a samu wanda zaizo ya dubamu da saukan mu amma sai Abba din ya hau fada kan hakan dole inna taja bakin ta tayi shiru.
Shine karshe suka yanke shawara a daki da yaranta kan sa,adatu ce zata zo Abuja ta dubamu da dan tsaraban da inna din ta hada muna kamar su dambun nama datayi mai yawa sai man shanu da kwai da dubula.
Duk a gidan malam mijin mai zube inna ta bada kudi aka hada komai a can da tare zasu zo da maizube din sai aka tashi ranan da zasu zo din wani a cikin yan uwan maizube din ya fadi ya rasu da asuba.
Shine dalilin da sa,adatu ta biyo hanya ita kadai duk da bata taba zuwa Abuja ko wani wuri mai nisa irin hakan ba sai wanan ranan.
Jin haka yasa na bugawa yaya waya ina sheda mai zancen zuwan sa,adatu din dake hanya tafe shima yayi mamakin hakan yake tambaya tana ina yanzu nace tace sun kusa shigowa gari don motan safe ta biyo zuwa Abuja din.
Bai dawo gidan ba sai tare da ita sukaje tssha aka dauko ta niki niki da robobi tsaraban da tazo muna dashi din.
Munyi murnan ganin juna da yar uwan mu har mun manta da duk wanda ke wajen a lokacin yadda muka makalewa juna don daukin ganin .
Sai cewa ya j yayi kuyi a hankali kada ku kayar min da matana don Allah duk aka kwashe da dariya a wurin yadda mukeyi saida ya ba kowa sha,awa don hakan na nuna akwai shakuwa da kaunan juna a gare mu.
Daki muka shiga bayan gama murna sai mamakin yadda muka canza take yi har ta kasa boye hakan.
Fadilace ta kawo mata abinci har dakin don gaskiya ina gani kokarinta wuri kaskantar da kai da takeyi don aikin ta wurin boye ko ita waye gare mu ta nuna aikin da ya kawota garemu shine takeyi a gidan.
Yau dai naga sa,adatun nan da nake yawan jin labarin ta gun ku ta fada tana aje turen abincin a gaban mu nace ga anty fadila sa,adatu.
Ta juyo tana fadin ayo itace ashe gaskiya yayan mu tana yawan ban labarin ki anty sannu da dawainiya an gode fa.
Ni kaina naji dadin hakan da sa,adatun ta fadawa anty din sai na karbe da fadin wallahi sa,adatu ko ya j yana fadin banda kamar anty a rayuwana shi kanshi yafi yarda da ita sama da kowa a rayuwan shi.
Yana daukan ta tankar yar uwa a garemu yanzu don ya wuce zaman aiki a tsakanin mu sai zumunci da rufawa juna asiri a yanzu don shi yanzu bai san abinda zai saka mata dashi ba.
Wani irin yanayi ta nuna a fuskanta lokacin da nake fadin hakan ta dan sake dariyan yake kawai tana dagawa a sanyayye ta bar gurin.
Tana fita na bita da kallo a fakaice kafin muryan sa,adatu ya dawo dani daga kallon fadila din tana fadin .
Anty wanan gidan naku kamar a turai mutum yake ni ai ban gama kallo ba don kawai kada na bar abin kunya na shigo.
Ki gama mu fita sadiya ta fada da take kwance rub da ciki tana jagulan wayan sa,adatu din dake hannun ta tana dubawa.
Munyi hira sosai ranan a daki muka wuni sai bayan la,asar yaya Jafar ya shigo dakin ya same mu zaune mun baje tana muna hiran Asabe da Lantana na fafatawan da ake tsakanin su yanzu.
Sai dariya muke kwasa ina kwance a gurin dana sallame sallah ita kuma sa,adatu tana saman rogh din dake tsakiyan dakin sadiya na saman gado kwance.
Gaida shi sa,adatun keyi ya amsa tare da karasa shigowa dakin ya nufi bakin gado ya zauna yana tambayan ta mutanen gida ?
Tace duk suna gaida shi su inna sunce ai masu godiya kafin su hadu na alherin daya aika masu shekaran jiya dashi .
Dago kai nayi da sauri na dan kalleshi bai nuna komai ba yi yayi kamar bai ganni ba ma na kallon da nake masa.
Yanzu karatun ki yayi nisa ko ya tambaye ta tace insha Allah muna two hundred level ke nan yace ashe kun fara nisa sosai .
To ya zancen ku da baba yanzu dai ya amince ki karasa karatun naki kafin zancen auren naki ko mu tsaya mu sha buki kafim mu koma ne ?
Ya tambayeta a cikin zolaya tace Abba ai case ne wallahi ni ba do kai ba yaya ai ba zai yarda naci gaba da karatuna ba a yadda ya dage din nan .
Yanzu ko shiru baya zancen ma sam idan ba nayi masa wani laifi ba kuma a kan lantana ce dake zugashi zakaji yace yar abu kaza aure zan maki in huta ai.
Ya kwashe da dariya zakace ba ya j bane ya sake haka a gabanta yana kwasan dariya nice na katse su da fadin ga sako nan inna ta aiko ma dashi ina nuna masa kayan da tazo dasu din.
Abinka da wanda bai saba da hakan ba ya dago kai yana fadin wanan meye haka da yawa aka aiko muna kuma ?
Sadiya ce ta sauko saman gadon da take ta fara bude mai roban dake cike da dambun nama kafin ta koma gana kwai dana man shanu .
Yake fadin kai wanan duk namune haka amma inna tayi dawainiya da yawa gaskiya.
Ai kaima kana dawai niya dasu sosai har su rasa bakin godiya sa,adatu ta fada yake tambayan sadiya cikin basarwa wanan din da kika bude da farko meye shi sady ?
Tace barin debo ma kaci kaji dambu ne na nama aka soya yace a hakan na tuna mami idan tazo ana kawo muna shi muci muna US.
Ta debo mai a lokaci nace sai a dibarwa su mami a kai masu don wanan dai yayi muna yawa kan a nan.
Bai ban amsa ba sai diba da yayi ya fara ci wanda hakannda yayi yai muna dadi sai godiya yake daids ya danci sosai muna hiran mu da sa,adatu bai ce komai ya mike yana fadin zaki kwana biyu a nan ke nan ko ?
Eh to kwana biyu din innan mu tace nayi na koma kada Abban mu yayi fada idan na dade yace ba zai yi fada ba ai a wuri mu kike ba wani wuri ba.
Mu yaushe zamu tafi ina tare zamu koma da ita idan zamu tafi na tambaya yayi kamar bai ji me nake fadi ba yasa kai ya fita.
Wai mu ba zamu gida bane yayan mu sadiya ta tambaye ni nace sadiya ban san me yake nufi da tafiyan mu ba har yanzu sai ja muna rai yake yi.
Kai wai meye a zuwa gidan da kuka matsa dayine ina dai dole ku tafi kafin ku koma ai .
Ki bari kawai sa,adatu bafa komai muke mashi a nan din ba kawai kuntatawa iri na mazane kawai.
Anty a gaskiya kinyi dacen mijin aure ga hankali ga natsuwa gashi da son yan uwanki kamar nasa kowa yana fadin hakan gaskiya ki godewa Allah da wanan rufin asirin da yai maki ke kan.
Wani iri naji a raina sa,adatu ke nan ke fadin haka ina ga iyayyen mu da ya riga ya saye nasan akwai aiki a gabana kan abinda nake kokarin shiryawa nan gaba ke nan.
Don su ba zasu gane ABU A CIKIN DUHU SIRI NE BA ni kadai nasan irin rayuwan da nake yi da ya jafar din don ko sadiya dake zaune damu nasan kirkin shi zata fada a gida idan hakan ya taso .


ZAINAB IDRIS MAKAWA


ALLAH YA SADA MU DA RAHAMOMIN SA YASA MUNA CIKIN YAN TANTUN BAYIN SA YA NUFEMU DA AIKATA ALHERI A RAYUWAN MU AMIN, , , , , ,

LITTAFIN KUDINE YAR UWA KI BIYA KI KARANTA A CIKI SALAMA DA AMINCEWA DON ALLAH DON KIRA 08036959257 KO 09026931792 ACOUNT 2254380105 ZAINAB IDRIS MAKAWA ZINETH BANK, , , , ,


Washegari mun tashi lafiya tare da kannena dashi mukai breakfast a cikin raha yana zolayan su har muka gama.
Ya mike zai tashi nake cewa dashi zancen tsaraban da za a kaiwa su mami din sa,adatu tace dayani sai naje na gaida mami tunda ba dadewa zanyi a nan ba idan za,a kai masu.
Allah ya gani banda niyar zuwa gidan mami kuma kan abinda sukai mun a ranan yasa na tsani sake zuwa da niyar gaida mami din gidan ta kuma.
Duk da nasan hakan abune mai wuya a wuri amma ba yadda na iya dole na amsa da hakan na dakyau sai naga ya dan kalleni a falaice baidai yi magana ba ya barmu a wurin.
Kamar yadda muka tsara hakan muka shirya da yamma bayan sallah la,asar don fita zuwa gidan mami din a karo na biyu da zuwan mu garin duk da nasan akwai kalubalin da ba za,a rasa ba ga zuwan namu gidan dake jiran mu.
Tunda a yanzu na gane dai ba zan taba haske a wurin mami ba don ta nuna min hakan a zahiri bata dai kaunana a yanzu sam.
Amma don kada kanwar tawa ta gane akwai wani abu a tsakanin mu da mami din yasa na daure don na kaita ta gaida mami din wanda ita take ganin hakan girmamawa ne a wurin ta.
Driver ne ya kaimu a cikin wani haddaden jeep dake fake a gidan tun zuwan mu nake ganin motan a jiye sai gashi yau da moka fito naga itace zamu fita da ita wanda hakan umurnine daga maigidan nasan.
Dukkan mu ukun mun gama haduwa wurin tara kwalliya da kure adaka inji bahaushiya wuri kwalliya muka dauki hanya har da fadila a wanan tafiyan sai da tayi mamakin jin cewa ta shirya zamu fita tare da ita.

Zaune take dakinta tana waya da yar uwanta dake fada mata hjyn su jikin ta ya dan motsa a ranan amma sun kaita asibiti taji sauki a lokacin tana dai kwance.
Bayan sun gama magana ne da yar uwan take tambayan mami din da cewa ashe jafar tare yazo da matar shi kasan wanan karon dazun nake jin haka da suke waya da yaya a falon hjy.
Dan wani basarwa mami tayi kafin tace tare sukazo ai yar rainin wayau yarinya da take ganin yanzu daidai take da kowa tunda ya maida ita wani abu a idon duniya.
A dama haka zata gani yanzu ai yaya tunda ta samu tsuntsu daga sama gasshe a hannun ta ba dole ta dauka tafi kowa ba.
Wai ki duba yarinyar nan saida ta kwana kusan biyar a kasan nan kuma a garin nan fa wai kafin zainab tazo gaidani .
Da sauri mama Ramatu din tace ita zainab din lalai yanzu wuyan ta ya isa yanka ke nan inda uwarta ce a garin zata iya hakkuri har kwanakin bata zo ta ganta ba.
Shina fadi nima Ramatu har yaran nan da basu san ciwon kansu ba suke ganin laifina kan hakan don nayi magana Nuriya kuma take fadin .
Ai bata burge ba tunda basu zo ganin mu da kama hannu ba da zasu zo shine fa wai jafar din har da daukan fushi dani don hakan.
Shi jafar din ta tambaya da mamaki tare da fadin kai yaro kamar wanda aka shanye da asiri kan yarnan wanan abubuwan da yakeyi akanta ?
Barni da mara mutunci zanyi magani su daga shi har ita don ba zai bar kasan nan ba sai da auren wata matar wanan karon .
Ta san cewa ban haifa mata dan ita kadai ba don su juya shi yadda suke so ita da iyayyen nata da yakewa bauta.
Wai yaya kina ganin zai yarda da hakan yanzu dama can bai yarda ba balle yanzu din kuma ya yarda ?
Zan tsaya sauraren shine Ramatu ai wanan karon umurni kawai zan bashi bawai rarashi ba daga shi har ita ai basu fi karfina ba Ramatu.
Zan zauna ne in saka masu ido tsawon wanan shekarun ba haihuwa ko batan wata tare dasu sai bakin kazafi da sheri da suke kokarin kulawa yaro ko yaushe shiko idon shi ya rufe baya ganin hakan ko kadan ?
Ai gara kan a gwada don shi bai sanin dadin hakan sai idan anyi zai gane gata akai masa da yin auren.
Shidai nagani Ramatu amma yaran nan da yake kansu daya duk basu ban goyon bayan hakan ba ai ni zan tsaya bin ta kansune halan.
Aisha ce ta shigo dakin a fusace tana fadin nifa mami ban ganewa wanan mai aikin naki ba fa duk akace tayi min gyaran daki sai wani abina ya bace a dakina.
Wayan ta katse tana kallon yar nata kafin tace wai bata daina wanan halin ba har yanzu kawai wanan karon idan zargina ya zamo gaskiya zan koreta ne don na gaji da zanbar yan aiki a gidan nan.
Kwanaki ina fada maku daga cire agogo in shaga ban daki sama ko kasa na nemeshi ban gashi ba a gidan nan.
Wazai dauka mami banda ita mudai tun barin mu da zee wallahi bamu kara samun yar aikin kwarai ba a gidan nan abu kamar da sa hannu a hakan.
Ita ma din aka sani ko hakan take wanan mai iya kilibibin tsiya da takom saka wa zai sani idan ma tanayin hakan ?
Kai haba mami gaskiya bata taba hakan ba ida ba dai wanan case na yaya j da ita ai zainab mutunce a wanan lokacin.
Tsuki mami din taja tana mikewa ta fito daga dakin tana kwalawa mai aikin kira da tantano tantano hat tana sarkewa wurin daga murya.
Matar ta fito da sauri tana amsawa da akala zatayi haihuwa bakwai ko shidda da haihuwa don dai ta dan manyanta kadan.
Tana fadin gani hjy mami ba tsaya jiran komai ba take fadin wai saunawa zanyi warning dinki kan taba muna kayane idan bamu baki ba.
Ni hjy mai kuma akace na dauka yanzu karya za ai maki muna tare da wasu a gidan nan bayan ke da za ace sune suke daukan muna kaya.
Wallahi sunma tallahi ban daukar maku komai ba hjy ta fada a cikin wani yanayi na bacin rai da rudewa lokaci guda.
A wanan lokacin mukayi sallama muka shigo gidan duk abinda suke fadi a kunnen mu wanda shigowan mu bai hana matar cigaba da magana ba tana fadin.
Hjy mezai sa na dauki abinda ba nawa ba idan ba a banba sai dai idan ba a duba bane da kyau.
Ban duba ba na nema banga dankune dana cire ba na aje saman side drower dina yanzu kuma na nema kaf dakin ban gani ba.
Da mamaki muka karaso tsakiyan falon inda suke matar tace nikan ban dauki dan kunne ba wallahi kuma ban maga yan kunne a wurin ba gaskiya.
Don Allah rufawa mutane baki mutanen banza duk haka kuke sai an yarda daku kwana biyu ku yaudari mutum mami ta fada a cikin takaici.
Wanda nasan gugan zana ce akai muna gaba daya lokaci guda harni dana shigo da yan uwana a gidan lokacin yasa mami fadin hakan don ta sokeni kawai.
Sallama na kara yi don kawai su bar zancen tunda mun shigo muzanci bada kyau a yadda sukewa matan .
Aisha ce ta amsa tana fadin kune a gidan sannun ku da zuwa tana yar sake yake a fuskanta muka karaso mami na fadin.
Ni dai ban taba dace da yan aikin kwarai ba a gidan nan kowa ka yarda dashi sai ya ha,ince ka a karshe ya nuna ma halin yan duniya.
Ta sake fadi a fusace jeki wallahi kifoto mata da dankunen ta kafin na hadaki da security ranki ya baci.
Ta juya zuwa wurin kujera ta zauna muma zama mukayi saman kujerum muna gaida ita .
A cikin mamaki ta dago kai tana amsawa tare da mamakin hakan don bata iya boye mamakin taba na zaman da mukayi akan kujera tana zaune sama itama a lokacin muke gaida ita.
Wanda ta dauki hakan a raini ne sosai a wurin ta, don kamar zaman tsara da tsara ne mukayi da ita a falon a ganin mami din.
Saidai ta daure ta amsa muna da kyat tana wani jan kamshi a tare da ita a daidai lokacin da wani yaron gidan yake shigo da roban da fadila tayi siling din kayan tsaraban Sa,adatu da tazo dashi.
Can ta juyo tana kallon shi tare da fadin wanan fa daga ina haka kuma tana kallon shi tana son karin bayani kan kayan da taga ana shigowa dashi falon.
fadila ke fadin hjy tsarabane da akazo dashi daga anchau shine aka kawo maki.
Inane haka kuma ta fada a wullakance tana dan bata fuska , a cikin dan murmushi
Showing 309001 words to 312000 words out of 390011 words