daga hannun shi.
Ki kamani in koma saman gado ya fada a hankali don haka sai na aje cup din sa sauri har yana faduwa kasa .
Ban damu da hakan ba nayi saurin kai hannu ina kamashi ya mike a hankali muke tafiya har zuwa bakin gadon ya dan zaunan kannen nasa suka kara mashi sannu ya amsa da kai kawai.
Har saida ya kwanta sannan na dago ina sauke ajiyan zuciya ya jamal dake tsaye ya tokare jikin shi da mirrow dakin yace dani sannu zainab da kokari.
Nayi dan murmushi na juya inda na aje cup din na dauka tare da nufan kofan fita daga dakin kai tsaye.
Fitana daga daki yayi daidai da mikewan mami ta nufi bakin gadon da yake kwance ta zauna a gefen shi a hankali jin hakan yasa ya dan juyo kai ya dan kalli wurin.
Ganin mami ne ta zauna a kysa dashi yasa ya dan juyo gareta yana fadin yaushe kuka shigo mami ina barci ko na dan samu barci ke nan ashe.
Don jiya bamuyi barci da dadi ba dagani har zainab a wahalce muka kwana a gidan nan amma yanzu naji sauki sosao barci kawai nake ji da kasala ya fada yana gyara kwanciyan shi.
A falo na samu su fadila da sauran yan aikin gidan suna zaune a cikin jimamen meke faruwa ne sunga su mami sunzo rai bace.
Gashi kuma har lokacin basu ga na fito part din ba hjy tana ta aika sadiya a duba ko lafiya anace mata ban fito ba.
Suna ganin fitowa na fadila tare da mai aikin wanke wanke da shara su kayo kaina suna gaidani sauran ma suka biyo bayan su suna gaidani.
Na amsa ina wucewa har na dan taka nake fadin anty in ganki mana ta biyo bayana da sauri sauran ma suka watse a lokacin.
Tunda basu ga wani alaman komai a tare dani ba muna shiga dakina a tare tana bayana nake fadin ko za,a samu freash meat da milki a gasawa oga yau baya jin dadin jikin shi tun daren jiya.
Aiya da sauki ko ta tambaya nace yaji sauki yanzu sosai yana can tare da su mami da yan uwan shi don Allah a gasa mai idan za a samu a aika da wuri na fito da kudi ina mika mata.
Take fadin jiya an bada kudin da za ayi sayayya barin aika a ciki a sayo komai yanzu ta fada da sauri tana fita na dan bita da kallo.
Wanka na shiga don a matse nake a lokacin ina shiga na sakewa kaina ruwan zafi sosai don har saida naji ya kama min jiki na goga sabulu na fito .
A gurguje na shirya duk da barcin daya cika ni a lokacinn don har idona sun fara nauyi a lokacin don barcin da nake ji.
Saidai babu daman yin hakan gareni don su mami dake gidan a lokacin dole in koma in sallamesu kafin su tafi.
Saidai ina shiga dakin ban samu mami da Aisha har jalal a dakin ba sun fita zuwa dakin hjy su gaisa da ita .
Sai ya mamud da jamal tare da wani likitan da aka kira shi ya jafar din yana zaune ya dan jingina jikin shi da gado.
Ina shigowa suka dan kalloni sai na dan tsargu da hakan na daburce ina tambayan mami su har sun fitane ?
Ya mamud ke fadin sun shiga wurin hjy yanzun nan da likita ya shigo zai duba jafar din na dan juyo ina gaida likitan kafin na sake juyawa zan fita daga dakin.
Muryan ya makud ke fadin ki tsaya zainab ga maganin da likita ya bashi da lokacin da zaisha idan time yayi na dan dakata likitan yana yi min bayanin komai.
Na tsargu da irin kallon da yaya jafar din ke min yasa ban ko tsaya fahinta ba na juya na fice daga dakin, wanan halin da yaya jafar yake nuna min na kishi a gaban wasu.
Dakin hjy na nufa a nan na samesu zaune nake gaida hjyn da kwana bata amsa ba take fadin ke yar nan ashe abinda ke faruwa ke nan har wa yanda basu kwana a gidan ba sunji sunzo mu bamu sani ba.
Kiyi hakkuri hjy ban fito bane sai yanzu ya mamud ne ya kira ya fada masu bani bace na kira na fada a ladabce.
Yanzu ya jikin nasa da sauki ko nace yana ma zaune suna hira na fada sai ga fadila ta shigo tana fasin madam an gama komai kamar yadda kika ce ayi.
Na amsa da godiya ina fadin gani fitowa in duba mami ke fadin bari su leka ta ji me likitan ya fada game da jikin nasa ni dai kafin su fito na bar dakin kai tsaye.
Na samu sun shirya komai yadda ya dace na dan duba kafin na dauka na nufi dakin nasa dashi suna cikin dakin dukkan su a lokacin na samu likitan ya mike yana tsaye suna magana da mami na shigo dakin.
Kai tsaye na kai gaban shi na aje na dauko dan stole na dora akai ban kai ga mikewa ba mami ke fadin wanan meye kuma aka kawo mashi ?
Duk idanuwan su yana kan abincin na bude va tare dana bata amsa ba kamshine ya game dakin lokaci guda da tururin abincin yana tashi sama.
Gurfane nakai a gaban shi tare da dan dago kai ina fadin a zuba da yawa zakaci ko ya dan kada kanshi kadan ba tare dayayi magana ba na fara zuba mai a hankali saida ya dan kai yadda yake tunanen zai iya ci yace ya isa.
Good likitan ya fada yace wanan ya dace dashi a yanzu yadda yaji jikin nan dole sai irin wanan abincin dama normal milk danye na tsiyayya mai tare da ajewa gefe na mike tsaye duk suna kallon abinda nakeyi a lokacin.
Juyawa nayi zan fita yake fadin ina kuma zaki ki zauna muci don nasan kema baki karya ba har yanzu zan tafi in duba sadiyace ban gata ba tun dazun na bashi amsa na fita.
Gaskiya zainab tana da kokari wallahi tasan duk abinda ya kamata ba sai an fada mata ba jalal ya fada Aisha ta amsa da gadkiya kan .
Da gaskiya gun sadiya din zan tafi don duk abinda nakeyi hankalina yana gareta na rashin ganin ta da banyi ba din.
Tana kwance ta rufe jikinta wai sanyi take ji alaman dai bata da lafiya ke nan na karasa wurin ta hankali tashe.
Ina kware abi rufan tare da dan kiran sunan ta ina tambayan ta meya sameta ta nuna min kanta ke ciwo.
Fadila ce ta shigo dauke da abinci a ture take fadin dama yanzu nake fadin kila baki san bata da lafiya ba haka ashe kina nan ma.
Ta aje kayan tana fadin dama ina son in fada maki daren jiya bamuyi barci ba a gidan nan duk wanda ya kwana a gidan nan a jiya yaji tsoroa gidan nan da bamu san dalili ba.
Allah ya taimaka daga hira sadiya tayi barci a wurina nan muka kwana a dakina a tsorace sai kusan asuba muka daina jin tsoro .
Basar da zancen nayi ta fadin kai kodai iskan da kukaji anyi jiuan ne kuke jin kamar motsine anty tace wata kila ko hakan ne wallahi.
Nan dai muka zauna a tare mukayi break fast a daki mu uku muna hira wayana ne ke ringing a lokacin na dauka .
Malam ne kakana jin na ambaci sunan malam din yasa su kallona muna gaisawa na mike na fice a dakin .
Mun dade muna magana dashi yana ban labarin artabu shi da bakin shi a daren jiya din inda yai nssaran koran su fata fata ta yadda ba zasu kara tunkaranshi ba da yardan Allah.
Nan ya fada min wasu abubuwan da zanwa jafar din nayi mai godiya bayan munyi sallama na fito zuwa dakin hjy na samu tana sallah a lokacin.
Na juya na fita daga dakin fafila ke fada min su mami sun tafi ya mamud yace naje na duba jafar din da suka bari shi kadai a dakin shi.
Na shiga na samu ya dan mike zai watsa ruwa shigowana ya jiyo yana fadin wanka nake son inyi ko zan kara jin karfin jikin nawa a yanzu
Bari na gyaro ban dakim na fada ina kallon shi jikin shi yayi wani irin radau radau kamar yasha duka ko sunyi fada da wani a lokacin.
Bi jikin nasa da yaga inayi da kallo yasa ya dan juyo yana kallln jikin nasa yace wanan kike kallo aiba komai bane tunda sun barni da raina.
Ke nan su din ne suke baka wanan wahalan na tambaye shi ina kallon shi yace ya zasu dani tunda yanzu na daina duk wani abinda suke so na taka masu doka suke gani
Zaman lafiya shine kabi tsarain su da dokan su a zauna lafiya ko kinsan kwamciyan kinan a tare danine dalilin wanan azaban da nake sha a yanzu.
Na zargi hakan dama tunda naga wanan wahalan naka yayi yawa a yanzu idan har shiga dakin zai saka su dinga baka wahala haka zan daina shigowa yaya don su daina.
Kina tsoron hakan ne ya tambaye ni nace ba wai tsoro hakan nakeji ba tun farko yaya ka riga da kashiga kungiyan su yanzun ko ya zama dole a bisu a sannu don ka zauna lafiya dasu din .
Dan murmushi ya sake a fuskan shi tare da fadin koma me zasuyi min a yanzu sai dai suyi don na daina wanan harkan har abada ke nan insha Allah.


ZAINAB IDRIS MAKAWA




ASSALAMU ALAIKUM FATAN ALHERI GAREKU DUKKA MASOYA ALLAH YA TAIMAKA YA BADA SA,A A RAYUWA AMIN


LITTAFIN NAN NA KUDINE YAR UWA KIBBIYA DARI UKU KI KARANTA A CIKIN SALAMA YAR UWA.


Idan na tsaya fadan irin wahalan da yasha a wanan lokacin zamu bata lokaci a labarin don amai da gudawa yayi shi yafi a kirga tun yana iya tashi yaje da kanshi har yakai baya iya tashi a lokacin.
Kuma ban daina mashi amfani da maganin wurin malam da kakan maya da suka bamu ai amfani dashi don matsalan.
Duk da nasan maganin suna da karfi suna daya daga cikin abinda ke karasashi zama weak a yanzu saidai hakan baisa na tsorata ba don malam dake kara min kwarin gwiwa da shi da maya a ko wani lokaci.
Har yan uwan shi ba,a bari sun san da zancen wanan rashin lafiyan nasa ba cewa ake ya yayi tafiya a lokacin.
Haka kuma ya mamud ya gargadi duk wani wanda ke gidan a lokacin idan azo nemasa yayi tafiya dazun da asuba duk da sunyi mamakin jin ogan nasu yayi tafiya ba tare da sanin su ba.
Don ya saba idan zaiyi tafiya ya tarasu ya dan raba masu dan kudin kashewa a hannun su sai sukaji ya tafi bai samu ganin su ba hakan sai bai masu dadi ba a zukatan su.
Sannu a hankali jikin ya fara dawo mashi daidai duk da hakan kuma ba a leka asibiti dashi ba nice sai yan uwan shi muke fama dashi haka a gida har Allah ya kawo mai sauki a hankali ya fara fitowa falo yana shan iska idan ya gaji ya koma daki kuma.
Yau da kanshi ya fito dan karamin falon shi ya zauna ya dan mike kafan shi a saman dan karamin stol dake wurin.
Ya dafe goshin shi da hannun shi daya tare da kurawa kasan dakin ido yana tunane.
Yayana yau da kanka kafito na fada abinda yasa shi dan dagowa ke nan daga yanayin da yake zaune din, ya dan dago kanshi ya dan kalleni tare da dan sake murmushi ta gefe fuskan shi.
Aje dan cup din da na shigo dashi a hannuna nayi daga gefen shi ya kalla ya wani bata rai kamar karamin yaro a lokacin.
Dan murmushi nayi na koma gefen shi na zauna ina kallon shi kafin ince sauki ya samu ke nan tunda har ka fara tsanar magani a yanzu.
Bana jin dadin sha sa a yanzu ya fada yana kawar da kanshi gefe daya nace hakkuri zakayi kasha daga gobe shike nan ya kare ai.
Zama ya gyara a irin yanayin dana riskeshi a ciki da farko sai dan shiru daya biyo falon tsakanin mu na dan lokaci.
Kafin muryan shi ya maye shirun da fadin zainab nasan kina kokari dani ba kowa bane zaiyi wanan abinda kike min duk da kinsan makasudin matsala kika zauna dani haka kuma kika yi jinyana a hakan .
Duk da irin halin da mami da yan uwana suke nuna maki a kaina hakan baisa kin gujeni da halina ba duk nasan abin yana damun ki a cikin zuciyar ki kuma.
Kiyi hakkuri ki yafe min duk wani abinda nayi maki tun haduwana dake zainab ina rokon ki da kiyafe min don Alla.
Da sauri nakai hannu saman bakin shi ina rufe bakin nasa da hannu ina fadi cikin murya mai nuna alaman kuka a lokacin .
Ka daina fadin haka yaya ko nayi aurena nayiwa kuma wa mijina nayi don ance aljannan mu mata yana karkashin kafan mazajen mu.
Kai din kuma koba aure a tsakanin mu kacancanci hakan a gareni ya don kaimun komai a rayuwana yaya ka ingata rayuwana ka taimakawa kanwa da yan uwana ashe nima din ba zan saka ma da irin alherin da kake min ba a kullun.
Taimako a tsakanin mu Allah ya hada zaman rayuwan mu a wuri daya hakan na nufin mun zama daya da kai a yanzu.
Idan kana cikin farin ciki ko akasin hakan nima hakan ya shafeni don nayi ma abu ba sai ka gode min ba kaina nayiwa hakan.
Wasu hawaye masu zafine suke zubo min na kasa magana naji ya jawoni zuwa jikim shi yana dan buga min baya kamar karamar yarinya a lokacin.
Zainab ki godewa Allah da ya sa kika zama silar shiryuwana a duniya dana mutu a cikin wanan halin da ko uwata ta kasa fitar dani a ciki sa ya zanyi me zan fadawa ubangijina a wanan halin.
Ke din zainab alherice ga duk wanda kika zauna dashi ke haske gun duk na tare dake zainab farin cikine ya dace dake a yanzu ba kuka duk da wani farin ciki sai a kuka bawa ke iya nuna hakan.
Don haka kiyi kokan ki a yanzu don kukane ya dace damu a yanzu don godiya gun ubangijin mu.
Ina son ki sani ni jafar nayi maki alkwari a yanzu duk wasu munanan halaiyan da nakeyi a baya na daina su har abada kuma inawa masu irin halina na baya da Allah ya fitar dasu a cikin sa kamar yadda yai min sanadi dana barshi nima a yanzu.
Yakai yanzu kunyan kaina nake ji da duk wani na tare dani dayasan hakan a kaina ina bakin ciki a yau dana wayi gari ina tuna nayi wanan halin dabbobin a baya zainab.
Sai kawai naji ya fashe da wani irin kuka mai taba zuciya a lokaci daya , rudewa nayi na rasa abinyi sai can na koma fadi in girgiza kai don Allah yaya ka daina wanan kukan bashine yanzu a gaban kaba.
Dacewa yayi ka koma ga Allah har idan kasan akwai wani sauran abin haramun a tare dakai har yanzu kayi gagawan fitar dashi a gare ka .
Ta hanyar yin sadaka ko ka tambayi malamai abinda ya dace kayi da wanan abin shine nake ganin abinda yanzu ya saura kayi .
Ma,ana a cikin dukiyan ka ko wani kaddara daka aje da kudin hharamun sai kayi gagawab fitar dashi a hannun ka don a yanzu ya haramta a hannun ka tunda ba ta hanyar halal aka sameshi ba.
Ajiyan zuciya naji ya sauke tare da lumshe idanuwan shi yana gyara zaman shi tare da mike kafafuwan shi duka biyu kafin yace.
Duk ba wanan bane damuwa na zainab don nasan dukiyana na zufanane na sameshi a kashin kaina ga baki daya.
Elimenatis din mu kawai na wayewa ne da harkan homo bawai don arziki bane ko wani abu kawai dai hakan wayewa ne a garemu duniya ta dauki mutum da tsoro ko wani abu can.
Ai akwai wa yanda basu da komai kuma suna ciki kungiyan tare da kowa kawai ni yanzu abinda ke damuna shine.
Sai ya dan ja numfashi yana girgiza kai kafin ya bude ido ya kalleni yana nunani yace damuwa na shine zaman mu dake zainab a yanzu.
Ban san a wani matsayi aurena dake yake gun malamai idan zasuyi bayani zainab ina tsoron kada su fada
Showing 360001 words to 363000 words out of 390011 words