sauri a dan razane don sanin kwanan wasan don wancan karon da kakar maya ta ban magani yadda muka kwashe dashi.
Malam bai tsaya jin ta bakina ba don ya fahinci irin tunanen da nakeyi a lokacin sai cewa yayi dani zaki iya mana sai kace ke din ba mace bane.
Yana fadan hakan yake miko min maganin dake kulle a cikin wani dan kyale ja na karba kafin ya juya yana dauko wani a haka dai duk yai min bayanin ko wani maganin da amfanin sa gareshi.
Nabar gidan malam a hanya wayan ya jafar ya shigo min na dauka da kyar bayan mun gaisa yake fada min yaso shigowa satin nan don mu dawo amma yafiya ya kamashi zai fita ba zai dade ba zai dawo sai yazo ya dauke mu mu dawo.
Jin hakan take wani tunane yazo min a zuciyana don na gama yanke shawara a kansa ko yanzu.
Do duk abinda zanyi karshe nice mai laifi a wurin mami ba zata ga hakan ba sai laufin da zata dora min da banji ban gani ba.
Haka na dawo zuciyana cike da zargi iri iri a lokacin don ni abin har tsoro ya fara ban don mutum ba abin yarda bane ashe haka.
Don ko waye lalai na jikin sune don yadda mami take kafa kafa da yayan ta nake gani ashe hakan bashi ya dace tayi kawai ba a rayuwan ta a kan yayanta.
Don bayan sa ido irin wanan da takeyi ya zama dole kuma uwa ta dage da addu,a da neman tsari gun yayayen ta ashe .
Koda ta hanyar yawan yin sadaka ko alheri da sunan yayanta Allah ya tsare mata su don sherin zamani.
Amma da yake ita mami yanzu irin rayuwan turawa ne gareta duk ta mance da wanan a rayuwanta batayi sadaka ba zuwa garesu don hakan balle wani neman taimako gun malamai a kansu don abin yanzu saida hakan .
Saidai kada mutum ya zure don gudun fadawa ga halakan ubangiji don yadda da irin abubuwan nan gaba daya yana juya kan mutum ya manta da Allah watarana.
Sai mu kula mu dinga sadaka da sunan yayayen mu da yawaita alheri ga marayuwa da masu karamin karfin shine mafita.
Washegari kawai na tashi ina fadawa inna zan tafi fambeguwa tayi mamakin hakan saidai bata hana mu zuwa ba sai ta fadawa Abban mu shima ya yarda.
Da sa,adatu da sadiya mukai tafiyan inda Allah ya taimakeni shine mun tafi washe gari sai ga waya ana neman su sa,a datu makaranta nace su tafi tare da sadiya don naga bata sake jiki ba.
Suna tafiya nima na tsiri tafiya kan zanje na duba wata kawata na dawo kafin su dawo haka na samu hanya na balle ba wanda yasan inda na nufa.
Ni kaina ban san inda zan nufa ba na juyo zuwa kaduna kawai gidan wata kawata da mukai yayin zuwa makaranta a tare lokacin can dabaran zuwa ya fado min don su din gidan sune na kansu bana wani ba.
Ban sha wani wahala ba sosai wurin gane gidan saidai itace da farko bata gane ni ba saida nayi mata kwatance da kyau tace ta ganoni ta rungumeni.
Mun zauna ana yaushe rabo a nan take ban labarin ai mahaifin su ya rasu bayan rabuwan mu bada dadewa ba.
Na tausaya masu sosai don ni kaina naga sauyi sosai a gidan maganane kawai ban yi ba tun shigowana.
Gidan da yake da yawan arziki ga yan aiki da jama, a amma yanzu shiru babu kowa tun wajen gidan shara da tulin ganyen bishiya zasu tareka a waje shiyasa da farko harna zata ko ba kowa a gidan ne yanzu.
Mun kai wani lokaci muna hira kafi mu ci abinci mu kwanta barci na kashe wayana gaba daya tun shigowana garin kaduna na jefa a jakana.

Ya jafar ya kira layin nawa yafi a kirga da safe zuwa rana don hakane ya nemi layin Abban mu yake tambayana.
Abban yake fadin bata fadama zasu ziyara nan fambeguwa wurin yan uwan mahaifiyarsu ba yace ok kila ta fada min na mantane ya kashe wayan bayan sunyi sallama da Abban yace masa bari ya samo lamban da za a samemu dashi a can.
Abba ya shigo gida ranshi a bace yana wa innan mu fada kan zuwana wuri mijina bai sani ba gashi yanzu ya bugo waya yana tambayana.
Itama inna hankalin ta ya tashi nan ta buga waya sai dai wayan baya shiga hankalin inna ya tashi take tambayan sadiya ko ba service a garin tace sun baro services a can lafiya kafin su dawo.
Hankalin innan mu ya kara tashi gashi yarta di ba waya ke gareta ba balle su kira nata layin suji ko lafiya nake.
Har dare inna na kokarin kiran layina shiru babu layin hankalinta kuma yaki kwanci da hakan har sadiya ta dawo daga zari,a ta samesu a hakana itama ta gwada layin nawa bai shiga.
Sai cewa ake layin yana kashe idan sun kira sadiya dake gefe tace aiko anty mu bata kashe wayan ta haka idan dai ba wani matsala ne ya faru da wayan ba.
Har washe gari basu sameni ba haka yasa sa,adatu fita ta samo layin wata yar garin data sani ta kira akan taje gidan ta duba in lafiya nake ta fada min na kunna wayana ya jafar nason magana dani.
Basu akace wa kawar babu wata bakuwa a gidan wace suka zo duk sun wuce koda ta kira sa,adatu dare yayi lokacin don haka saidaf safe sa,adatu ta sameta take fadin abinda aka fada mata.
Sai hankalin su ya tashi sosai nan inna hankalin ta ya kawo cewa akwai matsala ta bangarena ke nan lalai wanan abin da nayi yana da alaka da zance da yaya jafar di nan hankalin ta ya kara tashi sosai.
Sai gashi ya jafar din ya kara kiran Abban sun gaisa yake tambaya ko na dawo dan layina baya shiga ana fadin layin yana rufe har lokacin.
Mamaki ya kama Abba yake fadin bata kira kaba ke nan danace su sanar mata bayan sunyi sallama ne Abban ya shigo gida ya hau inna da fada ta inda yake shiga banan yake fita ba.
Dole washe gari sa,adatu tayi asubancin zuwa fambeguwa da kanta ta duboni ko taji inda nace dasu zan tafi daga can don hankali su ya kwanta.
Saidai tana zuwa din kamar ta karo tashin hankalime gare su don ta dawo da labarin ba wanda yasan inda na tafi sai innan mu ta fashe da kuka.
Dole ba yadda za ayi aka fadawa Abban mu komai shima nan hankalin shi ya tashi ya fara fada inna cewa komai ya sameni itace don itace ta kirkiro da surfan aje gun yan uwanta ai.
Daba haka ba ai da ina gida asirin su rufe yanzun me zasu fadawa mijina cewa nayi tafiya na bata ba a san inda nake ba ko me ?
Daga shi sai inna da yan uwana ake kumbiya kumbiyan maganan a tsakanin su har karshe dai saida Asabe ta san da zancen itama hankalin ta ya tashi sosai.
Inna taje gidan malam tana kuka take zayana masa komai malam din yai murmushi tare da fadin nasan za a rina don yarku na cikin wani hali wallahi.
Sai dai kada ku damu sosai za a san abin da akayi ta dawo gida lafiya kada abin ya kai ko ina amma hankalin ta ne ya tashi sosai da mijin nata har mahaifiyar shi.
Nan dai malam di yace za ayi rokon Allah duk inda na shige na dawo gida lafiya ba tare da wani abu ya faru dani ba insha Allahu.
Abba kan ya saka inna a gaba har ya kai inna itama ta hasa ta mayar mashi da amsa a cikin zafin rai ta fadin shin malam kana ganin laifina a nan.
Kai tunda yarka tazo garin nan ka taba zama da ita ta fada ma halin da take ciki a gidan auren ta daudai da rana daya malam a gidan nan.
Abba yace owwoo yanzu kika fito mi a mutum sak watau duk abinda yar nan tayi da sanin kine Asiya boye min kawai kikeyi dama ?
Tace wallahi bada sanina bane malam don babu uwar da zata koyawa yarta mugun abu haka tabar dakin mijin ta da mutane suke hangen tana a cikin daula ne ita.
Saidai mu iyayyen mun kayi sakaci wani lokaci har abu ya girma ba tare da mun maida hankalin da halin da yaro ke ciki ba sai abu ya lalace.
Shike nan Asiya kin sai komai dai da yarinyar nan tayi ke nan to wallahi bari kuji baku isa ku kunyatani ba a idon jama,a.
Duk inda taje koma wani iya shege take ji dashi a zuciyar ta zata dawo nan ta sameni sai ta koma gidan mijin ta bata mai dani mutumin banza a garin nan ta tona min asiri ko watau kunga Allah ya rufa min asiri ta tsatson ku ?
Kaiya kaiyya ina ta fada har sau biyu kafin tace shine matsalan malam bahaushe wallahi kaji na fada ma yarinya tana cikin matsala watau kai ko a jikin ka malam don kawai dan abim duniyan da kake samu daga wanan mutumin ko ?
Ya rufe maka ido ba zaka dawo da hankalin ka wuri daya ka natsu kaji ko meye matsalan yar taka ba da miji nata kadai kawai burin ka ta dawo ta koma koma meye ta karata can dashi ko ?
To ban yarda yata ta halaka a haka ba don kawai kana kwasayin abin duniya kai yanzu idanuwan ka sun rufe ba zaka nemawa yarka manufa ba.
Nan Abba shima ya taso kamar zai daki inna a ranan kan wanan maganan har yana fadin idan ta kuskura ta kashe aure na da ya jafar a bakin auren su ke nan itama.
Ran inna ya baci matuka tana mayar mashi da martani har yakai saida su sa,adatu suka ja inna zuwa daki sannan Abban ya fita .
A waje ya hadu da lantana dake labe tana saurare ta rasa gane zancen da akeyi da farko amma ta dan tsuntsunci wasu daga cikin maganan inda ta fahinci akwai matsala ke nan ga aurena dama tana neman sanadin da zata katse duka jin dadin daulan data hangomu a cikin sa ni da innan mu da kowa a dakin mu da wanan bakin cikin take kwana take tashi dashi a kullun.
Abban mu yana fita gidan malam ya nufa don ya kai karan inna a can ya sa ai masa iso a wurin malam din nan ya samu wuri a waje ya tsaya yana cika yana batsewa har malam din ya fito ya sameshi a wurin.
Bayan sun gaisa ne ya koro magana ya fadawa malam din komai saida malam din ya gama jin Abba ya nisa tare da fadin.
Bello ka ban mamaki matuka duk da matar ka ta baka haske a cikin zancen auren yarka zuciya ya hana ka gane hakan ?
Malam wani matsala take kira wa yarinyan nam fisabililah duk wanda yaga yar nan yasan tana a cikin daula ai.
Malam ya katse shi da fadin kaiya amma bakai tunane ba bello a nan ka yanzu barin fito maka baro baro ka sani yar ka na cikin matsalan aure a rayuwa ta a gidan mijin ta don haka ka daina wanan kumfan bakin da kake yi a yanzu.
Kamata yayi ka natsu a sama ma yarinya mafita ga rayuwan ta ayi abinda zai kawo zaman lafiya garesu da kwanciyan hankali .
Don babu auren da za ayi tsaon wata daya ko biyu zuwa uku ace babu wani abinda ya taba shiga tsakanin mata da miji irin na aureta a tsakanin har wanan lokacin.
Bale yarka dake neman shekara shidda yanzu a gidan mijin ta ya kake ganin wanan abin zai kasance komai hakkurin yar ka kuwa ?
Jikin Abban mu yayi sanyi wani zufa ya fara keto mai lokaci guda ya kara gyara zama yana cire hulan kanshi.
Kafin ya nisa yana fadin yanzun malam kana ganin hakan yana yuyuwa a tsakanin su kadafa yarinyar nan taiwa mutumin nan sheri kuma kan hakan ?
Malam yace malam Bello ke nan ka godewa Allah daya baka ya kamar wanan yar mai hakkuri da sanin ya kamata do sauran zancen ba zai fadu ba.
Abba yace wa iyazu billahi ban samu zama da ita ba gaskiya malam ban san da wanan zancen ba sam wallahi.
Ya dan dade suna tautanawa da Abban kafin suyi sallama da juna ya nufo gida gwiwan da sanyi sai tunane yake a ransa.
Yana hanya bai karasa gida ba kiran ya j din ya shigo mai haka ya bar wayan har kiran ya katse don ko ya dauka baisan amsan da zai bashi ba a lokacin.


ZAINAB IDRIS MAKAWA



ASSALAMU ALAIKUM WARAHAMATULLAH YAN UWA DAFA MUN WUNI LAFIYA ALLAH YA GAFARTA MUNA KURA KUREN MU AMIN.

LITTAFIN KUDINE YAR UWA DON ALLAH IDAN BAKI BIYA BA KADA MU SHIGA HAKKIN JUNA PLEASE, , , ,


Ina kwance ina barci dakin da muke kwana nida kawata nake jin suna kus kus kus da mahaifiyanta a waje.
Matar na fadin yanzu yaya zamuyi da bakuwan nan gashi gidan nan haka muke babu abinda zamu dafa balle ai mata abin karyawa.
Wani irin tausayin sune ya kamani lokaci guda na tuno sanin da nai masu a baya can da irin daulan da suke a cikin sa.
Lafewa nayi kamar ina kan barcin har lokacin sai ta shigo ta zauna a bakin gado bayana tayi zugun tana tunane.
Nima tunanen nake a raina bandai rasa komai a gidan mijina ba na rayuwan duniya sai kwanciyan hankali kawai dana rasa a tare dani.
Wanda ko wace mace ke burin tayi aure ta kai gareshi watau ko wani gida da mutum yake ganin ana rayuwa da nasu kalan kalubalin rayuwa da suke fuskanta.
Sai can na motsa kamar a lokacin na falka daga barcin take fadi daga bayana a sanyaye zainab kin tashi nace eh besty na mun tashi lafiya ya gajiyan dawainiya ?
Tayi dan murmushi tana fadin haba dai wani dawainiya kuma besty kinfi haka a gareni ai kin sani.
Gaakiya ta fada don lokacin gaskiya ta tsare min komai a makarantar da muke zuwa din don ko yanzu ban nuna mata ni din wata tsiya bace saidai ta gane hakan kawai a wurin yanayina.
Mikewa nayi daga saman gadon na kewaya bandaki bayan na fitone na dawo na zauna a bakin gadon.
Jakkar hannu na na dauka daga inda yake aje a kasa na dauko kudi masu yawa a ciki ba tare da nasan ko nawa bane na mikawa Nafisa din ina fadin.
Kiba umma wanan kudin banyi tsaraba da zanzo ba don ina tamtama koba zan sameku har yanzu a gidan nan ba.
Kallon mamaki tayi min tana zatgin ko naji shawaran su da mahaifiyar tane da sukayi na tare da fadin don Allah ki bata kice tayi hakkuri dashi ba yawa.
Haka ta fita cike da mamakina a ranta na irin kudin dana debo mata din ko a ina na samesu haka sai sheki sukeyi a hannun ta.
Uwar ba irin makwadaitan matan nan bane don haka ta taso yar nata a gaba zuwa dakin nata tana fadin ke yar nan wanan kudi haka masu yawa ?
Ta samu na idar da sallah nafila ina addua na dago kai ina fadin wallahi umma ba komai ban samu yo maki tsaraba bane shi yasa.
Umma tace ba zan karbi kudin nan ba don gudun fadawa ga halaka kin gani nan na tsaya a matsayin da Allah ya zaunar dani da diyana a gidan nan.
Don tun lokacin da mahaifin su ya kwanta dama yan uwan shi da abokan aikin shi suka wawashe abinda ya bari sai gidan nan da mota daya muka tsira dashi nake tsorin duk wani abin haram da zai fado a hannun mu.
Lah umma don Allah kada kimin mumunan zato a gareni ina nan a yadda kuka sanni har yanzu ba canzawa nayi ba umma.
Ina da aurena a kaina tunkafin na karasa karatuna igiyan aure ya hau kaina muna kasan chaina ne zaune da mijina tun wanan lokacin .
Sai naga sun kalli juna ina da yarta tana fadin haba nikan na sani zainab don kamanin ki da yanayin ki kawai mutum zai kalla ya gane ke din bata wasa bace yanzu nayi murmushi da jin hakan.
Kafin na dago kai ina fadin umma dan matsala muka samu da mijina nazo nan na karasa ina hawaye.
Subbahanallahi umma ta fada don jin abindana fada na zancen mijina take fadin keko yar nan Allah ya rufa maki asiri da gani me zai kaiki wanan kasadan kuma ?.
Umma ba wanda zai taba
Showing 321001 words to 324000 words out of 390011 words