ce dashi bana son wanan mutumin yace saboda me ?
Nake fada mai abinda yaiwa yayan mu yake fadin bai yar, , , ki muna shiru waya aike ki fada mai wanan zancen sadiya ?
Tayi wani wiki wiki da ido na fada maki ba komai ne sadiya zata sani ba daya shafi mijin ki a yanzu.
Halimatu meyasa kika faye surutu haka waya aikeki fada mai wanan zancen barta ai idan surutu ta iya ai sai an dafa wanan bakin mai yawan surutun tsiya fadila ta fada a dan hasale.


ZAINAB IDRIS MAKAWA



LITTAFIN KUDINE YAR UWA KADA KI DAUKARWA KANYI NAUYI KI BIYA KI KARANTA A CIKIN SALAMA.
BA TARE DA DAUKAN NAUYIN KOWA A KANKI BA DON ALLAH, , ,

Bayan anty fadila ta karewa halimatu fada taja mata kunne sosai tare da tsoratar da ita illan yawan surutu a gaban kowa haka.
Ban kara jin duriyan shi ba har dare muma dari dari muka koma a gidan don abinda ya faru ranan don hankalin mu ya tashi ga baki daya a gidan .
Can cikin dare ne sosai ina barci nake jin hayaniyar su sama sama har na kai ga mikewa tsaye don firgitan da nayi saboda a tsorace na kwanta dama.
Takawa nayi zuwa kofa har na bude zuwa inda nake jin sautin na tashi sosai na hayaniya a gidan.
Muryan ya Jafar naji yana fadi a cikin fada duk son da zan ma ba zai taba kai wanda nakewa yan uwana ba .
Tun farko ban yarda ka shiga rayuwa naba saida na fada ma muhunmancin yaran nan a gurina ka yarda amma yau kaine da samun daman warning din ta akaina waya baka wanan matsayin na taba min family na .
Me kake tunanen kaika a gidan nan idan baka sani ba yau ka sani yarinyar nan she is my everything in dis world mu ba haka traditional din mu yake ba dole ne namiji ya zauna da mace ko yayane kuwa.
Muryan Nabil din naji kadan kadan da alama yasha wahala sosai a wurinyana fadin kayi hakkuri son kane ya rufe min ido har nake jin ban son ganin ta a gidan nan.
Amma hakan ba zai sake faruwa ba insha Alllahu nayi ma alkawarin hakan kayi hakkuri kada ka koreni don Allah ya fada a dan marairaice.
Kamar ma kuka yake yana magana motdin da naji a bayana ya sa tsoro ya kamani har na tashi kurma ihu sai ji nayi an rufe min baki da hannun maishi.
An jani zuwa part dina fadilace ashe itama hayaniyar nasu ya tayar da ita ta fito saida muka shiga dakin take fadin .
Ke baki tsoro su fito su sameki a wurin kijawa kanki wani laifi wanan ai ba abin saurarara bane ga mutum don abin babu dadin ji wallahi.
Anty a cikin barci naji hayaniyar tasu shiyasa na fito kada fa yaya ya illata abokin nan nasa nake gudu a kaina na karasa a dan maraice.
Ya nakasa shi mana ina ruwan ki ke wanan su ta shafa ki koma ki kwanta kuma kiyi kamar bakiji komai ba don kadama ki soma yi mai wanan zancen kashe gari.
Tana fadin haka ta fice dakin nabi bayan ta na rufo kofan da sauri na koma bakin gado na zauna ina tunanen irin kalaman da naji suna fada.
Karshe dai mikewa nayi daga wurin na nufi ban daki na dauro alwala na fito na fara sallah har tsawon wani lokaci kafin barci ya saceni a gurin danayi sallah barci ya daukeni nan.
Wanan ya jawo min makara gashi a ranan zamu koma makaranta hutun mu ya kare late na fita daga gidan sukuku dani jiki ba karfi.
Duk zirga zirgan da nayi a school wanan zancen bai fita a zuciyana ba sai faman kulawa nake ina warwala a cikin zuciyana.
Sai yamma lis na dawo gidan a gajiye don ba abinda nake bukata a lokacin sai wanka da bukatan hutu bako zancen cin abinci a raina.
Gashi kuma magariba ya gabato a lokacin don haka na fada bayi nayi wanka dana fitone na zauna wurin mirrow ina gyaran jikina sai naji an turo kofan dakin nawa.
Dan waigawa nayi kadan halimatu ne ta shigo tana fadin yayan mu ashe kin dawo tun dazun nake duban dawowan ki ai.
Eh na fada ba tare dana dago kai na kalleta ba a inda take tsaye taci gaba da fadin yau kin dade sosai yayan mu.
Eh na fada ina rufe man dana shafa tare da fadin kin san yau dole mu dade ai tunda yau muka koma school din.
Tace yaya Jafar ma ya dawo naga ya murda kofan ki yaji a rufe ya sake fita amma bai tambaye ki ba ya fice.
Don kamar ma ranshi a bace yake muna gaidashi da kyar ya amsa muna gaisuwan ya fita abinsa bai tsaya kulamu ba.
Mikewa nayi a wurin ina fadin halimatu kin faye surutu wallahi ba anty ta fada maki ba komai ne zaki fada ba wai.
Tace ta fada min na wuce ta kai tsaye zuwa wurin kayana ina dubawa ta sake fadin yayan kin sani wanan shegen Nabil din yau ya tafi naga ya dauki jakarshi da yamman nan ya bar gidan nan.
Wani irin juyowa nayi na harareta kafin in juya naci gaba da neman rigan da zan saka a jikina ba tare da yi mata magana ba.
Saidai can kasan zuciyana na cike da zargin maganan data fada min ke nan yaya ya koreshi saboda wanan case din namu dashi ke nan.
Riga na saka kafin na tayar da sallah magariba tare da umartan ta ita ma taje tayi sallah yanzu zata fice na kirata na nuna mata kofan bandaki koda ban fadaba ta gane me nake nufi da hakan don haka ta shige simi sim ba tare da wani magana ba.
Anan tayi sallah mun idar muna zaune kowa na addua anty fadila ta turo kofan ta shigo tana fadin wai ashe tana nan ?
Dama wanan yar rigiman ce ban gani ba nake neman ta don ban san kin dawo gidan ba ma sannu da dawowa ta fada tana kallona.
Sannu anty na fada ina shafa addu,a a jikina tare da fadin yau zirga,zirga yai min yawa a gajiye na dawo gidan nan don driver ya dade shima yana jiran na fito.
Karatu ko ina sai an daure kafin dadin shi yazowa mutum sai kiga wata rana sai labari insha Allah.
Zo muje ki ci abinci ta fada tana kallon halimatu dake zaune a gefena a wurin da mukai sallah din.
Idan nayi isha,i zan taso yanzu ta fada tana kallona nima ban tankata ba jin abinda ta fada lokacin.
Halimatu ta fara mikewa ta fice ni kuma na tsaya nade kayan danayi sallah don bana barin su a wurin idan nayi sallah.
Na nufi kofa ke nan ya shigo dakin ba tare da yai magana ba yake miko min wayana dake hannun shi kaina dago ina karba nake kuma gaidashi lokaci guda.
Ya amsa min a yanayin yana a cikin damuwa har lokacin nake fadin a cikin karfin hali yaya yau ko lafiya kake naga yanayin ka a haka ?
Tambayan nawa yazo mai a bazata don ba wani dogon zance mukeyi a tsakanin mu ba dama ya dan buda baki da kyar yana fadin .
Kawai na gajine daga wurin aiki nake yanzu ina son in watsa ruwane Allah ya taimaka na basa amsa dashi ina bin bayan shi bayan ya juya zai fita.
Kusan lokaci daya muka fito daga dakin nawa ina binshi a baya baisan dani ba saida muka kawo kofan part din shi.
Mamaki a fuskan shi yake kallo na ya dan kauce na shiga ban tsaya ba na nufi bedroom din shi direct ban dakin na nufa na hada mai ruwan zafi.
Na fito daga bandakin naga dakin a hargitse ko
ina dan dakin yana bukatan gyara a lokacin don haka na zage na fara gyara yana tsaye da waya a hannun shi yana magana a wayan dakin na shiga gyara a hankali kamar yadda yanayina yake nake aikina.
Ya gama ya cire kayan shi ba tare da damuwa da ina dakin ba a lokacin ya shiga ban dakin har na karasa gyaran dakin na fita bai fito ba.
Gashi ina aikin ina tunanen irin yadda yaya yake durawa cikin shi ruwan barasa don irin kwalaben dana gani a dakin bazakace shiya durawa cikin shi giyan ba haka.
Nikan da mamaki na bar dakin idona yana kokarin zubar da hawaye lokaci guda dan tausayin halin da yake ciki kuma gashi a matsayin mijina yake zama gareni da wanan halin.
Na gyara dakin ne dan kawai abinda naji yana fadawa Nabil a dare jiya game da matsayina gareshi daya fada.
Gashi yanzu nima ina jin a raina na na fara son kasancewa da mijina tunda dai a zaman mijina dai yake gashi idan yayi wani shiga ya fito kokai waye sai ka kalleshi ka kyasa mai dan kyau da kamala da baiwa irin na kyau da Allah yai mai ga zati da kamala a fuskan shi .
Ban nufi dakina ba falo na sauka wurin su fadila na samu sun ci abincin na zauna take tambayana bazakici abincin bane ?
A koshe nake na bata amsa da hakan ina kaiwa kwance don aikin dana danyi yanzu jikina ya saba da hutu dan bana aikin komai.
Shiyasa da na danyi aiki kadan jikina zai yi ciwo don rashin sabawa da hakan da banyi ba a yanzu.
Gashi a kullun wani irin kyau da kwarjini nake karawa sai wani haske da annuri da nake karayi ko yaushe.
Makerin budurcina a lokacin yagama fitar min da duk wani sura da akeso daga jikin diya mace su baiyana na cikan budurci sun fito min fili.
Ni kaina nasan a yanzu nakai lokacin shiga tsarana idan ana kwatance a fagen kyau da kira na ya mace.
Kawai ba zato ba tsamani aka shigo gidan kai tsaye ba sallama ba komai sai ganin katan maza mukayi su uku a kanmu sai wani binmu da kallo sukeyi kamar mazurai.
Gashi dan rigan dana saka a jikina na shan iska mai dan hannun shimi ne a jikina sai tsagan dake kasan rigan daga gefe daya.
Irin dai rigunan matan su na zuwa wani taro na muhinmin din nan shine lokacin saye a jikina wani purple dashi haka mai laushi.
Mun razana da ganin su haka yasa ni mikewa tsaye da sauri sai bin jikina sukeyi da kallo irin na yan iskan turawa din nan.
Who are you people ?
Na fada a razane a cikin bacin rai sai dayan yace dani we are jackson Friends .
Na kallesu a yatsune ina fadin wanan gidan Muslim ne bamu da jackson a gidan nan na basu amsa a cikin gatse.
Muryan ya Jafar ne ke saukowa daga sama yake fadin kai ku koma dakin ku yanzu ina da baki a gidan.
Juyawa nayi na kallo inda yake fuskan shi a daure tamau kamar bai taba dariya ba a rayuwan shi.
Jin abinda ya fada yasa na mayar da fuskana inda suke su duka na bisu da dan harara kafin ma inyi magana har fadila ta fara takawa don barin wurin duk a tsorace take a lokacin da ganin bakin nasa.
Dakin sa muka shiga basu ba har yaya din bin mu yayi da kallo saidai shi din kallon don me muka tsaya dasu muna magana haka.
Kafin ya juyo don yace dasu su zauna sai ya samu sun mutu a tsaye suna kallon mu ya fara magana a daidai lokacin suke sauke numfashi tare da fadin.
Waaawooo wanan ai ba kowa ne zai sameta ya kyaleta ba sai dai kai jakckson da baka son harka da mata sai maza kawai da ka hada both da zaka more a wurin wanan yarinyar gaskiya.
Wani irin mugun kallo ya watsa masu yana kaiwa zaune tare da jawo remote din tv dake aiki da muka bari a wurin yana aiki.
Ya juyo ya kallo su lokaci sun kai zaune daga tsayen da suke suna shakiyanci a tsakanin su fuska daure ya kallesu yana fadin meya kawosu wurin shi.
A cikin dariya dayan dayafi zama shakiyi a cikin su yake fadin ai da ganin mu gidan ka kasan maganan daya kawo mu tunda kaki daukan wayan mu tun dazun.
Don me zakaiwa sabon guy din ka haka jackson kana son ka zama mai kamawa da sakewane ko yaushe.
Gaka da sa,an samun gayu irin da kowa ke son ya samu amma sai ka dinga sakacida wanan daman naka.
Kodai yanzu ka fara canza ra,ayine ka fara sharing din both side samun wanan zukekiyar yarinyar a gidan ka ?
Don ba kowa zai zauna da wanan bai morewa rayuwan shi ni,imar dake jikin ta ba na mata koda kuwa baya jin dadin hakan a zuciyar shi.
Stop it philis,
She is my wife you can't talk haka a kanta kamar yadda kaima kasan ba zan taba fadin wani zancen banza ga family din ka ba ya fada yana mikewa tsaye.
Suma din mikewa sukayi don sun san shi sarai zai iya ficewa ya barsu wajen hakan ba karamin aikin shi bane wanan.
Da sauri dayan ke fadin haba man kada kai fushi damu mana mun san ba,a kyauta da hakan don kowan mu nan baya wasa da sister shi ko wata yar uwansa.
Jin hakan yasa ya koma ya zauna yana huci tare da kallon su daya bayan daya kafin ya sauke ajiyan zuciya.
Ya hade hannayen shi wuri daya yana sauraren abinda zasu fada dayan dayake abokin shi na sosai yace man dazun wanan sabon guy din naka ya samemu da wani zance .
Mun kira wayan ka yafi a kirga kaki ka daga yasa mukazo har gidan nan don mu baka hakkuri kan abinda yai maka don bai boye muna komai daya faru ba a tsakanin shi da sister din ka.
Wani irin kallo ya dago kai da idanun shi da sukai masa ja ya jefesu dashi kafin yace masu ku barshi kawai bana son kowa a kusa dani a yanzu.
Kada kace hakan jackson kasan baza mu iya daina wana harkan ba a yanzu don haka kayi hakkuri da wanan guy din don rashin sa gareka babban hasarane a wurin ka.
Don akwai masu son su kasance dashi na mika kudi masu yawa aka bakashi don haka kada kayi sakacin dazai kubce maka.
Let him go ya fada da karfi tare da mikewa tsaye kallon juna sukayi suma suna mikewa suna kallon shi .
Kada kaiwa kanka sakaci da wanan guy din don kowa sonshi yake a garin nan ya juyo ya kallesu yasa kai ya fice daga gidan.
Basu fita ba saida biyun suka juyo suka kalli dakin dana shiga kafin subi bayan shi shida abokin shi da sauri dama sun fi shakuwa a tsakanin su.
Ban yarda na fito dakin ba sai da zan kwanta na dauki drink da snack na shige dakina dashi sai bayan na gama abinda nakeyi nasha na kwanta.
Washe gari nayi samakon fita school acan ma na bata lokaci sai yamma na dawo gidan.
Bayan sati da yin hakan monday na shiga school a dan makare tun daga nesa nake jin hayaniya na tashi department di mu na hanzarta na shiga.
Abin mamaki na tarasa a wurin wai ana taya wasu ma,aurata murnan aure a tsakanin su .
Dan murmushi nayi na gefen fuska na ratsa mutane ina neman wurin zama daga can baya na samu wuri na zauna a wuri daya.
Wata na samu irin yan ra,ayin rikau din nan na addinin buda su na kasan jin hayaniyar yai yawa yasa na dan juya wurin ta duk daba wani shiri mukeyi a tsakanin mu ba ina tambayan ta ina ango da amarya don ni duk maza nagani a wurin gaba dayan su babu amaren.
Saida ta tabe baki take fadin wai a tsakanin sune sukai auren ai ga ango nan da bakin kaya amaryan kuma da fararen kaya a jikin ta.
Na dan gyara zama tare da kallon ta da kyau ina fadin kai shirme ke nan ina aka taba aure tsakanin namiji da namiji kuma in ba shirme ba ?
Sunayi ta fada tana runtse idanuwan ta a daidai lokacin da ake bi ana raba alawa bayan dogon adduan samun zaman lafiya da akai masu a tsakanin su.
Malami ya shigo aka fara lectures ni dai zaune nake tunane ranan nayi kala kala a raina kafin a fito don yin break.
Wanan matar mai addinin buda na sama take kara wayar min dakai game da auren jinsi da akeyi yanzu a tsakanin maza da maza ko mata da mata.
Driver na kira ya mayar dani gida don yau
Showing 234001 words to 237000 words out of 390011 words