ina fadin saukin abin mun dan huta a Dubai kafin mu karaso nan din shine saukin mu ai.
Zama tayi daga gefe tana fadin ya bayan rabon mu ni kuma ina fadin ya jikin mama da sauki ko ?
Mama ta samu sauki sosai kafin na iso na samu baban yaran nan ya kaita asibiti an kula da ita nace kin fada min a waya yanzu dai jikin da sauki ko ?
Tace da sauki sosai uwar dakina ya wajen ku da alama abubuwa a yanzu kamar sun kamkama don alama ya nuna hakan.
Gaba dayan ku kunyi wani irin kyau kun kara haske kamar mutum ya sace ku wallahi nikan gaskiya da badon na san kuba sai nace baku bane gaskiya.
Dan murmushi na sake kafin nace kai anty ke nan wanan zuzutawan haka tace gaskiya na fada ance alaman kwanciyan hankali yana ga mai kiba .
Don wallahi kun sauya sosai a yadda na san ku don haka abubuwa a yanzu suna tafiya da sauki ga alama.
Bandai fadi komai ba sai murmushin da nakeyi sadiya ce ke fadin bayan ki kan ai munji dadin yaya fiye ma da yadda kika barmu anty.
Ke kan akace ko shekara nawa kayi baka ga mutum ba kada ka tambayi halinsa don hali na nan bai canza ba sadiya har yanzu.
Sadiya kan ai sai abinda ya karu na bata amsa ina mikewa tare da bude fruits salad din da ta shigo muna dashi na fara zubawa a hankali.
Naga kamar kun kasa cin abincin nace bari na hada maku wanan din ku dan ji nauyi yayane zaiso shan wanan din a yanzu don naga baici abincin sosai ba shi.
Mun zuba mai sadai bamu da halin shiga part din shi a yanzu sai dai idan ya fito barin gama na kai masa na bata amsa ta bini da kallo saidai ban san me haka ke nufi ba.
Kadan nasha na mike muka fito tare a dakin ina karewa gidan kallo a tsanake babban gidane kan wanan gidan sai dai part din mu yana kallon juna da nasa a sama amma akwai wani irin falo babba a rsakanin mu dashi.
Na karbi kayan da ta dauko a hannu ta na nufi part din data nuna min nasa sai dana kwankwasa na tura kofan na shiga dan karamin falone na wuce sai dakin kwanan shi ko ina yana kamshi a part din
Yana kwance saman gado ga sytem din shi a gefen kanshi bude sai dai ba aiki yake a ciki ba da alama yana aikin barci ya dauke shi.
Ganin halin da yake ciki yasa nayi shawaran juyawa kada in tayar dashi daga barcin sai dai hakan baikai ga samuwa ba naji ya motsa yana fadin.
Meke sa idan kin shigo kin samu ina kwance kike saurin juyawa ki fitane kin dauka zanyi barci mai nauyin da har za a shigo min ban sani ba ?
Banson in tayar da kaine daga barci don naga kamar ka samu barci a yanzu idon shi ya bude gaba daya ya sauke a kaina yana fadin.
Na dauka kina zaton ko zaki samu ina abinda baki kaunan ganin inayi ne yasa zaki koma don kin ganin a kwance.
Wanan yanzu ai ba damuwa na bane yaya tsakanin ka da mahalicin ka Allah ne wanan ka daina ko kayi wanan ya saura gareka kuma ?
Haka zaki fada yanzu ko ya fada yana kallon cikin idanuna sai ban yarda mun hada ido dashi ba na aje mai tiren a saman dan karamin table din dakin da yake kala daya da gadon nasa ina jawo table din zuwa gaban shi.
Don na kawar da zancen nace ga wanan ko zaka sha don naga bakaci abincin ba sosai dazun.
Naci mana ya fada yana mikewa kinsan bana cin irin wanan abincin kada ya saka jikina budewa sosai.
Da jikin ka zai budewa ai daya dade da budewa yaya don ruwan kwalban da kake durawa cikin ka sosai.
Zainab bana son jin wanan zancen a bakin ki don sanin kankine a yanzu na daina wanan harkan don haka bana son a tayar min da wanan zancen kuma .
Kayi hakkuri idan hakan dana fada laifine na barka lafiya na fada ina kokarin ficewa dakin yake fadin bakiji ba ko ?
Na juyo ina dan kallon shi yake fadin zuwa dare zamu fita zuwa gidan mami mu gaidasu idan zaku iya fita a yau din ko kuma a barshi da safe sai mu tafi.
Zaifi kyau yau din mu tafi na bashi amsa daga inda nake na rungume hannayena a jikina eh hakan zaifi don mamud ya fada mata muna garin tun safe.
Tayi fadan hakan ke nan na tambaya badan na shiryawa hakan ba fadan me zatayi tunda mun shigo kasan ko ?
Zo ki zauna ya fada yana gyara zaman shi da kyau tare da fadin idan bake ba wata mace ce zata shigo wurin mijinta aga ta fita haka da sauri.
Ai sai a dauka akwai rashin jittuwa a tsakanin mune kila kinkoga hakan ba zanji dadin shi ba daga zuwan mu ki bada mu haka ?
Yaya ke nan ka dauka ba,a san zaman da mukeyi da kai bane a hakan kana dauka kowane zaka iya wasa da hankalin shi a hakan.
Sai dai idan kin fadawa wani wanda ban debe tsamani fadilace ko zaki iya fadawa ban taba ki kamar sauran maza.
Wani kallo na watsa mashi da sauri tare da fadin kada ka daukeni yarinya kamar da bansan kaina ba har yanzu.
Ko a da can ban fada mat komai game da zaman mu da kai ba balle yanzu da hankalina ya kara zo min na fahinci me kake nufi dani.
Me nake nufi dake zainab ya fada a daidai lokacin da yakai cibin mix fruits din a bakin shi tare da bissimila a fili na dan kalleshi.
Don a kwaishi da wanan akidar na fadan bissimila ga duk abinda zaikai a bakin shi ko wani lokaci idan zaici abu.
Niko nasan kin kara girma a yanzu zainab don nasan kin fara kiyasta wasu abubuwa a tare dake .
Ban fara kiyasta komai ba saidai a yanzu din zan fara mutukar wanan halaiyar naka munana suna tare dakai yaya don ba zan zauna da wanda ke sabon Allah a fili ba haka gaskiya.
Da nai maki me a cikin zaman namu dan dama ina zargin hakan a gareki tuntuni saidai ki sani ba kowa zaki fadawa wanan zancen a yanzu ba ya yarda da zancen da zaki fada.
Saboda basu gani a jikina ba kome yasa ka fadi hakan ai jikin shike nuna kana cikin wani hali keko naki bai nuna hakan ba.
Shine hikimar ka a kaina banda wani hikima ko basira a yanzu da da can baya wanda yafi in ganki cikin farin ciki kamar haka ?
Da alama dai dadin zancen yake yana kuma bugun cikina da wayaun manyan yaji wani shiri nake a kansa yanzu da mukazo gida.
Farin ciki a haka yaya farin ciki zuciya tana cike da damuwa da tashin hankali akan mutum kullun ?
Zainab meye matsalan ki a yanzu dani kallo shi nayi da mamaki kamar zanyi magana sai kuma naja bakina nayi shiru ina kallon shi ban iya furta kai din kaine matsalata ba a yanzu kamar yadda na bashi amsa a zuciyana da hakan.
Bakinane yai subul da baka nace ina ko naga matsala dakai kana da irin su Taju dake debe maka kewa duk lokacin da bukatan hakan ya taso maka.
Na sani zainab nasani banda wanan din da kike ganin shine matsalan ki a yanzu dani baki da sauran matsalan komai bayan wanan.
Koshi din ai zaki iya idan kina so sai ki gwada ki gani ko zakici nasara a kaina har ki samu yadda kike so din.
Ka dauka yaya ina da feeling a kanka ne kamar yadda baka da wanan feeling din a kaina haka nima haka kwata kwata ban taba jin wani feeling akan kaba irin wanan.
Take naga annurin fuskanshi ya canza lokaci guda yace kina nufin baki da feeling kamar sauran mata akan mijin ki ?
Miji miji fa kace yaya ko yau bakin ka ya mantane har ka furta hakan a gabana bayan zaman kanwar ka nake ga idon kowa.
Haka dai kika fada zainab wanan zancen ai ya dade da wuce ko ga idon kowa don wayau ki yafi nawa yawa zainab.
Banda wayau bayan hakanndin haka ka tsawa zamana da kai yanzu kuma lokaci yayi da hakan zai kawo karshe na fada ina barin dakin.
Dakina koma raina na min zafi don wanan maganan da mukayi a yanzu watau yaya daukan jarababba yake min ko me ?.
Shiko na fita na barshi da tunane na a zuciya don abinda yake zargine ke shirin faruwa wanan yarinyar gab take da daukan wani mataki a kansa yanzu.
Me zanwa zainab na wake kaina kada ta kasa hakkuri ta fasa abinda ke tsakanin mu ne?
Wata zuciya tace mai baka saba da wanan halin nata bane a baya babu abinda zatayi duk hakan barazanane kawai na mata ka riga da ka gama da ita ko don babu inda ka ragota a yanzu kan wurin zamantakewa ya fada.
Sai kawai ya shafe zancen da basarwa don yasan haka dinne ba wani abinda zanyu inma zanyi din nice dai a kasa bashi ba.
Don babu mai yarda da duk wani abinda zan fada a yanzu don za a dauka sherine kawai na mata a hakan.
Hannun shi yakai ya shafo gaban shi da kusan wata da watani ke nan yake fama da wanan matsalan yaji shi a lankwas kamar kullun.
Hannun ya mayar a fuskan shi yana shafowa a hankali shi yanzun ma ba zaice ga ta inda matsalan ya fara mashi ba.
Don dai yasan cewa da farko bayan maganin dana basa a Dubai yana tare da lafiyan shi na mazakuta sai daga bayane ya fara fuskantar wanan matsalan da yake ji a yanzu tare dashi.
Gashi ya kasa fadawa kowa bayan likitan shi da yagani kan wanan zancen a chaina ya kuma dubashi yace lafiya komai nasa yake.
To a ina wanan matsalan ya taso masa shi dai ba zaice zainab din bane da wanan matsalan sai kawai yake danganta kansa da kawai don yanzu baijin sha,awan ko wani irin jinsi don jin dadin rayuwan shi ya kawo masa hakan.
Da kyat ya mike ya shiga bathroom don ya watsawa jikin shi ruwa sai dai har ya fito zuciyar shi yana cike da tunane kala kala daya kasa fahinta.
Nikan sallah nayi sai a lokacin na samu barci ya daukeni sosai don na samu barci har lokacin sallah la,asar ya wuce ni sosai.
Bayan na samu na tashi da kyat na shiga bandaki na dauro alwala nayi sallah ban fito ba dakin na zauna ina dan dube dube a cikin wayata sabuwa daya saya min.
Sosai nake jin dadin wayan don komao na wayan yana da kyau sosai kafin hankalina ya dauko ga tunane ba abinda yazo min a rai sai zancen zuwa gidan mami daya ce zamuyi da yammanan nake tunanen yadda mami din zata karbe ni .
Dukda mun shirya sama sama a yanzu da ita sai dai ina tsoron halin dan adam tunda har yanzu bawai na kwanta mata a rai bane.
Koma meye wanan karon kam nasan ba zan yarda daduk wani rainin wayau kowa ba a kaina don ga kura mai laifi basu gani saini da banci ban sha za a dinga dora laifi a kaina ?
Sadiya na tuna tun fitana dazun ban kara ganin ta ba hakan yasa na mike zuwa dakin da take tana ciki da waya tana faman yin game hankalinta ya dauku a wayan.
Jin motsina yasata dago kai tana kallona tare da fadin ashe kin tashi yayan mu na shiga dazun na samu kina barci.
Ke wai me yasa bakya jin magana sadiya wanan yasa nake hanaki rike waya don sai ya canza maki akidar ki ga baki daya wallahi.
Ina fara magana tayi saurin lkashe wayan tana ajewa gefen filonta da sauri zaune nakai cikin bacin rai ina fadin kinga akan wayan nan zamu samu matsala babba dake don akan wanan hali zan mayar dake na dauko binta mu zauna tare don ita ban taba jin tayi wani abin rashin ji ba .
Ina kokarin yi mata wanan nasihan ne don gujewa gurbacewan rayuwan ta nan gaba a kan waya duba ga yadda naga daga shi har kannen sa basu da lokacin kowa akan wanan nauran a rayuwan su don zai iya zama dakai na tsawon awan ni ba tare da yai magana dakai ba hankalinshi naga waya yana tabawa kawai.
Duba ga hakan nake tsoron kada ta tashi da wanan akidar nan gaba ya zame mata hitina a rayuwa gashi mu ba diyan wasu a tarihin mu.
Idan na fara irin wanan fadan taka natsu sosai ta daina duk wani abinda takeyi ko yanzuma din da nake magana hakane ya kasance a tsakanin mu.
Kuma ina son ki saurareni da kyau kiji duk wani tambayan da fadila ko wani zai maki akan rayuwan mu kada ki yarda inji ance ga abinda kika fada don idan naji da Inna zan hadaki wanan karon.
Bazan fada mata komai duk tambayan da zatayi min idan kinyi hakan kin kyautawa kanki na bata amsa ina mikewa don barin dakin.
Shiru tayi tana bin lafiyan filo ta kwanta tana kallona har fice dakin ta sauke ajiyan zuciya tare da fadi ta rasa meya sa nake yawan tsanan ta mata hakane ?
Daki na koma har lokacin banjin dadi a kasan zuciyana kawai naji na tsani komai sai bacin rai dake kara min yawa nakeji .
Duk a kan dan maganan da mukayi da yaya J a ranan kawai nake jin raina yana wanan bacin da yake min.
Allah ya taimaka har tara na dare ya wuce banji yace mu fito zuwa gidan mami din ba daya fada zamu shiga da dare.
Hakan yasa na fara shirin kwamciya kafin Fadila tayi min sallama ta shigo dakin tana fadin taga fitan mijina a cikin daren nan ko lafiya ya fita a wanan lokacin.
Tabbas tunane na ya fara zama min gaskiya akan fadila shiyasa yanzu nake taka tsantsan da ita wani lokaci.
Don na fara zargin wani abu akanta da yanzu wayau na da hankalina suka fara kawo min haske akanshi don yawan tambayayin da take min lokaci lokaci koda a wayane kuwa idan muna wayan.
Har yakai hankalina da tunanena sun fara hasko min wasu abu a kanta ko yanzun ma tambayan data jefo min ya kara rikitani tana fadin.
Ko dai mijin naki bai bar wanan harkan bane har yanzu a cikin mamaki na juyo ina fadin harka wani harka ke nan fa ?
Sai kuma ta rasa abinda zata fada min kan hakan tace wai irin dai halaiyar nan da yakeyi a baya.
Ance mutum mai yawan murmushi baka fahintar bacin ranshi lokaci guda sai dai ya jefaka a cikin kwankwanto da zargin kanka kaida yakewa wanan murmushin a lokacin.
Hakan ne ya faru da fadila dani sai kuma ta fara dan kame kame tana fadin a yanzu kan ai komai ya wuce da alama akwai fahinta a tsakanin ku a yanzu.
Dama babu ne na tambaye ta cikin alaman mamaki a fuskana naci gaba da fadin ban taba fada dashi ko wani rashin yarda wanda ya shafi ni dashi har wani ya sani na bata amsa.
Tare da karewa da fadin bana shiga harkan shi hakan ya kara jawo mana zaman lafiya a tsakanin mu wanda ko wace mace ke fata da mijinta.
Itama din kallon mamaki ta bini dashi lokaci guda tana dan murmushi a fuskanta nima hakan nakeyi.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
YA HAIYYU YA KAIYUMU YA ALLAH KA KARBI IBADUN MU KASA MUNA CIKIN YAN TATTUN BAYIN KA A WANAN WATAN MAI RAHAMA DA DAUKAKA ALLAHUMA AMIN, , , ,
LITTAFIN KUDINE KI BIYA DARI UKU KI KARANTA YAR UWA DON ALLAH KI GUJEWA SHIGA HAKKIN WANI YAR UWA KAN ABIN DUNIYA, , , ,
Na san mai karatu zakiyi mamaki jin abinda na fada akan fadila hakan kuma ya samo asaline tun ranan dana fara gane waye fadila a gurin mu.
Ranan kishin ruwa kawai ya tayar dani a cikin dare na fito don neman ruwan da zan sha a lokacin.
Banyi amfani da ko wani irin haske ba don nasan inda ruwan yake sauri kuma ya hanani tsaya na dauki ko wayana in haska.
Har na dauko ruwan zan fito naga kamar gittawan mutum a falon namu karami.
Naji tsoro iya tsorata nayi shi don haka na samu wuri na lafe a bayan kofan kitchen din muryan fadila naji tana waya a hankali.
Tana fadin wallahi duk dabaran da zanyi in gane wani abu a gareta nayi shi har yanzu ban gane komai ba a wurin ta .
Showing 297001 words to 300000 words out of 390011 words
Zama tayi daga gefe tana fadin ya bayan rabon mu ni kuma ina fadin ya jikin mama da sauki ko ?
Mama ta samu sauki sosai kafin na iso na samu baban yaran nan ya kaita asibiti an kula da ita nace kin fada min a waya yanzu dai jikin da sauki ko ?
Tace da sauki sosai uwar dakina ya wajen ku da alama abubuwa a yanzu kamar sun kamkama don alama ya nuna hakan.
Gaba dayan ku kunyi wani irin kyau kun kara haske kamar mutum ya sace ku wallahi nikan gaskiya da badon na san kuba sai nace baku bane gaskiya.
Dan murmushi na sake kafin nace kai anty ke nan wanan zuzutawan haka tace gaskiya na fada ance alaman kwanciyan hankali yana ga mai kiba .
Don wallahi kun sauya sosai a yadda na san ku don haka abubuwa a yanzu suna tafiya da sauki ga alama.
Bandai fadi komai ba sai murmushin da nakeyi sadiya ce ke fadin bayan ki kan ai munji dadin yaya fiye ma da yadda kika barmu anty.
Ke kan akace ko shekara nawa kayi baka ga mutum ba kada ka tambayi halinsa don hali na nan bai canza ba sadiya har yanzu.
Sadiya kan ai sai abinda ya karu na bata amsa ina mikewa tare da bude fruits salad din da ta shigo muna dashi na fara zubawa a hankali.
Naga kamar kun kasa cin abincin nace bari na hada maku wanan din ku dan ji nauyi yayane zaiso shan wanan din a yanzu don naga baici abincin sosai ba shi.
Mun zuba mai sadai bamu da halin shiga part din shi a yanzu sai dai idan ya fito barin gama na kai masa na bata amsa ta bini da kallo saidai ban san me haka ke nufi ba.
Kadan nasha na mike muka fito tare a dakin ina karewa gidan kallo a tsanake babban gidane kan wanan gidan sai dai part din mu yana kallon juna da nasa a sama amma akwai wani irin falo babba a rsakanin mu dashi.
Na karbi kayan da ta dauko a hannu ta na nufi part din data nuna min nasa sai dana kwankwasa na tura kofan na shiga dan karamin falone na wuce sai dakin kwanan shi ko ina yana kamshi a part din
Yana kwance saman gado ga sytem din shi a gefen kanshi bude sai dai ba aiki yake a ciki ba da alama yana aikin barci ya dauke shi.
Ganin halin da yake ciki yasa nayi shawaran juyawa kada in tayar dashi daga barcin sai dai hakan baikai ga samuwa ba naji ya motsa yana fadin.
Meke sa idan kin shigo kin samu ina kwance kike saurin juyawa ki fitane kin dauka zanyi barci mai nauyin da har za a shigo min ban sani ba ?
Banson in tayar da kaine daga barci don naga kamar ka samu barci a yanzu idon shi ya bude gaba daya ya sauke a kaina yana fadin.
Na dauka kina zaton ko zaki samu ina abinda baki kaunan ganin inayi ne yasa zaki koma don kin ganin a kwance.
Wanan yanzu ai ba damuwa na bane yaya tsakanin ka da mahalicin ka Allah ne wanan ka daina ko kayi wanan ya saura gareka kuma ?
Haka zaki fada yanzu ko ya fada yana kallon cikin idanuna sai ban yarda mun hada ido dashi ba na aje mai tiren a saman dan karamin table din dakin da yake kala daya da gadon nasa ina jawo table din zuwa gaban shi.
Don na kawar da zancen nace ga wanan ko zaka sha don naga bakaci abincin ba sosai dazun.
Naci mana ya fada yana mikewa kinsan bana cin irin wanan abincin kada ya saka jikina budewa sosai.
Da jikin ka zai budewa ai daya dade da budewa yaya don ruwan kwalban da kake durawa cikin ka sosai.
Zainab bana son jin wanan zancen a bakin ki don sanin kankine a yanzu na daina wanan harkan don haka bana son a tayar min da wanan zancen kuma .
Kayi hakkuri idan hakan dana fada laifine na barka lafiya na fada ina kokarin ficewa dakin yake fadin bakiji ba ko ?
Na juyo ina dan kallon shi yake fadin zuwa dare zamu fita zuwa gidan mami mu gaidasu idan zaku iya fita a yau din ko kuma a barshi da safe sai mu tafi.
Zaifi kyau yau din mu tafi na bashi amsa daga inda nake na rungume hannayena a jikina eh hakan zaifi don mamud ya fada mata muna garin tun safe.
Tayi fadan hakan ke nan na tambaya badan na shiryawa hakan ba fadan me zatayi tunda mun shigo kasan ko ?
Zo ki zauna ya fada yana gyara zaman shi da kyau tare da fadin idan bake ba wata mace ce zata shigo wurin mijinta aga ta fita haka da sauri.
Ai sai a dauka akwai rashin jittuwa a tsakanin mune kila kinkoga hakan ba zanji dadin shi ba daga zuwan mu ki bada mu haka ?
Yaya ke nan ka dauka ba,a san zaman da mukeyi da kai bane a hakan kana dauka kowane zaka iya wasa da hankalin shi a hakan.
Sai dai idan kin fadawa wani wanda ban debe tsamani fadilace ko zaki iya fadawa ban taba ki kamar sauran maza.
Wani kallo na watsa mashi da sauri tare da fadin kada ka daukeni yarinya kamar da bansan kaina ba har yanzu.
Ko a da can ban fada mat komai game da zaman mu da kai ba balle yanzu da hankalina ya kara zo min na fahinci me kake nufi dani.
Me nake nufi dake zainab ya fada a daidai lokacin da yakai cibin mix fruits din a bakin shi tare da bissimila a fili na dan kalleshi.
Don a kwaishi da wanan akidar na fadan bissimila ga duk abinda zaikai a bakin shi ko wani lokaci idan zaici abu.
Niko nasan kin kara girma a yanzu zainab don nasan kin fara kiyasta wasu abubuwa a tare dake .
Ban fara kiyasta komai ba saidai a yanzu din zan fara mutukar wanan halaiyar naka munana suna tare dakai yaya don ba zan zauna da wanda ke sabon Allah a fili ba haka gaskiya.
Da nai maki me a cikin zaman namu dan dama ina zargin hakan a gareki tuntuni saidai ki sani ba kowa zaki fadawa wanan zancen a yanzu ba ya yarda da zancen da zaki fada.
Saboda basu gani a jikina ba kome yasa ka fadi hakan ai jikin shike nuna kana cikin wani hali keko naki bai nuna hakan ba.
Shine hikimar ka a kaina banda wani hikima ko basira a yanzu da da can baya wanda yafi in ganki cikin farin ciki kamar haka ?
Da alama dai dadin zancen yake yana kuma bugun cikina da wayaun manyan yaji wani shiri nake a kansa yanzu da mukazo gida.
Farin ciki a haka yaya farin ciki zuciya tana cike da damuwa da tashin hankali akan mutum kullun ?
Zainab meye matsalan ki a yanzu dani kallo shi nayi da mamaki kamar zanyi magana sai kuma naja bakina nayi shiru ina kallon shi ban iya furta kai din kaine matsalata ba a yanzu kamar yadda na bashi amsa a zuciyana da hakan.
Bakinane yai subul da baka nace ina ko naga matsala dakai kana da irin su Taju dake debe maka kewa duk lokacin da bukatan hakan ya taso maka.
Na sani zainab nasani banda wanan din da kike ganin shine matsalan ki a yanzu dani baki da sauran matsalan komai bayan wanan.
Koshi din ai zaki iya idan kina so sai ki gwada ki gani ko zakici nasara a kaina har ki samu yadda kike so din.
Ka dauka yaya ina da feeling a kanka ne kamar yadda baka da wanan feeling din a kaina haka nima haka kwata kwata ban taba jin wani feeling akan kaba irin wanan.
Take naga annurin fuskanshi ya canza lokaci guda yace kina nufin baki da feeling kamar sauran mata akan mijin ki ?
Miji miji fa kace yaya ko yau bakin ka ya mantane har ka furta hakan a gabana bayan zaman kanwar ka nake ga idon kowa.
Haka dai kika fada zainab wanan zancen ai ya dade da wuce ko ga idon kowa don wayau ki yafi nawa yawa zainab.
Banda wayau bayan hakanndin haka ka tsawa zamana da kai yanzu kuma lokaci yayi da hakan zai kawo karshe na fada ina barin dakin.
Dakina koma raina na min zafi don wanan maganan da mukayi a yanzu watau yaya daukan jarababba yake min ko me ?.
Shiko na fita na barshi da tunane na a zuciya don abinda yake zargine ke shirin faruwa wanan yarinyar gab take da daukan wani mataki a kansa yanzu.
Me zanwa zainab na wake kaina kada ta kasa hakkuri ta fasa abinda ke tsakanin mu ne?
Wata zuciya tace mai baka saba da wanan halin nata bane a baya babu abinda zatayi duk hakan barazanane kawai na mata ka riga da ka gama da ita ko don babu inda ka ragota a yanzu kan wurin zamantakewa ya fada.
Sai kawai ya shafe zancen da basarwa don yasan haka dinne ba wani abinda zanyu inma zanyi din nice dai a kasa bashi ba.
Don babu mai yarda da duk wani abinda zan fada a yanzu don za a dauka sherine kawai na mata a hakan.
Hannun shi yakai ya shafo gaban shi da kusan wata da watani ke nan yake fama da wanan matsalan yaji shi a lankwas kamar kullun.
Hannun ya mayar a fuskan shi yana shafowa a hankali shi yanzun ma ba zaice ga ta inda matsalan ya fara mashi ba.
Don dai yasan cewa da farko bayan maganin dana basa a Dubai yana tare da lafiyan shi na mazakuta sai daga bayane ya fara fuskantar wanan matsalan da yake ji a yanzu tare dashi.
Gashi ya kasa fadawa kowa bayan likitan shi da yagani kan wanan zancen a chaina ya kuma dubashi yace lafiya komai nasa yake.
To a ina wanan matsalan ya taso masa shi dai ba zaice zainab din bane da wanan matsalan sai kawai yake danganta kansa da kawai don yanzu baijin sha,awan ko wani irin jinsi don jin dadin rayuwan shi ya kawo masa hakan.
Da kyat ya mike ya shiga bathroom don ya watsawa jikin shi ruwa sai dai har ya fito zuciyar shi yana cike da tunane kala kala daya kasa fahinta.
Nikan sallah nayi sai a lokacin na samu barci ya daukeni sosai don na samu barci har lokacin sallah la,asar ya wuce ni sosai.
Bayan na samu na tashi da kyat na shiga bandaki na dauro alwala nayi sallah ban fito ba dakin na zauna ina dan dube dube a cikin wayata sabuwa daya saya min.
Sosai nake jin dadin wayan don komao na wayan yana da kyau sosai kafin hankalina ya dauko ga tunane ba abinda yazo min a rai sai zancen zuwa gidan mami daya ce zamuyi da yammanan nake tunanen yadda mami din zata karbe ni .
Dukda mun shirya sama sama a yanzu da ita sai dai ina tsoron halin dan adam tunda har yanzu bawai na kwanta mata a rai bane.
Koma meye wanan karon kam nasan ba zan yarda daduk wani rainin wayau kowa ba a kaina don ga kura mai laifi basu gani saini da banci ban sha za a dinga dora laifi a kaina ?
Sadiya na tuna tun fitana dazun ban kara ganin ta ba hakan yasa na mike zuwa dakin da take tana ciki da waya tana faman yin game hankalinta ya dauku a wayan.
Jin motsina yasata dago kai tana kallona tare da fadin ashe kin tashi yayan mu na shiga dazun na samu kina barci.
Ke wai me yasa bakya jin magana sadiya wanan yasa nake hanaki rike waya don sai ya canza maki akidar ki ga baki daya wallahi.
Ina fara magana tayi saurin lkashe wayan tana ajewa gefen filonta da sauri zaune nakai cikin bacin rai ina fadin kinga akan wayan nan zamu samu matsala babba dake don akan wanan hali zan mayar dake na dauko binta mu zauna tare don ita ban taba jin tayi wani abin rashin ji ba .
Ina kokarin yi mata wanan nasihan ne don gujewa gurbacewan rayuwan ta nan gaba a kan waya duba ga yadda naga daga shi har kannen sa basu da lokacin kowa akan wanan nauran a rayuwan su don zai iya zama dakai na tsawon awan ni ba tare da yai magana dakai ba hankalinshi naga waya yana tabawa kawai.
Duba ga hakan nake tsoron kada ta tashi da wanan akidar nan gaba ya zame mata hitina a rayuwa gashi mu ba diyan wasu a tarihin mu.
Idan na fara irin wanan fadan taka natsu sosai ta daina duk wani abinda takeyi ko yanzuma din da nake magana hakane ya kasance a tsakanin mu.
Kuma ina son ki saurareni da kyau kiji duk wani tambayan da fadila ko wani zai maki akan rayuwan mu kada ki yarda inji ance ga abinda kika fada don idan naji da Inna zan hadaki wanan karon.
Bazan fada mata komai duk tambayan da zatayi min idan kinyi hakan kin kyautawa kanki na bata amsa ina mikewa don barin dakin.
Shiru tayi tana bin lafiyan filo ta kwanta tana kallona har fice dakin ta sauke ajiyan zuciya tare da fadi ta rasa meya sa nake yawan tsanan ta mata hakane ?
Daki na koma har lokacin banjin dadi a kasan zuciyana kawai naji na tsani komai sai bacin rai dake kara min yawa nakeji .
Duk a kan dan maganan da mukayi da yaya J a ranan kawai nake jin raina yana wanan bacin da yake min.
Allah ya taimaka har tara na dare ya wuce banji yace mu fito zuwa gidan mami din ba daya fada zamu shiga da dare.
Hakan yasa na fara shirin kwamciya kafin Fadila tayi min sallama ta shigo dakin tana fadin taga fitan mijina a cikin daren nan ko lafiya ya fita a wanan lokacin.
Tabbas tunane na ya fara zama min gaskiya akan fadila shiyasa yanzu nake taka tsantsan da ita wani lokaci.
Don na fara zargin wani abu akanta da yanzu wayau na da hankalina suka fara kawo min haske akanshi don yawan tambayayin da take min lokaci lokaci koda a wayane kuwa idan muna wayan.
Har yakai hankalina da tunanena sun fara hasko min wasu abu a kanta ko yanzun ma tambayan data jefo min ya kara rikitani tana fadin.
Ko dai mijin naki bai bar wanan harkan bane har yanzu a cikin mamaki na juyo ina fadin harka wani harka ke nan fa ?
Sai kuma ta rasa abinda zata fada min kan hakan tace wai irin dai halaiyar nan da yakeyi a baya.
Ance mutum mai yawan murmushi baka fahintar bacin ranshi lokaci guda sai dai ya jefaka a cikin kwankwanto da zargin kanka kaida yakewa wanan murmushin a lokacin.
Hakan ne ya faru da fadila dani sai kuma ta fara dan kame kame tana fadin a yanzu kan ai komai ya wuce da alama akwai fahinta a tsakanin ku a yanzu.
Dama babu ne na tambaye ta cikin alaman mamaki a fuskana naci gaba da fadin ban taba fada dashi ko wani rashin yarda wanda ya shafi ni dashi har wani ya sani na bata amsa.
Tare da karewa da fadin bana shiga harkan shi hakan ya kara jawo mana zaman lafiya a tsakanin mu wanda ko wace mace ke fata da mijinta.
Itama din kallon mamaki ta bini dashi lokaci guda tana dan murmushi a fuskanta nima hakan nakeyi.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
YA HAIYYU YA KAIYUMU YA ALLAH KA KARBI IBADUN MU KASA MUNA CIKIN YAN TATTUN BAYIN KA A WANAN WATAN MAI RAHAMA DA DAUKAKA ALLAHUMA AMIN, , , ,
LITTAFIN KUDINE KI BIYA DARI UKU KI KARANTA YAR UWA DON ALLAH KI GUJEWA SHIGA HAKKIN WANI YAR UWA KAN ABIN DUNIYA, , , ,
Na san mai karatu zakiyi mamaki jin abinda na fada akan fadila hakan kuma ya samo asaline tun ranan dana fara gane waye fadila a gurin mu.
Ranan kishin ruwa kawai ya tayar dani a cikin dare na fito don neman ruwan da zan sha a lokacin.
Banyi amfani da ko wani irin haske ba don nasan inda ruwan yake sauri kuma ya hanani tsaya na dauki ko wayana in haska.
Har na dauko ruwan zan fito naga kamar gittawan mutum a falon namu karami.
Naji tsoro iya tsorata nayi shi don haka na samu wuri na lafe a bayan kofan kitchen din muryan fadila naji tana waya a hankali.
Tana fadin wallahi duk dabaran da zanyi in gane wani abu a gareta nayi shi har yanzu ban gane komai ba a wurin ta .
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22Chapter 23Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32Chapter 33Chapter 34Chapter 35Chapter 36Chapter 37Chapter 38Chapter 39Chapter 40Chapter 41Chapter 42Chapter 43Chapter 44Chapter 45Chapter 46Chapter 47Chapter 48Chapter 49Chapter 50Chapter 51Chapter 52Chapter 53Chapter 54Chapter 55Chapter 56Chapter 57Chapter 58Chapter 59Chapter 60Chapter 61Chapter 62Chapter 63Chapter 64Chapter 65Chapter 66Chapter 67Chapter 68Chapter 69Chapter 70Chapter 71Chapter 72Chapter 73Chapter 74Chapter 75Chapter 76Chapter 77Chapter 78Chapter 79Chapter 80Chapter 81Chapter 82Chapter 83Chapter 84Chapter 85Chapter 86Chapter 87Chapter 88Chapter 89Chapter 90Chapter 91Chapter 92Chapter 93Chapter 94Chapter 95Chapter 96Chapter 97Chapter 98Chapter 99Chapter 100 Chapter 101Chapter 102Chapter 103Chapter 104Chapter 105Chapter 106Chapter 107Chapter 108Chapter 109Chapter 110Chapter 111Chapter 112Chapter 113Chapter 114Chapter 115Chapter 116Chapter 117Chapter 118Chapter 119Chapter 120Chapter 121Chapter 122Chapter 123Chapter 124Chapter 125Chapter 126Chapter 127Chapter 128Chapter 129Chapter 130Chapter 131