalilin hakan ba.
Bai fita dakin ba nima kamar an dasani a dakin haka muka zauna sai wuraren sha biyun rana ya bar dakin ya nufi part din shi.
Nima daki na gyara duk da wata tazo wai itace mai gyara amma ban yarda da hakan ba dana tashi kafin tazo na gyara dakina tsab balle yanzu da nake jin tsoron duk wanda ke gidan tare damu zaune sai nake masu bugu daya gaba dayan su ma aikatan gidan.
Ban fito ba saida sadiya ta shigo dakin tana fadin yayan mu kun tashi ke nan dazun nazo zan shiga anty ke fada min yaya yana ciki kwance.
Fadila fa na fada da mamaki tace eh ita ke fada mi hakan sai na koma barci yanzu na tashi yunwa nake ji sosai tana shafan ciki ta.
Ina mamakin fadila a raina nace ke nan bakici abinci ba kema tun dazun jin hakan yasa na mike muka fito falon tare ganin fadila dake mazurai yasa nace barin duba yaya ya fito mu karya na nufi part din nasa.
Na samu yayi wanka har ya saka tufafi a jikin shi a cikin daure nake fadin wai sadiya bataci abinci ba tun dazun tana jiran mu fadila ke fada mata kana dakina.
Bakiji lokacin da ta shigo dakin bane muna kwance ya fada na zaro ido waje a cikin mamaki yace eh ai hakan yayi kyau don zata shiga duhu kan abinda take hadawa yanxu.
Haka dai muka fito suka shiga gaidashi yana amsawa cikin basarwa har ya zauna yana fadin kanwata ya akayi baki ci abinci ba kika tsaya jiran mu ?
Haka dai muka zauna duk abin yana daurewa fadila kai don ta kasa fasara matsayin da yaya j yake ciki a yanzu don bayanin data tara nata yanzu ya bayar da ita kuma.
Wayan shi ne ya shiga kuka alaman kira na shigo mashi a lokacin ya basar kamar bai ga kiran ba haka yasa na duba ya mamud ne na dan dube shi sai ya dauki wayan ba don yaso ba sun gaisa yake tambayan shi naji yace bana gida na fita tunda safe.
Haka yasa na dago ido ina kallon shi vikin mamaki don da alama abinda ya fadi yake shiri sikatawa don laifin daba nasu ba ya shafi kowa a yanzu ke nan.
To meye laifin su ma akan wanan maganan dashi ya jawa kanshi hakan kome aka fada ai naga shiya jawa kansa dai hakam.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
HASBUNALLAHU WANI IMAL, WAKIL YA HAIYU YA KAIYUMU BIN RAHAMATIKA YA ASTAGIS , , , ,
LITTAFIN NAN NA KUDINE YAR UWA KI BIYA KI KARANTA A CIKIN SALAMA DA SAUKIN FAHINTA BA TARE DA DAUKAN HAKKIN KOWA BA A KAN KI YAR UWA, , , , ,
DON KIRA 08036959257 KO 09026931792 ACCOUNT ZAINAB IDRIS MAKAWA ZINETH BANK, , , , , , ,
Kwana biyar rabon mu da gidan mami har ranan ya J bai leka gidan ba tun mami na boye zafin hakan da take ji har ya kai ranan ta zauna a falo suna magana da yaranta ta sako zancen rashin zuwan shi gidan da baiyi ba.
Kowa yai shiru a falon sai jamal ne ya bata amsa ba tare da ya dago kaiba yake fadin mami ya zaizo kuna masu cin fuska irin haka ko waye ma ai dole yaji zafin hakan.
Shike nan kada a fadi gaskiya don kawai ya dauki yarinyar tafi kowa ko me zaice tayi laifi kada a fada.
Harni zainab zata ce saita huta zata zo gaidani da ace matsiyatan mahaifan ta ne garin nan har zata kwana uku bata gansu ba ?
Haba haba mami wanan abin fa ke batawa ya j rai daku ko ya iyayyen zee suke ai yanzu an zama daya dasu mami jalal ya fada.
Ji wani maganan banza da wa suka zama daya wa yan nan kaskantattun mutanen Aisha ta fada tana wani kauda kai.
Ke ni kike fadawa maganan banza haka ku mi shiru mami ta fasa a hasale tana zarewa kowan su idanu lokaci guda.
A daidai lokacin ya mamud ya shigo falon ganin yadda ya samesu kowa ranshi a bace yake fadi tun kan ya zauna.
Ba wanda ya bashi amsa sai ya juya wurin mami yana fadin mami mai ya faru kuma na ganku rai a bace ?
Barsu da batun banza kasan su jamal da jalal kamar wa yanda yarinyar nan zainab ta asirice su basu son ayi zancen ta ko kadan.
Zancen me kuma mami ina dai anyi wanan zancen ya tafi waya tayar da maganan kuma yanzu ?
Nice na tayar kan zancen rashin zuwan shi gidan nan yau kwana biyar ke nan da yin wanan zancen bai leko ba.
Zaizo mana mami abinda akai masu ne ba a kyauta ba idan ke kin fada masu ita wanan mara hankalin ina ruwanta da rashin haihuwan su har yanzu ?
Ko ita din da take haihuwan yaushe ta iya kula da yaran da har take fadawa wani bai haihu ba ?
Ta samu wurine a wurin mami don taga mami ta saka yar mutane a gaba akan danta yasa itama ta fadi hakana jalal ya fada .
Ya salam yaran nan me kuke son mayar dani ne yanzu bari kuje dukkan ku rayukan ku zai baci dani wallahi kan wanan zancen.
Kiyi hakkuri mami ya mamud ya fada yana kaiwa zaune kafin yace barin gwada kiran jafar din yanzu muji in lafiya yake don na kirashi yake ce min yana wani aikine.
Ya kira shi saidai bai dauki wayan ba har ya katse ya kara kiranshi wayan ya nuna yana busy.
Yace kin gani duk na kira busy yake saka min harni fushin ya shafeni ke nan ya fada yana kallon uwar tasu.
Yayi fushi mana indai don kan yarinyar nan ne zainab mai shegen bakin wayau su na yan kauye yarinya kwarkwar da shegen bakin wayau zanyi maganin ta ai don ba zan yarda ya kara barin kasan nan ba tare da kara aure ba.
Da sauri duk wanda ke falon ya dago kai yana kallon ta don jin abinda ta fada din .
Kai haba mami kada ki soma wanan abin don zai zama tonun asiri a garemu baki daya tunda kinga ko zainab din dai hakkuri takeyi dashi ai.
Hakkurin me mamud kune baku gane wanan yarinyar ba tun farko ni yanzu na dawo daga rakiyan ta ai.
Tunda na gane me take hadawa kan dan uwan ku idan da baida amfani a gareta zata zauna dashi tsawon wanan shekarun hakane ?
Tunda ta kasa shawo kanshi ai gara a auro wace zata zama silar barin komai nasa zaifi ta fada tana kawar da kai gefe daya a hasale.
Wanan shawaran naki baiyi ba mami sam wallahi don ya j din ba zai taba yarda da hakan bama wallahi .
Ke dai ki barshi a yadda ya zabawa kanshi illa dai a tayashi da addua shine abin yi a yanzu don wallahi tonawa kai asiri kawai za ayi ga hakan.
Ya mamud na shiru jamal ya dauka yace kai mami ina kika samu wanan shawaran kuma yanzu ?
Ya fada yana kallon ta yace kindai san waye ya jafar ai kin kuma san haiinsa idan zainab ta zauna ta rufa maku asiri duniya bata jiku ba wanan da zaki aura masa itace zata zama silar tona maku asiri a duniya .
Wai kanshine farau wanan halin idan na kara masa aure ai ita yarinyar da zan aura masa ba wata bace ta daban a cikin yan uwa zan aura masa wace ta waye ta san kanta har ta taimaka masa ya daina wanan halin da ake masa zaton yana yi.
Au mami yanzu baki yarda yana komai ba ke nan ya jamal ya tambaya cikin mamakin jin abinda mahaifiyar tasu ta fada.
Idan ma yanayi sai ka dauki laspeaker kayi shela zai fi ma sauki idan da har na yarda da zancen ku yanxu ban yarda da hakan ba.
Lalai mami akwai abinda ke damun ki ya mamud ya fada tare da fadin ke da kanki ba wani ya fada maki wanan abinba duk da mun san da haka amma ke kika gani fa da idanuwan ki.
Nayi da kai na gansa a wani halin a lokacin ko wani ya fada ma hakan cewa yaga yana aikata wanan abin .
In ma har zargi ake masa a bari ya kara auren sai mu tabbatar da hakan daga bakin wata ba a bakin wanan yar sherin yarinyar ba zainab.
Duk shiru sukayi sai can Aisha da har lokacin bata sanda zancen ba tace wai ma har me yake aikatawa haka mai muni da ake ta wanan zancen wai ?
Iyaka dai zainab tace yana neman mata ko ba a nema ita aka nemeta ne wai da ake wani tarewa kada a kara masa aure .
Waya gane me take samu ina gidan su da yan uwanta kawai take aikawa inba wanan karon data kawo muna wanan tsaraban ba haka ?
Ya jamal daya mike ya watsa mata wani irin harara daga inda yake kafin ya juya ya fice falon suka bishi da kallo cikin mamaki.
Yana zaune dan falon dake part din shi saidai wanan karon ba komai yake yi ba zama yayi kamar mai tunanen wani abu a zuciyan shi.
Kafin wayan shi dake gefe ya dauki kara ya kalli wayan saida ba sunan mai kiran nasa wanda hakan ya bashi mamaki waye zai kirashi da bakon lanba ne ?
Ya raya a ranshi yayan shi mamud ne ya canza layi don kin daga mai kira da yakeyi a kwanan kin nan.
Ya dai daure ya daga kiran ba tare da yin magana ba muryan jalal yaji a wayan yana gaidashi ya amsa yake fadin bros kwana biyu gashi har yau mami tana zancen ka.
Ya J rashin zuwan ka yasa mami tana shirin karayi ma aure don ta dauka laifin zainab ne hakan .
Wani murmushi ya sake a fuskan shi yana fadin aure fa jalal ita mami din ta fadi hakan yace wallahi yau take fadin hakan a gaban kowa dake falon .
Nan dai ya kwashe komai ya fada mai a cikin bacin rai har yana fadin ni bansan meyasa mami take kin zainab dinka ba yaya ga Nuriya da take mata iskanci amma bata ganin hakan.
Kada ka damu jalal ta dai fadi hakan ne kawai amma tasan ai banda ra,ayin mata biyu a rayuwana.
Bai tsaya jin ta kanin nasa dake fadin kada ka bari ta san ni na fadama don tayi warning din mu kada wanda ya sanar ma da hakan.
Ya kashe wayan ya mike tsaye cikin hasala zuwa dakin shi don ya watsawa jikin shi ruwa kafin nan ya fito.
Ya fito ya samu miscal har uku a ciki hardana jalal din daya kara kiranshi sai na ya mamud bai kira kowa a cikin su ba don yasan zance dayane dai suke kiranshi a kai.
Fitowan shi yayi daidai da shigowan ya mamud gidan muna gaisawa sai gashi taro na musanman aka hadawa yaya din a babban falon gidan da akayi don karban baki maza.
Sun gaisa yake tambayan shi ko lafiya kwana biyu bai shigo ba yake fadin lafiya kalau yake yana hutu ne a gida kawai.
Kana ganin rashin shigan ka gida wurin mami hakan da kayi shine mafita a gareka yanzu.
Dan murmushi ya sake tare da fadin mamud ya kake son nayi da mami meye laifin yarinyar nan zainab mamud ?
Idan mami bata godewa zainab ba ba kuwa zata hattare ta ba haka tana kokarin maida mun mata abin tsana a gareta.
Shima mamud din dan murmushi ya sake ma dan uwan nasa yana fadin duk mun san da hakan mun fadawa mami din komai.
Amma ta nuna ba hakan ba ni yanzu hukuncin da take son dauka a kanku don kawai maganan wanan mara hankalin Nuriya da mami ta hau shine matsalan dake shirin kunno muna kai a yanzu.
Wani matsala ke nan ya tambaya kamar bai san komai ba a kai sai mamud din ya dan dukar da kai kasa yana fadi a sanyaye mun dai fada mata zatayi kuskure idan tayi hakan don zai shafi gaba dayan mu gaskiya.
Duk zancen da sukeyi a kunnen fadila sukeyin shi kafin J din yace dashi ku barta duk wance zata aura min taje ta aura zata gane true colour dina lokacin.
Dan kallon fargaban jin abinda ya fada da fadila tayi mai yasa shi fadin fadila live dis place please.
Da sauri ta mike daga zuba ruwan juice din da takewa ya mamud ta koma ciki da sauri cike da biyayya a gareshi don bin umurnin shi.
Hakan baisa ya je gun mami din ba saida aka dauki kwanaki ya tafi bai wani tsaya ba suna gaisawa ya juya ya fito fuska a daure.
Nikan a lokacin ba abinda nakeyi sai sha hakkuri don mu samu ya sallameni zuwa gida gashi a bangaren fadila gulman abinda taji yana cin ta don a gaskiya duk da tana aiki akan shi ne hakan bai hanata sona a cikin ranta ba duk da ta kulla da ina ja baya da zancen ta a yanzu don ba kamar da muke ba sai mu zauna ba wani zance mai tsawo kamar yadda muka saba a baya da ita.
Satin mu biyu da zuwa Nigeria sai ga wayan sa,adatu take fadin ai gata ta hanya zuwa wurun mu inna ta aiko ta ta duba lafiyan mu.
Sam banji dadin hakan ba duk da hakan yana cikin karamawan iyayye a gare mu don asan mu din muna da gata yin hakan kamar al,adane na malam ba haushe.
Don inna tayi tayi da Abba
Showing 306001 words to 309000 words out of 390011 words
Kara matsawa nayi dan nisa dashi a cikin murmushi nace kaiyya idan kai hakan ga yaya mamud baka kyauta ba kuwa .
Don baka da dan uwa mafi soyuwa a gareka bayan shi da jamal duk da ban zauna dasu ba munyi wanan zancen amma naga damuwa karara a tare dasu kan sanin ko kai waye da sukayi.
Shiru yayi gashi yana son bani hakkuri saidai ya rasa kalman da zaiyi amfani dashi wurin bani hakkuri a bakin shi don shi a nasa ganin tsaya a bata lokaci wurin ba mace hakkuri wani abune can na daban .
Gyara kwanciya naga yayi ya mike saman gadon tare da lumshe idanuwan shi sai hakan da yayi min a daki ya zama min wani bakon al,amari kuma tunda ban saba ganin hakan ba ni.
Sai mukai shiru na dan lokaci kowa da abinda yake tunane a ransa sai da na jefo mai tambayan da baiso ne ya bude idanun sa lokaci guda da nace.
Yaushe ne zamu gida muga su inna na tambaya cikin kallon shi inji amsan da zai bani lokacin sai cewa yayi dani sai idan kun kara hutawa zan shiryawa zuwan ku din.
Ba wani hutu don ba aikin komai nakeyi ba ko wani abu a nan yanzu don haka gida muke son zuwa mu ganesu.
Zaku tafi amma ba yanzu ba ya fada yana kara gyara kwanciya vikin dan kara lafewa saman gadon kamar mai shirin yin barci a dakin.
Iya kuluwa na kulu da jin amsan daya bani a lokacin don haka ban ko iya bude baki na ce dashi wani abu ba sai faman tunane da nakeyi a can kasan zuciyana wanda na kasa tsayar da zance guda kan hakan.
A hankali nake ji saukan numfashin sa dake nuna min ya samu barci ne a hakan na sauka saman gado a hankali zuwa bandaki don i kewa ya daga nan na tsaya yin wanka.
Har na fito yana a inda na barshi a kwance yana barci bai tashi ba balle in sa ran fitan shi daga dakin nawa sai abin nasa yake ban mamaki.
Haka na daure na karasa bakin mirrow ina shafa mai a jikkina da sauran al,adun mu na mata idan munyi wanka.
Kamar ance in daga kai yana kwance ya lafe a inda yake din ya kura min ido yana kallona nayi sauri kawar da kai daga hada idon da mukayi dashi da sauri.
Mikewa nayi zuwa wardrobe dina na bude sai lokacin nace dashi an lodawa mutum kaya haka kamar wanda zaiyi wani abu dasu ba sakawa ba.
Idan basuyi maki ba sai ki kyautar ya fada yana juyawa daga barin da yake kwance din nace har yaushe zamuyi amfani da wanan kaya haka wai ?
Har na gama na shirya a boboye duk yana dakin banu abinda nake ji sai haushi da takaici nasa na yadda ya zauna min a dakin da bansan dalilin hakan ba.
Bai fita dakin ba nima kamar an dasani a dakin haka muka zauna sai wuraren sha biyun rana ya bar dakin ya nufi part din shi.
Nima daki na gyara duk da wata tazo wai itace mai gyara amma ban yarda da hakan ba dana tashi kafin tazo na gyara dakina tsab balle yanzu da nake jin tsoron duk wanda ke gidan tare damu zaune sai nake masu bugu daya gaba dayan su ma aikatan gidan.
Ban fito ba saida sadiya ta shigo dakin tana fadin yayan mu kun tashi ke nan dazun nazo zan shiga anty ke fada min yaya yana ciki kwance.
Fadila fa na fada da mamaki tace eh ita ke fada mi hakan sai na koma barci yanzu na tashi yunwa nake ji sosai tana shafan ciki ta.
Ina mamakin fadila a raina nace ke nan bakici abinci ba kema tun dazun jin hakan yasa na mike muka fito falon tare ganin fadila dake mazurai yasa nace barin duba yaya ya fito mu karya na nufi part din nasa.
Na samu yayi wanka har ya saka tufafi a jikin shi a cikin daure nake fadin wai sadiya bataci abinci ba tun dazun tana jiran mu fadila ke fada mata kana dakina.
Bakiji lokacin da ta shigo dakin bane muna kwance ya fada na zaro ido waje a cikin mamaki yace eh ai hakan yayi kyau don zata shiga duhu kan abinda take hadawa yanxu.
Haka dai muka fito suka shiga gaidashi yana amsawa cikin basarwa har ya zauna yana fadin kanwata ya akayi baki ci abinci ba kika tsaya jiran mu ?
Haka dai muka zauna duk abin yana daurewa fadila kai don ta kasa fasara matsayin da yaya j yake ciki a yanzu don bayanin data tara nata yanzu ya bayar da ita kuma.
Wayan shi ne ya shiga kuka alaman kira na shigo mashi a lokacin ya basar kamar bai ga kiran ba haka yasa na duba ya mamud ne na dan dube shi sai ya dauki wayan ba don yaso ba sun gaisa yake tambayan shi naji yace bana gida na fita tunda safe.
Haka yasa na dago ido ina kallon shi vikin mamaki don da alama abinda ya fadi yake shiri sikatawa don laifin daba nasu ba ya shafi kowa a yanzu ke nan.
To meye laifin su ma akan wanan maganan dashi ya jawa kanshi hakan kome aka fada ai naga shiya jawa kansa dai hakam.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
HASBUNALLAHU WANI IMAL, WAKIL YA HAIYU YA KAIYUMU BIN RAHAMATIKA YA ASTAGIS , , , ,
LITTAFIN NAN NA KUDINE YAR UWA KI BIYA KI KARANTA A CIKIN SALAMA DA SAUKIN FAHINTA BA TARE DA DAUKAN HAKKIN KOWA BA A KAN KI YAR UWA, , , , ,
DON KIRA 08036959257 KO 09026931792 ACCOUNT ZAINAB IDRIS MAKAWA ZINETH BANK, , , , , , ,
Kwana biyar rabon mu da gidan mami har ranan ya J bai leka gidan ba tun mami na boye zafin hakan da take ji har ya kai ranan ta zauna a falo suna magana da yaranta ta sako zancen rashin zuwan shi gidan da baiyi ba.
Kowa yai shiru a falon sai jamal ne ya bata amsa ba tare da ya dago kaiba yake fadin mami ya zaizo kuna masu cin fuska irin haka ko waye ma ai dole yaji zafin hakan.
Shike nan kada a fadi gaskiya don kawai ya dauki yarinyar tafi kowa ko me zaice tayi laifi kada a fada.
Harni zainab zata ce saita huta zata zo gaidani da ace matsiyatan mahaifan ta ne garin nan har zata kwana uku bata gansu ba ?
Haba haba mami wanan abin fa ke batawa ya j rai daku ko ya iyayyen zee suke ai yanzu an zama daya dasu mami jalal ya fada.
Ji wani maganan banza da wa suka zama daya wa yan nan kaskantattun mutanen Aisha ta fada tana wani kauda kai.
Ke ni kike fadawa maganan banza haka ku mi shiru mami ta fasa a hasale tana zarewa kowan su idanu lokaci guda.
A daidai lokacin ya mamud ya shigo falon ganin yadda ya samesu kowa ranshi a bace yake fadi tun kan ya zauna.
Ba wanda ya bashi amsa sai ya juya wurin mami yana fadin mami mai ya faru kuma na ganku rai a bace ?
Barsu da batun banza kasan su jamal da jalal kamar wa yanda yarinyar nan zainab ta asirice su basu son ayi zancen ta ko kadan.
Zancen me kuma mami ina dai anyi wanan zancen ya tafi waya tayar da maganan kuma yanzu ?
Nice na tayar kan zancen rashin zuwan shi gidan nan yau kwana biyar ke nan da yin wanan zancen bai leko ba.
Zaizo mana mami abinda akai masu ne ba a kyauta ba idan ke kin fada masu ita wanan mara hankalin ina ruwanta da rashin haihuwan su har yanzu ?
Ko ita din da take haihuwan yaushe ta iya kula da yaran da har take fadawa wani bai haihu ba ?
Ta samu wurine a wurin mami don taga mami ta saka yar mutane a gaba akan danta yasa itama ta fadi hakana jalal ya fada .
Ya salam yaran nan me kuke son mayar dani ne yanzu bari kuje dukkan ku rayukan ku zai baci dani wallahi kan wanan zancen.
Kiyi hakkuri mami ya mamud ya fada yana kaiwa zaune kafin yace barin gwada kiran jafar din yanzu muji in lafiya yake don na kirashi yake ce min yana wani aikine.
Ya kira shi saidai bai dauki wayan ba har ya katse ya kara kiranshi wayan ya nuna yana busy.
Yace kin gani duk na kira busy yake saka min harni fushin ya shafeni ke nan ya fada yana kallon uwar tasu.
Yayi fushi mana indai don kan yarinyar nan ne zainab mai shegen bakin wayau su na yan kauye yarinya kwarkwar da shegen bakin wayau zanyi maganin ta ai don ba zan yarda ya kara barin kasan nan ba tare da kara aure ba.
Da sauri duk wanda ke falon ya dago kai yana kallon ta don jin abinda ta fada din .
Kai haba mami kada ki soma wanan abin don zai zama tonun asiri a garemu baki daya tunda kinga ko zainab din dai hakkuri takeyi dashi ai.
Hakkurin me mamud kune baku gane wanan yarinyar ba tun farko ni yanzu na dawo daga rakiyan ta ai.
Tunda na gane me take hadawa kan dan uwan ku idan da baida amfani a gareta zata zauna dashi tsawon wanan shekarun hakane ?
Tunda ta kasa shawo kanshi ai gara a auro wace zata zama silar barin komai nasa zaifi ta fada tana kawar da kai gefe daya a hasale.
Wanan shawaran naki baiyi ba mami sam wallahi don ya j din ba zai taba yarda da hakan bama wallahi .
Ke dai ki barshi a yadda ya zabawa kanshi illa dai a tayashi da addua shine abin yi a yanzu don wallahi tonawa kai asiri kawai za ayi ga hakan.
Ya mamud na shiru jamal ya dauka yace kai mami ina kika samu wanan shawaran kuma yanzu ?
Ya fada yana kallon ta yace kindai san waye ya jafar ai kin kuma san haiinsa idan zainab ta zauna ta rufa maku asiri duniya bata jiku ba wanan da zaki aura masa itace zata zama silar tona maku asiri a duniya .
Wai kanshine farau wanan halin idan na kara masa aure ai ita yarinyar da zan aura masa ba wata bace ta daban a cikin yan uwa zan aura masa wace ta waye ta san kanta har ta taimaka masa ya daina wanan halin da ake masa zaton yana yi.
Au mami yanzu baki yarda yana komai ba ke nan ya jamal ya tambaya cikin mamakin jin abinda mahaifiyar tasu ta fada.
Idan ma yanayi sai ka dauki laspeaker kayi shela zai fi ma sauki idan da har na yarda da zancen ku yanxu ban yarda da hakan ba.
Lalai mami akwai abinda ke damun ki ya mamud ya fada tare da fadin ke da kanki ba wani ya fada maki wanan abinba duk da mun san da haka amma ke kika gani fa da idanuwan ki.
Nayi da kai na gansa a wani halin a lokacin ko wani ya fada ma hakan cewa yaga yana aikata wanan abin .
In ma har zargi ake masa a bari ya kara auren sai mu tabbatar da hakan daga bakin wata ba a bakin wanan yar sherin yarinyar ba zainab.
Duk shiru sukayi sai can Aisha da har lokacin bata sanda zancen ba tace wai ma har me yake aikatawa haka mai muni da ake ta wanan zancen wai ?
Iyaka dai zainab tace yana neman mata ko ba a nema ita aka nemeta ne wai da ake wani tarewa kada a kara masa aure .
Waya gane me take samu ina gidan su da yan uwanta kawai take aikawa inba wanan karon data kawo muna wanan tsaraban ba haka ?
Ya jamal daya mike ya watsa mata wani irin harara daga inda yake kafin ya juya ya fice falon suka bishi da kallo cikin mamaki.
Yana zaune dan falon dake part din shi saidai wanan karon ba komai yake yi ba zama yayi kamar mai tunanen wani abu a zuciyan shi.
Kafin wayan shi dake gefe ya dauki kara ya kalli wayan saida ba sunan mai kiran nasa wanda hakan ya bashi mamaki waye zai kirashi da bakon lanba ne ?
Ya raya a ranshi yayan shi mamud ne ya canza layi don kin daga mai kira da yakeyi a kwanan kin nan.
Ya dai daure ya daga kiran ba tare da yin magana ba muryan jalal yaji a wayan yana gaidashi ya amsa yake fadin bros kwana biyu gashi har yau mami tana zancen ka.
Ya J rashin zuwan ka yasa mami tana shirin karayi ma aure don ta dauka laifin zainab ne hakan .
Wani murmushi ya sake a fuskan shi yana fadin aure fa jalal ita mami din ta fadi hakan yace wallahi yau take fadin hakan a gaban kowa dake falon .
Nan dai ya kwashe komai ya fada mai a cikin bacin rai har yana fadin ni bansan meyasa mami take kin zainab dinka ba yaya ga Nuriya da take mata iskanci amma bata ganin hakan.
Kada ka damu jalal ta dai fadi hakan ne kawai amma tasan ai banda ra,ayin mata biyu a rayuwana.
Bai tsaya jin ta kanin nasa dake fadin kada ka bari ta san ni na fadama don tayi warning din mu kada wanda ya sanar ma da hakan.
Ya kashe wayan ya mike tsaye cikin hasala zuwa dakin shi don ya watsawa jikin shi ruwa kafin nan ya fito.
Ya fito ya samu miscal har uku a ciki hardana jalal din daya kara kiranshi sai na ya mamud bai kira kowa a cikin su ba don yasan zance dayane dai suke kiranshi a kai.
Fitowan shi yayi daidai da shigowan ya mamud gidan muna gaisawa sai gashi taro na musanman aka hadawa yaya din a babban falon gidan da akayi don karban baki maza.
Sun gaisa yake tambayan shi ko lafiya kwana biyu bai shigo ba yake fadin lafiya kalau yake yana hutu ne a gida kawai.
Kana ganin rashin shigan ka gida wurin mami hakan da kayi shine mafita a gareka yanzu.
Dan murmushi ya sake tare da fadin mamud ya kake son nayi da mami meye laifin yarinyar nan zainab mamud ?
Idan mami bata godewa zainab ba ba kuwa zata hattare ta ba haka tana kokarin maida mun mata abin tsana a gareta.
Shima mamud din dan murmushi ya sake ma dan uwan nasa yana fadin duk mun san da hakan mun fadawa mami din komai.
Amma ta nuna ba hakan ba ni yanzu hukuncin da take son dauka a kanku don kawai maganan wanan mara hankalin Nuriya da mami ta hau shine matsalan dake shirin kunno muna kai a yanzu.
Wani matsala ke nan ya tambaya kamar bai san komai ba a kai sai mamud din ya dan dukar da kai kasa yana fadi a sanyaye mun dai fada mata zatayi kuskure idan tayi hakan don zai shafi gaba dayan mu gaskiya.
Duk zancen da sukeyi a kunnen fadila sukeyin shi kafin J din yace dashi ku barta duk wance zata aura min taje ta aura zata gane true colour dina lokacin.
Dan kallon fargaban jin abinda ya fada da fadila tayi mai yasa shi fadin fadila live dis place please.
Da sauri ta mike daga zuba ruwan juice din da takewa ya mamud ta koma ciki da sauri cike da biyayya a gareshi don bin umurnin shi.
Hakan baisa ya je gun mami din ba saida aka dauki kwanaki ya tafi bai wani tsaya ba suna gaisawa ya juya ya fito fuska a daure.
Nikan a lokacin ba abinda nakeyi sai sha hakkuri don mu samu ya sallameni zuwa gida gashi a bangaren fadila gulman abinda taji yana cin ta don a gaskiya duk da tana aiki akan shi ne hakan bai hanata sona a cikin ranta ba duk da ta kulla da ina ja baya da zancen ta a yanzu don ba kamar da muke ba sai mu zauna ba wani zance mai tsawo kamar yadda muka saba a baya da ita.
Satin mu biyu da zuwa Nigeria sai ga wayan sa,adatu take fadin ai gata ta hanya zuwa wurun mu inna ta aiko ta ta duba lafiyan mu.
Sam banji dadin hakan ba duk da hakan yana cikin karamawan iyayye a gare mu don asan mu din muna da gata yin hakan kamar al,adane na malam ba haushe.
Don inna tayi tayi da Abba
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22Chapter 23Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32Chapter 33Chapter 34Chapter 35Chapter 36Chapter 37Chapter 38Chapter 39Chapter 40Chapter 41Chapter 42Chapter 43Chapter 44Chapter 45Chapter 46Chapter 47Chapter 48Chapter 49Chapter 50Chapter 51Chapter 52Chapter 53Chapter 54Chapter 55Chapter 56Chapter 57Chapter 58Chapter 59Chapter 60Chapter 61Chapter 62Chapter 63Chapter 64Chapter 65Chapter 66Chapter 67Chapter 68Chapter 69Chapter 70Chapter 71Chapter 72Chapter 73Chapter 74Chapter 75Chapter 76Chapter 77Chapter 78Chapter 79Chapter 80Chapter 81Chapter 82Chapter 83Chapter 84Chapter 85Chapter 86Chapter 87Chapter 88Chapter 89Chapter 90Chapter 91Chapter 92Chapter 93Chapter 94Chapter 95Chapter 96Chapter 97Chapter 98Chapter 99Chapter 100Chapter 101Chapter 102Chapter 103 Chapter 104Chapter 105Chapter 106Chapter 107Chapter 108Chapter 109Chapter 110Chapter 111Chapter 112Chapter 113Chapter 114Chapter 115Chapter 116Chapter 117Chapter 118Chapter 119Chapter 120Chapter 121Chapter 122Chapter 123Chapter 124Chapter 125Chapter 126Chapter 127Chapter 128Chapter 129Chapter 130Chapter 131