sama.
Banyi nawa ba ga hakan na sameshi shi kadai zaune ya tasa computer a gaban shi yana aiki ga cup din ruwan a gefen shi da yake sha.
Idona na akanshi bayan nayi sallama ya amsa min ba tare daya dago kan shi ba har na karaso inda yake zaune din idona yana akanshi.
Alokacin na kula da jikin shi daya tashi kamar yayi fada da wani yajin mai ciwo a haka nagaida shi da aiki na samu wuri na zauna daga gefenshi sai lokacin ya dago kai ya kalleni yana fadin.
Gobe din zasu tafi ko nace eh baka basu hakkuri su dage tafiyan nasu ba dazun yace hakan zaifi kyau ai ga kudi nan ki dauka a basu dubu dari uku.
Wanan kuma ku fita idan zaki iya ko kuma ki hadasu da fadila taje ta rakasu su sai tsaraba dashi.
Na dago kai a cikin mamaki nake fadin an ko gode wallahi amma dai ban tsamani zasu iya kashe wanan kudin duka saidai su gyara motan su da ya uzaifa ke neman kudi dashi ya lalace.
Jin haka yasa ya dago kai da sauri ya kalleni saina dan tsargu da kallon da yai min din naci gaba da fadin .
Ina nufin tunda mahaifin su Nafisa ya rasu yan uwan shi da abokan shi suka kwashe abinda ya bar masu suke cikin halin wahala motan daya da aka bar masune yaya uzaifa ke dan haya suna samun abinci yanzu kuma motar ta baci sun shiga wani hali ko abinci yana masu wuya a yanzu.
Zainab ke mai kikai msu akan hakan na dago kai da mamaki ina kallon shi don jin abinda ya fada din yace eh a matsayin ki na wace tafisu zarafi a yanzu wani taimako ya kamata ace kinyi masu.
Nan ma dai shiru nayi ganin ya tsureni da idanun shi yasa nayi karfin halin fadin ni me zan masu kuwa nadai taimaka masu dana abinci a lokacin da nake gidan su.
Nafisa kawatace ba yar uwata ta jini ba a makarantan da mami ta sakani a kaduna kafin mu dawo abuja muka hadu da ita ta taimaka min sosai a lokacin.
Tun wanan lokacin take a raina don bazan iya mantawa da karancin da taimin ba a lokacin shine dalilina nazuwa gidan su a yanzu na nemeta.
Ko a yanzun ma sun min karcin da ko wani dan uwana ba zai iya min haka ba don umma ta nuna tankar nice nafisa a wurinta ta sakani a hanyar daya dace kuma.
Nasan da hakan ko baki fada ba don ba zai yuyu matana ta tafi surun da banyi bincike a kanshi ba in kyale ta.
Na bincika nasan komai a kai don haka nake tambayan ki ai ya kamata ire iren su dake cikin wani hali kuma kina tare dasu in dinga sani don a taimaka masu ga rayuwa.
Ba wai ki shiru a kyale mutum a cikin wahala ba haka irin su ba zan san da halin da suke ciki na bukatan taimako ba ai ga kuma suna a cikin bukatan suna kuma cikin makusantan mu a yanzu.
Irin wanan alheri nakan so inyi shi saidai rashin sanin wa zan tunkara da hakan tunda bawai kusantan mu irun su sukayi ba.
Bayan hakan ma ai banda wani lokaci a yanzu da zan san hakan har insan wani na cikin irin wanan halin.
Yanzu ki basu wanan din ki bar ni zangana dashi yaron a waje inji abinda za a taimaka mashi dashi kafin su tafi.
Da wanan ya duka yaci gaba da aikin da yakeyi a cikin laptop dinshi kawai bai sake magana ba kuma bayan wanan din.
Kara dago kaina nayi idona ya sauka akan wuyan shi daya fi yin miki da yawa yana nuna kokawa yayi da wani ko wasu.
Sai abin ya ban mamaki sosai don a iya sanina dashi dai bansan shi da fada ba ko daga murya saidai idan ranshi ya baci bai iya nunawa mutum hakan ba a lokacin da ranshi ya bacin .
Har na mike ban bar tunane ba akan jin ciwon nasa sai faman tunanen inda ya samu miki hakan a jikin shi.
Dakin da umma din take na koma suna zaune nima na samu wuri na zauna a gefen ta tare da aje mata sunjin kudin duka a gefen ta.
Ta dago kai da sauri tana fadin na meye wanan kuma nace umma shi yace abaku kowa dari dari har yaya uzaifa.
Wanan kuma wai ku shirya fadila ta rakaku kasuwa ku sayo tsaraba dashi na bata amsa duk suka kalloni kafin su juya kuma su kalli juna ita da yarta.
Kai umma ta fara girgizawa kafin tace dani haba zainab ai wanan ya zama lalura kuma mu da mukazo neman lada za, a bamu wanan kudi haka ?
Don haka dauki kudin nan ki mayar mashi kice mun gode don Allah da zumunci muka kawo masa ke badon wani abin hannun shi ba.
Da sauri na tare da fadin a, a umma ko na mayar masa ba zai karba ba fada zai min kan hakan ko yanzu saida yayi min fada sosai kan zancen motan ya uzaifa dana fada mai ta baci.
Kai ta dago ta kalli Nafisa dake daga gefe zaune itama Nafisa din da sauri tace wallahi umma bada wani manufa na fada mata motan yaya din ya baci ba a cikin hirane har muka dauko zancen lalacewar motar tashi.
Yanzun dai na fahince ku so kuke ko mayar dani tsohuwar banza a cikin ku, ku bata min ladana da kimana a idon mijin ki ko ?
Wallahi umma ba yadda kike tunane zancen yake ba sam ban roke shi akan hakan ba sai don kawai ya tambayani zancen uzaifa nake dan fada mai abindana sani game dashi kawai .
Shine yake fada don me ban fada mai tun jiya ba yasan da hakan sai yanzu nake fada mashi zancen .
Amma wallahi ba rokon shi nayi ba akan hakan na dan marairaice mata ta bini da kallo kafin tayi ajiyan zuciya tana kawar da kai gefe daya.
Dakin yayi tsit a tsakani mu kafin ta dago tana fadin gaskiya hakan bai mun dadi ba wanan ai sai yaga kamar roko mukazo yi dama gunsa.
Umma yadda fa kike zato sam ba haka abin yake ba Allah sam umma ban rokeshi ba ko kadan yadda na fada maki haka zancen yake.
Idon ta ta kara saukewa kan kudin dana aje din a gabanta tace wanan kudin a gaskiya yayi yawa zainab don haka ki raba biyu ki mayar mai da rabi.
Murmushi nayi na mike tsaye tare da fadin Nafisa nasan umma ba zata fita ba ki shirya mu fita anjima karfe hudu.
Ina fadin haka na koma dakina don indan huta saidai tunane ya hanani hakan don a gaskiya zancen lamarin yaya ya fara daure min kai yanzu kuma.
Tunanen irin fada da naga yanayi a cikin mafalkine ya dawo min a raina zubur na mike daga kwancen da nake tare da wani irin tsoro da ya ziyarci zuciyana a lokacin.
Cikin kaduwa na mika hannuna inda wayana yake aje na fara neman layin malam kakana don in kirshi nayi sa, a wayan yana shiga don shi yace duk abinda na gani wanda ya fara daure min kai na kirashi don asan abin yi.
Bayan mun gaisa ne yake tambayan ya muka isa nace lafiya kalau ya sake tambaya to ya muka kwashe nace baiyi wani magana a kai ba har yanzu malam.
Saidai gaskiya naga wani abinda ya daure min kai dashine nan na koro mashi komai duk yadda abubuwan da yayi a barcin sa.
Sai da na gama fada mai komai ya danyi shiru kafin yace dani dama na fada maki sai kin jajirce don iri abubuwan da zaki gani a yanzu .
Don ko ke idan sun fahinci wani abu zasu iya juyowa gareki su farmakeki insha Allahu har in kin dage da addua ba zasu taba galaba a kanki ba da yardan ubangiji.
Dasu yake fada a mafalkin don ga zahiri kin gani da idon ki idan zaki tuna a baya irin yawan mafalkin da kika dingayi a lokacin yanzu shine ya fara baiyana maki a fili zakiga zahiri saidai irin kallon da kike ganin mutumin na maki yanzu din kece zaki masa da yardan Allah.
Mun kai wani lokaci da malan din yana min bayani kafin muyi sallama dashi ina masa godiya.
Ajiyan zuciya na sauke tare da lumshe idanuwana lokaci guda abubuwan da nasha gani a cikin mafalkina a baya ke dawo min a raina.
Dakin su umma kuma ina fita sadiyama dake kwance gefe ta daga tana fadin zanje in kwanta umma tunda ance za, a fita anjima.
Sadiya na fita dakin Nafisa ta kalli umma din tana fadin umma hakan da ki kaiwa zainab baiyi ba sai ta dauka kamar da wani abu ai.
Dole inyi fada Nafisa don na rasa abinda zan fada kan hakan iya gaskiyana ke nan don a yanzu kusan daya na daukeku a wurina don yarinyar nada hankali sosai wallahi.
Ita din a yanzu wani haskene ubanguji ya kawo muna a rayuwan mu a yanzu ban san kalman da zanwa yarinyar nan godiya dashi ba a yanzu.
Don ko wanan kudin kawai ya isa ya taimakawa uzaifa a halin yanzu na yarda alheri danko ne baya faduwa kasa banza.
Kin taimaka mata a baya yanzun kuma itace take taimakon ki a yanzu da abinda yafi wanda ke kika taimake ta din.
Umma a lokacin fa ba ma wani abu bane nake taimaka mata dashi sai dan abincin tara na da muke ci tare kuma in saya muna wani abu muci tare.
Don haka kawai yanayin ta yake ban tausayi yasa naja ta a jiki muna yawo tare ko ina tare zaka ganmu har dai sukazo suka koma abuja da zama ga baki daya.
Alheri Nafisa kona kwayan dabino ne sai ya rikede wata rana ya zama maka kamar girman zinari.
Haka muka fita da yamma ina a cikin damuwa har umma na tambaya ko dan abinda tayi min ne na koma haka kuma ?
Dan murmshi nayi tare da fadin umma ai ba afushi da zancen ku don kome kuka fada idan mutum ya kwatar da hankalin shi mai amfanine a garemu.
Abubuwane dai kawai suke ban mamaki dan dawowan nan namu umma a game da yaya jafar din yanzu.
Ina dai ba wanda zai iya illanta muna ke bane yar nan umma ta fada a dan razane.
A, a umma lamarin fa dai ya shafe shi ne ni bai shafeni ba tace to Allah ya sauwaka daga haka kowa yai shiru a motan.
Mun zaga sun sayo abinda suke so sai dai ba sosai ba don a karshe duk abinda suka nuna suna so basu saya ba nakan saya nace ya ban sha,awa nima.
Mun dawo a gaji lokacin magariba ya yi mun samu ana sallah magariba bamu tsatsaya ba muma muka gabatar da sallah kafin mu shirya masu kayan su a wuri daya.
Yau ma kamar ince yaya jafar yafi shan wuya a cikin barcin ko ince mafalkin shi don dambe sosai yayi a mafalkin nashi da kuma surutu da banjin abinda yake fada har saida na tayar dashi daga barcin nasa.
Yana falkwa da kyat ya fara fadin bani ruwa in sha zainab ki taimaka min da ruwa sai kuma zufa da yake karyo mashi a lokaci guda ya jiki sharkaf duk da sanyin AC dake akwai a dakin lokacin.
A cijin gigita na falka na nufi inda goran ruwa yake na dauko mashi ya kafa kai zuka daya ya zuke ruwan goran duka kamar wani mai cutar masha ruwa.
Ni dai ina tsaye gefe na rugume hannaye ina kallon shi a cikin mamaki na rasa abinda zanyi mai a lokacin .
Kamar an tuna min na shiga karanta mashi Amanal rasulu har zuwa karshe kafin naga ya koma ya kwanta lankwasa saman gadon yana sauke numfashi guda guda ya dafe goshin shi da hannun shi.
Ranan kan naji tsoro kwarai da wanan abin dayayi a gabana gashi kuma na dauki alkawarin duk wani abinda ya sake faruwa dashi ba zan sake kiran mami in fada mata ba .
Tunda tace kazafi nake son na kullawa danta don kawai in bata mata sunan zuri,anta a duniya nake fadin haka .
Shiru ne ya biyu dakin na dan lokaci ina tsaye a kanshi na kura mai ido kafin inga ya sauke wani ajiyan zuciya ya gyara hannun shi dake saman goshin shi da alama kanshi ke masa ciwo sosai a lokacin.
Hannuna nakai a hankali saman kafada shi jin hakan yasa ya sauke hannun nasa da sauri ya kallo inda nake tsaye ya sauke idon shi akaina.
Meke damun ka hakane yaya ko baka da lafiya ne baka fadawa kowa ba matsalan dake damun ka kada yai ma yawa a hakan.
Murmushin karfin hali naga yayi tare da dan jan jikin shi ya koma baya yana fadin koma ki kwanta abinki ba abunda ke damuna mafalkine kawai nayi.
Ka dinga addua idan zaka kwanta zaifi akasari idan mutum ya kwanta ba tare da addu,a ba hakan ne yake faruwa dashi.
Nagode ya fada tare da juyawa kamar wanda baison ganina a lokacin don haka na gane na zama mai karfe kafa a yanzu ke nan.
Juyawa nayi side din da nake kwance da farko na koma na kwanta ina karanto muna addua a fili ta yarda har yake iya jin abinda nake karantawa.
Haka dai muke kwance ba wanda ya iya komawa barci a lokacin ganin shirun yai yawa na mike na shiga bandaki na dauro alwala na fara gabatar da Nafila.
Ko me ya gani yakai kusan rabin awa naga shima din ya mike ya nufi ban dakin ya dan dade a ciki kafin ya fito daga ciki da alama alwala yayi shima yazo ya fara sallah.
Saida akai kiran sallah muna zaune shiya fara mikewa ya sake dauro alwala kafin nima nabi bayan shi .
Ina idarwa ban tsaya gaidashi ba na mike zuwa dakina na kwanta don barcin da nake ji sosai a lokacin.
Barci ne mai nauyi ya daukeni can cikin barcin nake jin ana ja min kafa hakan yasa na bude idanuwana da kyar don ganin mai tayar dani din.
Da kyar na iya bude idona shine tsaye a kaina yana saye cikin kaya irin na motsa jiki kamar bashi bane ya wahala a daren jiya din haka ?
Ki tashi kada kisa su makara rana ya soma yi ya fada yana tsaye a kaina zan tashi na fada ina gyara kwanciyana don barcin bai sakeni ba.
Ya kara fadin zaki tashi ne fa don sun shirya nake ganin tun dazun haka yasa dole na mike ina mamakin shi a raina har lokacin kamar bashi ba .
Mota nan waje da zasu tafi dashi munyi magana da yaron zai kawo min takardun shi in duba inda ya kamata a sashi ya fara aiki.
Da sauri na mike zaune don jin abinda ya fada nace a cikin mamaki mota yaya eh ya tafi dashi ya fara amfani dashi.
Ganin na tashi yasa shi ya juya ya fita daga dakin nabi bayan shi da kallon mamaki ga mutum har mutum a fili amma ya samu rauni ga imanin shi.
Yanzu wa zan fadawa wanan maganan ya yarda dani a yadda muka kwana dashi a daren jiya a wahalce dashi har a yarda da abinda na fada yadda ya mike haka da safe.
Gashi gari ya waye ya mike tangararam kamar wani abu bai faru dashi ba haka a daren jiya din don haka yanzu dai ya tabbata a zuciyana shi din yana wani kungiya ke nan na asiri ko wani abu na boye da mutane basu sani ba ?
Wanka na shiga na fito na shirya tsab kafin inje dakin umma din na samu har sun karya fitowan mu kawai suke jira a lokacin.
A, a wai har kun shirya kome na fada ina kallon nafisa dake zaune a cikin shirin ta .
Tace fitowan ki kawai muke jira mu da yanzu munyi nisa kinsan yau umma nada ganin likitan ta ai.
Gaskiyane na fada ina kawai tsugune kasa don gaida umma din a cikin ladabi da biyayya ta amsa min da dan fara,anta a fuska don jin dadi.
Ita a zaton umma din abubuwa sun fara kamkama a tsakani da yaya yanzu don haka takw ganin hikimar ta yayi na cusani a gareshi datasa inyi don dole.
Saidai da ace a lokacin umma tasan kusantan shi da nakeyi yana sashi shiga cikin ukuba a kullun na kwanta a kusa dashi da bata umurceni da yin hakan ba a lokacin.
Don wanan zuwan da nake daki shi
Showing 336001 words to 339000 words out of 390011 words